Header Ads
Showing 6001 words to 9000 words out of 152002 words

Chapter 3 - AMATULMALEEK COMPLETED BY Mamuhugee.txt

Ads the beginning of article before Image

11 Jun 2024

855

Ads at the middle of Article

daukanta ya kira shine ma'aikacin tashar ya kawosa har inda Maamah take zaune kaman almajira ita da yaranta yace "gatanan"


Kallanta drivern yayi dakyau kafin ya dawo da kallansa kan mutumin Dake nuna masa ita Yana wasi wasin idan wannan din ce akace ya dauka yakai gidan ASH TALBA sbd ko masu aikin gidan bazasu dauki wannan aikin gidajensu ba bare gidan ASH din da kansa.


Lura da fahimtar tinanin dayake gudana a zuciyar drivern yasaka Dan tashar sake basa tabbacin ita din dai ce,daga kauye ta fito shiyasa.


Kasa cewa komai driver yayi sai kawai ya dauki jakar kayanta ya Bude bayan black range Rover Din dayaxo da ita yana sake kallansu maamah din cikin danne mamakinsa da Dan shakkar idan ba kuskuren daukansu zaiyiba.


Maamah dasu AmatulMaleek ma da basusan inda kansu yake ba rakubewa sukai tareda dunqulewa guri Daya bayan motar Babu me iya motsawa sukai shiru Maamah din najin zuciyarta na Dan sake sanyi da taimakon gaggawar dasu AmatulMaleek din zasu samu Dan kuwa data koma dasu a wannan halin ba lallai ta samu Isa gida da duka yayanta biyu ba Kila ta rasa ran Daya a hanya kafin su Isa,sai gashi Allah ya dubi maraicinsu ya kawo sassauci a lamarinsu ta samun Kiran Abeeda.


Tafiya me Dan tsayi sukai kafin suka Isa,
Koda suka Isa tini sanyin ac yakusan sankarar dasu Abdulhameed Duk da sun Saba da sanyin Allah Amma wannan din yayi musu karfi da yawa sosai.




Babban makeken luxury gate din gidan ASH TALBA aka wangalewa motar gidan dasuke cikinta suka shige harabar gidan datake da Wani irin girma da tsari irin na gidajen turai da Kuma masu abin duniyar qasa da qasa,


Motacin Dake harabar sunkai takwas koma fiye,
Motoci ne wainda babu me karamin kudin da zaka iya lissafawa bare manyan,
Dukkaninsu baqaqe ne sai farare guda biyu aciki sai Ash Daya.


Parking yayi daga gefen da ake ajiye duka motacin gidan Dana mutan gidan Banda na ASH dake gefensu daban sbd ta inda yake fitowa daga sashensa da Babu Wanda yake bin kofar idan ba shi ba Dan haka ta Nan yake fitowa ya shige motacinsa yabar gidan batareda ma kana gidanba bare kasan fitarsa.




Tinda Sharif driver yayi parking ya fito yake Dan Jin zuciyarsa na sake shiga shakku idan baiyi kuskuren dauko Wanda Basu aka aikesa daukowaba.


Bude musu motar yayi Yana kallansu yace maamah tafara fitowa tukuna idan ya tabbatarda sune aka sakasa daukowa saisu shiga.


Wayarsa ya fitar cikin nutsuwa ya Nemo numbern Madame din ya Saka kira.


Saida yayi mata kira biyu kafin ta daga Kai tsaye ya sake gaisheta Yana cewa


"Hajiya ga baqin na dauko Amma bansaniba ko na samu kuskuren daukowa wainda Basu ba....


Katsesa Abeeda tayi da cewa


"Bata wayar naji"


Da sauri ya miqawa Maamah wayar Yana cewa "yi magana taji"


Karban wayar maamah tayi tana sallama Abeeda ta kashe wayar tareda miqewa daga zaunen datake ciki lafiyayyan bedroom dinta sanyeda jallabiya ash da mayafi me Dan girma na sallanta ta ajiye wayarta tana nufar kofar barin bedroom din sanyeda slippers masu tsananin laushi da tsadan kudinsu zasu ciyar da maamah din da yayanta na sati uku koma fiye.


Tinda ta tinkaro babban palonta ta nufo kofa ma'aikatan Dake gyaran palon suka ringa gaisheta cikin tsananin girmamawa sun Dan sauke Kai sbd Koma me zai fitarda Madame din harabar gidan a daidai wannan time din me tsananin mahimmanci ne.


Sharif dayaji madame ta kashe wayarta Babu amsar komai Shan jinin jikinsa yayi sbd ta tabbata kenan yayi kuskuren dauko wainnan kauyawan dajin.


Kallan maamah yayi cikin sauri Yana cewa


"Kinga maza shiga na mayar daku inda na daukoku kafin na Rasa aikina"


Juyawa mota maamah tayi tana kokarin komawa batareda tace masa komaiba Dan itama batasan dalilin kashe wayar Abeedan ba.


Cikin fada da daga murya yaci gaba da yi mata sauri sauri Yana cewa


"Wai bazakiyi sauri ba muje?
Kema kinyi gangancin biyoni bayan kinsan Babu ta inda kukeda arzikin Azo daukanku da mota irin wannan Amma haka kawai kika biyoni gashi Kuma Kinga irin gidan da akazo bazaki Bude Baki kice bakuda Hadi da irin wanna guraren"


Shiga motar Maamah ke kokarin saiga fitowar Abeeda harabar gidan tini ta dagakata daga shiga motar tana tsayuwa a inda take gabobin jikinta na Neman saki idanuwanta dasukai Dan ja suna tsayuwa a kan Abeeda wadda itama nata idanuwan akan Maamah din suke tana kallan Wani irin mugun mummunan yanayin da Asmaunta ke ciki kamar wadda Tayo gudun hijira.


Suturar jikinta ta kalla taji hankalinta na mummunan tashi kafin ta tsayar da idanuwanta akan fuskar Asmaun da sauran kadan takoma skeleton sbd rama da bushewa.


Maamah kasa kurar da nata kallan tayi kan Asmau sbd alkunya da muzantar dataji tanayi agaban Abeedan sbd yanayin datazo gidan dashi kamar almajirar data debo tafiyar qafa.


Qasa tayi da kanta lokacinda Abeeda ta tinkarota Kai tsaye jiki a tsananin mace da baqin cikin ganinta ahakan tana isowa hannunta take kokarin kamowa tana ambatar sunanta muryarta na rawa sosai.


Kasa bari maamah tayi Abeeda din ta a kamata sbd jikinta Babu inda yake da tsafta ita kuwa tamkar wata tauraruwar datafi taurari take komai nata na musamman ne sbd Jin dadi,Hutu da daular da Allah yayisu acikinta.


Sharif na ganin Hakan yasan ba kuskuren ne dai aka samu ba Dan haka a Jere ya Sako ajiyar zuciya Yana Bude mota da sauri yahau kokarin kamo Abdulhameed sbd AmatulMaleek bazata dauku garesa ba tinda ta fara zama yar budurwa.


Yanda Sharif ya dauko Abdulhameed kamar matacce ya Saka gaban Abeeda mummunan faduwa tana kallan Motar cikin tashin hankali tace


"Meya samesa?
Ina AmatulMaleek?
Meya samesu?"


Jiki na rawa murya na sauri sharif yace


"Ahaka aka daukosu daga Tasha inaga basuda lafiya sosai sunyi Nisa musamman ita macen ko numfashi ma batayi...""


Bai qarasaba Abeeda ta katsesa da cewa


"What??


Kallan maamah tayi tana Isa motar jikinta na rawa takai hannunta kan AmatulMaleek Dake kwance ba Rai ta janyota kafin tayi Wani yunkuri tini sharif ya kira masu aikin gidan mata su biyu suka iso gurin Dan daukan AmatulMaleek Dan baiyi tinanin Madame din tasu zata iya taba mutanenba.


AMATULMALEEK
Regular 700
Vip 2k
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070


##MAMUH#
#LOVE
#ROMANCE
#INSIDELIFE
#ASH TALBA
#NAUFAL
#MADAME
#ABOKIYAR NISHADI
#MEERAH HERBS


Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#




AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar


5
Abeedan bazata iya daukanta ba Dan haka dole masu aikin ne suka dauki AmatulMaleek din maamah Kuma tana dauke da jakarsu suka dunguma zuwa ciki.


Kai tsaye sashen masu aiki aka nufa dasu dayake akwai daki na musamman acan aka Bade musu Daya aka kwantar da AmatulMaleek din gefen Abdulhameed Daya farfado shi Amma baida karfin iya motsawa sai tsoro Mai karfin gaske Daya shigesa ganin inda suke kaman baa duniya ba duk da baisan yanda aljanna take ba da lahirar.


Abeeda da kanta ta fice tana bawa masu aikin umarnin su fara yaran kafin a kirawo likita yazo ya dubasu cikin gaggawa.


Abdulhameed suka fara yiwa wanka fes suka dirji uwar dauda da kurar jikinsa kafin suka fito dashi.


AmatulMaleek kuwa kasa barinsu maamah tayi da kanta ta daure ta wanketa tsaf ta fito da ita.
Kaya aka Basu suka Saka Wanda AmatulMaleek din take aka karbo kayan Husnah Talba daga bangaren iyayen gidan aka Bata maamah ta Saka mata hakama Abdulhameed kayan haidar aka Saka masa take suka Dan yi kyan Gani Babu Bata lokaci likita tazo ta fara dubasu Duk da shi Abdulhameed ana basa tea me tsananin kaurin gaske ya shanye katan Kofi yafara Dan samun kuzari.


AmatulMaleek kuwa ana Bata tea din haka ta amayosa Dan haka dole aka sake gyarata kafin likitar tazo.


Ita kanta maamah ta tsaftace kanta cikin 'yar suturar da aka Bata Dan baayi qasa a gwiwar Kai kayansu store ba aka ajiye sbd Babu Wani sutirar arziki acikinsa.


Da farko sosai hankalin Abeeda ya tashi da ciwon na yaran Dan Bata dauka yunwa da wahala ne tareda iska Dasuka wuni suna sha a hanya ba tin asuba ya jijjigasu gaba Daya.


Likita Abdulhameed ta yara dubawa dakyau ya tabbatarda gajiya ce da azabar yunwa a tareda shi Dan haka ruwa kawai ya daura masa Dan karfinsa Daya tafi ya Dawo.


AmatulMaleek kuwa bayan yunwa iskane ya shigeta sosai Wanda Bata Saba sha ba sbd basa zuwa koina koyaushe suna kauye cikin gida a zaune,Se yunwa da wahalar hanya ta doguwar tafiyar da tinda tayi wayo Bata taba ba.


Itama ruwan ya daura mata tareda allura kafin ya tafi yace basa buqatan magani da sun samu hutawa sosai sukaci abinci wadatacce zasu warware Inshallah.


Sai bayan tafiyar likita Maamah ta iya dagowa ta Kalli Abeeda datafi nuna damuwarta akan ciwon nasu sbd Bata taba ganinsu a wannan halinba bayan ciwo ga wahalalliyar yunwa Nan a tareda su bayyane a jikinsu.


Kan maamah ta dawo da kallanta tareda qurawa Maamah din idanuwanta tana sake kallan qashin wuyanta Da kamar turosa Akai waje duk koina jikinta qasusuwanta a bayyane,
Jin tayi hankalinta ya ninka tashi tareda shiga tsoro Amma tayi kokarin dannewa tareda boyewa sbd kada ta muzanta Maamah din da kallanta dakuma mamakin.


Fitowa tayi maamah na biyeda ita kaman yanda ta umarta suka nufi sashenta sai alokacin maamah ta Dan saki numfashi sbd sanyin AC Daya gama kame koina na sashen da Wani irin kamshi na gidan kudi da basai anfada Maka ma.


A palonta na farko ta zauna ahankali kan kujera tana nunawa Maamah gurin zama tareda sakawa aka kira me aikinta ta kusanta.


Khaltume na zuwa ta Dan tsaya daga gefen Abeedan cikin girmamawa tace gata tazo.


Abeeda Dake kokarin dauke kallanta daga Maamah sbd kallan yafara damunta da alama ta Dan juyo ta kalli khaltumen Kai tsaye tace a hadawa Maamah abinci a dining.


Dawo da kallanta tai kan Maamah din cikin yar kulawa tace


"Asmau meye kikeson ci??
Me zaa dafa Miki kici a cikin gaggawa?


Dan dagowa Maamah tayi tana kokarin Hana damuwa da sanyinta bayyana ta saki Dan numfashi tareda yaqe ta Bude Baki tace


"Kowanne irin abincin ma yayi basai sun wahala ba"


Juyawa khaltume tayi da kallanta kan Madame dinsu tana jiran umarnin abinda zaayi din.


Abeeda Bata juyoba ta kalleta tace


"Kije koma me Akai a ajiye mata ta taso taci batareda Bata lokaci ba."


Murmushin yaqe Maamah ta sauke tana dagowa ta zubawa Abeedan Idanuwanta cikin kulawa da ganin yanda itama Abeedan ta fada sosai tayi Wani irin haske kamar na Wanda beda jini ko kadan.


Numfashi ta sauke kafin ta Bude Baki cikin kulawa tace


"Abeeda Yaya muka sameku?
Yaya Husnah da Haydar?
Duk suna lafiya?
Yaya labarin su hajiyar porthcrt?kowa lafiya dai ko?


Numfashi Abeeda ta sauke kawai fuskar Asmau take kalla wadda magana takeyi Amma bakin dayake bushe da wuyanta ne suke kashe mata jiki Dan haka Bata iya Bude Baki sosaiba ta gyada Kai ahankali cikin sanyi tace


"Kowa lafiyansa kalau,
Asmau meya sameku haka keda yaran kuka koma kamar wainda ke rufe a kejin wahala?
Meyake faruwa ne?
Kuma cikin qunci da wahala ne?
Bakwa samun abinci ne?
Andena Kai Miki abincin da ASH yasa aringa kaiwa duk wata ne?


Shiru Maamah tayi tareda Dan sake sakin murmushin yaqe tana cewa


"Ana kaiwa kinsan gidan taro dakuma rayuwar kauye baka samun abu ka ringa cinyewa Kai Daya Se iyalinka,Idan ankai ana bawa kowa ya Dan Saka albarka,Allah dai yaci gaba da biyanki keda Mijinki har karshen rayuwarku,ai Kunata kokari....


Katseta Abeeda tayi da cewa


"Asmau bayan yunwa wane masifar kuke ciki haka da kika koma kaman wadda take kwance tana jinya??
Asmau Kin ganki kuwa?
Kinga 'yayanki kuwa?


Sake sauke numfashi maamah tayi tana Dan son Hana kanta da zuciyarta bayyanarda abinda zai damar da Abeedan Dan haka ta sauya tambayar ta Abeeda da jefa mata tata tambayar idanuwanta akan Abeedan tana cewa


"Yaya maigida ASH TALBA? Yana lafiya?
Yakuma akaji da hakurin rashin Alhajin??


Numfashi itama Abeedan ta saki sbd sanin zurfin ciki da iya shanye damuwa da duk abinda ya wuce na Asmau Dan haka tasan ba komai zata fada mata ba ayanzu din sai kawai tayi Baya ahankali ta gyara zamanta a lallausan Luxury kujeran Dake palon nata tana cewa


"ASH lafiyansa kalau yau da safen Nan yayi tafiya Dan Daman rasuwar Nan ta tsayar dashi,
Alhaji kuwa lokacin yayi Se fatan Allah yayi masa Rahama da samun Jin qansa.


Shiru sukai dukkaninsu kowanne zuciyarsa a sanyaye Banda Abeeda Dake jin bazata iya fadawa Asmaun damuwarta datai niyaba a duk randa suka Hadu sbd Bata taba tinanin ganinta a wannan mummunan halin itada yayantaba kamar wasu gawar dataqi Rami.




Ita Kuma maamah Jin tayi itama jikinta na sanyi tareda Jin nauyin fadawa Abeedan damuwarta sbd kada ta damu sosai gashi da alama Sam rayuwarta da alama batasan meye ma damuwaba Dan haka bazata lalata mata komaiba da tata damuwar zasuyi kwana biyinsu su koma salin alin zata bar damuwarta a cikinta ta duqufa da yiwa yayanta addua.




Abincin da akace a jera mata khaltume ta gama jerawa ta matso ta sanar musu angama jerawa.


Kallan maamah Abeeda tayi tace mata taje taci abinci tukuna.


Miqewa maamah tayi ta nufi inda abincin yake a Jere cike da table din da tasan zamansa yafi karfinta Dan haka sai kawai ta Kalli khaltume Dake ajiye kulan farfesun qaton catfish akan dining cikin nutsuwa da mutintawa tace bazata iya cin abincin anan ba akaita kitchen ko can dakin da aka saukesu taci.


Abeeda Dake waya cikin nutsuwa da Wani irin sanyi na Wanda Hutu kawai ya sani batasan me suke fada ba har khaltume din ta fita da Maamah din suka dauki kayan suka fito dasu har zuwa sashen masu aikin.


A lokacin AmatulMaleek tayi bacci hakama Abdulhameed Amma shi suna shigowa dakin ya Farka Yana ganin maamah din ya tashi zaune Yana kallanta tareda matar Dake bayanta Yana Jin son komawa gida gaba Daya na shigarsa.


Ajiye kayan sukai a qasa gefen Dan madaidacin gadon Dake dakin tayiwa khaltume data juya zata fice Godia sosai cikin Nutsuwa.


Bayan ajiye kayan da ficewar khaltume kallan Abdulhameed maamah tayi tana qarasowa gadon dayake kwance shida AmatulMaleek ta miqa hannu ta fara taba AmatulMaleek taji jikinta zafin Kai a sauka sosai ba laifi take ta sauke ajiyan zuciya me sanyi kafin ta Maida kallanta na Abdulhameed Shima ta tabasa taji ba zafi Sam Kwata kwata a nasa jikin Dan haka ta kamosa ya sauko gadon Yana kallan kayan abincin Dake ajiye kasa Yana cewa


"Maamah yaushe zamu koma gida?"


Zaunar dashi tafara yi a qasa kafin itama ta zauna tana cewa


"Kwana biyu zamu insha Allah mu koma,
Kaci abincin dai tukuna kafin Amatu ta tashi itama taci."


Doya da dankalin turawa ne da aka cakudasa da kwai dasu pepper sai kamshin spices yakeyi.


Wani mugun yawu me kaurin gaske Abdulhameed din ya hadiye harda ita Maamah din Amma dayake sunada dangana sai jikinsu Bai Wani dauki rawa ba.
A natse ta zuba musu kafin ta sake Bude dayar kulan sukai arba da farfesun kifin Shima ta zuba musu duk a cikin guri Daya sbd kada su Bata plates din dasuke qal tasan Se sunyi tsada,
abinda ma ita Bata saniba shine ko spoon da matar gidan take amfani dashi baa bari Koda wasa yazo bangaren masu bare kayan abincinta Wanda wainnan din daga yau sun tashi daga kayan cin abincin madame Abeeda sedai Kuma a ajiyesu Dan baqin da basuda wani mahimmanci,
Shi oga kwata kwata kuwa Sam bama kowa ke taba kayan da ake masa amfani dasu ba sbd Wani irin qyanqyaminsa da tsaftarsa data Baci tayi yawanda idan Yana gari aikinsa na musamman ne da ake taka tsantsan da kiyayewa dashi.


Abdulhameed duk da Yana cikin kulaficin son komawa gida a take harma da tsoron inda yaga sunzo din Amma sosai ya saki cikinsa ya ringa cin cimar da Bai taba cinta arayuwarsa ba Dan kuwa baitaba ganin ko dankalin turawa da idanuwansa ba bare ci hakama doya har gwara kifi suna Gani a masu siyarwa na kauyensu da masu zuwa ruwa su kamo.


Dadin dahuwar wadda take ta musamman Dan kuwa duka masu aikin gidan wainda suke da karatu akan aikinsu ake dauka Dan haka masu girkinsu komai nasu kamar a 5star restaurants kake,
Hakama masu aikin tsafatace gidan Suma kusan sai wainda suka samu training me kyau ake dauka sbd kusan gaba Daya rayuwar taurawan datake cikin ASH TALBA tagama kama iyalinsa da kusan gidan komai a daki daki akeyinsa kan tsari da rashin tarkacen da zai damesa.




Ita kanta maamah taci abincin sosai ba laifi suka sha Wani homemade drink da ko zaa kulla musu bomb ya watse dasu basusan dame dame acikinsa duk da fruits ne zalla Amma dai Sam basusan meye shi din ba sudai sunci Kuma sun koshi.


Suna gamawa ta rabe kayan gefe sbd na Amatu da suka rage Mata.


Toilet dayake dakin suka shiga
Dayake ta iya amfani duk da irin wainnan abubuwan sbd tasowa gidan masu arziki Dan haka Bata manta yanda ake amfani da wasu abubuwan ba da yawa.
Wanke musu hannuwansu tayi nata Dana Abdulhameed daketa lashe hannun.


Sabulun tasaka ta wanke masa hannu da kyau itama ta wanke nata kafin ta goge musu bakinsu suka fito tana ce masa ya koma yayi bacci kafin azahar ta qarasa yi ya sake warwarewa.


Hayewa yayi gadon Yana cewa


"To Amma bazaki fita koina ki barmu anan ba ko?


"Babu inda zani Ina Nan zaune harku tashi Nima Dan rintsawa zanyi kafin lokacin yayi."


Yana Jin Hakan ya sauko daga gadon Yana cewa
"To zan kwanta a gurinki"
#MAMUH#
#ASH TALBA
#LA HOT
#FRIENDSHIP
#LIFE
#AMATULMALEEK
#NAUFAL TALBA




*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
YANCI DA RAYUWA
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070
Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest #




AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar




6
A qasa kan tiles Maamah tayi kwanciyarta kan daddumar sallah tareda Abdulhameed Daya shige jikinta tin tana jiran farkowan AmatulMaleek har bacci ya Dan fixgeta itada Abdulhameed din.


So biyu ana Aiko khaltume dubasu ko sun tashi Amma Basu tashi ba Kuma Madame tace kada a tashesu Dan haka aka barsu sukai bacci sosai batareda Maamah din ta san ta dauki lokaci sosai haka tan baccin ba.


Sanyin tiles ya dayayi musu yawa ya farkar da ita dole lokacin karfe biyun Rana harda minti talatin da takwas Dan haka cikin sauri ta tashi tana janye Abdulhameed Daya cukuikuyeta sbd sanyi ta miqe tsaye tana kallan gadon Taga AmatulMaleek din itama tana motsawa alamar tashi zatayi Dan haka toilet kawai ta wuce Tayo alwala ta fito tayi sallah tana idarwa Amatu na farkawa Dan haka itace ta kamata da kanta takaita toilet tabarota.


Ita kanta Amatu ta Dan iya aiki da wasu abubuwan bandakin sbd zuwan da suka taba yi tafara Dan wayo lokacin.
Fitsari tayi Tayo alwala itama ta fito ta tsaya gefen Maamah tayi sallah tana idarwa Abdulhameed na na tashi

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads