Header Ads
Showing 9001 words to 12000 words out of 152002 words

Chapter 4 - AMATULMALEEK COMPLETED BY Mamuhugee.txt

Ads the beginning of article before Image

11 Jun 2024

1084

Ads at the middle of Article

daga baccin Shima.


Da sauri Maamah ta miqe ta rakasa toilet sbd fitsarin dayake cewa ya matsesa.


Bayan fitsari harda zawo yayi sbd abincin Daya Dan fara tabashi kasancewar ciki Bai Saba da wannan dadin ba,
Fitowa yayi bayan Maamah ta wanko masa hannuwansa da kyau da sabulu
Gefen AmatulMaleek ya zauna Yana kallan kayan abincin Dake gefen ajiye yafada mata nata ne sunci sun rage Mata tin dazu.


Kallansa Amatun tayi bayan ta Kalli kayan abincin Amma Bata motsaba sbd ba Maamah ce ta Bata ba.


Maamah kuwa toilet din tahau wankewa sosai sbd kada su lalata musu guri Dan tasan tsananin karfin tsaftan masu gidan sbd duk Wanda ko kalilan sani yayiwa ASH TALBA yasan inda qazanta take da inda yake akwai Nisa me yawa da zurfi.


Sosai ta Saka karfinta ta wanke toilet din tayi masa fes ta fito tana kallan Amatu Dake zuru tana kallan Abdulhameed Dake ta fada mata dadin abinda suka ci din tana bacci.


Wani sanyayyan murmushi maamah tasaki tana qarasowa fuskarta a sake ta kallesa tana cewa


"Gashi Kuma bazaka sake ci ba yanzu sbd yafara lalata Maka ciki."


Dariya yayi Yana maqale kafadarsa Yana cewa


"Zan sake ci mana ai idan munkoma bazan sake ci ba shikenan."


Daga Maamah har Amatu da batada karfin jikinta qaramar dariya suka saki sbd yanda yake matse da a dauko abincin.


Maamah ce ta janyo abincin bayan ta zauna itama a tareda su qasan.


Bude abincin tayi da kanta ta zubawa AmatulMaleek komai kaman yanda suka hade tana cewa


"Ki cinye tas sbd Kinga ba karfi jikinki ta yanda zaku samu kuzari sai muje akaimu ku gaida mommynku Abeeda harma da sauran mutanen gidan."


Gyada Kai kawai AmatulMaleek tayi tana Saka hannu a abincin sbd itama ya shiga ranta sosai duk da batada kwadayi Amma shi abinci irin wannan basama ganinsa bare.


Abdulhameed ma dole tareda Amatun ya sake cin abincin itama Maamah hannu ta Saka sukaci abincin tare su uku Abdul naci Yana tambayar AmatulMaleek idan tanajin dadin dayake ji a abinda sukeci din.


Dariya Amatun ta Dan ringa yi masa tana cewa


"Maamah wlh 'dan Nan naki duk ya haukace sbd cin abinda be taba ci ba."


Itama Maamah din yar dariya tayi tana cewa


"Kyalesa yaci ai na kwana biyu ne muna komawa kaman yanda ya fada shikenan."


Cikin kulawa da tsananin so da kaunar juna sukaci abincin su uku suna Dan magana Sam sama,Maamah kusan duk Rabin cin abincin nata su take gyarawa kidin tana ja ye musu qashinsa abubuwan data San bazasu iya ci ba tana musu fira cikin kulawa da kaunarsu.


Suna gamawa wannan Karan su ukun suka shiga toilet suka wanko hannuwansu Maamah na fitowa ta tattara gurin tareda kayan ta fito dasu ta nufi hanyar kitchen tana isowa khaltume da Masu aikin abincin Dake girkin dare kallanta sukai tareda karban kayan hannunta.


Kallan khaltume tayi tana cewa Ina zata wanke kayan saita wankesu da kanta.


Karban kayan khaltume tayi tana cewa ta barshi kawai.


Kasa tafiya maamah din tayi sai data taimakawa khaltume gurin wanke kayan kafin ta koma.




Zama sukai a dakin shiru daga ita Se su Amatu suna Dan firarsu sama sama sbd daga Amatun har Abdulhameed sun warware kamar ba'a nade aka shigo dasu ba ba lafiya sosai Daman yunwa ce da wahalar hanya Se iska da sanyin kwanan Tasha.


Har yamma Babu Wanda ya shigo inda suke aka nemesu Suma haka sukai zamansu.


Koda Akai sallan magrib Wani abincin aka sake kawo musu Basu ci ba sai da sukai sallah tukuna suka zauna sukaci a plate Daya su dukansu dayake wannan Karan farar Basmati rice ce da brown chicken stew wadda Babu Mai sosai acikinta sbd lafiyansu da suke kulawa da ita sosai a gidan.


Kazar Dake cikin miyan zata Kai guda harma da Rabi Kila Dan kuwa duk yanda sukaci ta Basu cinyeba hakanan suka tattara kayan Maamah dince ta sake fita dasu takai kitchen ta dawo.


Har Akai ishai baazo antafi dasu can gurin masu gidan ba sbd umarnin da Abeeda ta bayar na a barsu suyi kwana biyu suci su huta yanda ya kamata kafin su fara Dan zagayawa sbd sam Bata kaunar ganinsu a yanda suke din.


Da daddare maamah barwa Abdulhameed da Amatu gadon tayi sbd baida Wani girman da zai daukesu su uku Dan haka tayi kwanciyarta qasa tabarsu a saman sukai bacci.


Bacci sukai sosai Wanda suka jima Basu irinsa ba sbd samun gurin baccin me nutsuwa ba sauro ba komai Dan haka har Akai asuba Basu saniba Saida gari yayi haske Maamah ta Farka tana tashi zaune kafin ta miqe ta nufi toilet Tayo tsarki da alwala tana fitowa kafin ta tada sallah ta tana Amatu tana Kiran sunanta a nutse.


Cikin baccin dabe saki Amatun ba ta Bude idanuwanta masu Dan girma tana cewa


"Maamah baccin be sakeniba"


"Tashi kiyi sallah Se ki koma tinda Babu aikin da zamuyi anan din."


Sake Dan juyawa tayi tana Bude idanuwanta tareda Kai hannuwanta duka biyu tana ture kafafun Abdul Dake kanta cikin Wani shegen mugun bacci Wanda ko a gida haka suke kafin safe ba qaramin shuri takesha a gurinsa ba sbd Mayen baccinsa.


Saukowa tayi gadon tana murza idanuwanta ta nufi bayin ta shige tana Bude idanuwanta dakyau sbd kada ta zame.


Koda ta fito Maamah tagama sallah tana zaune tana Dan kokarin tada Abdul Shima cikin kulawa da rarrashin ya tashi yayi sallan.


Sallah tayi tana idarwa itama ta zauna gefen maamah din wadda da kanta takai Abdul toilet yayo fitsari da alwala,
Inda ma Allah yayi mata babban rufin asirin dukkaninsu yayan nata Babu me fitsarin kwance da batasan ya zatai ba.


Bayan sun gama sallah Amatu ce ta kwanta qasa Maamah din Kuma da Abdul suka koma kan gadon suka kwanta dukkaninsu baccin ne ya sake daukansu hankali kwance.




Se qarfe Tara aka kawo musu abincin breakfast Wanda Tintini Daman sun tashi har sunyi wanka sbd kada Azo a taddasu da kowacce irin rashin tsafta.


Ayau ma lafiyayyan breakfast suka sake karyawa dashi Wanda kusan iri Daya Dana jiyan ne sedai yau tareda Wani Irin tea me shegen kauri Daya Saka Abdul ringa fadar akwai Madara sosai a cikin shayin.


Haka suka sake wuni guda Babu Wanda yazo ya tafi dasu sedai abincin da aketa kawo musu da lokacin cinsa yayi.


Bata damu da cewa Se sunje gurin Abeeda ba sbd tasan tana sane dasu Kila wata hidimance ta riqeta Batada lokacin ganinsu yanzu.


Abdul kuwa Jin yayi shikam yafara son gidan sbd dadin dasuke ci Kuma basa komai bayan kwanciya da Shan AC Wanda sanyinsa yafara taba Amatu ita Dan Sam Bata son sanyi duk da tana yarinya yanzu ne ze tabata.




****Kwanaki kusan hudu masu kyau aka Basu suka huta yanda ya kamata bayan ci me kyau da sha me kyau Babu abinda suke Samu,
Hatta yar suturar sakawa anbasu dukda ba masu yawa bane Amma sukam a gurinsa me yawan ce,


Abdul sosai a yanzu yaji bayason su koma gida Dan kuwa shi ko wannan ci a koshin da abinci mekyau aka barsa ganin yakeyi duniyarsu ta gyaru Dan haka tini shi Kam ya fara kumatun Kwana biyu,
Amatun ma ta Dan yi kumatun duk da batada jikin kiba ko kadan Amma dai ita cima me kyau da wuri take nunawa,
Maamah kuwa sosai ta dage da kulawa da inda aka ajiyesu din sbd karsu lalata inda aka ajiyesun kafin su tafi hakama duk takai kayan abincinsu kitchen seta Dan taimaka musu da Wani aikin sbd Bata Saba da zama Babu aikin komai ba Jin takeyi duk ba dadi sbd su Basu Saba da Hutu ba da wahala suka Saba.




Ranarda suka cika kwana biyar da zuwa aka Aiko khaltume ta tafi dasu cikin asalin gidan inda masu gidan suke,
Kai tsaye sashen Abeeda aka nufa dasu khaltume na gaba suna biye da ita.


Abdul na hannunsa na riqe cikin na maamah sbd kada yanda yake kalle kalle,
Amatu kuwa tana gefen maamah din itama tana Dan kallan koina.


Babban palon Abeeda ko yau aka nufo dasu suka zauna 'yayanta na gefenta matse da ita suna Dan kallan makekiyar flat screen tv din Dake aiki a palon ba murya sosai.


Abdul sai taba Amatu yakeyi Yana nuna mata abubuwan da duk idanuwansa suka Gani na mamaki ita Kuma tana gyada masa Kai sbd batasan me zata ce masa ba.


Basu Wani jimaba Abeedan ta fito fuskarta dauke da murmushi me yalwa da kulawa tareda kauna a Fili tana kallansu ta qaraso sanye cikin Wani milk dry lace Daya gama bayyanar da kudinsa sbd yanda take a kwance kamar cotton.


Zaunawa tayi idanuwanta dasuka fada suna kan AmatulMaleek wadda gabaki daya Babu abinda ta baro na mahaifiyarta Asmaun sai haske data Fi Asmau Amma komai na maamah dinne.


Manyan idanuwanta farare ta kalla tana mamakin Irin kamannin Asamun da Amatu ta koma sak,
Numfashi ta sauke ahankali tareda sake fadada murmushinta da kulawanta tana miqa hannunta ta Kila Abdul Wanda yake kallanta Amma ya kasa zuwa sai maamah Daya kalla wadda cikin murmurshi ta gyada masa Kai tana cewa


"Jeka ka gaida mommyn UK da kaji Amatu na fada"


Amatu kuwa cikin nutsuwa da girmamawa itama ta Bude Baki ta gaidata cikin Dan sakewan fuska da ganin mommyn.


Amsawa tayi itama tana Jin kaunar yaran tace


"Asmau AmatulMaleek ta fara zama budurwa Ashe,
Allah yasa dai kada iyayen Nan nasu Maza suyi tinanin yimawa auren kauye da wuri sbd bazamu yarda ba Sam da wannan dabiar ta kauye"


Dariya mara sauti maamah tayi tana cewa


"Toh ai sedai ace Allah ya tsare Amma Kam Kila Hakan zaa samu"


Dan kame fuska Abeeda tayi tana sake qarewa Amatun kallo Tana cewa


"Sam wannan bazai yiyuba sbd zasu kashe rayuwarta ne,Ina Sam Sam,wannan ai rashin hankali ne da cutatar da rayuwar Yara qanana sbd wasu shekarun nasu da gaske Basu kaiba."
#MAMUH#
#AMATULMALEEK
#ASH
#ROMANCE
#NAUFAL
#FAMILY
#WEALTH
#LA HOT




*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070


Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story #


AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar


7
Maamah kasa cewa komai tayi sbd batasan mema zata ce din ba idan Akan wannan maganar ne Dan kuwa ko ita bazata taba son ayiwa AmatulMaleek auren wuri na kauye ba Amma Babu yanda zatayi idan su kawu suka Yanke mata Hakan.


AmatulMaleek kuwa da Abdul dasuke gurin Basu Wani Maida hankali ga abinda su maaman ke magana akaiba Dan kallo sukeyi,


Ganin Hakan Abeeda takira khaltume ta tafi dasu palon Husnah da Haydar suyi kallon acan.


Bayan antafi dasu AmatulMaleek din zuwa can Abeeda kallan Asmau tayi a natse tana son jin da gaske idan auren kauye din zaawa AmatulMaleek.


Shiru Maamah tayi sbd batasan me zata fada ba Dan kuwa kota Bude Baki ta fada ko kada ta fada Abeeda tasan batada ta cewa akan Hakan,


San numfashi kawai ta sake tana cewa


"Tinda Bata karatu Kam ai auren dole ne da wuri Koda bamuso Hakan ba"


Cikin mamaki da Dan takaici Abeeda tace


"Ke Zaki yarda kenan ayi mata Hakan?
Kuma Asmau me zaisa ki bari 'yarki taqi karatun Boko?
Yanada mahimmanci fa kema kinsan Hakan.


Fada Abeeda ta hau yi sosai Wanda ya Saka maamah yin shiru kanta a qasa batareda tasan me zata ce ba Dan kuwa fada ne Abeedan keyi kamar tanayi da 'qanwarta ko 'yar aikinta.


Abeeda ji tayi duk haushin Asmau ya rufeta Dan haka ma ko firar kirki basuyiba saita damuwa da takaici.


Su Amatu kuwa suna can zaune palon su Husnah duk da Husnah din Bata Nan tana can tareda mum Aisha tin da Akai rasuwar Basu dawoba tkuna Haydar ne kawai anan.


Kallo sukasha sosai hankali kwance sai kusan magrib maamah ta jasu suka koma inda suke wato bangaren masu aiki.


Kwana sukai Abdul na firar abinda suka ringa kalla a TV ita Kuma Maamah cikin damuwa ta kwana sbd Abeeda datai mata fada da maganganu dasuka Saka zuciyarta rauni akan rayuwar datake ciki da 'yayanta.


Amatu kuwa data fahimci damuwa a tareda mahaifiyarta itama sanyi jikinta yayi Dan haka dukansu a sanyaye suka kwana.


Koda gari ya waye maamah data Dan fara sabawa da fitowa Taya masu aiki ayyukansu,fitowa tayi ta nufi dakin khaltume ta kwankwasa mata ta tambayeta idan akwai aikin da zaa Taya dashi.


Ba musu khaltume ta nufi kitchen da ita ta tayasu da aikin fere dankali da doya harma da wasu ayyukan Dan kuwa maamah din tanada nutsuwan aiki da tsaftan Daya sakasu Dan bari tana Saka hannu a aikin.


Dayake kowa ya samu Rana shanya garinsa yakeyi sai gashi cikin kwanaki kalilan masu aikin gidan Kokuma ace khaltume datake babba a cikin ma'aikatan gidan sun mayarda Maamah din kamar me aikinsu Suma kusan duk wasu ayyukan kitchen din Banda girki itace take yi musu,


Ita Kuma Bata taba Jin gazawa ba ko jin an Renata ko wulaqanci ne sbd dadi ma takeji ganin tana yiwa Abeeda da Ash hidima a gidansu da karfinta tinda batada abin biyansu da tarin alkhairansu gurinta Dan haka da zuciya Daya take aikinta.


Abeeda batasan tana aikinba sbd sam Bata zama sosai yanzu da asmaun iyakacinsu suzo su gaidata ta danyi fira sama sama da asmaun su koma.


AmatulMaleek ma data ga dai aikin na gaske ne itama sai tana biyo maamah din kitchen tana kama wasu ayyukan Dan kuwa zuciyarta Bata nutsuwa ganin mahaifiyarta na wahala duk da aikin gidan Sam bama zasu kirasa da aikin wahala ba tinda komai a tsare akeyinsa yanda yake a tsare.


Sunanan Babu cikakken sanin matsayin zamansu Wanda ake nufin jiran dawowar Me gidan sukeyi da mum Aisha maamah tayi musu gaisuwar rasuwar data sakota zuwa Amma ba alamar zasu dawo kusa hakama ita kanta Abeeda tafiya kamata tayi zuwa porthcrt ta kwana biyu Dan haka tana tafiya suka sake zama Wani iri a gidan.


Abdul dai tini ya koma Dan masu aikin gidan sbd maamah aka barwa Haydar Dan haka akace su koma can cikin gida suna kwana sbd Haydar din kafin maamah ta dawo duk da akwai masu aikin Dake kulawa da cikin gidan dama Haydar din Wanda kusan shekarunsa Daya da Abdul.




****Acikin kwana biyu da tafiyar Abeeda Haydar yaji dadin zama acikinsu maamah da Abdul da AmatulMaleek sbd su Kam tsananin son junansu da kulawa da juna sukeyi tareda wasa,
Duk da Amatu ta girmi Abdul sosai Hakan Bai hanata zaka qawarsa ba abokiyar wasansa Kuma abokiyar fadansa ba hakama itama Maamah sosai take sakewa da yayanta tana San biye musu wasu lokutan musamman idan ba kowa sbd idan akwai mutane tana bayyanarda kunyarta ta haihuwar fari ga AmatulMaleek sosai sosai shiyasa a duk lokacinda Abeeda tace mata "yarki AmatulMaleek" Jin Kalmar takeyi ta mata Wani irin nauyi.


Tsakanin Abdul da Haydar harma da Amatu cikin kwana biyu sunyi wasa da 'yar sabuwa Dan haka Koda Abeeda ta dawo tayi mamakin yanda Haydar yake wasa sbd sam Baya wasa Baya Wani fara'a kamar 'dan dayake cikin qunci,
Husnah ko tana Nan Sam Bata Wani sake masa sbd son girma da ganin batada lokacin wasan banza dashi ita datake zama 'yan mata,
hakama masu aikin gidan Babu me Dan wasa dashi kulawa kawai suke basa Dan haka Sam shi rayuwarsa ta yarinta Bai ganewa komai na Jin dadi da sakewan qananun Yara ba,
Idan ya Dan samu wannan sakewan to Brother Naufal dinsa Yadawo hutun daga school Yana Nan Dan haka shi wata sabuwar rayuwar ya Gani a tattareda su Amatu da maamah.


Abeeda bataji komaiba saima dadi dataji Haydar din ya sake Yana wasa sosai Dan haka saisu Amatu da Abdul suka samu sake da Daman zuwa sashen aduk lokacinda sukaso ganin Abdul din haka Shima da Bai taba sanin tayaya ma ake zuwa sashen masu aikin gidanba sai gashi yana zuwa a duk lokacinda yaso.


Dawowar Abeeda ma ta fahimci maamah na aiki cikin masu aikin gidan ko datai mata magana maamah ta nuna mata ta gaji da zaman banzan ne shiyasa take taimaka musu.


Abeeda Bata hanata ba duk da dai tasan Hakan Bai kamataba sosai Amma tinda asmaun naso saita barta kawai.


Kullum da daddare suke zaunawa a palon na Asmau su tattauna maganganunsu da yar firarsu ta Aminai kafin Asmau ta dawo ta kwanta.


Ita kanta Abeeda a yanzu datake samun Wanda kullum take fira dashi sai take Jin dadin rayuwar tata da kullum Hutu ne da Bada umarnin sai wayoyi Dan aiki ma ta Dena zuwa kwata kwata.


*****Satinsu biyar harda kwanaki da zuwa Amma har lokacin ASH TALBA Bai dawo ba gashi Yara sunyi sabo sosai da Haydar Wanda a yanzu ko abinci yafison yaci gurinsu Abdul ko Amatu wadda yakejin yafisonta antinsa akan Husnah dasuke uwa Daya,
Hakama maamah Jin yakeyi yafison zama a gurinta sbd yanda ko abinci sukaci itace take wanke musu hannuwa da Baki hakama yanda Abdul tasaba duk da ya Dan girma itace take masa komai Dan haka Shima a yanzu din itace take masa komai tini ya Dena son wankan masu aiki Sena maamah hakama Amatu itace ke masa Shirin zuwa school yafison nata.


Duk wannan hidimar maamah bata Dena zuwa kama ayyukan gidanba Dan kada suyi zaman banza Dan haka a sane khaltume ta sallami masu aiki biyu daga cikinsu tabar biyi masu shara da tsafatace gidan kawai aikin kitchen kuwa daga me aikin girka abinci sai maamah Dake sauran duka ayyukan batareda Jin gajiyawaba ko damuwar komai.


Shakuwar Amatu da Haydar yasa Abeeda Jin batason su tafi sbd 'danta ya samu sakewan da suketa son yayi ya more yarintarsa Dan haka ta ringa Jin batason tafiyar tasu ko dan Haydar.


Abdul kuwa yasamu abubuwa na karuwa sosai daga Haydar,
Kamarsu sutura masu kyau da takarma dasu kayan wasa haka masu girma da tsada Dan haka shima tini yaji bayason su koma musamman idan suna garden na gidan suna wasa dasu keke da lilonsu Haydar din su basuma San akwai irin wannan duniyarba a gidan Saida suka hade da Haydar.


Abeeda ba mace ce me yawan son fira ba shiyasa sai dare suke Dan zaunawa su zanta da Asmau wadda zuwa lokacin Asmau tafara Jin kanta a tsarge idan tana tareda Abeeda sbd matsayin ba Daya ba hakama ita datake cikin Yan aikinta Jin take kamar yanzu Abeeda tafi karfinta duk da so da kaunar junansu a jininsu yake Kuma Abeedan Bata taba nuna mata tafi karfin nata ba Dan kuwa bayan Maamah din Babu me zuwa ya zauna kujera Daya da ita suyi magana irin wadda Bata taba iyayi da kowa a duniya harma ASH TALBA Wanda yake mijinta da Bata hada komai da kowa dashi ba a zuciyarta da rayuwarta.




Lokacinda suka cika sati Shida cif a gidan su mum Aisha suka dawo tareda Husnah

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads