Header Ads
Showing 123001 words to 126000 words out of 152002 words

Chapter 42 - AMATULMALEEK COMPLETED BY Mamuhugee.txt

Ads the beginning of article before Image

11 Jun 2024

897

Ads at the middle of Article

tsomasa cikin yashi an fitar sbd qura.


Daqyar suka iso ciki barka da isowa anty Farha kawai tayi musu suka bita da kallan mamakin dayake Neman kashesu ta yanda suka riqasu isowa dakuma alaman cikin Hutawa Farhan take ba alamar mota suka biyo.
Kenan jirgi su suka biyo Kuma sun tabbatarda sbd Amatu ne aka sakosu jirgin sukuma aka jefawa hanyar Lagos su duk balain da zai cisu a hanyar ya Dade Bai cinyesu ba kenan.


Maamah ma Sam Babu qarfi a jikinta ga ciwon Rai ga ciwon jiki,
Daki kowannensu ya samu ya fada daqyar suka iya Kai kansu toilet suka sakarwa kansu ruwan zafi kowannensu yayo wanka Husnah ko abinci Bata iya ciba daga zaune tayi sallah ta zube a gurin tafara baccin wahala kaman ta mutu.


Mum Aisha kuwa abinci ta nema taci ta koshi kafin tayi sallah ta kwanta a watse.


Maamah Kam sallah tafara yi itama bayan wankan Bata iya cin abinci ba ruwan zafin tea kawai Tasha Wanda anty Farha ce ta kawo mata tana sha ta kwanta itama.


Kafin bacci ya dauketa Babu abinda takeji a zuciyarta Yana cinta da qunarta irin Jin rayuwar gidan ASH TALBA ta fita ranta gaba Daya,
Babu abinda takeso irin ta Dan tafi ta samu Hutu da Nutsuwar zuciya sbd takasa yarda da Husnah data Rena da hannunta zata iya turo Wani ayiwa Amatu fyade,fyadenma irin na wulaqanci tinda a cikin gida,a cikin gidan ma a lokacinda aure yake kan Amatun Koda kuwa baa son auren ai dai akwaisa Amma a Turo Wani Dan haiqe Mata...


Cikowa idanuwanta sukeyi da hawaye masu radadin gaske da baqin cikin zuciya me tsanani.




Koda gari ya waye Amatu sai ganinsu maamah din tayi sun iso taji tayi farin cikin ganin isowarsu lafiya sbd mahaifiyarta sedai Bata shigewa maamah din sosai ba sbd ganin kowa sedai kallan kallo musamman mum Aisha tanason magana Amma tana tsoron Wani tashin hankalin yanzu batareda sun San me ASH zaiyi dasu ba akan abinda ya faru ganin idansa a Greece.


Husnah qin fitowa tayi daga dakinta sbd kasa iya kallan maamah da batace komaiba akan abinda mum Aisha ta fada hakama Bata sake kallan ko inda take ba Dan haka Se takejin tana shiga shakku da fargaba ga Dad dinta da ko tinawa tayi da shi sai taji hankalinta na Neman gushewa da tashin hankali.


Haka suka wuni suka sake kwana gida kaman gidan mutuwa Babu me walwala kowa Motsawan ASH yake jira,
Babuwa Wanda ya iya kunna wayarsa sbd shakka da tsoro anty Farha ce kawai ke wayoyinta a gidan Kuma kullum sai tayi magana da Mr Jameel Wanda take bawa tabbacin lafiyar Amatu Dan tasan ASH na buqatan Jin Hakan Kodan samun qwarin gwiwan fuskan balain da suka Saka sa a ciki.


Case din dayake kusan police case ne shiyasa Sam Baya samun Daman komai da kowa daga karshe dai aka case din ya mutu ya samu Daman fuskantar Abeedan wadda tini ta sake komawa cikin mawuyacin hali me ban tausayi.


Mr Jameel ne ya duba footage na gidan Dan tabbatarda abinda ya faru lokacinda suke kokarin kashe case din ko zasu samu abinda zai Taimakawa kashe case din Amma abinda ya Gani din ya Sakashi shiga sabon takaicin tabbatarda tarin kolo mentals ne suke zagaye rayuwar ASH.


Mafi abinda yafi daga hankalinsa shine maganar fyaden da ake fada cewan Husnah ce ta aika Naufal,Tayaya zaace 'yar ASH din ce zataiwa matarsa Hakan bayan a lokacin ma ko noticing dinta ASH din beyiba bare ta damu har da Saka wannan mummunan abin ya faru.


Rasa yanda zai fadawa ASH yayi sedai ya tura masa clip na video din ta wayarsa batareda ya iya fada masa da bakinsa ba.


Bayan ya turawa ASH clip din waya yayi a Yola take ya sallami masu ayyukan gidan guda Daya ya bari hakama securities tini ya sallamesu yabar Daya.


Su mum Aisha na zaune daki kwatsam suka ga wutar gidan ta dauke gaba Daya.


Mamaki ne ya Saka dukkaninsu fitowa Husnah Dake tsananin tsoron duhu tini tafara rawar jiki tana fitowa Neman Wanda zata raba amma ko maamah Bata Gani ba bare iya tinkararta mum Aisha kuwa zafi ne Sam bataso tini tafara Jin kaman zata siqe.


AmatulMaleek Dake daki ma zafin ne ya fara damunta Dan haka anty Farha ta fita Babu jimawa ta dawo mata da rechargeable fans guda uku da manyan fitila sbd tasan aikin Mr Jameel ne wuta a gidan Kuma Se abinda hali ya bayar.


Ko maamah Dake daki Kai tsaye tinaninta yake akan hukuncin abinda ya faru ne zasuyita amsa shiyasa Bata daga hankalinta ba saima sanyi da jikinta ya sake yi.


Tama Rasa tayaya zata fuskanci Amatu akan abinda dukkaninsu sukaji cewan Husnah data fifita akanta itace silan lalacewan ma komai na rayuwar tasu Suma suna zaman zamansu a bangaren masu aiki cikin rufin asiri da Kwanciyar hankali Amma ta tura Naufal ya lalata musu komai gasu yanzu a bagiren da bama Susan sunan alaqarsu ba Dan kuwa a yanzu Amatun gujewa raban maamah din takeyi sbd tashin hankalin da kullum Baya qarewa.




Kwana biyu sukai Babu wuta a gidan take suka fara Neman rasa nutsuwarsu,
Mum Aisha guduwa takeson yi daga gidan saiga Naufal an tattaro an kawo mata a boys quarters na gidan take ta sake shiga tashin hankali sbd tabbas hadesu guri Daya da Akai umarnin ASH ne to me Hakan ke nufi?
Ko dai ta dauke Naufal din su gudu ne to Amma batada gidan kanta ma Bare ta gudun,lalacewan Naufal ta hanasu Tara abinda ya kamata su Tara din gashi komai na Neman kwabewa.


Husnah zaucewa tafara yi,ga rashin sanin halinda mum dinta take ciki sbd ASH ya rufe duk wata hanyar da kowa zaisan me Abeeda take ciki,
Hakama shi kansa Babu Wanda zai taba gwada kiransa yace ya samesa,
Kudi dasuke yanda suke so da su kusan dama gurin Mr Jameel suke karba to Shima kansa shakkar kiransa sukeyi bare ASH da haukansu bema Kai can ba.


Dawowan Naufal ya Saka hankalin maamah fita daga gidan gaba Daya ba a kanta ba akan Amatu dan haka ta Yanke shawarar dauke Amatun su tafi daga gidan kafin ASH ya dawo ayi duk abinda zaayi.




Duk wannan tashin hankalin da kowa yake ciki na Amatu daban ne sbd rashin yin period dinta wata biyu harda Dori ya Sakata shiga mummunan tsoro da firgici,
Kewan ASH da tinanin halinda yake ciki Yana ranta gashi ya Hana kowa ji daga garesa to yanzu Kuma data fara fahimtar halinda take ciki Jin tayi itama tana Neman zaucewa Dan batasan tayaya zata fara tabbatarda idan ciki ne a jikinta Dan haka ma ta fara Hana kanta yawan fitowa itama tana rife jikinta sosai Dan Hana maamah ko kowa fahimtar halinda take ciki duk da Bata tabbatar ba.


Anty Farha Dake zaune tana waya a bedroom dinsu kallan Amatu datai shiru tayi Nisa a tinani tayi tana nazarinta.


Tana gama wayar Amatun ta kalla tana ajiye wayar gefenta tace


"Amatu meyake damunki ne?
Ni na Rasa wannan yawan tinanin da damuwan,
ASH ne??


Juyowa Amatun tayi ahankali tana kallan anty Farha din jikinta na sake mutuwa da yanda maamah zasu San ciki ne da ita ga ASH Baya Nan,tsoro ma takeji na maamah din.


Magana zatai anty Farha din ta katseta da cewa


"Abuja fa nakeson komawa sbd komai acan ya Dan tsaya ana buqatan zuwana gashi kina cikin wannan halin,.abinda ma yasa nayi tinanin tafiyar sbd ganin mutan gidan kaman kowa ya nutsu kafin dawowan me gidan Amma bazan.......


Shigowan maamah dakin ne ya Saka farha da Amatun kallan kofar suna kallanta a natse.


Itama a natsen ta qaraso har inda kujera take ta zauna
Amatu ta Bude Baki ta gaidata hakama anty Farha.


Amsawa tayi a sanyaye tana kallan Amatu data kasa dagowa ta kalleta,
Qurawa Amatun idanuwanta tayi sosai tana kallanta,
Ita duk lokacinda ta Kalli Amatu hankalinta mummunan tashi yakeyi sbd yanayi da kaman datake mata da masu ciki,
Da ace zaman aure Amatun keyi da tabbas zatace ciki ne da ita Amma Sam ta kasa tantacewa ita gaba Daya ma kanta neman juyewa yakeyi shiyasa zata dauki Amatun su tafi ganin gida acan zata gane idan ma Wani abin na jikinta su San abin yi kafin ma kowa ya sani.


Bude Baki tayi tana dawo da kallanta kan Farha tace


"Farha inaga ni da Amatu ganin gida zamu tafi kafin dawowan ASH.....


Wayar da farha ke kokarin dauka ta fasa tareda dawo da kallanta kan maamah din tana cewa


"Ganin gida Kuma maamah?
Ina kenan?


"Kauye zamu je inshallah"


Mummunan faduwa gaban Amatu yayi sbd tsoro da firgicin abinda zai kadaitata da maamah batareda ta tabbatarda da gaske cikin ne a jikinta ba,tsoro takeji su tafi suna zuwa zaa gane ciki a jikinta batasan me maamah zata mata ba.
#MAMUH#




*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070


Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story #




AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar




69
*MUFEEDA'S FRAGRANCE*
*GIDAN KAMSHIII*
Munada kayan turaruka kala kala kama dasu
Turaran wuta
Turaran jiki
Turaran Kaya
Humra milk
Humra black
Kwalacca
Turaran moping
Freshener
Daidai sauran su
Ta a Very affordable price.
Zaku iya tuntubar mu a wannan
07040986690
Muna zaune ne a garin Kano da Abuja (life camp) sannan muna aika kayan mu ko ina a fadin kasar nan har ma da kasashen waje. Akwai tsarin wholesale wato sarı ga duk me bukata sai ya tuntube mu. MUNGODE
*MUFEEDA'S FRAGRANCE*
*GIDAN KAMSHIII*






************
Ita Kuma anty Farha abinda ya fara zuwa ranta shine meyasa zasu tafi ganin gidan haka kawai ana zaune kalau hakama Bada sanin ASH ba Amatun zata iya tafiya ne harma ita maamah din.


Akan Amatu anty Farha ta dawo da kallanta Taga yanda tayi sanyi gaba Daya kanta a qasa.


"Maamah harda Amatun zaku tafi gashi Abuja yakamata ta koma sbd karatunta da zata fara exams satin Nan"


Maamah dagowa tayi tana kallan Farha din tace


"Jarabawa Kuma tana wannan yanayin na yau lafiya gobe ciwo?
Abari dai muje kauyen ko maganin zazzabin muyi tukuna saita dawo ku tafi jarabawan"


Gyara zama anty Farha tayi tana fuskantar maamah da kyau sbd taji ta gwara su koma da Abuja tareda Amatun akan a tafi kauyen da ita sbd abune dama Sam ASH din batajin zai bari wato daukan Amatu tayi tafiya da ita bayan uban girman lefinsu a gurinsa Dan haka cikin lallami tace


"Maamah kiyi hakuri da tafiyan Nan kibari muje tayi exams din ta kammalo tukuna sai mu dawo zuwa lokacin ma ta warware Kuma ko yayane yakamata ASH yasan zakuyi tafiya..


Shiru maamah tayi sbd ambatar ASH da Farha tayi yasata Jin tashin hankalinta dawowa tareda fargaba.


Rokonta Ant Farha taci gaba dayi har ta amincewa tafiyarsu Dan Daman zaman Amatu a Nan dinne Bata so a yanzu da Naufal yake kusa dakuma fargaban ganinta kaman me juna biyun datake Amma batajin zata bari su tafi batareda ta tabbatarda meye ciwon Amatun ba dayaqi warkewa.


Anty Farha na ganin maamah ta amincewa tafiyansu Bata tsaya Bata lokaci ba ta kira Mr Jameel ta sanar masa aka Siya musu tickets washe garin ranar suka tafiyarsu batareda mum Aisha ma ko Husnah ta saniba maamah ce kawai tasan da tafiyan nasu itama bawai a ranar ba ta dauka sai Wani satin Amma suka barta Baki sake suka tafi.




AmatulMaleek na baro gidan Jin tayi nutsuwarta data Dan rasa ta shigeta sbd zamanta guri Daya dasu gaba dayansu hanata nutsuwa yakeyi Dan hatta maamah data haifeta yanzu fargaban kasancewa takeyi da ita Sbd abinda take tinanin tana dauke dashi musamman alqawarin da maamah din ta ringa nanata mata akan kaucewa duk abinda ya shafi ASH har sai ankai karshen matsalar Abeeda data auren nasa.


Ko da suka Isa Abuja gidan anty Farha suka sauka Batada raayin komawa mansion a yanzu da batasan wane rikicin ne Kuma ke tafe ba.


Wanka tayi taci abinci sosai tai sallah ta kwanta bacci.


Anty Farha wanka tayi taci abinci tayi sallah ta zari motarta ta fice zuwa shagonta Dake buqatanta.


Se dare anty Farha ta dawo tareda karima data biya mansion ta daukowa Amatun.


Daki Daya aka warewa karima wadda taji dadin dawo da ita gurin Amatun da Akai Dan haka ba wasa ta fara kulawa da aikin gidan da girkinsu da komai duk da anty Farha na aikin gidanta Bata Wani bari anai mata gaba Daya.


Kaman Daman jiran tafiyan Amatu akeyi a gidan Yola din kusan har ruwan gidan suka tsaya sedai su debo a reservoir da kansu acan gate din Baya na cikin gidan.


Zaman bacin Rai da baqin ciki sukeyi a gidan sbd maamah ko cokali Bata iya fitowa ta taba a kitchen da sunan Wani aikin,hakama me aikin gidan Daya abinci guda takeyi a wuni ta tafiyarta Dan haka kusan ci Daya sukeyi sai kame kame tinda Babu me girkawa,
Husnah Neman haukatata zafi da duhu da wahala ke Neman yi Dan har lokacin maamah Bata ce mata komaiba kaman yanda Bata shiga sabgarta ko Daya.


Mum Aisha kuwa dawainiyar Naufal ce da itace takeyi da kanta sbd ba masu aikin ke Neman zautata gashi a yanda yake dinma baida magana shi Kuma sai ta shidai su tafi daga Nan din kada zafi da duhu su kashesa bayan yasan batada gidan kanta kaman yanda Shima baida gidan kansa din.


Daga karshe mum Aisha masu fixing wutan gidan gaban Daya ta kira Amma securities suka tabbatarda Baa Basu izini ko Bada Daman kowa ya shiga ko gyara komai na gidan ba Dan haka su mum Aisha din suka sake shiga tashin hankalin tsaka me wuya.


Daga mata hankali Naufal yayi dole suka kwasa suka koma hotel sbd masifar tafara musu yawa.


Daga maamah Se Husnah aka bari gidan itama maamah datai Shirin tafiyarta kauye ta kwana biyu tukuna ganin halinda Husnah take ciki ya Sanyata fasawa sbd duk abinda tai mata din bazata iya tafiya tabarta gidan ba kowa ba ba uwa ba Uba Yana budurwa.


Ko sati biyu su mum Aisha Basu qarasa rufawa ba suka dawo sbd kudin datake kashewa sunfara fita hankali kada ta qarar da Yan kudadenta ASH ya dawo ya koresu basuda komai gwara su dawo su hakura suci wuyar har lokacinda zai dawo.




**A Abuja hankalin Amatu ya kwanta kadan tana waya da maamah duk da ba Wani sakewa Amma dai yafi babun sbd har lokacin ta rasa meyasa maamah ta kasa dawo mata daidai,
Anty Farha Kuma tana kulawa da Amatun tana Kuma kulawa da business dinta sai Kuma ASH da koyaushe Yana Jin lafiyar Amatun agun Farha Amma ya kasa barin yayi magana da ita duk azabtuwar dayake yi na rashinta da rashin ji daga gareta sbd laifin da kusan yakeji harda ita kasancewar tana taredasu a lokacinda ya samesu da wannan mummunan aika aikan.


Ganin yanda yake hukuntar da kansa na Hana kansa Gani ko Jin Amatun ya Saka Mr Jameel sake tura masa clip din komai ya sanar masa Daya duba.


Duk wannan lokacin Daya dauka Bai dawoba jikin Abeedan ne sai addua kawai Dan haka baiji buqatan dawowan ba Saida kusan komai ya dawo daidai aka samu kanta sedai tana Nan kwance Amma ansamu Bata koma coma din ba Dan haka ya samu kansa ya dawo daidai ya shirya dawowa.




*******
Yanda ya shareta ya Saka Amatun itama Jin rashin dadi a zuciyarta sosai tareda Shiga damuwa da wasi wasin maganar Husnah ta cewan Babu macen daya damu da ita fiyeda mum dinta,
Tsaya mata a zuciya maganar tayi duk da tasan tabbas mum Abeedan na buqatansa hakama na yanda abin yafaru Bai kamata ya baro ba sai komai ya daidaita to Amma itama meyasa zai hanata jinsa Kokuma shi ya jita.
Ga ciki dai a jikinta ya tabbata ta rasa Yaya zatai ta fadawa Wani hakama ta rasa Yaya zatai da tashin hankalin datake shiga akan cikin,
Yaya zatai idan cikin ya bayyana ma,
Gashi anty Farha tinda tasan da cikin ta tashi tsaye sosai akan kulawa da Amatun sosai sedai itama har lokacin Bata fadawa mr Jameel ba bare ya fadawa ASH sbd tafison ya dawo yagansa da kansa sbd fitowan Daya fara yi duk da Amatun na rufewa da kaya masu boye ciki yanzu datake sakawa.


Maamah ma nutsuwarta Dan dawo mata tayi sbd Jin shiru maganar komai na ciwon Amatun Bai bulla ba bare zargin da shedan ya Saka mata na cikin ya bulla Dan haka ta samu Dan kuzari da adduar fatan samun lafiyan Abeeda wadda suka San komai Kila yayi sauki tinda dai baa ce ta rasu ba to da sauki kenan lamarin.


Exams din su Amatu suka fara dayake ba Wani interval sai exams din nata suna sauri a satin qarshe da zata gama jikinta ya Dan ringa fara Bata Sabon laulayi zuciyarta na sake cika da radadi da damuwar fitowan da cikin keyi daga ita Se anty Farha ke renansa ba uwa ba mijin ba Yan uwa.






******Ranar Tuesday Wanda yai daidai da saura kwana Daya dawowansa Nigeria yana zaune Yana dubawa footage din da Mr Jameel ya tura masa Babu abinda Bai Gani ba Kuma Bai ji ba a rikicin da sukai suka jeho masa mata daga stairs.


Jajir idanuwansa sukai ya ajiye wayarsa gefensa ahankali Yana Dan lumshe idanuwansa Dan hadiye bacin ransa da zafin da ransa ya dauka sosai.


Shigowan kira a wayarsa ne ya sanyashi Bude idanuwansa batareda ya juyo ya duba me Kiranba Dan bama zai iya dauka ba kawai dai so yakeye ya wutar Dake cin zuciyarsa ta fara mutuwa.


Cigaba da Kiran aketa yi Wanda har lokacin Bai juyo ya Kalli wayarba karshe miqewa yayi tsaye tareda nufar window iskan wajen ya San kado masa sbd ba qaramar wuta da zafi ne yake ci a zuciyarsa ba Wanda Bai taba samun kansa a irin wannan Mafi girman bacin ran da zafin a rayuwarsa ba.


Mr Jameel daketa Kiran wayarsa Baya dauka kasa hakuri yayi sbd tashin hankalin abinda yake faruwa Wanda bazai iya barin ASH ya dandana radadin Dana sanin rashin daukan wannan wayarba har qarshen rayuwarsa ba Dan haka Kai tsaye saman ya hawo ya tsaya kofan dakin nasa ya fara buga kofan ahankali cikin nutsuwa da sanyi.


Bugun kofar ya sanyashi baro bakin window din idanuwansa Jan su na qaruwa ya iso kofar bedroom din ya Bude Kai tsaye ya zubawa Mr Jameel idanuwansa da suka sake sanyaya jikin Mr Jameel yayi qasa da Kai cikin mutuwar jiki da nauyin zuciya Shima ya furta


"Madame Abeeda... Shiru yayi Yana qasa da Kai batareda ya iya qarasawa ba..


Jajayen idanuwansa ya dago ahankali ya sake zubawa Mr Jameel Yana karance yanayinsa a sanyaye.


Ajiyar zuciya

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads