Showing 51001 words to 54000 words out of 152002 words
Chapter 18 - AMATULMALEEK COMPLETED BY Mamuhugee.txt
tsokan kaza da ganda da da egusi.
Ajiyar zuciya ta sauke sbd bdai taso cin abinci me nauyi ba Amma Kuma tana Jin yunwa Dan haka zataje taci kadan saita sha fruits suyi saurin narkar mata dashi.
Sama sama sukai magana da maamah dataga gajiya a tareda ita tace taje taci abinci ta kwanta ta huta.
Miqewa tayi ta fito ta biya sashen mum Aisha ga mamakinta Bata Nan tinda yamma ta fita kenan itama Bata dawoba.
Fitowa tayi ta wuce ciki Kai tsaye kitchen ta nufa ta samu fruits din ta debo kenan saiga Abdul ya fito hakama Husnah Dukkaninsu Babu Wanda yaci abinci Daman dan haka dole ta bisu zuwa dining din Badan taso ba sbd tasan Dad din Husnah na gidan Kuma akwai yiyuwar cin abincinsu a tareda shi.
Zaunawa sukai dukkaninsu Abdul na magana da Husnah tana murmushi sbd firar Haydar ne sukeyi dukkaninsu sunyi waya dashi yau din.
Basu fara cin abincin ba qamshinsa ya doso su Dan haka kowannensu ya dakata tareda juyawa ga hanyar shigowa Banda Amatun data kasa juyawa taji gaba Daya abincin ma kaman bazai shiga cikinta ba to Amma batasan tayaya zata miqeba tabar gurin bayan zuwansa.
Qarasowa yayi sanye cikin Balenciaga sweatset brown qafafunsa ma sanye da takarman zaman gida masu taushin fata sbd tsadansu.
Yana isowa ya zauna ahankali tareda amsa gaisuwar su cikin nutsuwa
Sai alokacin itama Amatun ta Bude Baki cikin sanyi da nutsuwa ta gaidasa.
Bai lura da ita ba Saida tayi magana ya Dan dago kadan ya amsa Yana daukan ruwan Dake gabansa marasa sanyi sosai yakai bakinsa yasha kadan ya ajiye.
Abincin da Husnah ta zuba masa Shima ya kalla
Yanason tuwo Amma yanzu dare yayi masa da cinsa sosai Dan haka kadan Shima yaci ya buqaci tea.
Husnah Bata iya dafawa ba Dan haka Amatu ta kalla wadda ita Kuma Daman hanyar barin gurin take nema Dan haka ta miqe ahankali ta bar gurin zuwa kitchen.
Tana aikin tana Shan fruits dinta Daman shi tuwon taci kadan a dining,
Tana gamawa ta juye ta dauko ta fito
Koda takai tea din daga Husnah har Abdul sun tashi ba kowa saishi a gurin Dan haka a natse ta iso ta ajiye tareda zuba masa ta juya tabar gurin.
Dakinta Takoma brush kawai tayi ta kwanta Dan baccin takeji sosai a yau din.
ASH kuwa Daman yace Abdul ya samesa bayan sun gama cin abincin Dan haka Abdul Yana kwatanta gamawansa ya fito a natse ya nufi palonsa tareda knocking cikin girmamawa da sallama ya shiga bayan ya basa izinim shigowa.
Zaunawa yayi bayan ya sake gaida Dad din.
A natse ya qarasa wayarsa kafin ya kasheta gaba Daya ya ajiye gefensa ya Kalli Abdulhameed din cikin nutsuwa yafara fada masa yafara shirye shiryen tafiya makaranta zaibi Haydar can inda yake zuwa nxt month Dan angama komansa kadan ne abubuwan dasuka rage.
Godiya sosai Abdulhameed yayi cikin bayyanarda farin cikinsa tareda adduar Allah ya Saka da Khairan.
Koda ya fito yasan Yan matan sunyi bacci Dan haka dakinsa Kai tsaye ya wuce cikeda murna da farin ciki me tsananin gaske ya ringa nafila yana godewa Allah tareda yiwa ASH addua da iyayensa babah da maamah.
Washe gari lokacinda ya sanarwa da Amatu kasa riqe farin cikinta yayi ta rungumesa tana Jin dadi sosai tareda yiwa ASH din addua Dan kuwa zuwa yanzu ta tabbatarda ba Wani maganar aurenta dayake gabansa Dan haka itama zata dage tayi abinda yake gabanta kawai,
Maamah ma sosai tayi farin ciki Kuma dole Badan tanada yanda zatayi ba ta tafi har palonsa tayi masa Godia ta fito
Husnah ma tayiwa Abdul din murna sbd Haydar ze samu na gida a tareda shi Koda maganar auren Amatu da Dad dinsu ta Isa kunnensa aqalla tasan Abdulhameed zai tsaya ya kula dashi batareda ya shiga Wani halin ba duk da dai su haryanxu soyayyar kuruciya ce yakewa Amatun.
Cikin farin ciki yau sukai breakfast dinsu a dakin maamah tareda ita suna gamawa Farha tazo tini Dan haka Amatu fitowa tayi ta Takoma bedroom dinta ta shiga wanka,
Kafin ta fito duk kayan da aka siyo jiyan Farha ta jera komai a inda ya kamata dakin ya sake sauyawa zuwa na budurwar da Bata rasa komaiba na duk Wata luxury rayuwa.
Dayake tayi latti ba Bata lokaci ta shirya kaman dai yanda kusan kayan duk dogayen riguna ne masu kudi
Acikinsu ta shirya suka fito Kai tsaye mota suka shige zuwa school.
Abinda yake bata mamaki da kawo mata Farha da Akai shine me zatai mata?
Haka kawai zata ringa rakata makaranta su dawo?
Bata tambayarba sbd batama ga Wanda zata tambaya ba hakama ita kanta Farha din yanda take kula da ita tana nuna mata wasu abubuwan da Bata saniba yasa take ganin ba takura sosai a yawonta da ita.
Kwana biyu duk suka fita sai anyi siyayyar abubuwan buqatanta harma da Wanda Bata buqatan,
Farha kaman designer ce kaman Kuma beauty designer,hakama abinda ta lura dashi shine kodai qanwar Mr Jameel ce Kokuma yar uwarsa sbd akwai kusanci a tsakaninsu hakama kusan komai shi Farha din ke kira Yana Bada kudin da kamar baisan zafinsu ba dayake kusan shine bankin ASH TALBA.
A cikin kwanakin dasukaita zuwa suna wucewa Farha ta Saka Amatu Dan fara sakin jiki da ita sosai duk kamun kan Amatun da rashin son mutanenta Saida ta sake da Farha duk da ta girmeta Amma Sam ba wanna tsakaninsu hakama a aynzu data fara sabawa da amfani da kayan da aketa siyowan taji tafi sakewa a cikin dogayen rigunan dasuka zama suturarta a yanzu,
Ta bangaren cikin gidan kuwa sosai kowa ya zama busy shiyasa kusan kowa a gajiye kowanne dare ake kwantawa,
Abdulhameed shirye shiryen tafiyarsa kawai yakeyi sosai hakama maamah duk Jin takeyi ta shiga sanyi sbd tinda ta haifesu Bata taba nesa dasu ba Koda na kwana biyu ne koyaushe tana tareda yayanta duk inda zasu Dan haka yanzu dazai tafi wata qasa duniyar Jin takeyi kaman bazai iyaba sedai tinowa da Haydar na can Kuma zasu kula da juna sosai yake sata Jin hankalinta ya kwanta,
Husnah Kuma exams ne a gabanta shiyasa ta kasa gane kanta sosai ta dage sbd kusan Amatu sosai take kawo wuta a nata karatun Dan haka yanzu da Bata kaunar abinda ma zaisa Dad dinta ya duba cigaban Amatu akan nata Sam Bata kaunarsa.
*****Ta bangaren ASH TALBA kuwa kusan kullum da Amatu ta gane Yana shan tea da dare koyaushe kafin ta shige saita dafa ta Kai dining a flask ta ajiye ta shigewarta,
Shima Daya fahimci yanzu kullum ana aje masa sai ya rage fitowa cin abinci tareda su Sai ya gama komai zai fito yasha ya koma ya kwanta.
Mum Aisha tayi tafiyar dole wadda take Jin idan batai ba zata iya fashewa a cikin gidan sedai a Tararda gawarta Dan haka tayi tafiya kanta ya fara warwarewa kafin ta dawo tasan yanda zatayi da yar cin Amana maamah wadda taci amanar aminta da zumunci.
Tafiyar Abdul tazo daidai da tafiyar Husnah porthcrt mahaifiyar Faisal ta rasu Dan haka sosai hankalinta ya tashi haka itama Maamah sosai ta shiga damuwa ga exams sunayi a lokacin,
Ranar da Abdulhameed ya wuce AmatulMaleek Tasha kuka a jikinsa kaman shine yayan itace kanwar
haka ya ringa rarrashinta Yana Bata qwarin gwiwan fuskantar rayuwarta batareda tsayawa kebe kanta ko takura kanta akan aurenda ASH Kila ya manta dashi.
Maamah ma taji dadin shawarar Daya bawa Amatun sbd so take Amatun itama ta manta da Wani maganar auren harsu samu Abeeda ta tashi Dan Tana tashi tasan ASH TALBA bazai qara ko kwana da auren Amatun ba zai sallameta asiri rufe batareda Abeeda ma tasan anyi auren an warwareba.
Abdulhameed ya tafi yabarsu da kewansa Dan haka maamah dole cikin kwanakin ta Maida kulawanta da tattalinta ga Amatu wadda ta shiga damuwa sosai na tafiyan Abdul sbd shine abokinta Kuma abokin shawararta.
Farha da maamah ne suka dage harta sake batareda ta Dade cikin damuwarba sbd exams dinta.
ASH TALBA tin washe garin rasuwar umman Faisal yaje yayi gaisuwa ya dawo,
Husnah ma itace ta riga Amatu gama exams dinta Dan haka babu Bata lokaci tayi Shirin tafiya porthcrt Kuma tareda maamah zasu itama tayi gaisuwa.,
A bangaren husnah da gangan ta da tafiyar maamah din sbd idan suka tafi gidan ze Kona ba kowa sai Amatu da masu aiki wainda suke bangarensu daban,cikin mansion dai ze kasance Amatu ce kawai Dan haka tsoro da firgici bazai taba barinta yin karatun da zatai exam me kyau ba sbd itama Bata karatun exam din ya lalace ne kwata kwata daga ranar da umman Faisal ta rasu.
Ita kanta Amatun da zasu tafi hankalinta tashi yayi sosai da barinta da zaayi ita kadai a gidan sosai ta shiga damuwa Amma batai magana ba sbd tasan ma ba lallai atafi da ita ba Kuma ko taje Yan uwan Faisal din da yawa basa Sonta ganin itace ta Hana ya auri Husnah ko gaisuwar rasuwar txt tai masa har so uku duk bayan awanni saita masa ta tura masa sbd bazata iya kiransa ba tin ranarda aka daura aurenta masu sake magana ba baice mata komaiba ko a waya haka itama batasan me zata ce masa ba,
A makarantar ma sosai suke wasan boyo da juna kaucewa juna sosai sukeyi basa son su Hadu.
##MAMUH#
Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#
AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar
31
Su Husnah na hanyar zuwa airport ta Ciro wayarta daga handbag dinta shedan na ingizata ta Dan shakka Amma Kuma zuciyarta na sake turata ta Nemo numbern Naufal ta tura masa txt din idan Yana son Neman gafarar AmatulMaleek ita kadaice a Mansion ko Babu kowa Se masu aiki hakama Dad dinta baya gari.
Tana tura sakon ta mayar da wayarta handbag dinta ta rufe tareda kallan maamah da itama itan ta kalla cikin kulawa ta saki murmushi tana Dan kwantawa jikin Maamah ahankali tace
"Maamah Allah yasa mum dina ta samu lafiya ta dawo cikinmu Ina kewanta sosai."
Numfashi me dumi maamah ta sake tana amsawa da "Amin ya Allah" zuciyarta na Dan nauyi sbd duk lokacinda ta Tina da Abeeda da auren mijin Abeedan Dake kan tata 'yar Jin takeyi hankalinta da duniyarta na jijjiga sosai cikin tashin hankali da damuwa.
Suna Isa airport Basu Wani jimaba suka hau jirginsu ya tashi Husnah na sauke ajiyar zuciya me sanyi.
Ranar da suka tafi din a school Amatu ta wuni Se magrib ta dawo gida cikin sanyin jiki tayi wanka ta fito taci abinci Takoma daki ta kwanta zazzabi na Neman rufeta sbd kadaici da rashin nutsuwar zuciya.
Bacci Rabi da Rabi tayi har tasamu asuba tayi ta tashi tayi sallah sai alokacin ta koma baccin kirki.
Bacci tayi cikin nutsuwa da Kwanciyar hankali har qarfe Tara kafin ta tashi tayi wanka ta fito daure da towel ta zauna gaban mirror ta shirya ta Saka undies kafin ta Saka doguwar rigar army green ta fito qamshinta na tashi ahankali cikin sanyi ta nufi kitchen Bata nufi dining ba Dan batajin zaa jera abinci tinda ita kadaice sedai ga mamakinta tini aka jera abincin breakfast dinta komai da komai Yana kan dining din dole can ta koma taci abincin tana gamawa ta miqe Takoma daki ta sake Dan gyarawa ta fito.
Dayake ko Farha kwana biyu Bata Nan ita kadai ta shiga mota driver ya jata zuwa school.
Acan ta wuni yauma sai yamma ta dawo tana gama komai ta shige ta rufe daki ta kwanta.
Kwana hudu da tafiyarsu maamah ta gama exams dinta ita Dan haka yau din data gama da wuri ta dawo tana shigowa mansion din ana Kiran laasar.
Wanka tafara yi Tayi sallah tana Jin nauyin dayake kanta kaman ya sauka tinda ta gama jarabawanta.
Abincin yau dinma baa dining taci ba a plate da trey aka kawo mata ta zauna Palo tana ci tana Dan kallo Sama sama.
Ko data gama da kanta takai kayan kitchen ta gyare gurin ta zauna tana Dan duba wayarta har magrib ta tashi ta shige daki tayi sallah
Tana idarwa Bata fitoba ta zauna a sofa tana waya da maamah suka jima suna wayar har Akai sallan ishai ta tashi tayi ta gama ta fito taci abinci kadan tareda Dan dakatar dasu Farida suka tayata fira a palon har 9 kafin suka tafi itama ta tashi ta shige bedroom dinta.
Tubewa tayi ta daura towel tareda shigewa wanka.
Tana cikin toilet taji kaman tashi Bude kofan dakin da rufewa
Gabanta yayi mummunan faduwa ta kashe ruwan wankan tana saurarawa.
Shiru Babu motsin komai Dan haka ta sake kunna ruwan tana qarasa wankan cikin faduwan gaba da mamaki.
Tana gamawa towel ta janyo ta daura tareda riqesa gamgam ta fito toilet din gabanta na tsananta faduwa.
Tana Bude kofar toilet din ga mamakinta sai Taga wutan dakin a kashe bayan tasan a kunne tabarta.
Hakan data Gani ya Sanyata sake qanqame towel dinta tana Neman juyawa toilet da sauri Dan ta rife kanta Amma taji mutum na kokarin fitowa daga gefen wardrobe na kayanta cikin matsanancin firgici da tashin hankalinta Dake barin jikinta ta qwalla Wani irin ihu me qarfin gaske da Gidan gabaki daya ya dauka.
Cikin sauri Yayi saurin sakinta jikinsa na rawa tareda nufar kofa ko Gani bayayi ya buge goshinsa da qarfi a kofa take ya saki Dan qaramin ihu Shima Amma Bai tsayaba ya fice da Wani irin sauri yabi ta kofan kitchen ya fita ya zagaya zuwa bayan sashen mum Aisha da akwai fence a gurin me tsayi da wire na wuta Amma dayake yasan inda ake zuwa ayi disconnecting Saida yayi disconnecting bayan shigowansa.
ASH TALBA after 9 na dare ya dawo gidan daga tafiyana Dan haka Yana shiga Shima wankan yafara shiga sbd rage nauyin tafiyar da yayo.
Fitowansa wanka kenan yaji ihun Daya ratsa kunnuwansa Bai fara kawo tinanin komaiba saida ya Tina da cewan akwai 'yar mutane a gidan Kuma Sam ya manta da Hakan Dan haka da sauri ya janyo bathrobe blue ya Saka kan towel Dake qugunsa ya fito dagashi sai slippers dinsa masu taushi ya nufi hanyar palonsu da sauri Yana jefa idanuwansa kan agogon Dake palon yaga karfe goma sha Daya Dan haka da sauri ya qarasa Yana sake jiyo ihunta Wanda take ya sake shiga mamaki da qara sauri.
Yana isowa dakin Bai tsaye komaiba ya Bude tareda shiga Yana nufan inda take jikin kofan shiga toilet tanata ihu dukkanin jikinta na Wani irin rawar tashin hankali Tama fice hayyacinta gaba Daya.
Wutan dakin yafara kunnawa Kai tsaye tareda nufarta Yana kokarin kamota daga jikin bangon tana sake qanqamewa tana jikinta na jijjiga,
Kafin ma ya sake wata motsin zuwa gareta tini jikinta ya saki zata zube a gurin ya tarota da hannu Daya Yana Saka Dayan kan kirjinta ya dafe towel dinta dayake warware Yana Shirin sauka daga kirjin.
Numfashi ya sauke ahankali Yana kallan dakin ahankali Yana duba Menene matsalar,
A bayan jikin wardrobe yaga shatin takalmin babba a gurin sbd tsaftar gurin yasa shatin qurar qasa Dake jikin takalmin ya maqale.
Wani sarawa kansa yayi batareda ya gasgata abinda ya ganin ba bare tantancewa Dan bama zai yiyu ace Wani ya iya shigowa Nan dinba.
Kan fuskarta da take tayi ja ya dawo da idanuwansa ya sauke ya kalleta dakyau ahankali tareda dauke idanuwansa Yana daukanta gaba data Dan kuwa tabbas idan abinda yagani Kuma yake tinani mutum tagani Kokuma aljan.
Fitowa yayi da ita daga dakin ya nufi hanyar palonsa da ita har lokacin batasan ko matsi Batayi.
Kofar bedroom dinsa ya tsaya cak da ita sbd bayajin zai iya shiga da ita dakinsa Bai Dan haka ya juyo palonsa ya kwantar da ita kan kujera ahankali Yana dagowa towel dinta na fara zamewa da sauri yakai hannunsa ya dafesa Yana juyar da fuskarsa tareda miqewa gaba Daya ya bar gurin.
Bedroom dinsa ya shiga Kai tsaye ya Bai tsaya shafa komaiba ya Saka pyjamsa dinsa na bacci masu Dan kauri sbd bayason sanyi sosai ya dauki wayarsa ya fita Yana Kiran Jameel akan gaba Daya a bincike Mansion din ciki da wajensa.
Jameel na Jin Hakan ya sanar da securities Dan haka tini suka kunna shegun fitilinsu masu shegen haske duk da akwai haske koina gidan.
ASH din Bai fada musu abinda yake faruwaba Kuma baida niyar fadan Amma ya basu Daman duk abinda suka Gani su harbesa ko menene Dan haka suka hau dubawa a shiryensu ba sauki ba Imani suna gani zasu Ma koma Menene ko waye ruwan bullet dinsu.
Sosai suke bincike gidan ciki da waje Amma Basu ga kowa ba ko komaiba sedai sunga anyi disconnecting security electronic wire din gidan an kashe gaba Daya.
Ganin haka suka Ankara da dai Wani ne ya shiga gidan cikeda mamaki da bacin ran Wanda yakeda wannan qarfin halin suka sake bazama suna sakawa ransu koma waye wlh saisun kamasa.
AmatulMaleek cikin firgici ta Farka tasake Bude Baki zatai ihu sbd batasan inda ma take ba ga ba haske sosai a palon,
Tana Bude Baki yakai hannunsa na dama Dake kusa da ita ya Dora a bakin tareda sauke mata idanuwansa a karo na biyu Yana mata kallan da bana fizge ba,
Rawa jikinta keyi sosai ta Dora tafin hannuwanta akan nasa dayake kan bakinta zata janye hannun nasa tayi ihun sbd Bata ganesa ba a firgice take har lokacin,
Saukan hannuwanta akan nasa yasaka shi janye nasa hannun Yana kallanta zeyi magana ta fasa kuka me qarfi sbd gane waye a tareda itan tana Kiran sunan maamah da Abdul harma da Haydar.
Shiru yayi duk kuka da ambatar sunanyen datakeyi Bai motsaba kaman yanda Bai waiwayo ya kalletaba sbd dole tana buqatan kukan ta fita shock data shiga,
Ta bangare daya kuwa tinani be barkatai a ransa gameda lamarin,
Sedai Kuma anyi na karshe Dan kuwa Shima Saiya kama ko waye da hannunsa idan kuwa Wanda yake zargi ne tabbas zai Basu mamaki me girman gaske.
Kuka da tashin hankalin data shiga ya Sakar mata zafin jiki tana ji tana Gani yabarta a palon ya wuce ciki bayan ya rufe kofan palon duk da yasan koma waye ko wace giyar yasha kaddara bazata kawosa har palonsa ba.
yanda Amatu Taga Rana haka Taga Daren a firgice ta kwana,
A tsorace ta kwana,cikin rawar jiki da damuwa tareda tsananin buqatan mahaifiyarta ta kwana,
Sai guraren asuba baccin wahala ya dauketa me Dan karfi Dan haka Koda ya fito da asuba ganin tana bacci qyaleta kawai yayi ya koma ciki a cikin gida yayi sallan asubar ranar sbd bayajin zai iya fita yabarta bayan baa samu kama koma waye ba akwai yiyuwar Yana