Showing 45001 words to 48000 words out of 92878 words
Chapter 16 - Asma'ul-Husnah Complet Book by Indabawa .txt
Amanci da albarka*
Dedicated to *My Lovelly Momy*
*Bismillahir Rahamanir Rahim*
*Alhamdulilah.*
Allah nagode maka da ka bani ikon fara cigaba da karashen littafin *Asma'u Husnah* Allah ina rokan ka da ka bani ikon kammala shi lafiya kamar yadda na fara lafiya.
Masu korafi akan littafin kucigaba da bibiyar sa zakuyi komai.
*Mahaifiya ta farin cikin rayuwa ta. Mahaifiya ta hasken idaniya ta. Allah dada lafiya da nisan kwanan Momy Ameen*
Allah ka jikan *Mahaifina, da dukkan musulmai baki daya.
*Kannena farin ciki na. Allah bar min ku. *Nusaiba and Hauwa'u (Yasmeen)*
One love.
Ina mika gaisuwa ta ban girma gare ki yar uwa Anty nah. *Rashida Abdullahi Kardam* Allah ya dafa Allah ya karawa Mama lafiya. Allah baki miji nagari da zuri'a daiyaba. Ameen.
Sai sakon gaisuwa ta ga *Hajiya Nafisa* Momyn mu. Allah ya kara girma ya kara lafiya da arzuki ya Allah ya raya zuri'a. Ameen.
Sai gaisuwa ga Dukkan nin yan uwa marubuta musam yan kkungiyar HAJOW tare da yan uwan abokan azurki masoya. Allah ya kare mana ku Ameen.
Masoya nagode da kaunar ku a gareni nima ina kaunar ku.
Allah marasa lafiya na gida dana asibiti Allah ya basu lafiya. Allah ka daukaka musulunci da musulumai. Allah ka karya kafirci da kafirce.
*Ameen*
Bari mu shiga cikin karashen littafin dan muji abinda zai faru.
*1-5*
Ganin halin da Aslam. ya shiga ba karamin dagawa Dady hankali yai ba.
Amman duk da haka ya ce bai yadda Aslam ya auri Pretty ba.
Aslam kuwa ba karamin tashin hankali ya shiga ba. dan jinin sa ba karamin hawa yayi ba.
Momy da batasan me yake faruwa ba yasa ta shiga tashin hankali na rashin ganin Aslam ba.
Dady ta tara dan ganin bata ga Aslam ba har dare.
Dady ne ya fada mata duk abinda ya faru.
Momy mamaki ta tsaya yi yanzu abinda Aslam ya zaba kenan.
Zama Momy tayi ta dafe kan ta. Dady ne ya zauna kusa da ita ya kamo hannun ta.
Kallon sa tayi idon ta jajir ta ce,
"Dadyn Aslam ya zan yi da Asma'u. Kai kan ka shaidane akan soyayyar dake tsakanin su. Ban san me ya samu Aslam ba har haka ta faru. Amman ka min izini gobe na tafi kano naji me yake faruwa."
"Ba komai. Ki kwantar da hanaklin ki. Na amince kije Allah ya kyauta."
"Ameen!"
Kwana Aslam yai a asibiti dan Dady ko wajen sa bai koma ba.
Sai Pretty ya kira ya ita ta kwana a wajen sa.
Washe gari Momy ta daga zuwa Kano.
Asma'u ce kwance zazzabi ya rufe ta dan jikin ta kamar wuta.
Sai rawar sanyi take, idanun ta sunyi jajir dashi.
Mami ce ta shigo dakin rike da wani dan bowl da karamin towel a hannun ta.
Zama tayi a gefen Asma'u ta yaye bargon da ta rufa dashi.
Hijab din jikin ta ta cire mata ta matsa kusa da shi ta na tsoma towel din a cikin ruwan ta dauko ta matse sannan ta saka mata ajiki.
Wata ajiyar zuciya ta sauke, tana mme bude idon ta da sauri.
"Sannu!"
Mami ta fada tana cigaba da Shafa mata ruwa a jikin ta.
Sallamar Momy, Mami ta jiyo daga sama. Ajiye ruwan hannun ta Mami tayi ta mike ta fita.
Ganin Momy yasa ta saki fara'a ta ce,
"Anty nah Oyoyo."
Ta rumgume Antyn tata.
"Mu shiga dana ciki."
Suka shiga dakin Mami inda Asma'u ke kwance.
Momy na shiga taci karo da Asma'u kwance da sauri ta karasa wajen ta ta ce,
"Asmy na lafiya?"
Ido Asma'u ta bude jin muryar Momy. Da sauri ta mike tana sakin murmushi. Idon ta kamar zafin wuta saboda haka kanta yake sara mata dan har harbawa yake.
Zama Momy tayi agefen ta tana kamo hannun ta. Ta ce,
"Asmy bah lafiya ne?"
Murmushi Asma'u tayi ta ce,
"Dan zazzabi nake."
Momy ta kalli Mami ta ce,
"Tin yyaushe kuma amman baki fada min ba."
"Yi hakuri Anty, Wallahi kwana ta uku ke nan."
Kallon ta, ta maida kan Asma'u ta ce,
"Sannu Baby nah. Kunje asibiti."
Mami ce ta ce,
"Kinsan Amsa'u ai, tana likita amman bata son shan magani."
"A'ah haka bazatai yiyu ba. Tashi muje."
Ta mike tana daga Asma'u
Mikewa Mami tayi tabi bayan su. Asibitin Malam Aminu Kano suka tafi. Suna zuwa suka wuce Emergency.
Suna zuwa suka shiga ganin likita da yake suna da hanya.
BP ta ya auna, sannan ya dauki jinin ta, ya auna.
Gado ya basu ya ce, sai ana mata karin ruwa.
Buhari suka kira suka fada masa suna asibiti.
Sosai Doctor yayi musu fadan akan me jinin Asma'u da ya ga ya hau.
Mami ta rasa me yayi sanadin haka ita gani take kawai damuwar rashin Dadyn ta ce.
Momy ce ta hau tunanin ko dai sun ssamu matsala da Aslam ne shiyasa hakan ta faru.
Nan da nan sai ga Buhari yazo. Lokacin Asma'u na bacci.
Zama sukai ranar a asibiti suka yini sai gab da magariba aka ssallame su suka tafi gida.
Suna shiga gida Mami ta shiga kitchen. Asma'u kuma Momy ta hada mata ruwan wanka ta shiga tayi.
Tana fitowa ta saka kayan baccin ta sannan ta tada sallah.
Momy ma sallah tayi sannan ta zauna tana kallon duk wani mmotsin Asma'u.
Tin aa hanya take fama da kiran wayar Aslam bai dauka ba.
Yanzu ma kiran nasa ta karayi. Ganin bai dauka ba ta fara zargin ko lafiya.
Wata ta ce, lafiya kalaou da ba lafiya zai kira ya fada mata.
Wata zuciiyar kuma ta ce ko wayar sa aaka dauke. Nan ma ta ce da zai sanar da ita.
"To ko nai masa wani abun ne?"
Ta tambayi kanta. Kai ta girgiza ta ce
"In haka ne da zai sanar dani."
Shiru tayi tana son ta gane me yake faruwa amman ta kasa.
Har akai isha'i tana zaune a inda take mikewa tayi tai sallah.
Sai da ta idar tai addu'a sannan ta kalli Momy da ta idar da sallah itama.
Ta ce,
"Momy ya Aslam kuwa lafiya ina neman wayar sa bana samu."
Kallon ta Momy ta yi ta ce
"Tin yaushe kuma?"
"Yau wajen kwana biyar fa rabon da muyi waya. Bayan Yaa Aslam kullum sai munyi waya dashi."
Kallon ta Momy tayi ta tausaya mata ta ce,
"Kuma ba abinda yya hada ku."
Kai ta girgiza ta ce,
"Lafiya muka rabu da shi."
Kai Momy ta jinjina ta ce,
"Kinga kar ki damu. Kin san ance jinin ki ya hau ki rage tunanii zan kira sa naji kinji. Ki kwantar da hankali ki."
Kai ta gyada ta mike ta hau gado ta kwanta.
Zuciyar ta in banda bugawa ba abinda take.
Gaskiya tana son Yaa Aslam bata san inda zata sa kanta ba.
Tana kwance Mami ta shigo mata da kunun da ta dama mata.
Amsa tayi ta dan sha sannan ta mika mata.
Kwanciyya ta koma tayi sannan ta dasa daga inda ta tsayaa a tunanin ta.
Washe gari Mami da Momy suna zaune a falo. Momy ta dubi Mami ta ce,
"Amina wata matsala ce ta kawo nifa."
Kallonta Momy tayi ta ce,
"Wacce irin matsala?"
Ajiyar zuciya Momy ta sauke ta ce,
"Akan Aslam da Asma'u ne."
Kallon ta Mami tayi ba tare da ta gani me take fadi ba.
Momy ce ta gyara zama ta fada mata duk abinda yake faruwa.
Kai Mami ta jinjina tana mamaki anya Aslam ne kuwa.
Mami ce ta ce,
"Kinga Anty kuyi masa yadda yake so, Allah yasa haka ne mafi alheri ita Asma'u sai ta hakura."
Kallon ta Momy ta yi ta ce,
"Wai ke Amina meyasa ko da yaushe kike son nuna min banbanci tsakanin ya'yan nan namu ne, kina zaton in nice Asma'u tayi ba dai dai ba zan barta ne, amman ke sai ki ce Allah yasa haka ne yafi alheri. Ai nasan daman da wannan addu'a."
Mami dai shiru tayi fana sauraron fadam da Momy ke mata.
Sai da ta gama sannan ta ce,
"Kiyi hakuri Anty amman ni ba abinda kike nufi bane, nasan tsakanin Aslam da Asma'u ba mai shiga ne, bansani ba ko wani abun ya shiga tsakanin ne ko sun samu sabani."
Kai Momy ta gyada, ta ce,
"Ki tuntubar min Asma'u "
Mami ta ce,
"Toh!"
Buhari da tin da Momy ta fara bawa Mami batun yana jin su har yanzu yaji jikin sa yayi mugun sanyi.
Garden yayi dan bazai iya shiga ciki ba a halin da yake ciki.
Yana zuwa ya hango Asma'u kwance a kan wata kujera. Ta kudundune jikina ta.
Idon ta a rufe kamar mai bacci. Juyawa yayi zai bar wajen ta mike tana kiran sunan sa.
Juyowa yayi yana sakar mata murmushi, ya ce,
"Ai na zata bacci kike."
Kai ta girgiza masa ta ce,
"Ina kwance ne kawai."
Dawowa yayi ya zauna gefen ta yana kallon ta cikin tausayawa dan yanzu da ya kara jin maganganun su Momy sai ya kara tausayawa Asma'u.
Kallon ta yayi dan ya bugi cikin ta ya ce,
"Ina Yaa Aslam kuwa? Kwana biyu bamuyi waya ba."
Murmushi ta dan ta ce,
"Yana lafiya."
Kallon mamakki ya bita da shi. duk yadda yaso ya bugi cikin ta bata fada masa komai ba.
Haka ya hakura ya barta sai kallon tausayi da yake mata dan yasan Asma'u ta ji Aslam zai aure ba karamin damuwa zatai ba.
Yasan zata iya shiga wani hali. To shi da me zai taimakawa kanwar sa kar ta shiga damuwa.
Ya jima yana tunanin nan kafin ya mike ya koma cikin gida.
Asma'u kuwa har lokacin number Aslam take ya kira amman No Answer.
Aslam kuwa duk kiran da take masa yana gani dauka ne yake gagarar sa. Dan shima ba karamin sun dauka yake ba amman sai ya kasa.
Yanzu kuwa kullum yana tare da Prety daga sune can sai sune can.
Duk abinda ta lissafa tana so ya siya mata.
Buhari ne kwance ya kasa gaskata abinda yaji su Mami na fadi.
Mikewa yai zaune ya janyo wayar sa. Number Aslam ya kira.
Bugu daya ya dauka. Gaisawa sukai kamar yadda suka saba sai dai bai tambaye sa Asma'u ba kamar yadda ya saba.
Buhari ne ya ce,
"Yaa Aslam daman Asma'u ce ba lafiya naji ba ka kira ya take bane."
Shiru Aslam yayi na dan wani lokaci kafin ya ce,
"Ai mata sannu. Yanzu ina wani aiki ne amman in na samu lokaci zan zo. kaji labarin aure na nan da sati biyu ko?"
Dif Buhari yayi jin abinda Aslam ya fada. Kai ya girgiza sannan ya ce,
"Au bikin naku har an matso dashi amman ban sani ba."
"A'ah ba wannan ba wata xan aura anan."
"Wata zaka aura!"
Buhari ya fada da mamaki sosai. Aslam ne ya katse masa tunani ya ce,
"Buhari kai ne dan uwana wanda kake kani a guna. Wallahi bansan me yake damuna ba. Lokaci daya naji ina son Pretty kuma ni ba son Asma'u ne bana yi ba kawai bansan me yake damuna ba."
Sosai Aslam ya bawa Buhari tausayi. Tabbas yana tausayawa Aslam amman yafi tausayawa Asma'u ita da take haukan son sa.
Shiru yayi. Aslam ya ce,
"Dan uwana dan Allah kada hakan ya zamo sanadin yanke zumuncin mu ka fuskance ni. Momy da Dady sun kasa fahimta ta."
Take Buhari ya gane Aslam ba acikin haiyacin sa yake ba.
Shiru yayi kafin ya ce,
"Ba komai Allah tabbatar da alherin sa."
Wayar ya kashe yai shiru. Sai ga hawaye na zubowa daga idon Buhari.
Tabbas dole yasan abinda zai ya kubutar da Asma'u daga damuwa.
To tayaya dole ta damu in har Aslam baya kiran ta. Kuma dole ta damu in bata ganshi a wajen ta na kwanaki ba.
Ya jima yana saka da warwarar yadda zai bullowa alamarin har da sai da ya samu mafita sannan ya samu sauki a ransa.
Zainab ya fadawa duk halin da suke ciki sosai ta tausaywa kawar tata.
Asma'u ce zaune a falon Dady ta zuba tagumi, Mami ce ta shiga ta same ta.
Zama tayi a gefen ta, ta ce,
"Asma'u jikin ne, Asma'u dan Allah ki rage damuwa kinji."
Kai Asma'u ta daga ta zare hannun ta da tai tagumi dashi.
Kallom Mami tayi ta sakar mata murmushin da bai kai zuciya ba.
Mami ta ce,
"Wai kuwa kin fadawa Aslam baki da lafiya.?"
Shiru Asma'u ta danyi ta ce a ranta.
"To ita yanzu wa zata na fadawa damuwar ta in ba Mami ba. Tinda ba Dady dole Mami ta zama kawar shawarr ta."
Kallon Mami Tayi idon ta sun kawo da kwalla ta ce,
"Mami bansan me yake damun Yaa Aslam ba. Kwata kwata baya kira na ko na kira sa baya dagawa. Bansan laifin da nai masa har yake hukunta ni haka ba. Mami wallahi ko bacci bana iya wa saboda ya sabar min shine mutum na karshe da nake magana dashi na kwanta bacci."
Sai ta fashe da kuka. Sosai Mami ta tausayawa yar ta ta. Lallashin ta tayi sannan ta ce
"Kiyi hakuri ki dage da addu'a kinsan haka na faru amman addu'a ita zata tsairatar da ke."
Kai ta daga ta ce,
"Mami bazan iya rayuwa ba Yaa Aslam ba. Yaa Aslam ya sabar min da son sa yadda bazan iya cigaba ba tare da shi ba."
Janta jikinta Mami ta yi ta ce,
"Ki daina fadar haka, ki sa a ranki ko da Aslam ko ba Aslam zaki rayuwa. Kina addu'a Allah zaba miki abinda yafi alheri a rayuwar ki."
Sosai Mami ta kwantar wa da Asma'u hankali.
Suna Zaune Buhari ya shigo. Ganin idanun Asma'u da hawaye ya tada masa da hankali.
Zama yayi a gefen ta ya ce,
"Hussyn Dady menene kuma?"
Jikin sa ta fada ta fashe da kuka mikewa Mami tayi ta fita.
Asma'u ce, ta ce,
"Yaa Buhari. Yaa Aslam ne, bansan me nai masa ba."
Ta fashe da kuka. Lallashin ta ya dinga yi. Ya ce,
"Baby nah ki kwantar da hankalin ki. Ba abinda kikai masa. Kuma insha Allahu Aslam naki ne, kinji."
Kai ta daga ta ce,
"Yaya da Gaske."
Kai ya daga mata ya ce,
"Kinga ki taso muje nai miki visa ki tafi saudiya. Daga nan ki yo addu'a tinda kinga kun gama karatu. in kin dawo a bude asibiti a fara aiki. Daga nan zzan zo muje wasu kasashen kar ki damu kinji."
Kai ta daga masa. Ta mike ta wanke fuska suka fita.
Mami kuwa tana fita itama sai da ta dan zubar da hawayen
Tana tausaywa 'yar ta. Tasan 'yar ta bata saba da son kowa ba. Da Aslam ta bude ido ta san rayuwa gashi yanzu wani al amari na shirin faruwa.
Dakin da Momy ta ke ta shiga jiki a sanyaye.
Kallon ta Momy tayi ta ce,
"Ya kukai da ita."
"Uhmm Anty ni a gani na kawai kibar Aslam ya aure wacce yake so. In yaso daga baya in Allah yayi Asma'u matar sa ce sai suyi auren. Yanzu dai ita ta ce, ba abinda ya hada su kawai dai baya kiran ta baya daukar number ta ne."
"Inna illahi wainna illahir rajiun!"
Momy ta dinga nanatawa.
"Shiken Amina tinda haka kika ga yafi shikenan. Zan je zanyi iya bakin kokari na a daura auren nan da Asma'u amman ni ba yawu na a auren Aslam da wata."
"A'ah Anty kada kiyi haka, kada ki so ma hakan ba kyau. Ki sa masa albarka kawai baki san mene alheri a rayuwar mu ba. In kika ce haka sai kiga wani abu mara dadi ya faru."
Shiru Momy tayi ta ce,
"Shiknan dole na tafi gida yau din man."
"A'ah Anty dan Allah ki bari gobe. Kuma dan Allah kada ki tada maganar nan."
Shiru Momy tayi kawai.
Buhari kuwa da suka dawo gidan su Zainab ya biya da Asma'u duk dan ta samu farin ciki.
Duk da jikin ta ba kwari. Ita kanta fitar da sukai ba karamin debe mata kewa tayi ba.
Dan ya dan samu sanyi a ranta duk da da tayi shiru abin yake fado mata a rai.
Basu dawo gida ba sai dare da siyayyar da Yaa Buhari yai mata.
Kayan ta ta hau hadawa wanda za tai tafiya dasu.
Sai da ta gama ta kwanta. Tana kwance nan sai tunanin Yaa Aslan ya fado mata
Na yadda yake jaddada mata son sa da yadda yake kwantar mata da hankali.
Kuka ta fashe da shi ta jima tana kuka sannan ta mike tayo alwala sanna ta zo ta tada sallah,
Kwana tayi tana sallah tana rokar Allah ya shige mata cikin al amuransa.
Washe gari da zazzabi mai zafi ta kuma ta shi. Dan ko 'kasa kasa sauka tayi.
Tana kwance Momy ta shigo dakin da break din ta a hannu.
Ganin ta a kwance yasa tai zaton ko bacci take wannan yasa ta fita bata tashe ta ba.
Wanka taje tayi ta shirya dan ta tafi gida.
Mami na falo Buhari na gefen ta ya zuba ta gumi.
Ajiyar zuciya ya sauke ya kalli Mami ya ce,
"Mami munje anyiwa Asma'u visa har dake ma zaku tafi tare. Amman na je na fadawa Uncle Abubakar kan a matso da biki na kusa. In lokacin ya yi Mami ke sai ki dawo. Ki bar Asma'u acan dan ta samu nutsuwa."
Kai Mami ta gyada masa dan gwara Asma'u bata nan za ai bikin Aslam da ace tana nan abin bazai mata ba dadi ba.
Buhari ya ce,
"To Mami jibi ne tafiyar."
Mami ta ce,
"Allah nuna mana."
"Ameen!"
ya asma.
Ya ce,
"Asma'u bata sauko ba ko jikin ne."
"Jeka duba ta. Wallahi ni bana son na ganta a irin wannan halin wallahi."
Mikewa yayi yai sama.
Yana zuwa ya tura kofar dakin. Tana kwance bata motsa ba.
Sai da ya shiga ya zauna a gefen ta sannan ya dago ta.
Idon ta ta bude wadan da sukai ja dasu. Dan wani irin ciwon kai ke damun ta wanda ya taba mata har idon ta. Dan idon ta wani zafi da nauyi yai mata.
Ido ta mayar ta lumshe saboda zafin da taji yana mata. Cikin karfin haki ta ce,
"Yaa Buhari ina kwana?"
Bai amsa ba ya jingina ta da gado. Tea ya hada mata mai kauri sai farfesun kayan cikin da aka yi ya dinga bata a baki.
Sosai taci dan rabon ta da abinci tin jiya da rana.
Sai da ta koshi duk idon ta a rufe sannan ya bata magani.
Mami dake ta taga tana ganin abinda suke hawaye ya wanke mata fuska.
Daki ta shiga tayi kuka sosai sannan ta mike ta wanke fuska tayi dakin Asma'u.
Lokacin da ya kwantar da ita kenan. Tana jin muryar Mami ta mike tana mika mata hannu.
Hannun ta Mami ta kama ta kwantar da ita akan cinyar ta tana shafa kanta.
A hankali a hankali har tayi bacci. Kallon ta Mami tayi. Asma'u ta rame ta kara gaske, sannan ta zama shiru shiru dan ko magana bata son yi.
Hawaye ne ya zubowa Mami tai saurin gogewa. Momy ce ta shigo cikin shirin ta.
Zama tayi a gefen Mami ta ce,
"Amina nifa bazan zauna ina ganin Asmaa'u a wannan halin ba sannan na kasa taimakon ta. Ko ba halin da Aslam ya canja bane yasa ta a wannan halin nasan kasance war sa da ita zata rage damuwa. Zanje nasan yadda zanyi sai munyi waya,"
Ta mike, kallon Mami tayi ta ce,
"Na miki transfer kudi, na kayan abincin wannan watan ne. Ki kula da Asma'u sai kinji ni."
Momy