Showing 12001 words to 15000 words out of 152002 words
Chapter 5 - AMATULMALEEK COMPLETED BY Mamuhugee.txt
wadda take matiqar ji da ita sbd yanda Ash Shima yake matiqar ji da Husnah din kasancewarta suna mata kallan 'dan uwansu da suka Rasa.
Daga isowarsu tun a harabar gidan mum Aisha ta hango garden din gidan da Haydar ke wasa tareda Abdul suna Jan gashin AmatulMaleek Da Maamah tagama kunce mata da wankewa tareda daure mata kafin da daddare ta mata kitsonsa Dan ta Saba itace ke Mata kitso tin tana yarinya Tin Bata iyaba kuma haryanxu bawai ta iya kitson bane sosai Amma de itace take mata ahakan.
Jan gashin sukeyi suna guduwa tana binsu fuskarta a Dan sake sbd ko taso tayi fushin dasu kasawa takeyi Dan batada zafin Rai ko zuciya ko kadan.
Abdul Daya Saba tsokanarta shike fadawa Haydar inda zasu ja gashin su gudu ai bazata iya kamasu ba.
Haydar ma da wasan ke masa dadi sake kamawa yakeyi Yana Dan ja ahankali.
Haydar din tafara kamawa tana cewa
"Wa na kama??
Zaku sake??
Hannunsa take kokarin dagawa sama ta kama kunnensa yafara dariya sosai me hade da ihun Kiran sunan Abdul Wanda yazo da sauri yaja janyesa suna dariya itama Amatun dariya takeyi duk da taso maganinsu.
Dakatawa mum Aisha tayi cikin Isa da Wani irin iKon Daya gama zama jikinta ta kallesu da kyau Taga Haydar ne ke wannan ihun da dariyar,abinda Bai tabayi ba,Babu Wanda a gidan ze ce ya taba ganinsa a cikin wannan Nishadin.
Husnah data fito motar a hankali itama riqe da qatuwar Apple iPad dinta sanyeda doguwar English straight gown black kallan gurin tayi fuskarta da Dan mamaki Kai tsaye tacewa khaltume
"Su waye wannan din??
Cikin girmamawa khaltume ta Dan dubi mum Aisha da ba ita tayi tambayarba tace
"Yar uwar Madame abeeda ce wadda take magana tazo tareda 'yayanta biyu yau sati Shida da zuwan nasu."
Mum Aisha da take ta fahimci Asmau ce tazo Bata tsaya sake Bata lokacinta a tsayuwarba ta wuce a natse qamshinta na cike iskar gurin, Husnah ma bayanta ta bi tana wucewa sashen mahaifiyarta Kai tsaye khaltume na bayanta da set din akwatinta biyu na lv suka shige
Ita Kuma mum Aisha saratu me aikinta ce ta ja nata kayan ta bita duk suka shige.
#MAMUH#
#MEERAH HERBS
FOR MORE PAGES FOLLOW ME @mamuhgee arewabooks
AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070
Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story #
AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar
8
Koda su Husnah suka dawo gidan take masu aikin gidan suka sake shiga taitayinsu sbd mum Aisha da Sam Babu sauki a lamarinta Dan kuwa ko barin kaya baa da iKon yi zaka iya rasa aikinka a gidan Dan kuwa itace me fada aji,itace me iKon zartarwa akansu.
Husnah ma kusan halayenta tafi dauka Dan itace tamkar madubinta Kuma yar lelenta Dan haka kusan halayenta ne Husnan ke dauka duk da yanxu ne take zama Yan mata Amma dai halayenta a Fili suke Tin yanzu.
Koda maamah taga dawowan Husnah sosai ta shiga farin ciki sosai da ganinta ta rungumeta tana ambatar sunanta cikin tsananin kaunarta tana tambayarta ya gajiyan hanya.
Amsawa Husnah tayi tareda gaida maamah din Dan kuwa duk Wanda yake tareda mahaifiyarta Kona sati ne saiyasan maamah a bakinta da matsayinta a zuciyata Dan haka tasan wacece Maamah din a gurin mommynta.
Maamah datake farin cikin ganin Husnah itace da kanta ta gyare mata dakinta fes yanda takesonsa tareda komawa kitchen aikinta,
Ta sanar da AmatulMaleek da Abdul 'yarta Daya ta dawo wato Husnah.
Dayake Abdul shi dinma dayake qanqani yasan sunan Husnah a bakin maamah hakama shi a farko ya dauka da gaske ita din 'yar maamansu ce sbd yanda take fadarta har cikin zuciyarta da gaskiar kaunar datake mata.
Amatu da Abdul sunji farin cikin dawowar Husnah dan haka suka kwana da Shirin da safe zasuje su mata sannu da zuwa kamar yanda maamah tace.
Washe gari maamah din da kanta sukaje tare takaisu suka gaisa da Husnah wadda Babu laifi ta Dan sake musu din Su Daman ba saurin sabo ne dasu ba Suma Dan haka suna barowa dakinta gurin mommy Abeeda sukaje suka gaidata itama cikin kulawa da kauna ta amsa musu kafin suka fito suka tsaya gurin Haydar Amatu ta shiryasa bayan Maamah tai masa wanka Yana ihun bayason Amatu ta shiryasa sbd kada ta gansa ba kaya Amma hakanan suka dannesa itada Abdul harta shiryasa suna masa dariya ya fito yaci abinci Suma anan suka ci abincin dole sbd mommy Abeeda din da Husnah suna kan dining hakama Haydar Dan haka dole akace Suma suzo su zauna.
Dayake Amatu nada hankali sai Bata Wani sake taci sosai ba kamar yanda Abdul ya saki ciki yaci ya koshi Shida Haydar suna wasa da dariya Wanda Hakan ne ya Dan raya gurin daga tsit din Daya dauka.
Suna Hakan mum Aisha ta fito take suka nutsu Amatu tayi saurin gaisheta tana sauke kanta qasa daga kallan dataga mum Aisha din na mata Wanda ya Sakata Jin jikinta na sanyi.
Husnah ce ta gayar da ita tana sake fuska sosai.
Itama mum din murmurshi tayi tana sake fuska tafara amsa gaisuwar Husnah kafin ta amsa ta Amatu data cire tsammanin zata amsata.
Abdul kuwa Sam baima San da ita ba saida tayi musu magana cikin yar tsawar data Saka Abdul sauka daga kan dining din Yana dawowa gefen Amatu idanuwansa akan mum Aisha din wadda kyanta da fadan datakeyi suka sakashi yin shiru tsoronta na shigarsa.
Daga wannan lokacin suka nutsu sama sama suka qarasa suka koma inda suka fito.
Bayan tafiyarsu Babu Wanda yace komai sai Haydar Daya gama Shima ya sauko khaltume ce tazo ta tafi dashi zuwa inda driver ke jiran fitowansa ya shiga mota aka tafi dashi zuwa school.
Koda suka koma daga Amatu har Abdul Babu Wanda ya fadawa maamah abinda ya faru saima zamansu da sukai daki suna abubuwansu.
Koda Rana tayi zaa tafi Kai Haydar Islamic school taredasu mommy Abeeda tace atafi su fara karatun kafin su tashi komawa.
Murna sukai sosai Dan kuwa Daman sunaso fita su Dan ga gari.
Su hudu aka tafi dasu harda Husnah wadda ta kwana biyu Bata zuwa sbd tafiyarsu.
A motar daga Abdul sai Haydar ne keta surutu suna farin cikin zuwan nasu makaranta tare,
Itama Amatun tana farin cikin zuwan makaranta duk da Babu Wani sakewa tsakaninta da Husnah Amma dai tinda gasu Haydar tasan batada kadaici.
Koda suka Isa makarantar tini akaiwa su Amatu komai Dan kafin zuwansu Akai wayar zaa kawosu.
Hatta uniforms da littafai da jaka a makarantar aka Basu sai gasu sun saje da sauran dalibai 'yayan masu fada aji.
Dayake sunada karatun addininsu sai Basu Wani muzanta ba a cikin mutane aka Basu ajinda yakeda daidai da karatunsu
Abdul cikin saa aka basa ajinsu Haydar Dan haka murnarsu ta Qaru,
Amatu ma ajinsu Husnah aka kaita.
Wuni Amatu tayi a makarantar a kame sbd rashin sabo da shiga mutane sabanin Abdul da kamar Daman anan yake Dan kuwa Haydar tini ya jonesa da abokansa suka ringa murnan samun sake.
Koda yamma tayi sosai aka tadasu driver na gate Yana jiransu Dan haka suka shiga mota suka dawo gida.
Koda suka dawo maamah taga yayanta cikin uniform din makaranta Jin tayi jikinta yayi sanyi da farin cikin ganinsu a Hakan tana tausayinsu yanda suke farin ciki gashi dole zasu koma inda suka fito.
Da farin cikin da daddare suka ringa Bata labarin makarantar datake kamar a turai sbd kudinta da tsarinta.
Ita dai murmurshi kawai takeyi tana sauraronsu har dai aka gama dokin Abdul yaci abinci yayi bacci.
Amatu kuwa uniform din nasu ta nade musu ta tattara littafansa Daya barbaza ta mayar a jaka kafin itama taci abincin ta sukai sallar ishai da maamah ta kwanta
Maamah kuwa ficewa tayi ta tafi gurin 'yar uwarta Dan sake nuna godiyarta akan abinda take mata.
********Ahankali su Amatu suka Dena dokin makarantar har suka fara sabawa yanzu Kam ba Doki karatu kawai Wanda kusan duk su biyun sunfi Husnah da Haydar kokari da Maida himma sbd ganin sukeyi sukam sun samu babbar sa'ar rayuwa ta zuwa makaranta bayan Basu tana Saka Rai da shiga kowace irin makarantar ba.
Husnah Sam babu Wani sabo sosai har lokacin a tsakaninta da Amatu Amma dai ta bangaren karatu hakanan take sakewa su koyawa juna ganin Amatu tafita saurin fahimtar karatun na islamiyya.
***ASH TALBA ya dawo kusan so biyu Yana sake tafiya Dan haka sudai su Amatu basuma San ya dawo gidanba harya komaiba sbd Basu taba ganinsaba Dan bayan 'yayansa da matarsa sai mum Aisha Babu me shiga bangarensa Dan haka ko maamah dataje suka gaisa Saida yabada damar Akai mata iso tazo har palonsa suka gaisa Kuma sun Dan jima suna magana duk da rashin son Jan zancensa Yana tsayawa Dana gida su samu lokacinsa.
Karatun su Amatu yafara daukan harama sbd karfin maamah da Abeeda taci akan komawarsu ba yanzu ba.
Kowanne dare a palon su Husnah suke zuwa su Hadu su hudu suyi karatunsu na islamiyya harma da karatun Boko dasu Husnah din suke koyawa su Amatu Dan haka sukam su Amatun suka Bude Kai suna koya Dan daga Amatun har Abdul din suna shaawan na bokon.
Ahankali ahankali sabo sosai ya shiga tsakaninsu duk da halin Husnah din akwai wuyar shaani Amma dai sanyin halin Amatu da zurfin cikinta yasaka take shanyewa zaman nasu na tafiya,
A yanzu Husnah da batada qawaye Amatun ce kawarta har islamiyya har gida Dan haka sai duk abinda ta cire na kaya ko abun buqata da bataso sai tana bawa Amatun tareda nuna mata sai tagama da abu take Bata Dan nuna itace a qasanta Kuma take cin alfarmarta Wanda duk lokacinda takewa Amatun Hakan Bata taba Jin komai ba ita sbd maamah Dake nuna musu Husnah da Haydar Yan uwansu ne datakejinsu a ranta kaman yanda take jinsu.
Kaf a cikin gidan mum Aisha ce wadda Basa zuwa ko inda tabi tabar kamshinta sbd tsananin fadanta da zafinta akansu musamman mahaifiyarsu Dan haka kusan Yan aikin gidan biyu ta sake sallama Dan haka maamah karfi da yaji ta koma 'yar Aiki a gidan Kuma aikinma Wanda ma'aikata uku zasuyi ita aka barwa tanayi.
Duk wannan wahalar da maamah din keyi haryanxu Bata taba Jin haushi ko bacin Rai ba,tsakaninta da Allah takeyi Kuma ko zatayi aikin dayafi wannan a gidan Abeeda batajin zataji Wani abu na dacin zuciya ko gajiyawa sbd Abeeda ta inganta rayuwarta tin kuruciyarsu har yanzu dasuka manyanta gashi Kuma yanzu tana inganta mata ta yaranta.
Waya aka siyawa maamah tana waya da Yan can kauye tana Jin lafiyarsu da Kuma abubuwan Dake faruwa na zumunci da haihuwar da aketa sake yi a cikin Yan watannin da batanan
Ahakan ne katsam aka sanar da ita rasuwar uwar gidan kawu bello wadda take tamkar Yaya agareta Dan haka dole suka fara Shirin komawa gida.
Acikin gidan ASH TALBA Mansion Babu Wanda hankalinsa Bai tashiba da Jin maganar tafiyar maamah gida sbd baiwar data komawa kowa a gidan hatta masu aikin gidan aiki suke Sakata Kuma tayi,hakama tsaftar sashen Abeeda tini ya dawo hannunta hakama cimar Abeeda din,
Ta bangaren mum Aisha ma Amatu ce sabuwar me mata shara duk da Bata Wani iyaba Amma so take ta koya sbd a Qaru dasu Suma,
Su Husnah ma dasukai sabo da sakewa sosai ayanzu suyi wasa da guje guje harma da wasan ruwa a swimming pool dasu Amatun duk sai sukaji jikinsu yayi sanyi Dan haka suka roki mommynsu ta Hana maamah tafiya Amma dole saita tafi.
ASH Baya Nan zasu tafi Amma Kuma Saida ya Saka aka Basu kudin Daya bawa maamah tsoro sosai Dan haka aka Bude mata acct kafin tafiyarta aka Saka mata sauran suka riqe hakama Abeeda ta Basu kudi sosai itama bayan tarin kayan sawa da aka basu Wanda duk kayansu Husnah ne Dana Haydar aka bawa su Amatu itama an bata kayan sawa sosai Dan haka kaya Niki Niki sukai bankwana suka tafi ana kewarsu.
Bayan tafiyarsu har ciwo sosai Haydar ya kwanta kafin yaji sauki yakoma rayuwarsa ta Baya Babu abokin wasa Babu abokin fira bare karatu.
Itama Husnah bataji dadin tafiyar tasu ba duk da Babu abinda takewa Amatun a tarensu bayan Gori da nuna mata kamar komai na rayuwarta saita kashesa tagama dashi take bata.
#MAMUH#
For more pages follow me @Mamuhgee arewabooks
*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070
Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#
AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar
9
Su maamah na isowa gida babban tashin hankalin farko data fara cin karo dashi shine rashin gurin zama Dan kuwa tini kawu bello yayi Amarya ya Sakata a cikin sashen Dan haka suka rakube dakin inna lami data rasu cikin 'yayanta da jikokinta data bari a dakin gashi dakik a cunkushe yake Babu ko filin da zasu aje kayansu sbd kaya da hargitsin dakin.
Batada zabi bayan ajiye tulin kayansu waje a rumfar dakin inna lami din idan sunyo wanka anan suke shiryawa gashi yayanta sunyo Wani irin fresh da kyan Gani tini aka fara Saka musu Baki gashi ko bandaki Amatu zataje saita bita ta rakata Tayo abinda zatai sun fito tare sbd tsoro da fargaban abinda zai iya faruwa.
Amatun ma kanta samun kanta tayi da tsoron gidan da mutanen gidan sbd yanda kowa yake binta da Bakin jiki data Dan yi sbd batada jikin kiba ko kadan Amma ta Dan ciko tayi haske sosai duk duhun da fatarsu tayi ta rinewa ta wanke daga ita har Abdul maamah ce kawai ta Dan yi rama ta wahalar aikin datake sha Amma Kuma duk da Hakan itama fatarta tayi kyau sbd cima me kyau muhalli me kyau.
Kwanansu biyu da dawowa Akai addukar sati ta rasuwar Dan haka sai kowa ya koma sabgoginsa,
Mafarin Bude babin dawowan damuwar maamah shine sace kayansu da aka fara yi Daya bayan Daya Kuma batada iKon magana zaayita fada ana tashin hankali a gidan akan ta maqalawa yayan mutane satar kayan kunce da aka Bata tazo dasu Dan haka sai ta Dena magana ko sun duba sunga an sace musu abu shiru takeyi Bata magana hakama yayan nata Babu me magana.
Kudinta ma baa bari ba haka aka ringa sace mata su kadan kadan Dan haka ta tattara sauran canjin ta Siya abinci dashi ta aje Wanda zasu ringa dafawa da yayanta suna ci duk da tasan basuda ikom cin komai su kadai tinda tana dakin inna lami dole duk abinda zata nemowa yayanta suci Suma saita Basu.
Kawu bello Daya ga Hakan Saiya barta da lalurarsu ya zame Dan kuwa sauki ne ya zo masa.
Lalurar fara yiwa maamah din yawa tayi sbd ciyarda Yara da yawa bazata iyaba tinda ba Sanaa takeyiba gashi duk abinda tazo dashi din ya qare Dan Tama manta da anbude mata acct ansaka mata Koda Bata manta ba tayayama zata iya cire kudi tana cikin wannan kauyen dajin.
Tin tana boye gazawarta tana Fadi tashin ciyar da yaran duka har gazawanta ya bayyana Amma Kiri Kiri kawu bello yayi mata biris yabarta da 'yayansa tana wahala dasu Dan bazata iya samowa ta bawa nata yayanba su ta Hana musu Dan haka tinda tana zaune dakin mahaifiyarsu a rakube dole ta taimaka musu itama.
*******Tafiya tafara Nisa sun wayi gari ko suturar sakawa Neman gagararta da yayanta takeyi sun koma inda suka fito ga yunwa da azabar aikin wahala Dan haka ciwo yafara kokarin kwantar da ita.
Amatu data fara iya aikin wahalar sai tana kamawa mahaifiyar tata dasu suna samu suna Dan rufawa Kai asiri.
Duk halinda take ciki Babu Wanda ya taba ko kallanta da daraja a gidan bare a tausayawa rayuwarta a dubi marayun yayanta Dan haka take Dan sake dauriya tana dagewa Dan inganta rayuwar 'yayanta Amma jiki da jini dole Jikin ya fara kasawa sosai harta fara kwanciya ciwo kadan kadan saiga abu na Neman tsanani.
Amatu ce dole tafara fita da kanta Tana debo itace da zogalan da suke dafawa ana siyarwa.
Fara fitan Amatu shine yafi daga hankali da zuciyar maamah ba ciwontaba Dan kuwa tana tsoron abinda zai iya zuwa ya dawo Bata kaunar abinda zai tana daraja da rayuwar 'yarta,
Tinanin idan ta kwanta jinya me karfi Yaya rayuwar Amatu zata kasance acikin wannan gidan?
Yaya zata iya tsayawa ta taimaka gurin Bata kariya daga sharrin mazan gidan?
Komai zai iya faruwa da Amatu tana daga kwance Babu abinda zata iya yi...
Innalillahi wainna ilaihirrajiun,wannan tinanin kawai ke gigitata hankalinta yayi mummunan tashi harta Saka abin a ranta damuwa tayi mata yawa ciwonta sai qara gaba yakeyi.
Babu abinda yafara zuwa ranta da tinaninta sai komawa Abuja gidan Abeeda sbd Koda Allah yasa ciwonta bana tashi bane tasan tabar yayanta inda zasu tsira da mutunci su kuma su samu kariya da kulawa.
Wanna tinanin nata na sake komawa can din yake sake qarfafa a zuciyarta sbd Daman baaso dawowan nata ba ta dawo Amma Kuma babban abinda yake hanata zama acan din shine tayaya zataje tayi zaman dindindin gidan 'aminiyarta duk da ta Dade da zama 'yar uwarta tamkar jininta.
Wanna tinanin shine yake sake addabarta,takasa tafiya takasa Jin nutsuwar zama Dan haka abin ya taru ya sake mata yawa.
Su Amatu ma gaba Daya a tsorace suke da ciwon maamah din Dan kuwa a yanda suke ganin wainda iyayensu suka rasu a cikin wannan gidan almajirai suke komawa na karfi da yaji hakama lalacewansu yawa takeyi Dan haka tsoro ya kamasu Dan su tsoron ma irin wasu abubuwan Dake faruwa a gidan sukeyi sbd maamah datake Saka musu tsananin tsoron Hakan Tintini.
Rashin takamaimai shawara da madafa yasa suke cikin garari kullum Kuma suna waya sosai da Abeeda a yanzu sbd wayar data dawo da ita wadda aka Siya mata tin acan Amma bata iya fada mata halinda take ciki ba.
****Acikin wannan mummunan halin dasuke ciki kwatsam suka wayi gari da Kiran Husnah a wayar maamah din cewan Abeeda ba lafiya sosai.
Labarin shine Mafi tashin hankalin labarin Daya samu maamah sbd Abeeda Bata taba ciwon da harya kaita kwance ba Dan haka zuciyarta tayi nauyi da tsoron meya samu Abeedan,
duk da ita ma a kwancen take Amma ciwon Abeeda ya sata danne nata azaban ciwon ta fara kokarin Shirin tafiya Dan kuwa ita kanta Abeedan zataso ta farfado Taga Asmau acikin wainda suke zagaye da ita.
Halinda ta shiga na tsananin damuwa da kokarin boye nata ciwon akan son zuwa inda Abeeda da kwana biyu batasan inda kanta yake