Header Ads
Showing 141001 words to 144000 words out of 152002 words

Chapter 48 - AMATULMALEEK COMPLETED BY Mamuhugee.txt

Ads the beginning of article before Image

11 Jun 2024

890

Ads at the middle of Article

masu gida akeci akanta.


Shiru kawai Abdul yayi sbd Bai dauka tinda ya amince ba zaace zaa daura auren yanzu ba.


Fitowa yayi yaje ya sanar da maamah wadda itama zataso Daman a daura auren Husnah ta samu me kulawa da ita yanda ya kamata tinda su dole yanzu zasu bar Nan din.


Albarka ta sakawa auren tana danne damuwarta da halin datake ciki ita tareda fada masa ya riqe yar mutane da kyau da kulawa.


Mum Aisha na ganin lokaci ya sake matsowa ta fito a rikice ta koma gurin ASH ta ringa kuka tana rokonsa Amma Sam baima Kalli inda takeba Saida su kawu suka shigo kallo daya tayiwa dukkaninsu batareda ma tasan waye nata angon a cikinsu ba ta fasa kukan baqin ciki sbd ganin su dukan kaman baqin aljanu kowannensu karnin shaddarsa kawai zai iya sumar da ita,ita datake shafa turaren da kudinsa zai ciyar da kaf gidan Sanda Fulde din na tsawon kwanaki koma satittika Amma ace aure zatai da wainnan fataken.
Ficewa tai tana Jin Hawan jininta na tashi da baqin cikin ganinsu kawai.


Tana ficewa kawu ashiru ya bita da Satan kallo Dan shi gaba Daya Sonta ma qara shigarsa yakeyi,
'dan nata ma da ake fada shi taje dashi agolanci zai amshesa ya hada da nasa manyan yayan ya riqe.




Husnah na daki ta rasa meyake mata dadi,ta rasa wa zata kira wa zata kama gashi Haydar yace tayi zamanta daki karya fito sai komai ya kammala sunga abinda ya faru tukuna.


Maamah ma tana dakinta zaune yanzu tinanin Amatu ne Kuma yake rufeta gashi dai ma zata koma kauye tabar Amatu anan karshe abinda taita tashin hankali Akai tana ji tana Gani Amatu zata cika gidan da yayan ASH batada ta cewa,
Amma Kuma har lokacin mamakin samun cikin Amatun Bai Dena jijjigata ba,
Tayaya ASH ya iya kebewa da Amatun har cikin ya samu?
Suna cikin gida Daya yarta tayi ciki harya bayyana Bata saniba,
Kunyar kanta da damuwa me nauyi ce ta sake danne zuciyarta gashi yanzu kiri Kiri tana kallo zata tafi tabarta zaman auren da Basu shirya ba.




Karfe goma sha Daya da mintina aka fara daura auren Abdulhameed Sanda Fulde da Husnah Ashraf Talba akan sadaki Naira dubu dari biyu Wanda Abdulhameed dinne ya biya abinsa da kansa mutane qalilan ne suka sheda a masallacin gidan nasa,
sai Kuma na maamah da kawu bello akan sadakinsa da Shima shine ya biya abinsa dubu Tara.
Na mum Aisha da kawu ashiru shine na qarshe da aka daura akan sadakinsa Shima Daya biya dubu Tara Dan dubu goma goma aka yanka musu sadakin.


Mum Aisha ko da aka gama daurin auren ciwonta ya tashi gaba Daya na hawan jini dole aka kwasheta zuwa asibiti,
Maamah kuwa kukan datasha kaman qaramar yarinya ita kadai cikin daki tana Jin baqin cikin su kawun Dan batasan ma inda zata fara zama da matansa ba da Babu hakuri ko hankali a cikinsu ba ko kadan,
Da anbarta ba aurenma zata iya komawa kauyen tayi zamanta Amma auren baida Wani amfani da girmanka.




Husnah na daki duk tayi zuru cikin matsanancin halin tsoro da fargaban Menene makomarta,
Yanda zuciyarta ke bugawa kaman zata fado da tsantsan tashin hankali ya Saka hannuwanta ma rawa sukeyi tana dai zaune cikin fita hayyacinta aka Bude kofar bedroom din nata aka shigo...


Haydar ne cikin cikin fararen manyan kaya da Dan adonsa Dan inganta auren yar uwarsa da nuna farin cikinsa Koda kuwa ana cikin damuwa ne.


Ganinsa ya Sakata juyo da jajayen idanuwanta ta zuba masa bugun zuciyarta na tsananta har yayi yawan da ba'a cika so ba.


Qarasowa yayi da sauri Dan ganin ta kusa rasa bugun zuciyarta yana isowa ya riqeta Yana cewa


"Andaura aurenki da Abd.....
Bai qarasa ba Idanuwanta suka juye tana sauke numfashi me qarfi ta sume a jikinsa Dan sanyin Daya ratsa kunnuwanta da zuciyarta haryafi karfin bugun zuciyarta a lokacin.


Tarota yayi jikinsa hankalinsa na tashi ya fara Ambatar sunanta da qarfi Yana Dan jijjigata.


Daukota yayi gaba Daya a ya Sauko zai fita da ita zuwa asibiti Abdulhameed Daya baro gurinsu kawu ya gansa da sauri ya qaraso Yana tambayar abinda ya sameta.


Kasa amsawa Haydar yayi Yana kallan fuskanta.


Hannuwa Abdulhameed din ya Saka ya karbeta daga jikin Haydar din Yana cewa


"Mu koma a kira likita yafi zuwan asibiti tinda kaman Suma ne"


Juyawa sukai suka koma saman tana jikin Abdul Daya daukota kaman Bai dauko budurwa ba kaman yarinya ya dauko.


Bedroom din nata suka koma ya kwantar da ita khaltume ta kawo ruwa da sauri tace a fara yayyara mata a Gani.


Abdul dinne ya Karba ya zuba mata a fuska Yana ambatar sunanta har lokacin tana jikinsa.


Ajiyan zuciya tafara saukewa tana jerowa kafin ta Bude idanuwanta ahankali tana sake sauke ajiyan zuciya Wani bayan Wani.


Khaltume na ganin Hakan ta sauke numfashi itama hakama Haydar shi kansa Abdul din ajiyan zuciya ya sauke.


Akan fuskar Abdul ta sauke idanuwanta ko kyaftawa Batayi jikinta gabaki daya ya matu Bata iya motsa ko hannunta ahankali ta Bude bakinta kuka na Neman kwace mata tace


"Thank you"


Kalman data furta ya Yanke zuciyar Haydar gaba Daya har hawaye suka ciko Idanuwansa ace tana yiwa namiji godiya Dan ya aureta.


Shi kansa Abdulhameed kalman yankan zuciyarsa tayi Dan haka ya dora hannunsa ahankali kan bakinta tareda girgiza mata Kai yana kallan cikin idanuwanta yace


"Dad dinki Bai Bani aurenki Dan kice thank you ba Ya bani ne sbd yasan kinada mahimmanci me girma a zuciyarsa da bazai iya Bada ki kauyen ba"


Kalamansa suka Saka hawayen cikin idanuwanta saukowa tana Jin zuciyarta na samun nutsuwan fara dawowa hayyacinta idan har da gaske tanada sauran mahimmanci a zuciyar Dad dinta.


Haydar juyawa yayi ya fita Dan amsa wayar iyayensu na porthcrt da yanzu ne suka gama magana da ASH ya sanar dasu auren Husnah din.


Bayan ficewan Haydar Shima Abdulhameed din sake rarrashinta yayi da magana ta sake dawowa hayyacinta kafin ya fice daga dakin tabi sa da kallo tana Jin yanzu Kuma da aka daura nata auren dashi batasan tayaya zasuyi zaman aurenba da Wanda ta girma duk da mantawama tayi da Hakan kwata kwata Amma dai koma yayane zuciyarta tana samun Nutsuwa da kulawansa tin kafin su zo yanzu tun suna Yara.


Ana gama daurin auren da duka Wani gaishe gaishe Akai Sallahn Azahar ASH ya shige.


Abinci yaci sama sama ya shige sashensa Babu Wanda ya sake ganinsa sai laasar ya fito cikin Shirin fita Bai buqatan driver sbd Mr Jameel Baya Nan da kansa yaja mota ya fita Kai tsaye gidan Farha ya nufa.


Ko Daya Isa motar Mr Jameel tana gidan Shima yanata ganin shege a gun Farha da gaba Daya ya rasa gane kanta duk ASH din ya ja masa.


Ganin Mr Jameel ya Saka ASH Dan kamewa Shima Mr Jameel din ganin ASH ya sakashi mamaki Amma ya boye ya danne mamakin tareda masa barka da zuwa ya masa jagora zuwa ciki Dan shi yafi awa Daya a harabar estate din Amma Farha taqi fitowa Dan haka zuwan ASH zai basa Dama da saukin lamarin tinda shi dole a iso dashi ciki sbd matarsa datake ciki.


Kofar palon yayi knocking tareda danna door bell lokaci daya


Karima na palon Dan haka Koda taji door bell din zuwa kawai tayi ta Bude
Gani Mr Jameel da ASH da kansa ya Sakata saurin yin gefe kanta a qasa cikin tsananin girmamawa ta musu sannu da zuwa tana gaidasu.


Lafiyayyar Palo ne me girma Daya Hadu sosai Dan haka guri Mr Jameel ya nunawa ASH din ya zauna Yana sake Saka kiran numbern Amatun a karo na kusan dari da Wani abun Bata dagawa karshe ma wayar a kashe.


Anty Farha na dakinta tana Shirin fita tareda karima siyayyar wasu abubuwan buqatan Amatun Dan Mr Jameel din dayake waje zata Saka ya kaisu ya dawo dasu Dan haka Bata San da baqin ba Saida ta fito a shirye sai ganin the great ASH TALBA tayi zaune palon Ya gauraya musu numfashin palon gaba Daya da qamshinsa me sanyi da gigitarwa.


Rikicewa tayi sbd ba zatan ganinsa da kwarjinin Daya cike musu gurin dashi Dan haka murya duk a rude ta Dake suka gaisa tace bara ta kira Amatu.


Shiga tayi dakin Amatun ta Tararda tana wanka ta fita ta sanar masa tana wanka.


Mr Jameel da duk ya gama susucewa da ganin Farha din fita yayi daga waje itama Farha din text tayiwa Amatu cewan ASH TALBA na gidan ta bi bayan Mr Jameel karima na bayanta suka fita bayan ta sanar masa Amatun zata fito.
Suna fita Mr Jameel ya juyowa Yana kallanta ta daure fuska tana sake Jin zafinsa na qin sanar mata tareda ASH din sukazo bare Amatu ta sani.




*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070


Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#




AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar






79
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs💯🔥👍
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku💯👍*


MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI'IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER


08142800199
07068558096




*************
Amatu na fitowa wanka a natse ta zauna ta goge jikinta tareda Shafa Mai da turare ta Saka Riga da wando na bacci masu santsi da tsada ta Saka huka mara nauyi ta ziro slippers ta fito Dan Jin shiru gidan da Kuma ruwan datake buqata ta Bude kofar dakin ta fito tana Jin qamshin dayake shiga hancinta Yana Sakata mamakin jinsa sbd tasan bame yiyu bane Jin wannan qamshin a gidan nan Kuma a daidai wannan lokacin.


Tsakiyan palon take sake kusantowa tareda Bude Baki cikin sautin muryanta me nutsuwa ta qwalla kira Kiran Karima.




Tinda ta ya jiya Karan Bude kofar bedroom da rufewa ya dago kansa a natse ya zubawa hanyar dayaji motsin idanuwansa Dake galabaice da buqatan ganinta harta fito daga hanyar bedroom din tana shigowa palon dakyau idanuwansa akan cikinsu Dayake gabanta ya koma Yana Jin Yana sake macewa akanta kowane lokaci da zai ringa Dora idanuwansa akanta.


Bata lura dashi ba Saida ta kawo kusan gab dashi idanuwanta suka sauka akansa cikin sauri ta tsaya cak tareda yar razana sbd Bata taba tinani ko tsammanin ganinsa ba Tako Ina a gidan.


Juyawa tayi ta Kalli kofar kitchen tareda kallan hanyar bedroom din anty Farha kafin ta Dake Dan janyewa gefe daga gabansa tana dauke kallanta akansa shikuma Yana sake zurfafa nasa kallan akanta tareda miqa hannunsa Daya cikin sanyi da nutsuwa yayi mata sallama Yana sake miqa mata hannun idanuwansa akanta.


Bata Kalli hannun ba ta Dan koma gefe daga nesa kadan dashi ta zauna a natse tareda dagowa ta gaidasa kaman yanda take gaidasa a Baya Babu sakewa Babu alaman sabo ko wata shaquwa da kulawa.


Hannunsa data bari a gurin kaman ma Bata Gani ba ya kalla tareda dawo da hannun Yana kallanta ya amsa gaisuwar tareda tasowa ya dawo inda take ya zaune sosai jikinsu na haduwa ya kamo hannunta Daya a sanyaye ya Bude Baki yace


"Girman laifin Ashraf yakai har haka ne?
Hukunci Zaki masa?
Ba Zaki sassauta ba ko kadan ne?


Hannunta Daya kama ta zare ahankali cikin nutsuwa batareda ta dago ta kallesaba ta girgiza masa Kai kawai ahankali alaman ba komai datakewa fushin.


Tsayawa yayi kallanta sbd gaba Daya ma taqi kallansa hakama taqi nuna fushin nata ko bacin ran nata yasan yanda zai Bata hakurin ya rarrasheta.


Miqewa tayi tana kokarin tafiya kitchen ta dauko abinda ya fito da ita ta koma daki,tana taku Daya ya riqo hannunta tareda sauke numfashi da ajiyan zuciyan masu sanyi jikinsa na mutuwa ya miqe tsaye a hankali ya dawo gabanta ya tsaya cikin kulawa ya janyota jikinsa tareda ya Bude Baki da Wani irin sauti mara hayaniya ya furta


"m sorry"


Rintse idanuwanta tayi ahankali tana Jin radadin zuciyarta na raguwa sedai Kuma batajin zata iya barin ya Ragu din tinawa da quncin data shiga akan shariyarsa.


Sai data Dan sauke numfashi a zuciyarta kafin ta dago idanuwanta masu rudasa ta kallesa cikin sanyinta kafin ta janye jikinta gaba Daya tana Dan dauke idanuwan nata akansa ta Bude Baki tace meyasa yake cewa sorry ita Babu komai fa daya mata.


Hakan data fada ya sakashi sake shiga damuwa Dan maganan yakeso suyi Amma tana toshe masa hanya.


Kitchen ta juya ta tafi ta dauko ruwanta ta fito har lokacin Yana tsaye hanyar dakinta take kokarin nufa ya sake takowa ya kamo hannunta tareda rungumota ta Baya cikin sanyi yace


"Please LA""


Shiru tayi batace komaiba
Ya sake zagayota da hannuwansa Yana fora hannuwansa akan cikinta Yana shafawa Yana Jin kaman ya Bude kirjinsa ya Sakata cikin zuciyarsa ko zuciyan ta samu sassaucin azaban Sonta take ji.


Ajiyan zuciya ya sauke hannunsa na kan cikin a sanyaye tace


"ASH is really sorry"


Hannunta ta Dora akan hannunsa ahankali Wanda Hakan ya Sakasa Jin sanyi da Wani irin nutsuwa sedai kafin ya Bude idanuwansa yaji ta janye hannunsa daga cikin nata tana janyewa gaba Daya daga jikinsa ta juyo batareda ta kallesa ba ta sake maimaita masa ba komai ya Dena damuwa da maganar.


Wannan Karan kusan abinda yake ranta na fushi ya Dan bayyana tareda hawayen da suka ciko idanuwanta masu radadi duk yanda taso dannewa da boyewa.
Ganin fushin datai Yana son bayyanar masa ya Sakata wucewa kawai bedroom dinta ta shige ta rufo kofar sbd batason yasan tana cikin quncin abinda ya mata Dan Bata buqatan basa Daman wanke kansa.


Hanyar data bi ya zubawa idanuwansa da suka sauya take sbd ganin hawayen Idanuwanta sun rikita masa lissafi.


Baya keta iyakar da Bata kamata ba da Babu abinda zai hanasa shiga dakin ya sameta Amma ba gidansa bane ko da tana matarsa bazai iya shiga kuryan ba.


Zaunawa yayi cikin tareda daukan wayarsa yana Sake Kiran wayarta Amma taqi dagawa Dan haka ya rubuta mata Sako Amma still ba reply ba motsinta.


Shiru yayi kansa na daukan nauyi kaman yanda zuciyarsa tayi nauyin.


Bazai iya sanin zaman awa nawa yayi ba a palon har sai da su anty Farha suka dawo itama anty Farha din tayi mamakin ganinsa shi Daya a palon Dan haka suna shigowa ficewa kawai yayi.


Yana fitowa harabar gida mr Jameel Dake tsaye kaman an dasashi a inda yake sbd abinda Farha ta masa Yama rasa inda zai Saka ransa,
Kallansa ASH yayi da idanuwansa da sukai Dan ja Shima ASH din ya dago ya kalla da nasa idanuwan kowannensu na kokarin boye damuwarsa.


Sai da safe Mr Jameel yayiwa ASH din bayan sun shiru kowa ya rasa abin fada.


Mota ASH din yaja yabar gidan ya kama hanyar gida.


Mr Jameel ma tada tasa motar yayi ya nufi gida.


ASH na Isa gidan Kai tsaye shigewa bangarensa yayi Daman Kuma dare yayi tinda kusan goma ta wuce.




Husnah da daddaren Haydar ne yazo da kansa suka ci abinci tare sbd idan ba Wani ya tsayu akanta ba ba lallai ta iya cin abincin ba sbd har lokacin tana cikin damuwa da sanyin jiki.


Maamah kuwa Abdul ne yaci da ita mum Aisha kuwa da aka sallamo tana daki a rufe Babu Wanda yasan halin datake ciki.


Su kawu kuwa a matse suke da su koma kauye amarci kawai suke Jira su fara darza.




Bayan ficewan ASH anty Farha dakin Amatu ta nufa Kai tsaye ta Bude tana ambatar sunanta ta ganta zaune tsakiyan gadonta idanuwanta sunyi jajir da alama kuka tayi sosai sbd Radadin abubuwan da suka dawo mata na wahalan datasha a wannan Dan lokacin da ciki.


Qarasowa anty Farha tayi tana rarrashinta tareda Bata hakuri akan ASH din ta sauko Hakan tinda yace ayi hakurin.


Shiru kawai Amatun tayi sbd haryanxu bataji zuciyarta ta sassauto akansa ba.


Hakanan anty Farha tayi rarrashinta da ban hakurin ta fito ta wuce dakinta
Ita Kuma kwantawa tayi duk da baccinta ya qaurace tin dazun.




Washe gari da zazzabi Amatun ta tashi sbd kukan datai da daddaren dakuma rashin samun baccin Daren Dan haka ko data tashi sai ciwon Kai yazo kafin daga baya zazzabin.


Dr beeba anty Farha ta kira sai gashi Dr beeba din Tai kira Mr Jameel ta sanar masa sbd ASH ya Bada umarnin komai Daya danganci Amatu da cikinsa ya ringa sanin komai koma Menene.


Ganin ba shine ya kirata akan taxo Amatun ba lafiya ba yasa ta kira ta sanar kafin ta tafi din.


Mr Jameel na Jin Hakan ya taho mansion din Dan dama Yana Shirin tafiya can dinne sbd su kawu dasu mum Aisha da zasu wuce Yola.


Yana isowa kusan komai na tafiyansu ya kammala su kawu har sun fito mum Aisha da maamah ma kusan duk sun fito lafiyayyar motar mansion dince zata kaisu Yola.


Mum Aisha jiran kawai takeyi su Isa yolan subar Nan ko kallanta kawu ashiru yayi saita Saka Yan Sanda sun makantar dashi Dan kudinsa na sadaki harda qari Mai yawa zata basa ya saki auren ya qara gaba.


Maamah kuwa abinda ta sani shine zata koma gida ne ta zauna Amma ba Wani zaman auren da zatai da kawu bello sbd tasan ko gurin Sakata baidashi.


Husnah tayi kuka sosai na tafiyan maamah din hankalinta ya tashi ta yanda zata zauna ita Daya a gidan yanzu ba kowa.


Yanda ta daga hankalinta ne Haydar yace su shirya gaba Daya su rakasu maamah din Yola su biyo jirgi gobe su dawo.


Dayake Daman da Abdul zaa tafi tin farko sai tafiyar ta qara yawa Jin su Haydar dinma zasu tafi.


Mr Jameel ya sanar da ASH Dr beeba ta sanar da Amatu ba lafiya Dan haka bayan sun fito yayi sallama da su tareda sallaman su kawu da abinda ya wuce tinaninsu suka ringa Godia hakama su mum Aisha da maamah sanyi jikinsu yayi da sabbin motocin Daya Basu kowaccensu daddaya bayan yasan a kauye zasu zauna Ina gurin bin mota ma bare Janta.


Har lokacin Husnah a tsorace take da Dad din nata ta kasa zuwa inda yake duk da ta zama matar Abdul idan ba ganin tayi su uzaifa sun bar gidan ba hankalinta baa kwance yake ba.


Shine ya fara ficewa mansion din tareda Mr Jameel dayake jansa zuwa gidan Farha.


Shiru sukai Mr Jameel na drivern yanason ya tambaya Yaya ake rarrashin mace ta sauko daga fushi a gurin Mr Jameel Amma Kuma dai ya fuske ya

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads