Header Ads
Showing 63001 words to 66000 words out of 92878 words

Chapter 22 - Asma'ul-Husnah Complet Book by Indabawa .txt

Ads the beginning of article before Image
Ads at the middle of Article

ya karasa ta shiga mota ta tayar harta danna horn mai gadi ya bude mata gate.


Mota shima ya shiga yabi bayan ta. Gidan Zainab ta tafi. Sabir kuwa yana biye da ita a baya.


Tana shiga shima ya shiga. Da sauri ta fita a mota tayi cikin gidan.


Tana shiga taci karo da Zainab, kallon ta Zainab tayi ta ce,
"Lafiya?"


Ganin ta da tayi ta shigo a firgice, bata rufe baki ba Sabir ya shigo.


Murmushi tayi ta ce,
"Au ashe tare kuke?"


Ciki Asma'u tayi ta barsu a nan falo. Zama yayi yana kallon hanyar da Asma'u tayi.


Murmushi Zainab tayi duk da yanayin Asma'u ya bata tsoro.


Lemo da ruwa ta dauki masa. Bai sha ba sai magana da ya farai mata.


"Zainab ke kadai kika fi kusanci da Asma'u a kawayen ta dan Allah ki taimaka ki shawon kanta. Wallahi ina son Asma'u amman ita taki ta gane"


Murmushi jin Dadi zainab tayi ta ce,
"Kar ka damu zan sanar da ita."


Kai ya girgiza ya ce,
"Na fada mata, amman taki ta fahimci irin son da nake mata ne"


"Ka barni da ita. Ina zuwa."
Ta mike tayi


Tana daya daga cikin dakin da ta ce na ta ne.


Saboda shi karami ne kuma komai na ciki kalar ta ne.


Tana kwance akan kujera idon ta lumshe hawaye na zubo mata.


A ranta take cewa
'Duk Yaa Aslam ne ya jawo mata. Yanzu ita bata da wani kwanciyar hankali. Daga wancan sai wancan. To wai ita tayaya zata auri Sir Sabir bayan tasan irin son da Nusaiba ke masa. Ai kamar ta zama azaluma ne "


Wata zuciyar ta ce,
'To ai shi baya son ta. In kinso shi ba wani abu bane."


Juyi tayi ta bude ido ta. Zainab ta gani tsaye akan ta.


Zaune ta mike ta ce,
"Ya dai?"


Kai ta girgiza ta zauna agefen ta. Ta ce,
"Lafiya naganki haka?"


"Uhnm Nida Sir Sabir ne!"
Ta fada mata duk abinda ke faruwa.


Zainab ma tana son Asma'u da Yaa Aslam to amman ba yadda zasu yi tinda shine ya nuna baya son ta.


Tinda haka ne gwara ta amshi Sabir din tinda shi yana son ta.


"Asma'u nima a gaskiya ina son ki da Yaa Aslam, but amman tinda haka ta faru ki yi hakuri ki rumgumi wanda yake son ki. Bance ki Yaa Aslam baya sonki ba, amman ki karbi Sir Sabir kuma ki yi istihara Allah zaba mafi alheri. Kiyi hakuri."
Zainab ta dafa kafadar ta.


Dagowa tayi da idanun ta dake zubar da hawaye ta ce,
"Zainab kinsan so amman baki san zafin sa ba. Nusaiba na kaunar Sir tin tana yarinya take son sa. Tayaya xan raba wannan soyayyar da take masa. Ki tayani wannan abin ina son Sir ya fara son Nusaiba ni na hakura dashi. Ina tausayawa Sir saboda yana sona ni bana son sa, kuma ni ba kinsa nake ba, kawai dai Yaa Aslam nake so. Gwara ya auri wacce yake so zai fi jin dadin yasan yai aure da ya aure ni ni kuma zuciya ta na wani wajen ki duba magana ta Zainab nasan ke zaki fahimce ni."


Ta fashe da kuka, jikin ta Xainab ta jata tana lallashin. Sai da tayi shiru sannan Ta ce,
"Zan sanar da shi amman ki daina kukan nan."


Kai ta gyada. Mikewa Zainab tayi ta fita. Ta sanar dashi indai yana son Asma'u to sai dai ya hada da Nusaiba. Sosai hankalin sa ya tashi. Lallabashi tayi kan yaje yai tunani sannan ya tafi gida.


Wajen Asma'u Zainab ta koma. Kallon ta tayi ta ce,
"Sis nai miki shishigi fa"


Kallon ta Asma'u tayi ta ce,
"Name fa?"


"Nace indai yana son ya aure ki sai dai ya hada ke da Nusaiba."


Shiru Asma'u tayi. Zainab ta ce,
"Kiyi hakuri in bakiji dadi ba."


"Ba haka bane. Amman ba komai."
"Yauwah dan Allah sis kina rage damuwa akan Yaa Aslam. Kina addu'a Allah ya yaye miki son sa."


Dagowa Asma'u tayi ta kalle ta ta ce,
"Wallahi kullum sai nayi wannan addu'ar amman kamar bana yi son Yaa Aslam kara shiga ta yake. Kwanaa biyun nan ji nake kamar nai hauka dan son ganin sa da nake. Na rasa ya zanyi da son sa. Ina son Yaa Aslam kuma yana daga cikin wadan da ya koya min son sa haka."


Ta fada hawaye na saukowa daga idon ta.


"To ya isa. Allah yasa haka shine mafi alheri"
Asma'u ta ce,
"Ameen!"


"Ina Mami?"
Zainab ta tambaya


"Uhmm Mami ta fita nima bata san nazo ba."


Asma'u ta ce,
"Me kika dafa ne?"


"Taso muje ki gani."
Ta mike ta kama hannun ta.


Dining sukayi suka zauna ta fara cin abinci.


Ranar har dare suna tare da yake Yaa Buhari bai dawo da wuri ba basu san har dare yayi ba.


Sai karfe goma sannan ya shigo, da ta ce, zata tafi kuma ya ce,
"Ba inda zata tinda Mami tasan tana gidan ta kwana kawai."


Haka dole ta kwana agidan. Washe gari tare da Zainab sukai komai tai wanka ta shirya ta ce zata tafi.


Hanata tafiya yayi a lokacin ya ce, Ta bari sa tafi tare gaba dayan dan zainab ma zataje gaishe da Mami.


Haka ta zauna har karfe biyu sannan suka tafi gaba dayan su.


A gida suka yini sai dare suka koma gida.


Mami kuwa sai jan Zainab take ajiki bama da taga tana jin kunyar ta.


Ita ta fiso ta zama free da ita kamar yadda Asma'u take mata.


Tin daga lokacin ya zama na yar boye ke tsakanin Sir Sabir da Asma'u.


A office ta maida kanta busy yadda ko ya ganta ba damar magana saboda yadda take tare da patient din ta.


Haka a gida da ta shigo taga motar sa take komawa, in kuwa har ta shigo da sun gaisa take guduwa sama.


In waya ya kira ma baya samu dan yanzu sai tai kwana nawa ma wayar ta a kashe.


Sosai ya damu, dan yana son Asma'u yana kuma jin tausayin ta.


A haka sai da suka debe wajen wata uku suna yar buyar nan.


Kuma baya taba samun damar da zai ganta.


Sunyi bikin Maimuna inda aka kai ta gidan mijin ta dake sabuwar gandu.


Gida ne mai kyau kuma komai ya mata. Sosai Asma'u ta bata gudumawa mai yawa banda wasu abun da ta dauke mata.


Asma'u da Zainab ne dai sukai mata Babbar kawa.


Wanna karan ma sai da Maryam tazo, Nusaiba dai bata zo ba dan a lokacin basa kasar.


Anyi biki lafiya an kai amarya gidan ta.


Sosai Nazir ya amshi kaddarar Maimuna tinda daman yasan ba budurwa bace.


To shi ita yake so, dan haka ya daura aniyar zama da ita da dadi ba dadi.


Duk da Maimuna ba ruwan ta yanzu abinda ya ce, shi take yi.
Zaman lafiya suke sosai yake faranta mata shima take faranta masa.










*MS Indabawa*
[1/18, 14:34] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR*
*Asma'u Husnah*


Part *2*


Na *Maryam S Indabawa*
*Mans*


🌐 *HAJOW* 🌐
*Hakuri da juriya Online writer's*


Dedicated to *My lovelly Mum*




Pagr *61-65*








Bangaren Sabir kuwa da abin ya ishe shi sai ya samu Yaa Buhari da batun yana son Asma'u.


Duk da Yaa Buhari yafi son Asma'u su daidai ta da Aslam amman bai sa shi rashin jin dadi ba.


Sosai yaji dadi dan shi yasan waye Sabir, Dan in Asma'u bata auri Yaa Aslam ba ta auri Sir Sabir ba komai.


Dan ya tabbata Sir Sabir ma zai kula masa da kanwar sa.


Daga nan kuwa Yaa Buhari ya tafi gida ya fadawa Mami.
Mami cewa tayi, a tambayi Asma'u aji daga bakin ta.


Yaa Buhari ya ce,
"Aah Mami in har aka ce sai anji daga bakin Asma'u to tabbas baza ta amince ba. Kinsan irin son da takewa Yaa Aslam."


Shiru Mami tayi ta ce, zata tambayi Momy taji.
Momy ma sosai taji dadi dan daman ta yaba da hankalin Sabir sosai.


Itama cewa tayi a bari sai abin ya matso a fada mata sanin halin Asma'u zata ce A'ah


A bangaren Sabir kuwa yadda yayi zai hada Nusaiba da Asma'u dan yasan in ba haka ba Asma'u baza ta taba yadda ba.


Yasan ko ba komai Nusaiba mai son sa ce dan haka zai samu duk abinda yake nema a gun ta.


Amman yayi wa kansa alkawarin sai ya yayewa Asma'u halin kuncin da take ciki na rashin Yaa Aslam.


Ko bata son sa shi zai zame mata farin ciki. Farin cikin da zata manta da Aslam.


Nusaiba kuma ta fawalawa Allah komai. Addu'a da istihara take amman kullum son Sabir kara shigar ta yake.
Duk da haka suna waya da Asma'u dan sun zama kawaye.


A bangaren Zainab yanzu auren su wata bakwai yanzu tana da ciki wata hudu.


Bakuga yadda Asma'u ke ji da cikin nan ba.
Dan gidan ta koma da zama ma saboda taya ta aiki.


Komai yi mata take. In Asma'u ta zauna hira da cikin kuwa kwa rantse da mutum take hira.


Sosai Zainab ke kara lalashin ta akan zancen Sabir.
Duk da yanzu ya daina mata maganar amman tana lura ba wai hakura yayi da ita ba.


Yau tana gidan Yaa Buhari ake sa ranar bikin ta da Sabir, an sanya rana shekara daya, saboda so ake a hada bikin da na Nusaiba akai masa mata biyu a rana daya.


Ya sanar da su manufar sa tayin hakan kuma sun yadda dan sun san kafiyar Asma'u.


In ta ce,
"Eh!"


Ba wanda zai sa ta ce,
"A'ah!"


In kuwa aka matsa to za'a ga ba dai dai ba.


Duk da Momi bata so hakan ba. Amman ta yadda dan san halin yar tata.


Momy ma tazo komai anyi shi cikin kwanciyyar hankali.


Asma'u kuwa tana can bata san ana yi ba.
Duk da Zainab ta sani. Sai dai Asma'u kanji yawan faduwar gaba.




Momy ce zaune a falo tare sa Mami da Yaa Buhari.
Bayan sun gama tsara komai ne, Momy ta kalli Buhari ta ce,
"Buhari kun yi maganar Yayan ka da Mami kuwa."


Dagowa yayi ya dan jima kafin ta ce,
"Wallahi Momy bamuyi ba. Kuma abin na raina kullum. Bama Asma'u da nake son sanar wa."


Kai Momy ta girgiza ta ce,
"Kasan sai a shekaran jiya na fada yadda da ba haka matar Aslam ta bar shi ba. Kaga yadda take masa kuwa ta maida shi bawa fa, ba abinda yyake iya yi sai da izinin sa. Aslam duk ya rame."


Tayi shiru ta ce,
"Jiya da na aika a kira min shi cewa tayi bazai zo ba, sai da ta shiga ciki yake bawa dan aiken hakuri kan ya bani hakuri tinda ta ce, bazai zo ba. Ni da ganin Aslam fa sai nai wata. Kudi kuwa account dinsa na hannun ta. Dan Allah Buhari yazamuyi Na fison muyi abu wanda baza mu.kaucewa Allah ba. Dan ni bana son bin malaman nan su fara juyawa mutun tunani da canfe canfen su."


Kai Mami ta gyada ta ce,
"Innaillilahi wa inna illahir rajiun. Yanzu yadda ta maida Aslam din kenan. To Allah kai mana magani."


"Ameen!"
Momy da Buhari suka amsa da.


Buhari na komawa gida ya samu Asma'u ya ce,
"Asma'u ina son magana da ke!"


Ganin da yadda yai mata maganar yasa ta san magana ce mai mahimmanci.


Kallon sa tayi ta ce,
"To ina ji."


Tana komawa gefen sa. Kallon ta yayi, ya ce,
"Ina son ki sa a ranki duk abinda ya faru da bawa mukaddari ne Allah ya riga da ya tsara, sannan ina fatan duk abinda yya same ki zaki amsa hannu bibiyu"


Kai ta gyada ta ce,
"Insha Allahu."


Ya ce,
"Magana zan miki guda biyu kuma kowa ce ina son ki amshi abinda zan fada miki."


Sai da ta dago ta kalle shi sannan ta ce,
"Insha Allahu zzan dauka."


Gyaran murya yayi sanann ya ce,
"Sabir!"


Jin suna da ya ambata yasa kirjin ta dukan uku. Ta dago da sauri.


Kai ya dauke ya ce,
"Sabir ya same ni da zance yana son ki. Dan haka mun ba shi dama dan nasan in take ce baza ki amshe sshi ba. Yau aka sa ranar bikin ku nn da wata shekara za ayi bikin ku insha Allahu."


Kasa tayi da kai tana zubar da hawaye.
To ita dan ta dan ta auri Sir Sabir mene, tinda ta rasa wanda take so ma.


To amman fa ita Nusaiba take ji. Kuma bazata iya bujurewa maganar su Mami ba.


Tana son Yaa Aslam amman kenan ya zama dole ta hakura dashi. Tinda tasan ba yadda zai tana da aure ta so wani ba kuma.


Duk maganar da Yaa Buhari yacigaba da fadi ba ji take ba.


Sai da taji ya ambaci Yaa Aslam sannan hankalin ta ya dawo kansa.
"Tinda naje Abuja naga halin da yake ciki ba san ba haka matar sa ta bar shi ba. Sai kuma yau da Momy tazo take fadan halin da yake ciki. Asma'u mune kadai yan uwan Yaa aslam dole mu tsaya akan sa da addu'a sannan da wani abun da muka sani na tsarin jiki."


Tinda ya fara magana take kuka har yanzu da ya kare abinda yake fadi


"Kar ki diba abinda yai miki ki 'ki taya shi da addu'a kinsan Yaa Aslma ya so ki a baya to yanzu ma ki dauka kaddara kuce tasa kuka rabu "


Shiru tayi amman sai hawaye dake ambaliya a idon ta.


"Asma'u!"
Ya kira sunan ta.


Dagowa tayi da idanun ta da suka rine da hawaye sukai jajir da su.


"Mene na kuka? Sabir din ne bakya so?"
Kai ta girgiza


"To Yaa Aslam din baza ki taya da addu'a ba?"
Shima kai ta girgiza.


"To yi hakuri ki daina kuka kinji."
Kai ta gyada masa.


Mikewa tayi jiki a sanyaye ta shiga dakin da take kwana.


Kayan ta ta fara hadawa tana cikin hadawa Zainab ta shigo.


Kallon ta ta tsaya ganin tana debo kaya daga cikin durowa zuwa cikin akwatin ta.


"Lafiya?"
Zainab ta tambaya.


"Tafiya zanyi. Sis yanzu a gida an daina so na mai sona a duniya mutum daya ne, kuma ya mutu wanda na dauka shima yana sona din ya daina, to Mami ma da Yaa Buhari sun daina. Wai har sun gaji dani zasu aurar dani ba tare da ina son sa ko an tambayen ra'ayi na ba. Zan bar muku gidan ku ina jin na tare muku wani abu shine yake son nai aure na bar muku gida. Zan tafi gida nasan can Mami baza ta koren ba dan nasan shi zai kai mata maganar Sir Sabir."


Buhari da yana tsaye bakin kofa shima ya shigo. Ya ce,
"Ko daya kanwata. Bazan taba daina son ki ko gajiya da ke ba. Ki fuskance ni. Nasan dai ke ba yarinya bace karama kinsan komai. Bai kamata ace kin kai yanzu ba aure ba. kin gama karatu har kina aiki ai gwara kiyi aure tinda kin samu mai son ki. Kada ki manta da fa tini kina gidan ki wa yasani ma ko da ciki ko 'da. Mutunci 'ya mace gidan mijin ta fa."


Fuska ta rufe saboda kunya. Yaa Buhari ya ce,
"Kiyi hakuri ki karbi zabin mu insha Allahu zaki ji dadi."


Kai ta gyada. Ya ce,
"To ki mai da kayan."


Kai ta make masa, ta ce,
"Ni dai gida."


Murmushi yayi ya ce,
"Husnah daru."


Kai ta gyada ta ce,
"Naji."


Ya ce,
"Kya bari dai gobe ko?"


Kai ta girgiza masa. Duk yadda yaso ta zauna ki tayi.


Da zai matsa mata ma sai ta saka masa kuka.
Dole suka bar ta ta tafi ba dan sun so ba.


Tana zuwa gida ta shige dakin ta ta rufe.


Kwanciyya tayi ta rasa wane tunanin zatai tunanin aure da za ai mata ne ko tunanin halin da Yaa Aslam yake ciki ne.


Mikewa tayi ta fada bandaki alwala tayo ta fito ta dinga yin nafila.


Ta jima tana yi sannan ta dauko kur'ani ta karanta, addu'a tayi masa sosai.
Sannan ta zame agun bacci ya dauke ta.


Buhari ne ya fadawa Mami, Asma'u ta taho wannan yasa ta zo daki ta dduba.


A kwance ta same ta a kasa, idanun ta sun kumbura


Tabata Mami tayi ta bude idanun ta. Jajir suke sai kace gauta.


Mami ta ce,
"Tashi ki hau kan gado."


Mikewa tayi ta hau kan gado. Fita Mami tayi ta kawo mata fura da ta dama.


Kawo mata tayi ta amsa ta sha. Mami na fita ta koma ta kwanta.


Bacci ne yaki zuwa wanna yasa ta mike tana ta addu'a.














*MS Indabawa*
*LABARIN RAYUWAR*
*Asma'u Husnah*


Part *2*


Na *Maryam S Indabawa*
*Mans*


🌐 *HAJOW* 🌐
*Hakuri da juriya Online writer's*


Dedicated to *My lovelly Mum*




Pagr *61-65*








Bangaren Sabir kuwa da abin ya ishe shi sai ya samu Yaa Buhari da batun yana son Asma'u.


Duk da Yaa Buhari yafi son Asma'u su daidai ta da Aslam amman bai sa shi rashin jin dadi ba.


Sosai yaji dadi dan shi yasan waye Sabir, Dan in Asma'u bata auri Yaa Aslam ba ta auri Sir Sabir ba komai.


Dan ya tabbata Sir Sabir ma zai kula masa da kanwar sa.


Daga nan kuwa Yaa Buhari ya tafi gida ya fadawa Mami.
Mami cewa tayi, a tambayi Asma'u aji daga bakin ta.


Yaa Buhari ya ce,
"Aah Mami in har aka ce sai anji daga bakin Asma'u to tabbas baza ta amince ba. Kinsan irin son da takewa Yaa Aslam."


Shiru Mami tayi ta ce, zata tambayi Momy taji.
Momy ma sosai taji dadi dan daman ta yaba da hankalin Sabir sosai.


Itama cewa tayi a bari sai abin ya matso a fada mata sanin halin Asma'u zata ce A'ah


A bangaren Sabir kuwa yadda yayi zai hada Nusaiba da Asma'u dan yasan in ba haka ba Asma'u baza ta taba yadda ba.


Yasan ko ba komai Nusaiba mai son sa ce dan haka zai samu duk abinda yake nema a gun ta.


Amman yayi wa kansa alkawarin sai ya yayewa Asma'u halin kuncin da take ciki na rashin Yaa Aslam.


Ko bata son sa shi zai zame mata farin ciki. Farin cikin da zata manta da Aslam.


Nusaiba kuma ta fawalawa Allah komai. Addu'a da istihara take amman kullum son Sabir kara shigar ta yake.
Duk da haka suna waya da Asma'u dan sun zama kawaye.


A bangaren Zainab yanzu auren su wata bakwai yanzu tana da ciki wata hudu.


Bakuga yadda Asma'u ke ji da cikin nan ba.
Dan gidan ta koma da zama ma saboda taya ta aiki.


Komai yi mata take. In Asma'u ta zauna hira da cikin kuwa kwa rantse da mutum take hira.


Sosai Zainab ke kara lalashin ta akan zancen Sabir.
Duk da yanzu ya daina mata maganar amman tana lura ba wai hakura yayi da ita ba.


Yau tana gidan Yaa Buhari ake sa ranar bikin ta da Sabir, an sanya rana shekara daya, saboda so ake a hada bikin da na Nusaiba akai masa mata biyu a rana daya.


Ya sanar da su manufar sa tayin hakan kuma sun yadda dan sun san kafiyar Asma'u.


In ta ce,
"Eh!"


Ba wanda zai sa ta ce,
"A'ah!"


In kuwa aka matsa to za'a ga ba dai dai ba.


Duk da Momi bata so hakan ba. Amman ta yadda dan san halin yar tata.


Momy ma tazo komai anyi shi cikin kwanciyyar hankali.


Asma'u kuwa tana can bata san ana yi ba.
Duk da Zainab ta sani. Sai dai Asma'u kanji yawan faduwar gaba.




Momy ce zaune

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads