Header Ads
Showing 54001 words to 57000 words out of 92878 words

Chapter 19 - Asma'ul-Husnah Complet Book by Indabawa .txt

Ads the beginning of article before Image
Ads at the middle of Article

take son sa shi kuma baya son ta.


A haka ta shiga motar ta, tayar da motar tayi ta nufi gidan su zee dan yin rabon kati da zasu fara.


Tana shiga ta gaida Maman Zainab sannan ta shige cikin dakin ta.


Tana kwance tana waya da Yaa Buhari sai soyayya suke yi.


Asma'u kuwa na zaune abin duniya ya isheta.


Jin hirar da Zainab take a waya shi yasa ta fara zubar da hawaye.


Wacce soyayya ce bata samu ba. Amman yanzu ita ce a halin soyayya ta juya mata baya.


Tana son Yaa Aslam baza ta taba daina son sa ba.


Dan addu'a take Allah ya cire mata son sa amman sai son sa dake daduwa.


Bata san lokacin da Zainab ta gama wayar har ta zo gaban ta ba.


Sai da ta dafa ta sannan ta dago kanta. Damuwa fal a fuskar Zainab ta ce
"Haba Asmmy mene kuma?"


Hawayen ta goge ta ce,
"Kar ki damu. Ina kati nan. Ina son zan kaiwa Maimuna yau dai naje gidan su."


Kai Zainab ta gyada mata ta ce
"Karfe biyu ai dai kya yi sallah kici abinci sai muje ko?"


Mikewa tayi ta shiga bandakin dake cikin dakin.


Alwala tayo tazo tai sallah ta ci abinci sannan ta mike.


Mikewa Zainab tayi suka fita. Duk inda suka san da yan class dinsu sai da suka kai musu.


A hanya Asma'u ta ce,
"Wato baza ki zo ki karbi aiki ba sai kinyi aure ko?"


Kai ta gyada mata ta ce,
"Ki bari naje na gama cin amarci na tukkuna sai na fara. Yanzu haka kawai a ban hutun sati biyu mai naci."


Kwafa Asma'u tayi ta ce,
"In ma zan baki ba."


Dariya Zainab tayi ta ce,
"Oh sai kin bani. kinsan zan iya tafiya ta ai ba tare da an ban ba ko My husband yazo ya amsar min. Ko Mami nah ta ce na je na huta."


Duka Asma'u ta kai mata ya ce,
"Wallahi yarinyar nan kin min wayo."


Zainab ta ce,
"Wace yarinyar? Anty dai."
Suka sa dariya.


Daga nan suka wuce gidan su Maimuna.




*INDABAWA*
[1/18, 14:29] Maryam S Indabawa🥰: LABARIN RAYUWAR

*Asma'u Husnah*


*part 2*




Na *Maryam S Indabawa*
*Mans*




🌐 *HAJOW* 🌐
*Hakuri da Juriya Online writers*
*Gidan Amanci da albarka*




Dedicated to *My Lovelly Momy*




*26-30*








Sabir kuwa tinda Asma'u ta fita ta bar shi da tunani kala kala.


Allah ya sani yana son Asma'u kuma yana son ya aure ta.


Mikewa yayi ya rufe mata office din shima ya fita ya tafi gun Buhari suna shirye shiryen biki.


Washe gari da safe Buhari ya dau hanyar Abuja a mota


Asma'u yau ma daga Wajen aiki ta wuce Gidan su Zainab.


Yaa Buhari ya isa Abuja lafiya. Momy sai nan nan take da shi.


Ta cika masa gaban sa da kayan abinci kala kala.


Suna zaune suna hirar su Mami. Tana kara tambayar sa ina 'yar ta.


Da yake haka take kiran Asma'u. Buhari ya ce,
"Tana nan ai su Asma'u an zama busy daga wajen aiki sai shirye shiryen biki.
Dan cewa tayi dama sai bayan biki aka bude. Damuwa dai ba laifi ta rage ta duk da tana cikin ta mu take nunawa ba ta cikin ta."


Mami ta girgiza kai ta ce,
"Allah sarki. Allah kawo miji na gari. Ni ina tunanin ma na samo mata miji da kaina dan na wuce haushin da aka bamu."


Dariya Buhari yayi ya ce,
"Haba Momy."


Momy ta ce,
"Wallahi."


Buhari ya ce,
"Ai kam tinda nazo naje na dubo Yaa Aslam da amarya."


Shiru Momy tayi kawai. Momy ta ce,
"To ni me kake so nai maka ne."


"Duk abinda Momy tayi nagode."
"To ai shikenan. duk abinda ka gani ka godewa Allah tinda kaki zaba."


Dariya Buhari yayi. Momy ta ce,
"Kaje ka huta ko?"


Kai ya dan sosa ya ce,
"Aah tukkuna dai zanje gidan wani aboki na daga nan zani gidan Yaa Aslam,"


Momy ta ce,
"Toh!"


Momy ya tambaya address din Aslam sannan ya fice.


Yana fita yayi gidan abokin sa anan duk ya bashi katin nan ya rabawa sauran abokan su.


Daga nan yayi gidan Aslam. Gida ne mai kyau ya hadu, yana zuwa ya ce,
"Oh ikon Allah da tini Asmmy na ce a gidan Yaa Aslam. ikon Allah ance matar mutum kabarin sa ko nan gaba zasuyi aure waya sani sai Allah."


Yana parking ya kira number Aslam. Aslam na dagawa ya suka gaisa kamar yadda suka ssaba.


Buhari ya ce,
"Yaa Aslam gani a compound din gidan ka."


Aslam da sauri ya mike ya ce,
"Da gaske."


Ya ce,
"Kazo ka gani."


Da sauri ya katse wayar ya fito. Yana ganin Buhari ya rumgume shi.


Dariya ya saki ya ce,
"Amman naji dadi mu shiga daga ciki."


Suka shiga. A falo suka zauna. Aslam shi ya kawo masa ruwa da lemo. Sanna suka zauna hira yana tambayar sa ya Mami da Mutan gidan.


Dan sunan Asma'u ma ya kasa ambata. Duk da a cikin ransa yana son ya tambayi Ya Asma'u take amman ya kasa.


Buhari ganin bai ga Matar Aslam ba ya ,
"Yaa Aslam Ina Anty nawa."


Kai Aslam ya dan sosa ya ce,
"Ta fita unguwa ne."


Buhari ne ya mikawa Aslam katin bikin sa. Amsa Aslam yayi yana washe baki yana ta sanya albarka.


Har magariba suna tare dan a gidan sukai sallah.


Buhari ya tashi zai tafi kenan sai ga Pretty ta shigo. Cikin shigar riga da wando, kayan sun matse ta sai wani mayafi da ta yafa abin ba kyan gani.


Buhari da farko bai gane wace ba sai da ya ga Aslam ya ce,
"Madam! Barka da zuwa."


Kallon su tayi a yatsine ta watsar ba tare da ta ce, Uffan ba ta wuce ta kwanta akan kujera tana kwallawa daya daga cikin yan aikin ta kira.


Da sauri ta karaso. Ta bata umarni ta dauko mata lemo.


Mikewa tayi da sauri ta miko mata ta dawo.


Buhari kuwa ya baki ya saka yana kallon ta.


Kallon su tayi a yatsine ta ce,
"Ina zaka ne?"


Kai Aslam ya girgiza ya ce,
"Raka shi zan yi."


Tsaki Buhari ya saki yayi waje. Da sauri Aslam ya biyo shi a baya.


Yana karasawa ya shiga motar sa. Aslam ne ya leko ya ce,
"To bro nagode a gaida gida da su Mami. Sai munzo bikin ko?"


Kai Buhari ya daga ya ce,
"Allah kawo ku."


Yai gaba. A ransa yana mamakin wacce irin mata Aslam ya aura.


Anya kuwa haka ta bar shi. Da wannan tunani ya karasa gida.


Yana zuwa Momy ya tadda a falo. Abinci ta bashi ya ci sannan suka tsaya hira.


Can Buhari ya ce,
"Momy daman haka Matar Yaa Aslam take?"


Momy ta ce,
"Ta maka rashin mutuncin ko?"


"Uhmm batai min komai ba. Ni ko kallo na ma batai ba. Amman Momy kinga da shigar ta take yawo. Bayan nasan Yaa Aslam ba yason shigar banza. Kuma Momy sam bata da tarbiyya kinga irin kallon da take mana kuwa."


Ajiyar zuciya Momy ta sauke ta ce,
"Wallahi kowa complain din da yake min kenan in yaje gidan Aslam. Bansan me yake damun Aslam ba. Amman abin ba dadin ji. Ka ganni nan ban taba ganin ta ba ma bare na san ya take."


Kai Buhari ya girgiza ya ce,
"Momy bafa kiga ba."


Momy ta ce,
"Uhmm wallahi Buhari na rasa ya zanyi, ni yadda aka ce min ma ita ta zama mijin ma. dan sai ta ce yayi zai yi in kuwa ta ce, A'ah bazai taba yi ba. Baka ga ba duk ya zama wani iri abin tausayi. Anan fa kullum yake cin abinci dan wata rana ma ni nake aika masa har gida. Wallahi al amarin Aslam yana bani mamaki sosai."


Buhari ya ce,
"To Momy bakya ganin ba haka suka barshi ba. In ba haka ba, abin ai yayi yawa."


Shiru Momy tayi tana nazari ta ce,
"Kuma fa haka ne, wallahi ban taba kawo haka ba. To yanzu ya zanyi."


Buhari ya ce,
"Zan fadawa Mami da Asma'u bama Asma'u tana da sani sosai a addini. Nasan zata san abin yi. Amman dai ya dage da addu'a muma mu dage da taya shi da addu'a."


Mami ta ce,
"Insha Allah!"


Haka suka tashi suka tafi kowa ran sa ba dadi.


Buhari kuwa sosai yake tausayawa Aslam dan ya kasa sukuni.


A haka yai bacci. Cikin dare ma ta shi yayi ya dinga masa addu'a.




Asma'u kuwa Sai magariba ta koma gida. Tana shiga taga motar Sir Sabir.


Kai ta dauke tayi cikin gida. Yana zaune a falo yana cin tuwon da Mami ta dafa.


Tana shiga suka hada ido. Durkusawa tayi ta gaishe shi ya amsa yana binta da wani kallo wanda tasan Yaa Aslam na mata.


Ido ta dauke har zata wuce sai kuma taga Mami ta fito daga kitchen hannun ta rike da lemo da ruwa.


Karasawa tayi ta amsa, sannan ta zauna.


Mami ce ta kalle tace,
"Kun dawo?"


Kai Asma'u ta gyada. Mami ta ce,
'Buhari ya kira ki ne?"


"A'a! Ya na ina ne banga motar sa ba."
Mami ta ce,
"Ya tafi Abuja,"


Wata faduwar gaba taji dan tasan wajen Momy yaje, kuma zai hadu da Yaa Aslam.


Shiru kawai tayi ta jingina da kujera tana lumshe ido.


Mami ce ta lura da canjawar da tayi. Kallon Sabir tayi shima Asma'un yake kalla.


Mikewa Mami tayi ta hau sama. Yana jin shigar war Mami daki ya matso kusa da ita ya zauna.


Asma'u bata ji zaman sa ba sai kawai muryar sa da taji a dai dai kunnen ta.


Ido ta bude da sauri. Ido suka hada yana kallon ta ido cikin ido.


Duk sun kasa dauke idanun su. Shi wani kallo yake aika mata.
Ita kuma wani abu taga yana fitowa daga idon sa yana shiga nata.


Da sauri ta lumshe ido dan baza ta iya jure kallon da yake mata ba.


"Husnah!"
Ya kira sunan ta cikin sanyin murya.


Ido ta bude a hankali ta sadda kan ta kasa.


"Husnah! Wai haka kike so ki cigaba da rayuwa ba farin ciki. Ke kenan baza ki samu wanda zai sa ki farin ciki ba. Ki tattara komai naki kin bawa Yaa Aslam, husnah ba haka rayuwa take ba. A duk sanda wani ya ce baya yi da kai a lokacin wasu keyi dake, ki dauri ki ban dama zan kasance miki yadda kike so na kasance."


Shiru Yayi yana kallon ta. Idon ta alumshe kuma daga dukkanin alamu tana jin sa. Kuma maganar ta ratsa ta.


"Husnah!"
Ya kara ambatar sunan ta.


Bude idon ta tayi da sauri jin kamar muryar Yaa Aslam.


Sai dai me ba shi bane, mikewa tayi da sauri tayi hanyar bene.


Har ta hau sai kuma ta juyo. Kallon sa tayi shima ita yake kalla.


Murmushi ta sakar masa kawai ta haye sama.


Mamaki ne ya lullube shi. Ya rasa murmushin nata me yake nufi.










*MS Indabawa*
[1/18, 14:29] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR*
*Asma'u Husnah*


Part *2*


Na *Maryam S Indabawa*
*Mans*


🌐 *HAJOW* 🌐
*Hakuri da juriya Online writer's*


Dedicated to *My lovelly Mum*






*31-35*




*Ba abinda zzan ce da masoya karanta littafai na sai godiya mai tarin yawa.*
*A gaskiya ina alfahari da ku. Allah ubangiji ya bar zumunci. Ina kaunar ku saboda Allah*






Zama yayi shima yai murmushin kawai.


Mami ce ta sauko. Hira suka dan taba sannan yai masu sallama ya tafi.


Zuciyar fal da tunanin Asma'u. Yana kaunar Asma'u son Asma'u yai masa wani irin kamu.






Asma'u kuwa tana shiga daki ta fada kan gado.


Ido ta lumshe ba wanda ya fado mata sai Yaa Aslam, Ta jima tana juyi duk ranta ba dadi sannan ta mike ta shiga cire kaya.


Tana gamawa ta fada bandaki wanka ta fara. Tana gama wa ta tayi alwala.


Sai da ta shirya cikin kayan baccin ta dogon wando da riga fare tas sannan ta tada sallah. Ta jima tana addu'a kan Allah ya kawo mata dauki sannan ta Mikewa jiki a sanyaye ta bude firij.


Lemo ta dauko ta koma kan gado ta zauna. Wayar ta ta dauka ta latsa number Yaa Buhari.


Da sauri ya dauka. Murya ta shagwabe ta ce,
"Yaya shine ka manta dani ko?"


Murmushi yayi ya ce,
"Tayaya zan manta dake Sis. Na ta neman number ki ke da wife ban same ku ba."


Ajiyar zuciya ta sauke ta ce,
"To Yaya Ya hanya yasu Momy da Dady."


"Suna lafiya. Ince kuma kuna lafiya."
Kai ta gyada masa.


"Asma'u me yake dumun ki?"
Dan yaji muryar ta ba dai dai ba.


Damuwar ta tai kokarin kawar wa sannan ta danyi murmushin karfin hali ta ce,
"Ba komai."


"Kin tabbata?"
ya tambaye ta.


Kai ta gyada masa. Yace
"To sai da safe."


Sukai sallama. Kwanciyya tayi tana tunanin Sir Sabir kuma.


"To tinda na rasa Ya Aslam me yasa ba zan karbi duk wanda ya so ni ba. Sir Sabir bai da makusa. Yana da kyau ga ilimi ga addini ga nutsuwa me kuma zan nema bayan nan."


Tayi juyi, ta kuma fadin,
"Duk da haka dai ina son Yaa Aslam ko ba komai Yaa Aslam yayanah ne,"


Hawaye ne ya zubo mata. Ta jima tana kuka sannan ya mike tayo alwala ta tada sallah.


Ta jima tana kai kukan ta gun Allah. Sannan ta hau karatun Alkur'ani.


Har akai sallah asuba tana kan sallaya. Wanka ta kara yi sannan ta dawo ta tada sallah.


Tana idar wa ta fada kan gado sai a lokacin wani bacci mai nauyi ya dauke ta.






Mami tinda ta tashi bata ga Asma'u ba ta leko ta tadda tana bacci ta sauka kasa kawai. Dan tasan ba zata aiki ba tinda bata sauko ba.


Aiki tayi ta hada musu break sannan ta yi wanka.


Har karfe biyu Asma'u bata sauko ba. Mami Ta hau sama ta dubo ta yafi sau uku amman bacci take kuma jikin ta ba zazzabi.


Wannan ne yasa Hankalin Mami ya dan kwanta.


Karfe biyu da rabi Zainab ta karaso gidan. Mami ta gani zaune a falo.


Har kasa ta durkusa ta gaishe ta cikin jin kunya.


Mami ta amsa cikin sakin fuska da soyayya.


Mami ta ce,
"Ki hau sama yau tana can ko aikin ma bata je ba."


Zainab ta ce,
"Mami lafiya dai ko?"


Mami ta ce,
"Lafiya lau, ina jin dai abin ne ya fado mata kuma."


"Allah sarki."
Zainab ta fada tana mikewa. Ta ce,
"Mami addu'a dai xamu ta taya ta da ita."


"Haka ne, Zainab Addu'a kuma kullum yi muke. Sai dai fatan Allah ya amsa.'
"Ameen!"


Ta hau sama. Asma'u na kwance ta daka mata duka. Da sauri ta mike tana sosa wajen da ta dake ta.


Tana mutsuka ido. Kallon ta Asma'u tayi ta ce,
"Zainab har kin zo?"


"Eh! Kinsan karfe nawa kuwa?"
Ta fada tana kallon idon ta da suka kumbura saboda kuka.


Asma'u ta ce,
"Uhmm wallahi bacci na sha ban sani ba."


Ta fada tana mikewa tsaya, kallo Zainab tabi ta dashi har ta shige bandaki.


Kai ya girgiza, a rayuwar ta tana son Asma'u tana jin Asma'u kamar kanwar ta, duk abinda ya damu Asma'u itama damun ta yake.


Ta rasa tayaya zata shawo kan Asama'u har ta daina damuwa. Duk da tasan da wuya.


Mikewa tayi ta gyara gadon ta share dakin sannan ta koma ta zauna.


Tana zama Asma'u ta fito tana tsane jikin ta. Kallon dakin tayi ta kalli Zainab ta ce,
"Ke dai bakya gajiya wallahi."


Ta zauna tana shafa mai, ta ce,
"Yau ina zamu?"


"Ke dai ki sauri zamu je, madobi fa."
Kai Asma'u ta gyada.


Mai kadai ta shafa ko powder bata shafa ba ta mike ta saka wata doguwar rigar Atamfa. Mai A shape. Tana da dogon hannu. Mayafin after dress ta yafa ta dau wayar ta da mukullin mota ta ce,
"Muje ko?"


Zainab ta ce,
"Kin karya ne?"


"A'ah muje zan dau Maltina ta ishe ni ma."
Mikewa tayi tabi bayan ta.


Mami tana falo tana ganin su ta saki murmushi ta ce,
"Kun fito."


Asma'u ta ce,
"Eh! Mami ina kwana?"


Mami ta amsa, da
"Lafiya lou kin tashi lafiya?"


Kai ta gyada ta mike ta nufi firij din falo ta dauki Malt guda biyu ta ce,
"Mami mun fita zamu je Madobi wajen yan ajin mu."


Mami ta ce,
"To a dawo lafiya. Allah kiyaye hanya."


Suka fita. Suna fita suka ci karo da Sir Sabir zai shigo.


Wajen sa suka karasa suka gaishe shi cikin girmamawa. Amsa yayi yana bin Asma'u da kallo. Bai taba ganin ta da irin wannan shigar ba.


Zainab ya kalla ya ce,
"Amare ina zaku ne?"


Asma'u, Zainab ta kalla ta ce,
"Wallahi kati zamuje rabawa daga nan mune har madobi."


Kallon su yayi ya ce,
"Madobi da kanku. A'ah muje na kai ku. Daman Buhari yai min maganar zuwa Madobin."


Asma'u, Zainab ta kalla ta ce,
"Sis kinga Sir Sabir ya rage miki aiki."


Asma'u dake danna wayan ta, ta dago ta kalli Zainab sannan ta kalli Sir Sabir da ya zuba mata ido.


Murmushi ta dan saki ta ce,
"Da ka huta ai."


Dan Hararar ta yayi ya ce,
"Ku shige muje."


Ya bude mata gidan gaba. Zainab dai kallon su ta tsaya yi tana cewa Allah yasa Sir Sabir ya so Asma'u dan ba karamin dacewa sukai ba.


Ga wani kallo da taga yana binta da shi.


Da haka ta shiga gidan gaba. Zainab ta shiga cikin gidan baya.


Maltina ta mikawa Zainab sannan ta mikawa Sir Dabir dayar ta hannun ta.


Bai amsa ba ya ce,
"Ke fa?"


Murmushi tayi ta ce,
"Na koshi."


Ya ce,
"Ban yadda ba sha ki rage min."


Zata ce A'ah ya ce,
"Ki sha ki ragen in ba rowa zaki min ba."


Fasawa tayi ta sha kadan ta mika masa, hannu ya kawo zai amsa ya hade da hannun ta.


Kallon sa tayi ya kashe mata ido daya. Kai ta dauke ta cigaba da kallon titi.


Shiru tayi sai Zainab da Sir Sabir da suke hira.


Sai dai shi da yake dan tabo ta, in anyi abu ya ce,
"Ko Husnah?"


Da haka har suka karasa gidan su Hafsat.


Anan suka dan jima dan shima Sir sabir suna tare da Baban Hafsat.


Har abinci suka ci sannan suka taho, ranar shi ya dinga yawo dasu daga can zuwa can.


Har magariba sannan ya kai Zainab gida. Ana sukai sallah magariba sannan Asma'u tai mata bankwana suka taho.


A mota kuwa kowa shiru yayi shi yana tunanin taya zai kara cusa kan sa awajen Asma'u dan ya tabbata Asma'u baza ta ki shi ba sai dan kawai tana son Yaa Aslam ne.


Itama a zuciyar ta rokan Allah take Allah yasa kar yai mata maganar dan bata so.


Can ya dago ya kalle ta ya ce,
"Kin fadawa Maryam bikin ne?"


Kallon sa ta danyi sannan ta kawar da kai ta ce,
"Na fada mata, ta ce, next week ma zata zo."


Kai ya gyada ya ce,
"Oh yanzu dai kun zama friends ko?


Murmushi ta dai yi kawai ba tare da ta bashi amsa ba.


Ya ce,
"Yaushe za muje ki gaida Mamah?"


"Ko yaushe ma!"
Ta bashi amsa.


"Da gaske?"
Ya tambaye ta.


Kai ta gyada. Kallon ta yayi ya ce,
"Ko yanzu ne?"


Kallon jikin ta tayi ta ce,
"A'ah dai."


"Saboda me?"
Ya tambaya.


"Kalli jiki na fa?"
Ta fada tana kallon kan ta.


Murmushi yayi ya ce,
"Me jikin naki yayi?"


"A'ah dai."
Ta fada tana tsare shi da idanun ta.


Da yake shima ita yake kalli take yaji motar na neman kwace masa. Saboda idon ta da suka ruda shi.


Da kyar ya kamo motar ya cigaba da tukin.


Daga haka bai kara cewa komai ba, har suka kara sa gdn.














MS Indabawa
[1/18, 14:30] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR*
 ASMA'U HUSNAH


BY *MARYAM S INDABAWA*
*MANS*


🌐 *HAJWO* 🌐
*Hakuri da juriya Online writers*✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻




*Gidan Hakuri

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads