Header Ads
Showing 27001 words to 30000 words out of 152002 words

Chapter 10 - AMATULMALEEK COMPLETED BY Mamuhugee.txt

Ads the beginning of article before Image

11 Jun 2024

856

Ads at the middle of Article

din kowa ya nufi bedroom dinsa Naufal kuwa Yana komawa fita yaso yi Amma rashin layin dazaiyi waya ya Sakasa fasawa dole ya shige da wuri.




Washe gari da safe kusan kowa fita yakeyi masu zuwa school da masu zuwa aiki Dan haka daga Amatu sai mamah da masu aikine a gidan yawanci da safe sai yanzu tinda mum Aisha sun dawo.


Amatu ce ta shiryawa mum Aisha da Naufal breakfast ta Jere musu a palon mum Aisha din sbd abincin dare ne kawai kusan Yan gidan sukeci gaba Daya atare sbd ASH da dare kawai yake zaunawa acikinsu cin abinci sai breakfast Wanda shikuma daga shi sai iya yayansa yake yinsa wannan shine qaidarsa sbd Yana son time dinsa na safe da yayansa kawai.




Bayan tagama shirya musu abincin Naufal ne ya shigo palon lokacin mum Aisha din Bata fitoba,


Sanye yake da designers qananun kaya blue Bai Wani Kalli Amatun ba Dan gargadi da iyakar da mum tai masa da duk wata macen Dake gidan Dan haka Koda ta gaidasa amsawa kawai yayi Yana zaunawa sama sama yayi breakfast din ya fice Yana ce mata idan mum ta fito ta sanar mata ya fita.


Ok" kawai ta furta masa batareda itama ta juyo ta kallesa ba daga gyaran palon datakeyi Hakan ya Sakasa dakatawa ya juyo Yana qure kallansa akanta sbd mamakin basarwanta da rashin basa mahimmanci.


Fararen yatsun hannuwanta masu tsayi da kyau ya zubawa hannu tana rufe zip din throw pillow data Dan Bude ta gyara na kujerun palon.


Gangarawa yayi da idanuwansa kan wuyanta da Shima fatarsa take fara tas kaman 'yar Hutu,
Akan kirjinta ya dawo da idanuwansa Ya kalla yanajin zuciyarsa na harbawa da qarfi.


Motsin juyowarta ya sakashi Maida idanuwansa kan kyakkyawar fuskarta yana juyawa yabar palon zuciyarsa na shiga wasi wasi.


Batasan duk abinda ya tsaya yayi din ba Dan haka aiknta taci gaba da yi harta gama mum Bata fito ba dan haka ta tattara ta ficewarta.




Naufal driver yasa ya fita dashi a Daya daga cikin manyan motacin gidan Dake haraba,
Kai tsaye layuka ya Siya manya masu numbers me kyau kafin suka wuce Kai tsaye gidan dayake buqatan zuwa na Amininsa zayyan acan driver ya ajesa ya wuce.


Dayake suna tareda da zayyan din acan Spain kawai dai zayyan din ya rigasa dawowa Dan haka Yana shiga suka cafke Babu Bata lokaci yasa zayyan ya samo masa lafiyayyar mace anan gidan ya wuni Yana hutawarsa tareda sauke nauyin dayake Jin tin kwanaki Yana cikinsa Dan tinda mum dinsa ta tafi gidansa ya rage Neman mata sosai sbd fadanta da zamanta a gidansa shiyasama kafin su dawo yafi sati biyu rabonsa da mace Dan haka a tsananin matse yake.




Ba qaramin dadi yaji ba a wuninsa gidan zayyan Dan haka sai dare ya koma gida Kuma Yana komawa shigewa yayi kawai Dan Baya buqatan komai bayan bacci yanzu.


Washe gari Bai fita ba sai Rana ya dauki mota da kansa ya fita Kai tsaye Wani guri suka nufa da zayyan Wanda ya kusan kashesa da dadi sbd mata ne masu aji manyan mata 'yayan masu kudi wasu Kuma manyan Yara Dan haka kusan budurwa hudu yayi lokaci Daya Kuma a ranar ya same yanda yakeso sosai ya huta qarshe a gidan zayyan suka kwana Wanda Shima ba anan yake zauneba gidan iyayensa yake zama wannan gidan hutawa ne kawai.




Washe gari tareda mum dinsa yayi breakfast batareda tasan baa gida ya kwana ba Dan kuwa sosai ya iya takunsa.


Ahankali ya goge sosai da Yan matan dayayi sabbi harya fara gajiya dasu yafara sauyawa Dan dama Babu Wanda maganar so take acikinsu kawai Jin dadine sai hutawa.


Ta bangare daya Kuma kwata kwata ya Dena kwana gidan Kuma Babu Wanda ya sani bayan securities da Babu abinda zasuce,


Acan Spain idan kanada budurwa baka iya kula wata macen sai ranarda kukai break up Amma anan yanzu mata kusan Shida ne dashi lokaci Daya Kuma Babu wacce Baya biyan buqatansa da ita duk da Basu saniba Amma dai sun San bazai iya zama a guri Daya ba.




Idan akace Naufal Neman mata yake kaman an ragewa lamarinsa girma ne Dan kuwa tamkar bunsuru haka yake da mata,
Sam baitaba gajiya da Neman mata ba,Baya iya kwana Bada mace ba,Baya iya wuni Bai Hadu da mace ba Sam Kwata kwata dai bazai iya rayuwa batareda yana samun mace ba.
Dawowansa Nigeria Babu abinda ta qara masa sai lalacewa da tabarbarewa sbd a yanzu Kam matan ma wasu sune suke nemansa sbd kwadayi da son abin duniya tinda kallan babban 'dan the grt ASH TALBA ake masa Wanda a yanxu yake matsayin Dan takarar governor na jaharsu duk da ASH din Sam Baya shaawan siyasan shiyasa ma yaqi komawa state din yayi zamansa Abuja Dan Baya buqata manya ne suke son tsayar dashi.


Duk Nisa da lamarin Naufal yayi mum Aisha Bata ganeba sosai Dan haka taci gaba da cusashi agurin ASH musamman yanzu da lamura suka dauki zafi a harkar siyasar sosai gidansu ya koma Saida aka qara masa securities da jamian tsaro sbd komai yanata sake tabbata.


Suna sosai Naufal Talba yayi sbd rayuwar Dayake zubawa da Yan mata yayan manya da yanda yake sakewa Yan mata kudi kaman baisan zafinsu ba.
Abokansa biyu ne zayyan Mande da Fahad Sadam Kuma Suma dukansu yayan manyan ne da bayan su kashe kudi basusan wahalarsu ba sai mata da su kadai abinda suke buqata.




AmatulMaleek kuwa lokacinda labarin cigaba da karatunta ya sameta tayi farin ciki me tsananin gaske tareda Jin girman kaunar haydar a ranta ta Qaru Husnah ma ta tayata murna Dan haka suka maamah da kanta ta tafi da Amatu gurin ASH suyi masa godiya.


Da daddare bayan sun gama dinner kowa ya watse Haydar ne yaje ya sanar da Dad din Maamah na son ganinsa,
Baya yiwa maamah shamaki da kansa kamar yanda ko mum Aisha datake jininsa idan zata gansa saita kirasa a waya Amma maamah koyaushe tace tanason ganinsa Yana Bata wannan damar sbd matsayinta daban daban yake a gurinsa sbd yayansa da matarsa dayasan son datakewa Asmau hakama yayansa a yanzu basuda Wanda suke so a duniyarsu kamarta idan ya cire kansa.


Haydar dinne a gaba sai maamah sai Kuma AmatulMaleek din datake bayanta suka shigo a natse tareda sallama qamshinsa Daya shiga hancinsu tareda sanyi ya sakasu sake shiga nutsuwansu Dan kuwa akwai Wanda qamshinsa kawai zakaji kasan ya cancanci respect,to kamshin ASH TALBA kusan Hakan ne kanajinsa zakasan ba qaramin mutum zaka ganiba.


Idanuwansa masu haske akansu suka shigo batareda ya lura da AmatulMaleek Dake bayan Maamah ba Saida Haydar ya ambaci sunanta tukuna Dad din ya lura da akwai mutum bayan Asmau.


Kujera ya nunawa Maamah din yace ta zauna ta zauna sbd akwai sakewa ba laifi tsakaninta dashi, AmatulMaleek kuwa aqasa ta zauna gefen Maamah din tareda Dan dagowa cikin nutsuwa ta gaidashi muryarta a natse ba rawan jiki ko sanyin murya kawai dai asalin nutsuwanta.


Kallo daya yayi mata ya fahimci itace AmatulMaleek 'din Asmau ya amsa da kulawa tareda mayar da hankalinsa kan maamah suna sake gaisawa tayi masa godiya sosai Akan karatun Amatu itama Amatun cikin nutsuwa ta miqa tata godiyar.


Tinda suka shigo Amatu Bata iya dagowa ta Kalli fuskarsa ba sbd Wani irin kwarjini da haiba ne yake cika duk inda ASH TALBA yake musamman ita da Bata Saba ganinsa a zahiri ba sedai a waya ko hoto uwa Uba yanzu da ake kirarinsa da sunan governor guda.


Haydar kuwa tinda suka shigo shidai nasa idanuwan akan Amatu suke har suka gama suka fice Ya bisu Yana tsokanarta akan zai fadawa Dad din ita zai aura idan ya tashi aure.


Harararsa Tayi tana murmushi Dan batasan ma me zata ce masa ba Dan takaici.
##MAMUH#




*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070


Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#


AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar


17
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs💯🔥👍
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku💯👍*


MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI'IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER


08142800199
07068558096




**********
Fara karatun AmatulMaleek ya Sakata qara gogewa a cikin wayewa duk daman Bata cikin duhun Kai a wanke take Dan duk wahalar dasuke a cikin gidan to basa cikin wahalar rayuwar tinda me kyau suke ci Kuma su sha me kyau hakama su kwanta me kyau su Saka me kyau Dan itama kusan komai sabo take sakawa yanzu da Haydar ya Saka Dad dinsu yayi noticing dinta a suna Banda kamanni Dan haka kamar yanda a Baya ake siyawa Abdul duk abinda aka siyawa Haydar to kusan itama hakanne yanzu komai nata ya sauya tana samun komai yanda ya kamata.


Naufal kuwa tini yafara aiki a matsayin director na kamfanin kasuwancin ASH empire Dan haka rayuwa taqara yi masa yanda yakeso duk ba wannan matsayin sukaso ba daga shi har mum Aisha Amma Kuma Basu cire tsammanin kaiwa inda sukesoba dan haka mum Aisha ta dage sosai tana sake cusa Naufal a gun ASH.


Gaba dayansu yaran gidan baa barinsu Jan mota da kansu bisa ga umarnin ASH Dan haka dukkaninsu drivers ne suke kaisu makaranta tareda security Daya hakama duk Wanda ya gama cikinsu driver yake kira yazo ya daukesa har Amatu
Haydar da Abdul kuwa dayake dama yanzu ne suke Shirin rubutawa exam din gama secondary school tare ake kaisu a daukosu tare.


Barnar Naufal tayi yawan da tini mutane suka fara sanin halayyar tasa Dan haka sai Hakan nason taba mutuncin Ash ga wainda suka fara sani batareda shi yasaniba.


Tafiye tafiye sosai Naufal keyi sosai Dan yafi sakewa idan ya bar garin yaje can yayo sharholiyarsa y dawo.


Ana Hakan matan da suka zubar da cikinsa a jikinsu yafi nawa Dan haka sai zancen yafara bayyana ga mum Aisha wadda ta kamasa dumu dumu sakamakon cikin wata yarinyarsa da aka zubar ta rasa ranta sanadin Hakan Dan haka tini zancen ya fita aka fara sharia saiga zance a duniya yafara yawo 'yan jarida Dake Jira tini aka yada labarin.


Tashin hankalin da baa Saka masa rana ba mum Aisha tashiga gashi Shima Ash Talba din dole sai ya fito yayi magana akan zancen da Yan jarida tinda a kotu ake.


Su Husnah kuwa mamaki sosai suka shiga Amatu Kuma Daman Bata shiga abinda Bai dametaba sosai kawai dai damuwarsu shigowar bacin sunan Ash da ake Neman yi Dan haka suka Dan shiga damuwa Maamah kuw sosai tashiga damuwa Dan Naufal din mutuminta ne Yana yinta ba laifi.


Cikin baqin cikin data samu kanta mata adadi mum Aisha ta samu case din ya mutu Wanda aka tabbatarda ba Naufal ne yake muamala da yarinyar ba Maza da yawa ne Kuma daga karshe ma dai ba wannan ne cikin farko data zubarba Kuma Babu Wanda ya tilastata zubarwa itace tayi Kuma Hakan yaxo da matsala har yayi ajalinta.


Mutuwar case din ya Saka familyn gidan samun nutsuwa da hamdala Amma ASH TALBA ya dakatar dashi daga fita aiki gaba Daya sbd hukuntasa.


Wannan hukuncin baiwa mum Aisha da dadi ba Dan haka ta daga hankalinta sosai,zagi da fada Babu ranar da Bata wuni sai a kwana Bata yiwa Naufal daga qarshe ma tayi rantsuwar bazai qara fita mansion din ba.


****Abu Daya da mum Aisha Bata sani ba shine hanasa fita shine ya bullo sabuwar matsalar cikin Mansion din,
Bai Dena fitaba sbd Yana ficewa yaje yayi abinda zaiyi ya dawo batareda ansan ya fita din ba Dan haka Neman matan nasa ya rage tinda Baya samun isashen time sosai a waje,


Ta bangare daya rashin samun yanda yakeso a aynzu yasa idanuwansa suka dawo Kan 'yan matan gidan masu aiki yafara farautarsu Daya Baya Daya yana lalabewa duk da qyamarsu yakeyi Amma dai tinda Yana samun yanda yakeso sai yana manejinsu hakanan.


A qanqanin lokaci kusan Yan matan biyu masu aiki ya Maidasu kaman matansa Babu ranar da baya kusantarsu idan yayi yau da wannan gobe da dayar zeyi.


*****AmatulMaleek datafi duk matan dasuke gidan kyau Tim daga masu gidan har masu aiki itace maqale a zuciyarsa da idanuwansa,
Kyakkyawa ce hakama Mai aji da kamewa ce Sam saikayi sati nawa a cikin gidan batareda ka Sakata a idanuwanka ba Dan Babu abinda yake fiddota sai ayyukan da baa rasaba tinda karatu yanzu Baya barinta ma ayyuka tini maamah ta dauke mata iyakacinta karatu da hutawa sai ranakun datake gida take Saka hannu a wasu ayyukan gidan.


Ta bangare daya siyasan ASH TALBA ya dauko zafi gadan gadan sbd lokacin zabe Daya gabato sai gidan yakoma tsaronsa yanata qara ninkuwa Dan Babu abinda Ash ya hada da tsaro tareda kariyar familynsa.


Husnah Bata Nan tana porthcrt gurin Hutu tareda Haydar gun dangin mum dinsu wadda daga can kafin su dawo zasuje dubota.


Abdulhameed ma wannan Karan ya sake zuwa kauye Shima ya dubo dangin nasu mahaifin a karo na uku Dan haka daga AmatulMaleek sai maamah sai su mum Aisha.


Kwadayinsa Naufal ya fara bayyanarwa akan Amatu Dan haka maamah tafara shiga fargaba da shakku Amma dai Bata nuna komaiba ganin itama Amatun tafara shiga taka tsantsan dashi.


Mum dinsa ganin wadda yafara kaiwa hari baqin cikinta ya tsananta ta kallesa a lokacinda suke zaune palonta tace


"Wane irin Dabba kakeson zama ne Naufal akan mata?
Wace masifa da balai ne wannan ni Aishatu take bibiyata,
Nayi Dana sanin dawowarka ma Dana sani nabarka acan qasar Kayita abinda kaga dama idan yaso ranarda ASH yasan abinda kakeyi Saiya dakatar da duka kudinsa da aka Sakar Maka kana wannan ta'addancin alokacinne zaka gane me nake nufi daka nutsu mu samu gurin zama da gurbi a wannan dukiyar......


Magana ya Bude Baki zeyi ta katsesa cikin baqin ciki da takaici tana cewa


"Ka fitarda macen aure kawai kayi aure tinda bazaka iya kame kanka ba kayo mummunan gado harka zarta,
To wlh Bazan iyaba,idan ka lalatamun komai to tabbas saikaga yanda baka so Dan wlh Nima dubu Daya bazaka sake samu ta hanyataba tinda zuciyarka ta Dade da mutuwa a gurin mata."


"AmatulMaleek kuwa da wuri da gaggawa kayi saurin dauke idanuwanka akanta Dan duk kaje ka lalata musu ita to ko ni wlh Kila qarshen zamana a karkashin ASH yazo bare Kai Dan akan Asmau zai iya aikamu inda mukaqi jinin zuwa wato inda muka fito Dan haka Maza Maza ka cire kwadayinka akanta tinda ka riga ka gama lalata Yan aikin gidan Nan tas,
Kai ko qyama bakaji ne?
Bazaka iya hakuri ba bayan kwana bibbiyu kaje ka samu na wajen ba ka biyasu ka sauke buqatarka Amma ace Yan aiki ma nema kake,mtswwee.


Zafi zuciyarta keyi kaman zata fashe Dan tana cikin baqin cikin wannan muguwar kaddarar ta hada jini da hamis Da Danta ya dauko halinsa.


Fadanta da zafinta koyaushe Sosa ran Naufal sukeyi Shima sbd idan ta fada kalamanta Sam Babu alkhairi a cikinsu koyaushe Dan haka Bai iya cewa komaiba Shima ya miqe yabar palon Dan kuwa ayanzu yake Jin AmatulMaleek din a ransa ko aurenta ze iya yi Dan biyan buqatansa idanma har be samu yanda yakeso ba kenan
Idan Kuma mum din ta matsa akan maganar auren Amatun zai aura kawai kowana ya huta.


AmatulMaleek data gaji da kadaici sai kawai ta fara fita wasu lokutan zuwa guraren Shan iska musamman tinda Hutu sukeyi gashi ba kowa.


Ana cikin Hakan Barr Faisal turaki ya ganta a cikin gidan zuciyarsa ta kamu da kaunarta alokaci Daya duk da ya jima sosai da familyn TALBAs din Amma Bai taba ganinta sbd shine lawyer din Madame Abeeda Kuma shine babban 'dan Wani yayanta Dake porthcrt da maman babansa da maman Abeeda uwa daya Uba Daya suke Dan haka dadynsa yayan madame Abeeda ne,


A UK sukai zama taredasu Abeeda har suka rigasa dawowa Nigeria Amma Shima ya jima da dawowa kawai dai Baya zuwa Nan dinne sbd madame Abeedan Bata Nan hakama da Husnah kawai yake communicating Shima sbd Husnah dinne tafi nemansa koda yaushe har shaquwansu yayi qarfi sosai da sosai,


A bangaren Husnah Faisal turaki ba iya Dan uwanta take kallansa ba,
So ne take masa me tsananin gasken da kusan ko familyn mum Abeedan sun sani,so ne me tsananin gaske gaba Daya ma she's obsessed,
Bata iya boye sonsa duk da tsakaninsa da ita baitaba fada mata so hakama yasan yanda take tsananin sonsa sedai bayajin zai iya takura kansa ya aureta batareda yana sontaba,Hakan zai cutatar da ita yakuma cutatar dashi Amma Sam ta kasa gane Hakan shikuwa a matsayinsa na dan Boko sosai da sanin YANCI ya gama ratsashi bayajin zai iya auren damuwa da takura tareda cutatar da juna Dan kuwa Yanda yake Sonta na tsakani da Allah har zuciyarsa ta Yan uwanta bayason ya aureta su lalata rayuwarsu gaba Daya ya zabi tsayawa kan raayinsa duk maganar da iyayensu da Yan uwansa keyi ya tsaya akan Hakan.




Ayau Kuma Daya zo duk da Husnah batanan yazo ne sbd aiki Daya dawo dashi Abuja da zama Dan haka yashigo su gaisa dasu mum Aisha harma da Naufal dayake mutuminsa.


Sosai yayi mamakin ganin AmatulMaleek wadda yake Jin sunan a bakin Husnah tin shekaru...


AmatulMaleek dinne tayi serving nasa duk Wani abin motsa Baki tareda gaidasa cikin nutsuwa ta juya ta fice daga babban palon gidan Takoma daki Dan dama fita zatayi zata wankin Kai.


Mum Aisha da lokaci Daya taso fahimtar Barr Faisal akan kallan Dayabi AmatulMaleek dashi take taji Babu ma abinda zata so a yanzu Daya wuce barr din ya aure AmatulMaleek din tabar gidan kafin Naufal ya janyo musu abinda zai riguzasu akan kwadayinsa da Amatun Dan tasan tinda ya qwallafa Rai akanta sai Allah idan zai hadiye wannan tsinannen kwanadayin nasa Dan haka zama ta gyara tafara yin bayanin waye AmatulMaleek din a gidan tareda yabon halayenta.
#MAMUH#






*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070
Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#




AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar




18
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads