Header Ads
Showing 6001 words to 9000 words out of 92878 words

Chapter 3 - Asma'ul-Husnah Complet Book by Indabawa .txt

Ads the beginning of article before Image
Ads at the middle of Article

Dubai ni da Moma. To da mun dawo zan shirya zuwa nijar."


"Allah dawo daku lafiya."












Kwance *Asma'u* take akan sofar dake dakin ta. Waya ce a kan cikin ta.


Sanye take da dogon wando, sai riga purple wacce da kadan ta wuce gwiwar ta.


An mata ado da stones sai kwalli suke yi. Kanta hula ce baka.


Idon ta a lumshe sai kace me bacci.
"Kina jina."


Ya fada daga cikin wayar. Sai da ta sauke ajiyar zuciya sannan. Ta amsa masa da.


"Eh! Ina jinka."


Ya cigana da fadin.
" *Husnah* wallahi kin sacen zuciya ta gaba daya. Ban da tunani da buri in ba na na mallake kiba."


Shiru tayi,
"Wallahi zan iya sadaukar da kome nawa dan samuwar farin cikin ki. Na miki alkawari ba abinda zai raba mu sai mutuwa."


"Yayanah na yadda dankai kuma nasan kai me sona ne. Nima bazan taba barin ka ba ko juya maka baya ba."


"Nagode *Husnah* Allah miki albarka. Allah mallakamin ke."
"Ameen Ya Allah!'


Aslam ya ce,
"Toh yanzu me kike."


Asma'u ta ce,
"Ina kwance ne."


Aslam ya ce,
"To maza tashi kije kiyi alawala kinga magariba ta kusa kiyi ta lazumi."


Asma'u tayi murmushi ta ce,
"Toh Yayanah."


Shima murmushi yayi ya amsa mata da
"Aha Sai Anjima."


Mikewa tayi ta shige bandakin ta tayo alwala. Akan sallaya ta zauna tana lazimi. Sai da taji kiran sallah sannan ta mike ta tada. Tana idarwa ta dauko alkur'ani ta fara karantawa.


Sai da aka isha'i sannan ta mike tayi sallah. Ta jima tana addu'a sannan ta shafa ta mike ta fita falo.


Tin daga bene ta fara cewa.
"Dady nah Oyoyo!"


"Oyoyo *Husnah* ta."
Ta sauko ta karasa wajen sa.


"Dady Ina yini?"
"Lafiya!"


"Dady ya aiki."
"Lafiya Alhamdulilah! Ya makaranta."


"Makaranta lafiya Dady!"
"Masha Allah! Badai wata matsala ko."


"Babu!"
"To Allah yayi albarka."


"Ameen!"


Ta juya wajen Ya Buhari.
"Ah Na Anty Zee barka da dawowa."


Hararar ta yayi ya dauke kai.
Dariya ta saki.


"Dady kaga ina masa sannu da zuwa ya harare ni."


Murmushi Dady yayi, ya ce,
"Wai wace Zee din nan ne?"


"Sis yi hakuri dan Allah!"
Ya Buhari ya fada yana marairace mata.


Asma'u ta kanne ido daya tace,
"Yo Dady ai ka gane kawai."


kai Dady ya dan daga ya ce,
"Oh nagane yar gidan Dady."


Suka yi dariya gaba dayan Dakin.
"Ai ni gara ya kawon surikar wallahi."


Mami ta fada tana kallon sa. Shi dai kasa yayi da kansa kawai.


"Ai fah!"
Dady ya fada yana kallon *Asma'u*


Gira ta dage masa. Suka saki murmushi tare.
"Uhmm Abban nah tashi muje kaci abinci."


Ta kama hannun sa.
"Mami ku taso muci abinci."


"To!"












Kamar kullum bayan tagama tsokanar Yayan ta ta haye sama. Tai wanka tayo alwala ta shirya cikin kayan baccin ta.


Kwanciya tayi tana jiran kiran sa. Ai kam ko minti uku batayi ba sai ga kiran sa nan.


Murmushi ta saki wanda ya kara fito mata da ainihin kyauwun ta.


Muryar Aslam ce ta daki kunnen ta bayan ta kara wayar. ya ce,
"Hello! Baby nah!'


Gyara kwanciyya tayi ta ce
"Na'am my Yaya."


Murmushi yayi ya ce,
"Ina matukar kaunar ki Habibaty."


Asma'u ya ce,
"Nima haka Yaya nah."


Aslam ya ce,
"Kinsan me?"


kai ta girgiza kamar yana ganin ta ta ce,
"A'ah!'


Aslam ya danyi jim sannan ya ce,
"Wani abu na gama tunani."


Da sauri ta ce,
"Na mefa?"


Aslam ya ce,
"Hmm tunani nayi a duk cikin duniyar nan duk cikar ta sai Allah ya hada mu a soyayya bayan nasan kin fini komai da komai. Allah nagode maka."


Ajiyar zuciya ta sauke ta ce,
"Haba Yayana me nafika, kai ma kasan ka fini. ni zan yiwa Allah godiya da ya hada ni da miji kamar ka."


Aslam ya ce,
"Baby kin wuce duk inda nake tunani. Ke ta daban ce. Haka son ki ma na daban ne a cikin zuciya ta."


Ta ce,
"Yayanah nima haka kake a zuciya kana da matsayin da ba wanda yake dashi a guna. Kana da gurbi na daban a cikin zuciya ta."


Murmushi yayi. ya ce,
"Kisani dake kadai zan so na rayu kuma na mutu. Har abadan da ke nake son na kasance."


Shiru tayi! Tana me sauraron sa tare da lumshe ido fuskar ta na fitar da wani murmushi na nishadi da farin ciki.


Ya cigaba da magana,
" *Husnah!* Zuciya ta da taki abokan juna ne da basa taba rabuwa ko agun bacci Ido biyu ko a cikin bacci na ke nake tunani haka ma a fili. Wallahi son ki ya zama jinin jikina rabani dashi tamkar raba ni da rayuwa ta"


Ido ta bude ta ce,
"Yayanah na yadda dakai haka duk abinda zaka fada suma na yadda dasu. Kar ka damu insha Allahu ni taka ce har abada."


Aslam ya ce,
"Nagode *Husnah* zan miki alkawarin bazan taba rabuwa dake ko juya miki baya ba."


Asma'u tace,
"Nima insha Allah bazan taba barin kaba sai dai in har ka ka bukaci hakan."


"Shittt!"
Ya fada da karfi.


"Indai nine bazan taba bukatar hakan ba."


"Allah ya sa."
ta fada a sanyaye


"Baki yadda ba."
ya tambaye ta


"Haba dai na yadda da Yayanah. Kai dai kawai kace Ameen."
Ta fada duk yanayin ta a sauye.


"Toh Ameen ya Rabbi."
"Yauwah ko kai fa."


Dariya ya saka.
"Lalai Baby nah. Kin mai dani kamar Baby ko."


Murmushi tayi ta ce
"Oh to mene in na maida kai Baby nah!"


Dariya yayi ya ce,
"Ba komai nasan zan sha gata ne ma."


Ta ce,
"Ashe ka gane."
"Eh! Amman fa kece Baby."


"Wai nice Baby shekarata nawa."
ta tambaya taba turo baki


Murmushi yayi dan yasan *Husnah* da son girma ya ce,
"Ni a wajena ina kallon ki kamar yar shekara biyar dai dai lokacin da yara suka fi shagwaba da rigima."


Baki ta bude ta ce,
"Lalalah! Ni din biyar fa kace."


Dariya Aslam yayi ya ce,
"Eh man."


Asma'u ta ce,
"Yaya ka manta shekara tane."


ya ce,
"Shine nace a wajena ai."


Ta ce,
"Oh! Saboda me to?"
"Saboda Babies abin rarashi ne da tarairaya da shagwabawa. Wannan yasa nake kallon Baby nah ahaka saboda na mata duk abinda na lissafa."


"Oh inkuwa haka ne. Na yadda ni Babyn kace."


Dariya yayi ya ce,
"Yauwah Baby nah."


"Toh nima kai Baby nane. Tinda ina son ina maka abubuwan da ka fada."


" *Husnah* kenan. Dare yayi aje ayi alwala azo ai addu'a"
"Toh"


Ta fada tana mikewa.










*Morning My Yan uwa*


Hhh wai da gaske Asma'u life na burge ku. To haka ake so mutum ya kasance kar ya dulmiya da duniyar nan sosai. A komai kana riko da alkur'ani kariya ne gare mu sosai.


Muna godiya da Allah yayi mu a matsayin musulmai kuma yake bamu ikin karanta sakonnin sa. Wanda duk karantawa da zamuyi muna samun lada mai yakai wannan dadi.


Kana karantawa kana jin dadi da annushuwa da nishadi. Sai alkur'ani.


Alhamdulilah


*Muje zuwa*


*INDABAWA*






*love u wujiga wujiga masoya na.*
[1/18, 14:06] Maryam S Indabawa🥰: *LABARIN RAYUWAR*
*ASMA'U HUSNAH*








BY. *MARYAM S INDABAWA*
*MANS*








*HAJOW*


*HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITERS* ✍✍✍




*Da farko ina mai bada hakuri dan zan canja sunan littafin nan daga *Asma'u Husnah* zuwa *labarin rayuwar Asma'u Husnah* wanda dalilin haka yasamu ne na wata yar uwa marubuciyya da tayi littafi mai suna *Asma'ul Husnah* wanda ni na canjawa nawa suna yanzu.


Ina fatan xaku cigaba da karanta *labarin Rayuwar Asma'u Husnah*


Nagode


*26-30*










Dedicated *FIRST AND LAST LOVE. MY MOMMY*


*Manzon Allah (SAW) Yace, "Idan watan ramadan yazo ana bude kofofin aljanna ana rufe kulle shaidanu" (mu yawaita abinda zai samu samun rabauta duniya da lahira)*










Da wuri ta kamala abinda zasuyi ta shirya tayi wajen Dadyn ta.


Tare sukai break, sannan ta tafi. Da wuri ta shige ajin su.


Text din Ya Aslam ne ya shigo.
"Morning Pretty nah. Ya kike tin dazu nake son kiran ki. Nasan kina aiki. in kingama ki turon hoton ki. Sannan naje Lagos ne Dady ya aike ni. Ina bukatar addu'ar ki."


Murmushi tayi ta maida masa da sakon.
"Na tashi lafiya Yaya nah. Kaima ina fatan kana lafiya. Ya hanya. Hotona yana can na tura maka yana jiran ka."


Ta tura tana murmushi, Zee ce ta taba ta,
"Sis Lafiya kike ta zuba murmushi haka."


"Lafiya lou wallahi. Kin karaso kenan."
"Eh!"


Dai dai shigowar malamin su. Sai karfe sha biyu ya fita wani ya shigo yai musu awa daya sannan suka tafi sallah.


Suna fito wa suka shiga cafeteria suka siyo lemo da snack, a nan kofar hall din su suka zo suka zauna. Karkashin wata bishiya.


A jaka suka saka abincin su dan ba lokacin zasu ci ba, kawayen su ne suka karaso wajen su uku.


"Ah *Asmy* da Xee."
Su ka fada suna dariya.


Murmushi sukai masu,
"Ya kuke?"


"Lafiya lou. Ya karatun."
"Alhamdulilah."


"Masha Allah!"
Suka zauna suna dan taba hira.


Sai karfe biyu suka koma aji dan daukar wani darasin.


Karfe hudu sun gama kowa yayi gida.










*WACECE ASMA'U HUSNAH*


*Asma'u* 'ya ce ga Alhaji Suleiman. Alhaji suleiman dan kasuwa ne duk da yana da kwallin masters a hannun sa. Ya karanci fanin kasuwanci. amman yafi sha'awar kasuwan ci da aikin gwamnati.


Sai daga baya ne ya nemi aiki sannan yake hada kasuwanci da aikin nasa.


Alhaji Suleiman dan gidan Malam Haruna ne, Malam Haruna malami ne, kuma dan garin kano ne. Cikin garin Madobi.


Yana da matar sa daya Aisha, Allah ya azurta su da Ya'ya uku maza sai autar su mace.


Alhaji Suleiman shine babba da matar sa daya hajiya Amina. Ya'yan su biyu, Buhari da *Asma'u Husnah*


Sai Abubakar me bi masa, yana aiki a banki matarsa daya masa'uda, da ya'yan sa biyar duk maza.
Abubakar, Suleiman, Abdulhakim, sai yan biyu. Dukkan su sun girma kowa ya kama aiki. yana zaune anan katsina shima.


Ilyasu shima matar sa daya soja ne. Yana da ya'ya uku duk maza suna zaune a kaduna.
Muhammad, sai yan biyu shima. Shima dukkan su sun girma suna aiki.


Sai kanwar su kuma autar su Mariya wacce take aure a kaduna itama mijin ta soja ne. Ya'yan ta uku duk maza. Umar, Usman, Aliyu.




Amina Maman *Asma'u* ta kasance yar aminin Kakan *Asma'u* wato Baba Haruna.


Amina su biyu Allah ya bawa mahaifin ta Malam Isah da matar sa Hafsat. Da yayan su Fatima da Amina.


Yayar ta na auren minister of Agriculture wanda suke zaune a Abuja.


Aslam shi kadai ne danta. Wanda shi kuma yayi karatu a Kasar waje fanin asibiti wato medicine kwararen likitane.


Amina da Suleiman sunyi auren soyayya ne wamda har yanzu suke shan soyayyar su.


Zuri'ar ta kasance ba mace a cikin ta illa *Asma'u Husnah*


*Asma'u Husnah* ita kadai ce jika mace ga Haruna da Isah, wannan yasa dukkan family din suke son ta da kaunar ta.


Bama Aslam da yake da son yara. Dan da aka haifi *Asma'u* sai da kyar ya bar gidan shima dan makaranta ne.


Soyayyar ta dai da ita ya tashi. Sai kuma Allah yayi *Asma'u* irin yaran nan ne masu shiga rai.


Dukkan yan uwan ta son ta suke. Yarinya ce wacce tin da aka haife ta take da kyan ta duk da baka ce amman bakin ta me kyau ne su ake kira da black beauty.


Dan *Asma'u* komai Allah ya bata. Shekarar ta biyu aka sa ta a makaranta. Inda tana da shekara biyar tana nursery two.


Allah ya bata kokari duk da karancin shekarun ta inda aka dinga mata jumping din classes.


Shekarar ta takwas ta gama primary ta tafi secondary. Tana da shekara goma sha hudu tayi candy.


A lokacin Ta fara girma dan ta fara kirgar dangi. Kyawun ta ya dada fitowa.


Tana yin candy ta samu admission inda take karantar medicine yanzu haka Asibiti zasu tafi.


Tin tana primary ta sauke alkur'ani inda yanzu haka tana da haddar sa akai.


Kuma bata daina yi ba. tana kanyi dan duk juma'a take bawa Mamin ta haddar. Karatun ta baya hana ta haddar ta. Kamar yadda duk asabar da lahadi take zuwa isilamiyya da safe.


*Asma'u* yarinya ce me fara'a da barkwanci da son jama'a. Koma abin hannun ta be rufe mata ido ba.


Akwai tarbiyya dan duk yadda mutum ya girme ta zata bashi girman sa.


Akwai ta da son zumunci. A duniya tana son Dadyn ta kamar yadda shima duk duniya bai da wacce yake so irin ta.


Kullum bata da buri sai na ganinnta kyautata masa. Yan uwa kuwa kowa ya samu abin mata ko ya burgeshi sai ace *Asma'u!*


Kowa sha'awar ta yake. Tin tana karama tayi mugun sabo da Aslam wanda in yaxo shi ke rainon ta gaba daya.


Da anyi magana zaice *Asma'u* matar sa ce. Wannan yasa Dadyn *Asma'u* shaidawa zuri'ar su cewa ya bawa Aslam *Asma'u* ko yana da rai ko be da rai *Asma'u* ta Aslam ce.


Aslam yaji dadin wannan hadin da akayi musu. haka ma Dadyn sa da Momyn sa.


Inda sauran yan uwa masu son ta kowa ya janye kudurin sa yana sanya musu albarka


Sam *Asma'u* bata san anyi ba dan a lokacin tana da karancin shekara bata san anyi ba.




*ASLAM*


Aslam saurayi ne dan shekara talatin kuma kwararen likita. Yana da katon asibitin sa wanda Mahaifin sa ya gina masa.


Aslam yaro ne me farin jini, shima akwai fara'a da son yan uwan sa.


Yan mata da yawa na son sa amman shi sam bai basu fuska.


Dan yakan ce shi yana da *Husnah* sa kowa yasan sa da *Husnah*


Daga cikin yan matan nashi ne ya hadu da preety wacce ta nace masa kuma tai wa kanta alkawarin duk daren dadewa sai ta aure shi.


Aslam kyakyawa ne na karshe. Dan sai ka zata balarabe ne. wannan ya samo asali ne saboda, kakarsa dan yar libiya ce.


Fari ne dogo jikin sa a murde dashi. Idanun sa manya, da siririn hanci sa da pink lips din sa.


Duk jikin sa gashi ne kwance luf luf. Haka nan kansa suma ce cike a cikin ta. Wacce ita take karasawa ake ce masa balarabe.


Aslam na son *Asma'u* sosai dan bai hada son ta da komai. Duk abinda zai faranta mata yana mata sai dai in yaga ba dai dai bane.


Shi yake kara daura ta akan karatun ta dan ta waya zai mata bayanin duk abinda bata gane ba.


Haka fanin addini ma duk takan tambaye shi koma meye dan ya riga da ya sabar mata.


Dan ko wankan tsarki shi ya koyamata kafin ayi musu a isilamiyya.


Haka wasu hukunce hukuncen duk yana sanar da ita dan babu kunya tana daukar sa tamkar Ya Buhari.


Aslam shi ya hana a sanar da ita maganar bashi ita da akayi duk da yaga ta girma.


Ya fadawa Dady kan a bari ya janyo hankalin ta tukunna. Dan haka bai dade da sanar da ita kudurin sa akanta ba.


Lokacin da ya tare ta ba karamin nauyi abin yayi mata ba sai daga baya da kyar ta sanar masa ta amince.


Amman duk son da yake mata in tayi masa laifi sai ya mata fada haka in koyar karatu ne ya tashi zasu ajiye batun soyayya a gefe. ya koya mata kome inda ya kamata ya koya mata.


Haka in fanin soyayya ne ba a baya ba wajen fitar da duk abinda ke zuciyar sa ya fada mata


Yasha fada mata.
"Wallahi *Husnah* duk abinda nake fada miki wallahi daga cikin zuciyata yake ba koya ko kwafar na wasu nake ba. Abinda nake ji game dake, shi nake fada miki."


Sosai yake mantar da ita duk damuwar ta da abinda yake damun ta ya faran ta mata.


*Asma'u* kanji duk duniya ba wanda ya kai ta wajen samun soyayya.












*INDABAWA*
[1/18, 14:08] Maryam S Indabawa🥰:  *LABARIN RAYUWAR*
*ASMA'U HUSNAH*




BY *MARYAM S INDABAWA*
*MANS*


🌐 *HAJWO* 🌐
*Hakuri da juriya Online writers*✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻




*Gidan Hakuri da juriya, tare da kawar da kai.*


Facebook @ Indabawa Hausa Novel
Wattpad @ Msindabawa
instagram @ Maryam S Indabawa








*31-35*




DEDICATED TO *MAMAH NAH* Allah kara miki lafiya da imani yasa ki gama lafiya.
*Ameen!*






*Manzon Allah (SAW) Yace "Kuyi sahur domin a cikin sahur akwai albarka"








Kamar ko yaushe tin asuba da ta tashi bata koma ba, bare yau da tasan suna da Sir Sabir.


Da wuri ta sauka kasa ta gama duk abinda ya kamata tayi. Ta dawo dakin ta tayi wanka ta shafe jikin ta da mai.


Durowar ta ta bude, ta tsaya kallon ta tayi minti Biyar a wajen sannan ta samu ta zaro wata bakar doguwar riga.


Hannun rigar an masa irin dinkin babbar riga da wani yadin material me multicolour (Kaloli daban daban.) Sai gaban rigar da aka masa ado da stone (duwatsu) aka jere wasu manyan jajayen stone (duwatsu) guda takwas suma.


Dago rigar tayi tana kare mata kallo, Ya Aslam ne ya siyo mata da yaje dubai. Juya ta ta kara yi, sannan ta dire akan gado.


Wani jan skin tied ta dauko sai jar bra da pant, saka su tayi a jikin ta. Sannan ta dauko rigar ta saka ta daure ta, ta ciki.


Jan hijab ta dauka wanda iya kar shi saman kirjin ta. Wani jan sandal ta dauko tasaka a kafar ta.


Sai bakar jaka da ta zuba abin da take bukata. A kan gado ta ajiye jakar da wayar ta.


Dakin Dady ta nufa, sai da yasa ta ci abinci sannan ya barta ya tafito.


Jakar ta ta dauka, sannan wayar ta.
Sakon Ya Haidar ta gani, budewa tayi tana murmushi.


" *Assalamu Alaikum*
Da fatan Baby na ta tashi lafiya, yasu Mami da Dady da Buhari. Ina fatan duk kuna lafiya.
Daman zan fada miki ne ina kan hanyar Kaduna, ina bukatar addu'ar ki, in na isa zan kira dan nasan yanzu ba kya kusa."


Murmushi tayi sannan ta nemi waje ta zauna.


Sakon fatan alheri da isa lafiya tayi masa sannan ta tura masa.


Ta jima tana tunani sannan ta tuna fa makaranta zata tafi.


Da gudu ta fita tayi dakin yayan ta. Bacci sa yake kamar kullum, gadon ta fada.


Da sauri ya mike,
"Ya Salam!'


Ya fada yana dafe kai. Murmushi ta saki,
"Ina kwana yayanah."


Harara ya wulla mata, ya mike ya shige ban daki. Zama tayi jiran sa.


Wayar ta ce tayi kara, ta dauka.
" *Asma'u* tara saura minti goma dai."


Ido ta zaro waje tana mikewa,
"Dan Allah da gaske,"


"Duba agogo ki gani."
"Innalillahi wainna illahir rajiun. Gani nan gani nan."


Ta fada tana nufar kofar ban dakin.
"Yayah! Yayah!"


Banza yayi mata. Kuka ta fashe masa dashi.
"Yayah!"


Ta fada cikin kukan. Shiru ya kara yi mata. Ya cigaba da cuda jikin sa.


Sai da ya gama sannan ya dauro shawul ya fito. Tana jikin kofar a tsaye.


Kallon ta yayi ya dauke kai ya fara goge jikin sa. Yana zama a gaban mudubi.


Karasawa wajen sa tayi da sauri, ta durkusa akan gwiwo yin ta tace,
"Yaya da Allah ka zo kakai ni makaranta na makara."


Mai ya cigaba da shafawa. Kuka ta saka masa sosai.


"Rufe min baki."
ya fada fuskar sa a bace.


"To Yaya dan Allah ka kaini makaranta."
ta fada tana hade hannun ta gu daya.


"Ina Baba da yake kai ki makaranta."


tace,
"Yaya na makara kuma Baba makara zamu yi dan baya gudu wallahi."


"Ni ba inda zan kai ki."
Kuka ta kuma saka masa.


"To ya isa tashi bari nasa kaya. Toh ta fada tana fita, dakin Mami ta ttafi dan mata sallama.


Kallo Mami ta bita dashi ganin idon ta yayi ja.
"Me yasami idon ki, kuma daman baki tafi ba."


Asma'u ta ce,
"Yaya ne yasa ni kuka."


Mami ta ce,
"Akan me?"


Tace,
"Na makara yaki yazo ya kai ni."
"Kin je tsokana har kika makara ko."


"A'ah!"
"Yanzu yana

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads