Header Ads
Showing 9001 words to 12000 words out of 92878 words

Chapter 4 - Asma'ul-Husnah Complet Book by Indabawa .txt

Ads the beginning of article before Image
Ads at the middle of Article

ina?"


"Shiryawa yake, yanzu zai zo ya kaini."
"Ok jeki same shi."


Juyawa tayi, sai gashi nan ya shigo, cikin blue (ruwan omo) din shadda wacce akai mata aiki da dark blue, (ruwan omo me turuwa) blue hula yasaka, da bakin takalmi sai bakin agogo a daure a tsintsiyar hannun sa.


Sosai yayi kyau, ya fito kamar wani tauraro, sai tashin kamshi yake.


Durkusawa yayi har kasa.
"Mami ina kwana. Da fatan an tashi lafiya?"
"Lafiya lou. Ya ka tashi."


"Lafiya Alhamdulilah! "
"To jeka maza ka kaita makarantar daga nan ka wuce aiki zan aiki driver ya kawo maka abincin ka kaga ta makara."


"To Mami sai na dawo."
"Allah kiyaye hanya Allah muku Albarka."


"Ameen!"
Ya mike ya fice, komowa *Asma'u* tayi ta rumgume Mami ta mata kiss (sumbatar) a kumatu.


Ta sake ta tana.
'Bye bye Mami."


"Bye Ayi karatu sosai banda kula kawayen banza."
"Insha Allahu."


Ta fada tana fita a guje tana mata bye bye da hannu.


Murmushi Mami tayi, dan *Asma'u* akwai ta da hankali ga nutsuwa, bar ta dai da tsokanar yayan ta amman komai nata cikin burgewa take yin sa.


Baka ce *Asma'u* Kamar yadda Dady yake baki, shi kuma Ya Buhari fari ne ya dauko Mami.


Amman komai na fuska da zubin jiki me kyau na Mami ne, dan Mami akwai diri hakan yasa ita ma *Asma'u* tana da diri me kyau.


Kamar yadda shi kuma Ya Buhari ya dauko zubin jikin dadi dan dogune, sannan jikin su a murde yake, suna da dan jiki dai dai gwargwado.


Bakin *Asma'u* bai mata muni ba sai kyau da ya kara mata. Dan Bakin ta me kyau ne, irin chocolate colour haka fatar ta take me kyau da taushi.


Kowa na sha'awar kalar fatar ta.


Kai ta jin jina.
"Allah bada sa'a."
ta fada a fili tana yin dakin Dady.


Tana fita har ya shiga mota. Da gudu ta karasa ta bude gidan gaba ta shige.


Hanya suka dauka. Cikin minti ashirin sun karasa makaranta. Har kofar department ya dire ta sannan ya juya.


Tana karasawa kofar hall din su ta hange, sa a gaban aji.


Sanye yake da ruwan madarar shadda wacce akai masa dinkin riga wacce da kadan ta wuce gwiwa da dogon wando.


An masa aiki a jiki da dark brown (ruwan kasa) zare sai dark brown hula da takalmi dake kafar sa.


Ta jima tana kallon sa, Sai bayani yake zuba musu. Daga bisani ta buya daga gefe dan kar ya ganta.


Tinda ya mata kashe din kar ta matso masa kofar aaji muddin ta makara.


Tana daga taga tana jiyo muryar sa, me sanyi da dadin sauraro. Sai da taga ya kusan fitowa sannan tabar kofar hall din.


Ya fito ya tsaya a kofar ajin yana kallon ta, duk da ta bashi baya amman ya tabbata ita ce.


Ya jima yana kallon ta ko zata juyo amman ina ko juyowa batai ba kamar tasan yana wajen.


Wajen ya bari ya nufi Office din sa. Yana bawa wajen baya tana juyowa bayan sa ta tsaya kallo.


Kai ta girgiza ta juyar da kanta. Zainab ce ta karaso wajen.
"Sannun ki, kin kyauta."


"Wallahi bansan lokaci ya tafi haka ba."
"Haka dai kullum bayan kin gama tsokanar ki ko."


"Ni yau ban tsokane sa ba."
"Ke din kuwa."


"Eh!"
Dariya zainab tayi,


"tashi ki rakani na siyo lemo dan Allah."
Mikewa tayi suka nufi cafeteria. Sai da suka siyo lemo sannan suka dawo.


Wajen da suka saba zama nan suka zauna gefen hall (dakinn daukar darasi) din su karkashi wata bishiya.


Suna zama, sai ga kiran Ya Aslam nan.
"Assalamu Alaikum!"
"Wa'alaikum salam!"


"Love!"
"Na'am Yayana ya hanya?"


"Hanya lafiya gashi har nagama komai yanzu sai gida, shine nace bari na karaso naga Queen of my heart."


"Wow! Amman kuwa da ka kyauta."
"Gani nan shigowa ckul din."


"Sai ka karaso."
"Aha."


Ta kashe tana murmushi.
"Waye zezo?"


Zainab ta tambaye ya.
"Ya Aslam ne."


"Oh Allah kawo shi lafiya."
"Ameen!"


Yan department din sune suka karaso wajen su uku. Hafsat, Amina da Khadija.


Bayan sun gaisa suka zauna. Hafsat sai hade fuska take Suna dan taba hira. Amman ita ta hade rai


Zainab ce ta ce,
" *Asma'u* wannan week end din zamu zo gidan ku, zamu kawo miki IV Fadila."


"Eh daman ai ke bakya zuwa gidan mu sai da dalili wai ke kunya."


Khadija ce, ta sa baki.
"Ke zuwa kike."


Murmushi Zainab tayi.
"Yauwah tambayar min ita dai."


Amina ce tace,
"Yo ke ina ruwan ki. Sun fi kusa kuma kowa yasan zee bata son zumunci."


Dariya Zainab tayi,
"Ai ita tasan ina da zumunci tasan kuma me yasa yanzu na daina zuwa gidan su."


Tsaki *Asma'u* tayi,
"Wai fa dan Yaya Buhari saurayin tane shine fa."


Khadija tace
"To kunji dalilin ta ko."


"Wannan ba dalili bane,"
Cewar Amina.


"Yauwah yar uwa."
*Asma'u* ta fada tana wa Zee gwalo.


Zuwan wata katuwar mota shi yaja hankalin su banda *Asma'u* da tayi kasa da kai tana wasa da wayar ta.


*Morning yan uwa ya kk ya gd da iyalai.*


Pls don't forget to vote @Msindawa


*MUJE ZUWA*




*INDABAWA*
[1/18, 14:09] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR*
 ASMA'U HUSNAH


BY *MARYAM S INDABAWA*
*MANS*


🌐 *HAJWO* 🌐
*Hakuri da juriya Online writers*✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻




*Gidan Hakuri da juriya tare da kawar da kai, gidan zaman lafiya. Na gaida ku.*






*36-40*


Dedicated to My great *Mamah* Allah ya jikan ki ba dan kin mutu ba.


Allah kara miki lafiya da nisan kwana mai albarka.


Nagaida ke mahaifiya ta abar alfahari na.




*Manzon Allah (SAW) ya ce,
Idan zaka so mutum kada ka nuna masa tsananin so.
in zaka kisa kada ka nuna masa tsananin ki.








Dukkan su hankalin su ne yayi kan motar, banda *Asma'u* da ta daukar da kan ta, tana wasa da wayar ta.


Khadija ce ta fara magana, ta ce,
"Kai motar nan ta hadu amman."


Amina tace,
"Ai daga duk kan alamu, ma na cikin ta zai fi haka hauduwa."


"Gaskiya kan motar ba karya, ko wane dan gayun ne a ciki."
Hafsat ta fada


"Ni kam ba ruwana da na ciki sai motar da ta burge ni."
Zainab ta fada.


"Kai Allah bani irin motar na."
Hafsat ta fada.


"Hassada kike yi tinda kika ce Allah baki irin ta sai dai kice Allah baki finta."
Amina ta fada.


"Duk karya ne irin haka nan, dan kaga Abu ka roki Allah yabaka irin sa shine haka."
Zainab ta fada tana tabo *Asma'u*


" *Asmy* kalli waccen motar amman tayi kyau wallahi."


Kai ta dago ta kalli motar, ji tayi gaban ta ya fadi.
"Eh tayi kyau."


Ta fada tana mikewa sakamakon kiranta da ake yi.


Can gefe ta koma jikin wata motar, ta dauki wayar.


"Hallo my beauty! (Kyakyawa)"
"Ya Aslam wannan ai tsokana ce."
amsa ta amsa masa da muryar shagwaba.


"Wacce tsokana nayi."
ya tambaya


"Wai beauty!"
ta bashi amsa.


"Oo Ke ba kyakyawar bace."
Ya tambaya.


Ta ce,
"Gaskiya ni ba kyakyawa bace. Wannan ai sai kasa ayi min dariya."


"Ba wanda zai miki dariya kinji, saboda kyan ki ba kowa ke da irin shi ba. Kina da wani kyau wanda kafin a samu mutum me irin sa ake dade wa. Ur skin is fresh with a beauty colour. (Fatar ki a murje, me kala me kyau)."


Ta ce,
"Uhmm please stop dis joking I beg you. (Dan Allah daina wannan tsokanar na roke ka."


Murmushi yayi ya ce,
"Wallahi I am not joking, I am telling the true. (Ba tsokanar ki nake ba ina fadan gaskiya ta ne.)"


Baki ta turo ta ce,
"Naji ya isa, ka karaso ne,"
"Eh! Gani kina ina ne."


Ta ce,
"Ina kofar department din mu,"
"Nima ina wajen."


"Kai ya Aslam!"
ta fada.


"Da gaske ina wajen."


"Ta ina."
"Ina cikin wata Ash marsandi."


"Oh na ganka. Ina ta bayan ka."
"To kizo man."


"A'ah Yaya please kai ka fito."
"To gani nan."


Baya ta juya masa.


Kofar motar ya bude, wani sanyi da kamshi me dadi ne ya fito.


Kafar sa ya ziro kasa. Safa ce da takalmi sau ciki bakake a kafar sa.


Daya ya diro sannan ya fito gaba dayan sa. Suit ce a jikin sa, ruwan kumkumadi.


Ya cire ta saman sai yar ciki da ya rage. Tin daga kafar sa na fara kallon sa inayin sama. har na karasa kirjin sa wanda yake a bude dashi na kirar cikaken namiji me jini a jiki wanda ya cika namiji.


Kan fuskar sa na gangara. Fuskar sa me kyau ce doguwa fari ne tas dashi, sai manyan idanu wadan da suke a lumshe, wanda ake ce musu (sexy eye)


Bakin shi dan karami ne, wanda yake da lebe me taushi gasu pink sai kwalli suke. Kansa cike yake da suma, kamar ta indiyawa.


Sai saje dake gefen fuskar sa, wanda ya kara fito masa da kyaun fuskar sa. Idon sa sanye da farin gilashi.


Masha Allah wannan gayen duk inda ake neman cikaken namiji me kyau da kwarjini ya kai ya ma wuce nan.


Yan mata da yawa kallon sa suka tsaya yi sai gulmar sa akeyi. Dan ya gama haduwa ba karya.


Waige waige ya farayi dan neman inda take, duk da ta juyar da kanta sai da ya gene ita ce. Dan duk jikin sa ya gama shaida masa, *Husnah* sa ce.


Cikin tafiyar kasaita da nuna kalama tare da nutsuwa yake tafiya.


Sannu a hankali har ya karasa gefen ta. Ta bayan ta ya zaro hannayen sa dake cikin alhiju ya rufe mata idanu.


Jin an rufe mata ido da hannu me laushi, ga kamshin turare dake tashi, tasan Ya Aslam ne.


Murmushi ta saki me sauti.
"Haba My Hero, ai nasan kai ne."


Hannun sa ya janye ya maidasu kan kafadun ta ya juyo da ita.


Kasa magana yayi ya kure ta da idanu.


Ido ta kashe masa guda daya.
"Yah dai."


Yawu ya hadiye tare da sauke ajiyar zuciya yana me sakin wani murmushi dake karawa fuskar sa kyau.


Wani kallon soyayya yake aika mata dashi.


Ba karamin kyau sukayi ba.
"Baby nah kinyi kyau fa."
ya fada yana kara kallon ta.


"Zaka fara ko?"
Ta fada tana nuna masa wasu kujeru da aka gina su.
Zama yayi ita ma ta zauna.


"Sannu Yaya nah Ya hanya?"
ta tambaya cikin kulawa.


Ya ce,
"Hanya Alhamdulilah."


"Sannu toh!"
"Yauwah! Naji dadin zuwa na dana ganki Sweetheart, kin kara kyau, ashe duk hoton da nake gani rage min kyaun ki yake yi."


"Yayana kenan yasu Momy."
ta fada tana wasa da yatsun hannun ta.


"Suna lafiya."
Ya fada yaba dago face din ta.


"Bari na karbo maka lemo."
Ta mike.


Kamo hannun ta yayi ya ce,
"A'ah yanzu na gama cin abinci ga naku can ma a mota."


Murmushi tayi,
"Kai Yayah."
"Eh!"


"Zakaje gida ne."
"A'ah! Daga nan zanyi gida."


"Ok."
"Ina sonki Baby nah."


Murmushi tayi ta dukar da kanta.
"Baby kunyar nan taki tana dada miki kyau."


Kai ta kuma dukar wa.
"Bari na wuce kar nayi dare. Tinda naga Baby nah ai nagodewa Allah."


Murmushi tayi.
"To nagode."
"Nike da godiya Baby nah "


Suka mike suka nufi motar. Dai dai karasowar Sir Sabir zai dauki motar sa.


Kallon juna suka yi, ya shige motar sa.
"Waye wancan."


Juyawa tayi,
"Sir Sabir wani lecturern mune."


"Kuna magana ne?"
Ya tambaya fuska a dan hade


Kai ta girgiza ta ce,
"A'ah!"


"Ina zee kuwa?"
Ya tambaya.


Kallon gun da suke tayi ta ce,
"Gata can bari na kira ta."


Ta tafi wajen su Zee,
"Zee kizo inji Ya Aslam!"


Ta fada tana kamo hannun ta.


Wajen su suka karasa.
"A bamu waje ko?"


Ya fada yana kallon *Asma'u* baki ta tabe ta bar wajen. Dariya yayi, yace,
" *Husnah* rigima."


Sannan ya dawo da hankalin sa kan Zee.
Bayan sun gaisa yake bata amanar *Asma'u* sannan sukayi sallama.


Wajen *Asma'u* yayi,
"Haba Baby na yanzu da Yayan naki kike fushi. Kiyi hakuri kinji."


Shiru tayi masa. Murmushi yayi, ya koma gaban ta,
"Ko so kike na rumgume ki na rarashe ki."


Ido ta zaro, tana girgiza kai. Ya jawo ta. Saurin janye hannu ta tayi. Tayi wajen motar sa.


Bayan ta ya bi, yana Murmushi ya shiga motar. Leda ya miko mata.


"Gashi ni zan tafi."
Amsa tayi ta ce,
"To Allah kiyaye hanya."


"Ameen nagode!"
Ta rufe masa kofar tana daga masa hannu. Tare da murmushi akan fuskar ta.


Sai da taga bata hango shi sannan ta koma wajen kawayen ta.


Ido suka bita dashi,
" *Asma'u* waye wancan."


Hafsat ta tambaya fuskar ta a hade. Kallon ta *Asma'u* tayi sannan ta dauke kai.


Zainab ce, tace,
"Yayan ta ne."


Khadija tace,
"Amman fa ya hadu. Wai meyasa ke kike baka ne."


Amina ce, tace,
"To ko zaki canja mata halitar ta ne,"


Harara ta Khadija tayi,
"Ni na tambaye ta, ta wani haden rai da dauke kai."


Hafsat ta fada, Mikewa *Asma'u* tayi ta kalle ta.
"kin tambayen an amsa miki ba shikenan ba. ko kin manta wa kike tambaya ne. *Asma'u* da batai miki komai bace kika dau gabar duniya kika daura mata, kin manta in nayi miki magana ko kallo na bakya yi shine kuma yanzu zaki zo kina tambaya ta. Kuma cikin isa sai kace ni yar kice. Ke bama zan fada ba. Kiyi abinda xakiyi."


Ta fada tana kama hannu Zainab suka shige hall.
"Haba *Asma'u* me kenan kika yi ke da bakya fada."


Kuka *Asma'u* ta fashe dashi,
"Ya zanyi kema kinsan dai Hafsat ta kaini bango ne. Duk makarantan nan ba wacce ta tsana kamar ni tin ina dauke kai sannan yanzu tazo tana min gadara. Akan abinda be kai ya kawo ba."


"Ya isah toh mene na kukan!"
Ta fada tana jan ta jikin ta tana rarashin ta.


Ta jima tana addu'a cikin ranta sannan taji sanyi. Kan ta, ta dago ta kalli Zainab.
"Nagode besty."


"Ba komai."
kasa ta duka zata dauki jakar ta. Sai a lokacin ta tuna da abinda Ya Aslam ya kawo musu.


Murmushi tayi ta dauki ledar tana dubawa. Takeaway yayi musu, guda uku sai dayar ledar kuma kaji ne guda biyu a ciki da lemuka na jarka.


Raba su tayi gida biyu ta mikawa Zainab.
"Besty dan Allah mikawa su Amina kayan nan."


Karba tayi tayi waje.




Su *Asma"u* na barin wajen, su Amina suka farayiwa Hafsat fada.
"Haba Hafsat, meyasa kike haka, yarinya bata tsare miki komai ba amman kin tsane ta gaskiya ki daina haka."


Hafsa ta ce,
"Tayaya zakice bata taren komai ba, yarinyar da ta shigo ta same ni sannan tazo tafi ni kokari shine bata fini komai ba."


Khadija ta ce,
"Yo dan tafiki kokari, ai kema dagewa ya kamata kiyi ba ki tsane ta ba."
Khadija ta fada tana bata fuska.


"To ku dake ni mana."
Hafsat ta fada.


"A'ah A'ah ba abin duka anan. Sai dai muyi miki addu'a Allah ganar dake."


Dai dai nan wata daliba da tayi kaurin suna a makarantar ta karaso gun su


"Hae Babies."
"Hae!"


Gefen Hafsat ta zauna.
"Dan Allah wa naga ta tsaya da yaron nan da yazo yanzu. Dan bayan ta na gani banga gaban ta ba."


"Oh ai *Asma'u* Suleiman ce."
Hafsat ta bata amsa.


"Wane department take,"
Suka fada mata tai musu godiya ta bar wajen


Zainab na fitowa Munasha na shiga Hall wajen *Asma'u* ta dosa kai tsaye,








Toh masoya *Asma'u Husnah* naga sakon ku na gode, ba ma yan threestart u always love my story tnc Allah bar kauna.




Hhhh yan facebook comment naku na min dadi ngd


Afternoon yan uwa


Don't forget to vote pls


*INDABAWA*
[1/18, 14:09] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR*
ASMA'U HUSNAH


BY *MARYAM S INDABAWA*
*MANS*


🌐 *HAJWO* 🌐
*Hakuri da juriya Online writers*✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻


Na gaida ku, yan 'kungiyar mu, Allah kara hade kan mu tare da dada mana hakuri da juriya da al umma.


Hajiya Nafisa na gaida ki. Allah kara daukaka Ameen.
Mamanah.








*41-45*


Dedicated to *My sweet Mum*
Allah kara miki imani da daukaka.




An Ruwaito Cikin Littafin Ibn Sinni, Daga *Buraidah (ra)* Yace: *Manzon Allah(ﷺ)* Yace: "Duk Wanda Yayi Wannan Addu'ar a Yayin da ya Wayi Gari da Kuma Lokacin da Yayi Yammaci, *{Rrabbiyallahu Tawakkaltu Alaihi La'ilaha Illah Huwa Alaihi Tawakkaltu wa Huwa Rabbul Arshil Azeeem, Lã'ilaha Illallahu Aliyul Azeem, Mãsha Allahu Kana, Wama Lam Yasha Lam Yakun, A'alamu Annallaha Ala Kulli Shai'in Qadeer, Wa Annallaha Qad Ahad'a Bi Kulli Shai'in Ilma},*
Sannan Ya Mutu Zai Shiga Aljanna












Tana karasawa wajen, tace,
"Hae Bae!"
Murmushi *Asma'u* tayi.


"Sannu!"
"Yauwah! Uhmm daman nace wanda yazo din nan sunan sa nake son ji."


Murmushi *Asma'u* tayi,
"Ya Aslam Sunan sa."


"Ok toh nagode."
Ta fada tana mikewa dai dai karasowar Zainab.


Kallo Zainab tabi ta dashi, ta karasa gun *Asma'u*


Fuskar ta a daure take tambayar ta.
"Me ya hada ki da waccan?"


Bin ta *Asma'u* tayi da kallo.
"Tambayata tayi."


"Akan wa?"
"Ya Aslam mana."


" *Asma'u* kin san wace wannan kuwa?"
ido Asma'u ta bude alamar tsoro. Ta girgiza kai ta ce,
"A'ah wace?"


"Toh! Ita ce wacce ake kira Munasha! Kinsan dai Munasha ita ce wacce ba abinda bata aikatawa, ki kula da ita dai."


Ido *Asma'u* ta zaro, saboda tsoro.
"Wallahi ban sani ba."


"Ki dai kula."
"Insha Allahu."


Daga nan suka fara cin abinci, suna gamawa aka fara taruwa a hall din. Gaba suka koma, sai ga lecturer su nan.


Sai karfe hudu ya fita, sallah sukayi suka shige library dan yin karatu.


"Sis Koyan lecture da Sir Sabir yayi muku yau."
Asma'u ta fadawa zee


"Toh!"
Ta fada tana koya mata, sosai take ganewa. Sai karfe biyar da rabi sannan suka fito, lokacin har anzo dibar su.


Sallama sukayi, suka wuce.




Tana komawa gida ta tadda Mamin ta a falo.


Kanta ta haye,
"Mami na ya gida?"


"Lafiya Alhamdulilah, Ya makarantar?"
"Lafiya Mami."


"Tashi kije kici abinci nasan baki ci komai ba."
"Lah Mami naci Abinci. Mami kinga yau Ya Aslam ma yazo makarantar mu."


Ta fada tana murmushi, fuska Mami ta dan hade, ta ce
"Wajen wa yaje?"


"Wucewa zai yi ya biyo."
Asma'u ta bata amsa.


" *Asma'u* ban yadda ki kara bari ya same ki a makaranta ba, ke bashi ba koma waye kar ki kuma haduwa da wani namiji a makaranta."


Fuska ta marairaice,
"Mami dan Allah kiyi hakuri, bazan kara ba."


"Ba komai baki bata min ba. Amman kika kuma shi zai batan rai."
"Kiyi hakuri insha Allahu bazan kuma ba."


"Kar ki damu tashi kije ki rage kayan jikin ki."
"Kin hakura toh!"
asma'u ta tambayi Mami.


Murmushi Mami tayi,
" *Asma'u* kenan. Na hakura, kinji."


Murmushi tayi ta tashi ta haye sama.


Murmushi Mami ta kuma yi, tana girgiza kai, *Asma'u* sam bata son bacin ran iyayen ta ko ya tayi musu laifi zata daga hankalin ta, har sai taga sun hakura.


Ita kanta Mami tasan ba wani abu bane dan Aslam yaje makarantar ba, amman in har bata tsawa tar ba nan gaba zata iya bawa kowa damar yin haka.


kuma hakan baya da kyau.


Tana shiga dakin ta ta fara lalubar number sa. Bugu daya ya daga.
"Yayanah ya hanya?"


"Hanya lafiya Alhamdulilah na kusa karasawa."
"Kai Yaya gudu kake yi ko?"


"So nake nayi sauri na karasa."
"Dan Allah ka rage gudun nan."


"To shikenan sai anjima."
"Aha! Ka kula da kan ka."


"Insha Allah!"


Ta kashe wayar tana sauke ajiyar zuciya ne. Bandaki ta shiga tayi wanka sannan ta fito.


Kwalliya tayi me kyau, ta saka riga da siket yan kanti ruwan madara da dark brown.


Brown (Ruwan kasa) din hijab ta dauka ta saka sanna ta dauko jakar ta tana duba wa.


Tana gama dubawa ta mike ta hau kan sallaya, tana jan carbi. Kiran sallah da taji ya sanya ta mike ta tada sallah.


Tana idar wa ta janyo Alkur'anin ta, tana karantawa. sai da akayi sallah isha'i sannan ta mike tayo.


Tayi Isha'i sannan, ta mike tayi shafa'i da wuturi. Tana idar wa ta fara yin addu'a.


Wayar tace tayi kara dubawa tayi. Sakon Ya Aslam ne ya shigo.
*Baby nah, na sauka lafiya. Zan kira ki anjima.*


Murmushi tayi, ta mike tayi waje.




Tinda ya gansu a tsaye ya kasa sukuni sam ya kasa samun nustsuwa, waye wannan da yazo

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads