Showing 117001 words to 120000 words out of 152002 words
Chapter 40 - AMATULMALEEK COMPLETED BY Mamuhugee.txt
gasgata Amatu Bata dakinsu a Daren Sam Bata yarda ba da abinda ake kokarin fada da tabbatarwa Amatu da ASH.
Mum Aisha kuwa gaba Daya hankalinta da nutsuwanta Bata taredasu a asibitin Yana gidan dasuka baro da abinda dai ya tabbata kenan Amatu ta zama matar ASH.
A gida kuwa tinda suka shige saman a palon ya fara zaunawa da ita a jikinsa suna fuskantar juna ya Ciro bakinsa daga nata Yana bin lips dinta dasukai Wani Dan ja da Kuma Hasken deep tsotsan daya musu.
Rigar jikinta yakeson zarewa Amma akwai sanyi bayason sanyin ya shigeta Dan haka gaban rigar dake Bude ya zira hannunwansa Yana mannota jikinsa kirjinsu ya hade da Dan karfi kadan,
Atare suka sauke ajiyan zuciya me hade da numfashi Yana ambatar sunanta kaman ransa na Neman fita,
Itama lumshe idanuwanta da baccin cikinsu ya gama tafiya gaba Daya tayi tana shafa bayan wuyansa ahankali kaman tsutsa na masa tafiya zuwa wuyansa da kirjinsa tareda sauke masa numfashinta masu dumi a cikin kunnensa na dama tini ya qarasa kuncewa.
Dago kanta tayi lokacinda ya sake ambatar sunanta ta Kalli fuskarsa kishinsa kawai taji Yana suka tareda mamaye zuciyarta tareda sonsa me tsananin gaske a lokaci Daya.
Cikowa idanuwanta sukai da hawayen galabaitan zuciyarta ta hade fuskansu tareda kama fuskansa da tafin hannuwanta ta hade bakinsa da nata wata irin fitinanniyar kiss me kunce Kai ta fara yimasa tana tsotsan lips dinsa da harshensa a lokaci Daya tana sake zagayo kansa da hannuwanta.
Kasa riqe kansa yayi daga rabata da rigarta gaba Yana shigarda ita jikinsa sosai Dan Hana sanyin shigarta ya miqe da ita har lokacin tana sake kashesa da nata salon kiss din.
A cikin bedroom din nasa kusan sabuwar duniyar suka Bude suna bajewa Dan kuwa Saida yagama susucewa gaba Daya tukuna suka Isa lafiyayyar gadon dakin suka hau suna watso kusan Rabin pillows din gadon ka suka Kai guda shiga qasa.
Lafiyayyar soyayyarsu suka sha ahankali kwance kafin tafara tinanin saukowa ta koma dakinsu kafin safe Wani ya fito yasan Bata Nan.
Bai bari ta koma din ba Dan Babu abinda ya shafesa da Wanda zai fito yaga Bata Nan din Dan haka wanka sukai ya kwanta cikin jikinta sbd gajiyansa da stress dinsa dayaji ya sakesa gaba Daya Wani baccin nutsuwa da Kwanciyar hankali ne ya daukesa itama dole tayi baccin a Nan sbd yanda ya kwanta jikinta bazata iya zamewaba Dan a zagaye da qugunta hannunsa duka biyun suke.
Babu Kiran sallah da alarm ake tashi sallan asuba dan haka Koda alarm din yayita yi ahankali qasa qasa Basu ji ba Saida sukai lattin sallah sosai.
Suna idar da sallah jikinta na Dan rawa ta silale ta sauko Jin gidan tsit tayi tinanin Basu tashi ba Dan haka tafara saukowa da sauri ahankali sedai ko gama saukowa bataiba ba aka Bude kofar shigowa dukkaninsu suka shigo gaba ki dayansu Banda mr Jameel da Bai shigoba.
Anty Farha ce agaba sai maamah da Husnah tukuna mum Aisha data shigo karshe ranta a hade sbd takaicin kwanan zaune kawai datai a asibitin.
Rawa jikin Amatun ya Dan dauka tana kallan maamah datai mata kallo daya ta dauke idanuwanta daga kallanta sbd zuciyarta zata iya bugawa.
Husnah ma zuru tayi tana kallan Amatun kallo na qurullan data iya gane ko yau din Babu bra a jikin Amatun hakama kusan gaba Daya qamshin Dad dinne yake tashi daga kayan jikinta.
Anty Farha ce tayi saurin yin gaba tana Jan Amatun da cewa
"Neman mu kikeyi ne?
Asibiti muka kwana Husnah ba lafiya lokacin kina kitchen kinje daukan ruwa Amma dai......
Maamah data kasa riqe bacin ranta da renin wayon da farha takeson kawo mata ta Saka hannu ta riqe hannun Amatun daga hannun Farha ta dawo da ita gabanta idanuwanta da sukai jajir akan Amatun data kasa kallanta har rawa da karyewa muryan maamah din keyi ta Bude Baki tace
"Amatu daga dakin ASH kike??
Qasa ta sake yi da kanta tana kasa cewa komai bayan hawayen Dake cikowa daga idanuwanta.
Magana anty Farha ta matso zatai Dan kare Amatu maamah ta daga mata hannu cikin tsananin bacin Rai tareda dawo da kallanta ga Amatu batace komaiba ta kama hannunta Rai a tsananin bace ta fizgeta zuwa cikin dakinsu ta Turo kofar.
Sakin hannun Amatun tayi Kai tsaye fushinta da tsananin zafin zuciyarta na qaruwa ta maimaita tambayarta tana tsoron amsar da zaa Bata Amma dai tanason Jin idan akwaima ko alalar gaisuwar datake shiga tsakanin Amatun da ASH batareda sanintaba.
Kasa amsa tambayar Amatu tayi idanuwanta na sauyawa zuwa ja hannuwanta na kakkarwa.
Cikin zafin zuciya Daya kasa boyuwa Maamah ta daga murya a zafafe tace
"Meya kaiki sama?
Menene alaqarki da zuwa saman?
Menene abinda su Mum Aisha suke fada???
Wannan Karan gudu hawayenta suka qara ta Bude Baki Babu abinda ta iya furtawa Se "kiyi hakuri maamah....
Wani ba zatan Mari ne maamah din ta dauketa dashi Wanda ya Sakata gigita sbd ba zatan saukansa da Kuma dukanta da baa taba yi ba.
Ita kanta maamah datai Marin rawa jikin ya dauka a fusace batama sanin me take fada tace
"Da gaske su Husnah suke kenan kina zuwa dakinsa ko me??
Kin taba kwana a dakinsa ne ko me nake Shirin Gani ko ji???
Kuka mara sauti ne ya kufcewa Amatu tana toshe bakinta da hannuwanta sake rawa tana kasa amsa tambayar maamah cikin matsanancin tashin hankali da tsoro.
A fusace maamah ta damqota tana jijjigata cikin fushinta Dake tsananta take sake maimaita tambayar da gaske ne tana zuwa dakin ASH?
Kukanta ke tsananta tana kasa amsa tambayar har lokacin hakama rawa jikinta keyi sosai sbd tashin hankali da tsoron Bata taba kaiwa wannan matakin ba da mahaifiyarta.
Maamah ma hawayen ne suka kufce mata tana fasa kuka sbd Bata taba tinani ba hakama Bata taba zata ba har lokacin ma ta kasa yarda da Hakan shiyasa takeson Amatun ta Bude bakinta da kanta ta fada mata.
Kukan maamah din ya sake gigita Amatun ta shiga tashin hankalin dayafi na farko tana fashewa da sabon kukan da Baya fidda sauti har lokacin sedai shesheka.
Cikin kukan maamah ta sake cakumo Amatun tana Neman illata sbd bacin Rai ta riqe hannunta Daya qam kaman zata tsaga mata shi tana Jin kaman karta tsaya Se tayiwa Amatun shegen dukan da zata Bude Baki ta fada mata gaskia duk da bazata taba yarda Amatun zata iya Hakan ba Dan haka cikin Nemo taurin zuciya ta share hawayenta tana kallan Amatun tareda Dan sassauta murya tace
"Amatu idan har kin yarda ni mahaifiyarki ce,nice na dauki cikinki na haifeki kimun alkawarin daga yanzu bazaki sake ko kallan ASH TALBA ba'a matsayin mijin yar uwar mahaifiyarki ba,kimun alkawarin babu alaqar da zata taba shiga tsakaninki dashi ba bare har abinda su Aisha suke magana ya tabbata,
Abeeda ta tashi bayan shekaru ko ke bazaki so abinda zai sake Sakata cikin Wani mummunan halinba tinda uwace a gareki,
Wannan auren na kaddara ne Kuma shi da kansa zai warware Miki shi ya sauke Miki nauyin auren tinda Abeeda ta tashi,
Abeeda kadai ce matar Dayake kallo a macen da zaiyi rayuwa da ita,
Babu abinda Zaki samu ko Qaru dashi da wannan auren zai lalata kuruciya da lokacinki sbd ke da ASH kaman sama da qasa ne akwai tazarar abubuwa da yawa da suka nesanta ku,
Ki dubi kauna da amincin dayake tsakanina da Abeeda ki tattara maganar ASH da aurensa ki aje a gefe kiyi rayuwarki,
Kimum wannan alqawarin Amatu,
Kimun alkawarin Nan Amatu ki tabbatar min da kin yafe auren Nan tareda ajesa a gefe kwata kwata kada yar uwata ta koma halinda ta fito.......
Amatu tinda take Bata taba gasgata da gaske mahaifiyarta data haifeta tafi son farin cikin kowa akanta ba,
Tafison Abeeda da yar Abeeda akanta,
A yau taji komai na duniya ya isheta ya fita kanta,
Ayau mahaifiyarta ce take rokonta akan ta koma bazawara sbd kada farin cikin 'yar Abeeda Dan kuwa Abeeda yanzu Babu Wanda yasan me takeso meye bataso...
Katseta maamah tayi da sake maimaita mata kalmomin alqawarin datake son ta daukan mata idanuwanta jajir akanta.
Gudu hawayenta masu tsananin zafi suka qara tana dauke kallanta daga Maamah din kuka me qarfin gaske yana kufce mata.
Kukanta ya Saka maamah fahimtar alaqawarin data nema tai matan yayi mata tsauri Dan haka hankalinta ya sake tashi sosai sbd idan har Amatu batai mata wannan alqawarin ba to alama ce ta ASH din Yana cikin zuciyarta.
"Innalillahi wainna ilaihirrajiun" maamah din tafara furtawa tana Neman Yanke jiki ta Fadi Amatu ta tarota sedai da qarfi maamah din ta tureta tana daga mata hannu alamar ko tabata kada ta kuskura tayi.
Hakan datai ya Saka Amatu sake fashewa da kuka kafin tayi Wani yunkurin Husnah ta shigo dakin tana ganin halinsa maamah ke ciki da gudu ta iso gurin tana riqo maamah itama ranta da jikinta duk a mace hawaye kawai ke ciko idanuwanta tana hadiyewa.
Anty Farha ma shigowa tayi sbd takasa hakura tsoro da tashin hankalinta kada su tada balai da masifarsu su Saka Amatun a cikin Wani halin.
Suna dakin ASH ya fito a shirye sbd kiransa da Akai asibiti yanzu din akan yau zai dawo da Abeeda gida Dan haka ko breakfast Bai tsaya yi ba hakama mum Aisha Dake palon Bata bari yasan da akwai abinda yake faruwaba ta hanasa fahimtar komai harya fice daga gidan.
Yana fita mum Aisha ta shigo dakin tana sake rura wutan Dake cin zuciyar maamah da Husnah.
Anty Farha kuwa ayau maamah kasa riqe kanta tayi tai mata tas cikin tsananin bacin Rai duk da har lokacin kanta ya kasa dauka bare yarda da Amatun da gaske taje dakin ASH a Daren.
##MAMUH#
*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070
Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#
AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar
66
*MUFEEDA'S FRAGRANCE*
*GIDAN KAMSHIII*
Munada kayan turaruka kala kala kama dasu;
Turaran wuta
Turaran jiki
Turaran Kaya
Humra milk
Humra black
Kwalacca
Turaran moping
Freshener
Daidai sauran su
Ta a Very affordable price.
Zaku iya tuntubar mu a wannan
07040986690
Muna zaune ne a garin Kano da Abuja (life camp) sannan muna aika kayan mu ko ina a fadin kasar nan har ma da kasashen waje. Akwai tsarin wholesale wato sarı ga duk me bukata sai ya tuntube mu. MUNGODE
*MUFEEDA'S FRAGRANCE*
*GIDAN KAMSHIII*
***************
Mummunan halin da Amatu ta shiga ya Sanya anty Farha hadiye nata damuwan maganganun su maamah da mum Aisha dasuka ringa gasa mata masu zafi da 'daci ta janye AmatulMaleek suka fito dakin jiki a sanyaye ta dawo da ita dakinsu.
Suna shiga dakin zaunar da Amatun tayi ita Kuma ta nufi toilet ta shige sbd maganganunsu sun Sosa ranta matiqar gaske musamman mum Aisha datake fadan nata cikin cin zarafi da quntatawa,
Ko Mr Jameel bazata iya kiraba a wannan lokacin sbd itama zuciyarta ta sosu matiqa idan ma ta kirasa bazata iya fadan komai ba kuka ne zaizo mata dan haka ta shige toilet ta rufo kofar batareda ta iya kallan Amatu ba da take nata kukan sosai itama.
Bayan ficewansu mum Aisha kan maamah ta dawo da maganganunta masu quntatawa ta qarasa damawa maamah din lissafi
Husnah kuwa takai matakin da idanuwanta Neman bushewa sukeyi qyam ba hawaye sai ja da radadin zuciya sbd ta kasa yarda da itam ace yau din wai Amatu ce da zuwa dakin Dad dinta da daddare bayan tasan mum dinta ance Koda wasa kar abari tasan da zancen auren bare wannan sabuwar tashin hankalin.
Abin baqin ciki da takaicinta shine yanda Dad dinta duk Isa,kamewa da class dinsa da manyan mata ke bibiya zai iya kallan Amatun ma a mace bare iya taba jikinta,
Babban buri,fata da adduarta shine duk rintsi kada Allah yasa Dad dinta ya Maida Amatu cikakkiyar matarsa,Allah yasa iya wannan da suka Gani ne abin ya tsaya yanda kawai gwara mum dinta ta sani Kila Hakan ne zaisa Dad ya bar Amatun ya dawo da dukkanin rayuwa da kulawansa harma da time dinsa gaba Daya kan mum din nata.
Maamah silalewa tayi zaune tana tare hawayenta sake saukowa kan fuskarta kwata kwata qasar ta fita ranta gaba Daya harma da rayuwa a cikin gidan ASH Dan haka Nigeria kawai take buqatan tattara Amatun su koma ta gaji bazata iyaba,
Zuciyarta bazata iya daukan wannan lamarin ba, bazata iya barin Abeeda ta tasan da maganar auren Nan ba tana guri Daya da ita gwara ta tattara Amatun su koma inda suka fito duk ranar Daya gaji da tafiyar tasu ya warware auren Amma tabbas ta gama zaman gidansa da Amatun.
****Duk wannan tashin hankalin da masifar baisan anayi ba daga shi har Mr Jameel sbd farha ce jinsa da ganinsa a cikin iyalinsa to itama tana cikin sanyin jiki yau din Dan haka wanka tayi ta shirya ta fice daga gidan gaba Daya ta fita kanta ya sake sbd taso fita da Amatun Amma Amatun bazata iya fita koina ba sbd kukan datasha gaba Daya kamanninta sun sauya ga zazzabi ya rufeta na take.
A asibitin kuwa duk wasu formalities na sallama da transfer din Abeedan zuwa Nigeria ta qarasa warware acan sun gama anso Basu nurse da zata ringa kulawa da ita Amma tinda tafiya zasuyi ha zama ba sai aka barta kawai akan zata ringa zuwa kullum nurse din tana dubata kafin tafiyarsu.
A motar ambulance ta asibitin aka kawo Madame Abeedan gida Dan haka suna Jin isowan motar kowannensu ya aro nutsuwar karfi da yaji ya yafawa kansa tareda fuskewa kada ASH ya gano abinda ya faru a gidan ko kadan.
Dayake Shima kusan hankalinsa gaba Daya Yana kan Abeedan da aka kawo gida sai Bai Wani fahimci komai ba hakama little Abeedan Dayaga Bai ganta ba hakama Farha sai yayi tinanin suna tare.
Husnah da maamah farin cikinsu duk da suna cikin dacin zuciya sun bayyana murnar dawowanta a Fili tareda rasa inama zasu ajeta.
Dakunan na qasa a cike suke sbd guda uku ne,
Mum Aisha Daya Se Husnah da maamah Daya sai anty Farha da Amatu Daya.
A sama Kuma bazai yiyuba sbd Hawa da saukan tinda ko motsi Bata iya yi sosai Se ahankali take Dan motsawa daga kallo sai motsi takeyi ko magana Bata iyawa sbd kaman paralyze ne a tattare da ita bayan ciwonta.
A dakin mum Aisha dole aka ajeta nan suka tare sunata dawainiyar murnar dawowanta.
ASH kuwa fita suka sake yi da Mr Jameel sbd so yake ba delay su koma Nigeria tinda Babu abinda zasu zauna suyi din anan Dan haka zai qarasa abinda zaiyi a qasar a ranar sai su Dan huta na kwana biyu kafin su wuce kawai.
Bayan fitarsa kusan yaqe da karfin halin danne ciwon ransu suka ringa yi a gaban madame Abeeda wadda ko Bata komai sunsan tana ji Kuma tana fahimtar komai din.
Wuni guda Amatu Tay a daki kwance cikin zazzabi me qarfi da ciwon damuwa Amma Babu Wanda ya Kalli dakin datake bare dubata sbd kowa a gidan ta ciki na cikinsa.
Anty Farha ma har dare Bata dawo gidan ba Dan haka daqyar Amatu ta iya tashi ta daddafa ta shiga toilet ta sakarwa kanta ruwan zafi sosai tayi wanka.
Dan karfi ta samu da kuzari na wankan datai Dan haka tayi brush ta fito a sanyaye jiki ba kwari ta zauna dole ta daure ta shafa Mai sbd sanyi ta tashi ta saka Riga da wando masu kauri sosai sbd sanyi ta Saka hijab tayi sallolin da suke kanta harma da ishai da lokacinta yayi.
Tana idarwa fitowa tayi Dan dole da yunwar da cikinta ya kasa riqewa kaman zata mutu.
Babu kowa a palon Dan haka Kai tsaye kitchen ta wuce ta Bude fridge ta dauko Coke me sanyi da biscuits ta zauna a kitchen din ta tura hakanan taci sbd bakin da ranta Babu dadi Sam.
Abincin dayake kitchen din ta duba Taga chicken noodles ce Akai duk da Bata Wani so haka ta daure ta zuba a plate ta tura tana ci tana Jin zuciyarta bataso Amma yunwar Bazata barta ba.
Ruwa Tasha me sanyi bayan tagama ta fito.
Husnah data fito daga dakinsu ce ta ganta ko kallan juna basuyiba Amatu ta wuce dakinta Kai tsaye lokacin kusan 10 ta kusa.
Rashin layin kasar yasaka ta rasa yanda zatai ta nema anty Farha Dan haka dole ta kwanta tana shiga damuwan rashin dawowan anty Farha din itama.
Harya kwanta ta manta Bata shigo da ruwa ba dole ta taso ta fito daidai Husnah ta sake fitowa wannan Karan bin Amatun da kallo tayi zuciyarta na tafasa da qunatata da tinanin Amatun dawowan Dad dinta take Jira waton yauma taje dakinsa ta kwana kenan bayan mum dinta tana gidan.
Wani baqin ciki da kishin Hakan ne ya danne kirjinta Dan haka batai tinanin komaiba ta nufi dakin mum Aisha gurin mum dinta.
Tana shiga har Madame abeeda ta fara bacci Amma ido rufe Husnah tafara kokarin dagata tana kokarin sakawa a kujera Amma ta kasa.
Mum Aisha ce ta fito toilet tana sauri ta gama tazo ta zauna ta qarasa warwarewa Abeeda komai na abinda ta fada mata asibiti kafin zuwan ASH.
Ta fada mata aure yayi Amma Bata fada mata wa yake aurenba jikinta ya birkice Dan haka yau zata qarasa cike aikinta.
Ganin Husnah na kokarin Saka Abeedan kan wheelchair yasata qarasowa tana kallanta da mamaki tana cewa
"Lafiyanki kuwa?
Kodai ciwon haukan ne ya motsa?
Kin dai San mahaifiyarki batasan kina samun juyewar Kai ba Akai Akai shine Zaki nuna mata Dan ta birkice bayan ance a guji birkicewan nata....
Dayake idanuwanta a rufe suke Husnah din Bata tsaya fahimtar tasirin da maganganun mum Aisha keyi ga mum din tata ba sai kawai taci gaba da kokarin Dora Abeedan harta samu zaunar da ita daidai Akai ta tura ta Kai tsaye ta fice dakin tana Jin aranta gwara takai mum din tata sama ta kwana can zata Fi ma samun kulawa da wali a dakin Dad dinta.
Tana fitowa Palo da ita ta nufi hanyar Hawa sama Kai tsaye tana turawa daqyar tana dagawa sedai lamarin Yana Neman gagara sbd bazata iya turata ita kadai ba zuwa sama.
Maamah data fito itama Dan zuwa sake dubo Abeedan kafin ta kwanta tana fitowa akan kokuwan hayewa da Husnah ke kokarin yi da Abeedan idanuwanta suka sauka Dan haka da sauri ta qarasa ta kamata tana kallan Husnah da mamaki da tsoron yanda ta hawo da Abeedan stairs din tace
"Lafiya kika daukota?
Ina Zaki kaita kika hawo stairs dinnan masu tsayi da ita?
Cigaba da kokarin qarasawa da ita Husnah ta fara idanuwanta jajir suna Neman tara hawaye tace
"Zata Fi