Showing 120001 words to 123000 words out of 152002 words
Chapter 41 - AMATULMALEEK COMPLETED BY Mamuhugee.txt
samun kulawa da sakewa a saman shiyasa zan kaita can kuma ko Dad ya dawo saman zai hawo da ita ma"
Da mamaki sosai maamah ke kallan Husnah din tana riqe Abeedan da kyau sbd sun kusa hayewa ko data fito ga Abeedan na Neman fin karfinsu a tsorace maamah tace
"Wanda baida lafiya irin haka meye zaisa a daukota zuwa Wani sama gaskia Sam wannan ganganci ne Husnah,kamata da kyau fa"
Amatu data fito daga dauko ruwa kitchen Dan bayan shigarta ta tarar Babu sauran ruwan sanyi a fridge sai ta Saka biyu ta Dan Jira suyi sanyi kadan ta dauko ta dawo.
Tana fitowa kitchen Taga abinda yake faruwa Madame abeeda da batama San andawo da ita ba Taga tana Neman gagararsu ta fado Dan haka ruwan hannunta ta jiye da sauri itama cikin mamaki me tsanani ta Isa Takai hannu zata kama musu Husnah tayi saurin tareta da hannunta Daya cikin zafin zuciya da baqin cikin yanda suke fama sun kasa qarasa hayewa da Abeedan tace
"Karki taba mum mahaifiya sbd kece silan wannan kakanikayi din da mukeyi da ita.
Mum Aisha ce ta fito tana kallansu da sauri ta hawo tana cewa
"Meye haka ne wai Husnah kikeyi,Sam ke bakyajin maganar kowa ne"
Hannu ta Saka suka qarasa cira wheelchair din zuwa stairs din sama na karshen gaba Daya suka ajeta sai alokacin maamah ta Kalli Husnah fuska ba wasa ko walwala ko kadan tace
"Banason Jin komai anan yanzu"
Tana fadar Hakan ta juya ta kalli Amatu zatace mata ta tafi kawai sai mum Aisha ta katse maamah din da cewa
"AmatulMaleek matar ASH ce Banga abin damuwa da daga hankalinda zaisa a dauko Abeeda tana fama da lafiyarta ku hawo da ita wannan tsaunin wahalar ba.......
Cikin Wani irin mugun shock dukkaninsu suka kalli mum Aisha din hankali tashe kafin suka Maida kallonsu lokaci Daya akan madame Abeeda data rufe idanuwanta ahankali tin kafin su juyo din gareta.
Maamah da Wani mummunan bacin Rai da fushin da basusan tana da shi ba ta kama hannun mum Aishan da qarfi tayi gefe da ita kadan duk da kowa na Jin abinda suke fada fushinta na bayyana cikin zafin tace
"Me kike kokarin yi?
Wace maganar ne wannan??
"Akwai karya ne a abinda na fada Asmau?
'yar ki Bata aure mijin Aminiyarki ba data tallafi rayuwarki?
Me yasa kika bari auren yazo har yanzu idan da gaske bakyaso?
Ita Amatun da kike ganin kin tsare kin killace akan auren so nawa ta kaiwa ASH din kanta?
Kuka da tashin hankali kuka ringa yi akan Naufal Akai masa sharrin fyade bayan shima ba yin kansa bane Husnah da kike bugun gaba da ita itace ta sirka maganinsa ta turasa yiwa Amatun fyade sbd Faisal,hakama a karo na biyu da gayya ta jaki zuwa porthcrt ta sake turasa yiwa Amatun fyaden da yayi sanadin gobarar tsohon Mansion da Kuma yankewan kafarsa da ASH yayi,
Ashe ba dadi rasa Wanda kakeso ni aka kassaramun 'da sbd yarki?...
Wani mummunan jiri da zufan tashin hankali ne me tsananin gaske ya fara tsiyayowa maamah Nan take bakinta na rawar masifaffen tashin hankalin abind mum Aisha din ke fadan Husnah tasa ayiw Amatu fyade yasata kallan cikin idon mum Aisha din tace
"Ki maimaita abinda kika fada naji kyau"""
Kafin mum Aisha data shiga mamaki da shakkar fushin datake Gani me tsanani akan fuskar maamah tayi magana Husnah ne tayi kan Amatu zata shaqota sbd tasan shikenan mum dinta jikinta rikicewa zeyi ta rasata gaba Daya hakama maamah dinma rasata zatai Amatu ta zama balai da masifar rayuwarta.
Baya Amatu tayi tareda kaucewa Husnah din
Husnah ta sake yi kanta ido rufe cikin tsananin fushi da rufewan zuciya da ido Wanda yasa maamah da mum Aisha sukayo kan Husnah din sbd qatuwar flower vase data dauka a haukace
Maamah ce ta tareta,mum Aisha kuwa kokarin kaucewa daga gurin tayi tana kokarin tura Husnah take flower vase din ta fada gurin wheelchair din da Madame abeeda take zaune idanuwanta jajir da abinda kunnuwanta ke ji mata take wheelchair din tafara wintsilowa kan stairs din kaman an jefo ball,
Gaba dayansu cikin gigitaccen tashin hankalin da baa Saka masa ranaba suka yo bakin stairs din Babu Wanda qafafunsa da hantarsa Bata tsalle a cikinsu.
Yanda ake gangarowa da kujeran daban madame Abeedan daban a stairs din ba kyan Gani daidai shigowan ASH da Mr Jameel Se anty Farha da itama atare suka shigo.
##MAMUH#
*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070
Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#
AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar
67
*MUFEEDA'S FRAGRANCE*
*GIDAN KAMSHIII*
Munada kayan turaruka kala kala kama dasu
Turaran wuta
Turaran jiki
Turaran Kaya
Humra milk
Humra black
Kwalacca
Turaran moping
Freshener
Daidai sauran su
Ta a Very affordable price.
Zaku iya tuntubar mu a wannan
07040986690
Muna zaune ne a garin Kano da Abuja (life camp) sannan muna aika kayan mu ko ina a fadin kasar nan har ma da kasashen waje. Akwai tsarin wholesale wato sarı ga duk me bukata sai ya tuntube mu. MUNGODE
*MUFEEDA'S FRAGRANCE*
*GIDAN KAMSHIII*
***************
Anty Farha ce ta saki ihu cikin matsanancin tashin hankali da firgici
ASH kuwa taku biyu yayi ya Isa inda Abeedan ta fado Yana tarota jikinsa gaba Daya da sauti me girma yake Kiran sunanta Yana jijjiga fuskarta Dake fidda jinin da baimasan na Ina ne yake fitowa ba.
Mr Jameel kuwa Wani irin tafasa zuciyarsa da gangar jikinsa keyi sbd tsananin baqin ciki da tashin hankali harma Da bacin ran da shi kansa baisan yanada shiba lokacinda yake kallansu mum Aisha din da maamah s da Husnah din a jere a saman Wanda alamu da komai ya bayyana qarara dambe ne sukeyi a saman suka jehota Kokuma sainsa da tashin hankalin da suka Saba.
Husnah ce ta sauko da gudun datake hada stairs kusan hudu hudu ko uku uku hankali da ganinta na Neman gushewa,
Maamah kuwa zubewa tayi a gurin sbd ganinta Daya dauke lokaci Daya tareda bugun zuciyarta,
Mum Aisha hannu ta Dora Akai tana neman sakin ihu.
Amatu ma bayan tayi ahankali tana zamewa qasa zuciyarta na dauke bugawa da Mafi girman tashin hankali da balain dayafi karfin kwakwalwanta.
Ambulance Mr Jameel ya kira Yana tare Husnah da mum Aisha da suka nufato inda ASH yake da Abeedan a jikinsa Yana cigaba da ambatar sunanta Dan ta Bude idanuwanta Amma Sam Babu alaman zai samu Hakan.
Cikin qanqanin lokacinda ba'a dauka ba ambulance ta iso hankali tashe aka dauki Abeeda Akai asibiti da ita batareda da kowa yabi ta kansu ba ASH din da Mr Jameel ne kawai sukabi bayan ambulance din.
Suna wucewa anty Farha da kafafunta ke rawar tashin hankalin lamarin sama ta hau da sauri ta kamo Amatu Dake zube qasa idanuwanta a waje zuwa jikinta tana ambatar sunanta cikin tsananin kulawa da kokarin dawo da ita hayyacinta.
Dagota tayi takamo ta suka sauko Bata tsaya da ita palonba ta wuce da ita daki.
Husnah data kasa dawowa daidai sai alokacin ta fasa Wani irin kuka me Qarfi da ihu tana zubewa qasa zaune duka jikinta jijjigan tashin hankalin da Bata taba shiga ba takeyi Dan kuwa idan mum dinta ta mutu sune suka kasheta.
Maamah ma kaman mara laka ko Daya a jikinta ta sauko ta shige dakinsu ta zube tsakiyan dakin tareda fasa nata kukan me tsananin gaske cikin matsanancin tashin hankali da Wani irin gigita.
Mum Aisha kanta a gigicen take sbd bayyanar ASH a daidai lokacinda abin ya afku ita shine babban masifaffen tashin hankalinta da Bata tsoro.
Dan haka itama tini tafara rawar jiki tana sake gigicewan.
A daki kuwa anty Farha kokarin kulawa da Amatu takeyi ganin yanda ta shiga shock me qarfi Dan kuwa abin tashin hankali ne me girma mara lafiya irin Abeeda ace an jeho daga stairs.
Hawayen ne masu tsananin zafin gaske suka fara tsiyayowa Amatun kafin kuka me sauti da qarfin gaske ya zo mata ta silale qasa tana cusa kanta cikin qafafunta tana yinsa sosai tareda fatan Babu abinda ya samu mum Abeedan.
Duk anty Farha ma na cikin tashin hankalin lamarin Amma ta danne kokarin rarrashin Amatun takeyi tana Bata tabbacin babu abinda zai samu Madame Abeeda inshallah.
Gaba dayansu gidan Babu Wanda yake hayyacinsa bayan anty Farha datake iya kokarin ganin Babu Wanda ya zauce a cikinsu Dan kuwa kusan dukansu zaucewa kowa keyi gashi tsananin tsoron ASH ya Hana kowacce tinanin binsu asibitin dubo halinda Abeeda take ciki.
Anty Farha din da suka gama ciwa mutunci da safen itace dai ta ringa binsu Daya Baya Daya tana dawo da kowa hayyacinsa musamman mum Aisha datafi kowa shiga tsoron ASH Husnah da maamah kuwa tashin hankalin rasa Abeedan ne yake Dan kokarin fin tsoron ASH din Dayake cike da cikinsu duk da Shima din tsoron abinda zai iyayi sukeyi.
Dayake dare ne kusan kowa dakinsa ya shige suka zauna jigum jigum hankalinsu da idanuwansu a yanayi na rashin sanin Ina suka kwana.
AmatulMaleek kuwa zazzabinta cikin tsakar Daren har tsoro ya bawa anty Farha Dan haka Amai ta ringa yi Wanda ya Saka kowa fitowa daga dikinsa.
Daman Husnah neman dalilin fitowa takeyi sbd tashin hankalinta na Dayan bangaren maamah akan Jin itace tasaka ayiwa Amatun fyade,Sam maamah ko inda take Bata kallaba bare tinanin akwai mutum tareda ita,
A aynzu batada karfi ko bawa komai hankalinta sai taji yanda Abeeda take zatai tinanin Husnah da abinda tayi mata din.
Cirko cirko suka tsaya Babu Wanda cikin awannin da aka barsu din Bai fada ba yayi zuru zuru a dare daya lokaci Daya sbd rashin sanin meye zai faru.
AmatulMaleek ta galabaita sosai Dan haka ko zama daqyar anty Farha ta zaunar da ita taje ta kawo mata tea me zafin gaske ta fara Bata.
Banda Husnah daga mum Aisha har Maamah datake Neman shiga sabuwar shock of her life zubawa Amatu idanuwansu sukai mum Aisha ta Bude Baki murya na rawa tanason magana Amma ta fasa sbd yau tashin hankalin na musamman ne,
Magana ce a bakinta Amma ba damar furtawa sbd a wannan tsaka me wuyan dasuke tada Wani balain ba nasu bane Dan haka tayi shiru harsun samu fita daga wannan mummunan tashin hankalin Amma tabbas wlh ta tabbatarda ciki ne a jikin Amatun,Dan haka tana cikin sabon tashin hankali Amma dai tashin Abeeda yanzu shine fatanta Dan duk yanda takeson Abeedan ta mutu Bata so ya kasance ASH ya taddasu dumu dumu sun jeho masa mata ba da Bata saman Kokuma da Bai taddasu ba zata iya zame kanta Amma gaba dayansu ya taddasu Dan haka tasan Allah ne kadai zai fiddasu wannan masifar shine rashin mutuwar Abeeda a lokacin.
Maamah ma kusan tinanin mum Aisha ne yakeson shigarta Amma tashin hankalin datake ciki yasa Bata yarda da abinda idanuwanta ke ganar mata ba bare Kuma yarda da lamarin Dan haka a rude tayiwa Amatun sannu tabar dakin hakama mum Aisha tana ji tana Gani ga abin tada fitina da magana Amma yau ba dama.
Suna ficewa tana gama Shan tea ta kwanta ko baccin awa Daya bataiba lokacin sallan asuba tayi suka tashi sukai sallah Banda ita da anty Farha taqi tadawa sbd ta ganin yanda ta galabaita din tabarta ta samu baccin.
Qarfe 7 saura Amatun ta sake farkawa ta tashi ahankali sbd ta samu Dan kuzari ta nufi toilet Tayo fitsari da alwala tana fitowa ta tada sallah.
Tana sallamewa ko tashi daga inda take bataiba Mr Jameel ya shigo gidan da sauran duhun asubar.
Baice komaiba ya buqaci su fito da kayansu jirgin da zasubi awa Daya ya rage ya tashi.
Hankali tashe suke kallansa Amma ba Daman magana shima Bai tsyaa komaiba Yana fada ya juya ya fice waje Yana jiransu sbd gaba Daya a siqe yake dasu kaman ya kwashesu yakaisu asibitin mahaukata yakeji yakai ya zubar ayita banka musu alluran hauka ko zasu huta da balainsu Daya ishi kowa har Yan aikin mansion din TALBAs sun dai gaji da masifarsu bare me gidan gashinan sun ja masa masifa Yana ganin ya samu Madame abeeda taji sauki.
Mum Aisha tasan zaayi Hakan Dan haka itace ta fara fitowa da akwatinta kafin maamah da Husnah dasuka so ko so Daya ne sunje sun duba Abeedan sunsan halinda take ciki Amma Sam Babu fuska Dan kuwa sanin wannan umarnin daga ASH ne Kila.
Anty Farha ce ta fito da nata kayan Dana Amatu suma suka fito Dan Mr Jameel cewa Yayi dukkaninsu kowa da kowa gida sukai su fito.
Babu me wanka a cikinsu bayan Amatu sbd itama ta sake samun qarfin jikinta ne anty Farha ta Sakata wanka da ruwan zafi sosai sharp sharp ta shirya cikin Riga da wandon Jean Se qatuwar jacket me tsayi da kauri tayi Rollin harda safa da facemask suka fito.
A yanda suka fito jikin kowa a mace idanuwa a jeme har lokacin Mr Jameel Babu wadda yacewa komai kawai kayansu ya zuba cikin babbar motar Daya zo da ita takaisu airport.
Tin a cikin mota ya bawa Farha tickets dinsu duka ta bawa kowa nasa da kanta tana kallansa cikin kulawa da sanyin jiki sedai ta kasa cewa komai sbd yanayinsa Babu walwala ko annuri ko kadan Kuma so da daman tin Madame abeeda na lafiya kalau kusan harma da duk me muamala Hulda da ASH ta Mr Jameel ake karanta ko gane halinda ASH yake ciki Dan kuwa mode din Mr Jameel shine yake bayyanar da mode din ASH Dan haka rashin annurin fuskar Mr Jameel da bacin Rai da damuwar dayake kwance a fuskansa yasa dukkaninsu sanin ba sauki ta gurin ASH din Dan haka Babu wanda ya sake ko Tari har suka iso airport suka sauka ko motan Bai fito ba farha ya kalla da idanuwasa Dake da Dan ja ahankali cikin nutsuwa yace
"Ki kula da L.A din,kema ki kula,Allah ya kaiku lfy"
Gyada masa Kai tayi a sanyaye itama zuciyarta na sake shiga damuwa.
Ko zama basuyiba aka kira flight nasu suka wuce kawai janye da kayansu Babu me qarfin jiki.
Kowa a zuciyarsa matse yake da son sanin halinda madame Abeeda take ciki Amma Babu dama Babu kuka alamar zama a bari su sani bare alamar sanin.
Jirginsu na dagawa mum Aisha ta sake ajiyan zuciya a boye Dan harga Allah a tsinke take ganin takeyi ASH miqasu zeyi ga hukumar qasar tasan sedai labarinsu ba dai su din ba.
Husnah hawayenta har sun bushe sun Dena saukowa sai jajir da idanuwan sukai,
Maamah ma dai kukan ya tsaya Se nauyin Daya danne mata kirji da zuciya.
Tafiyar zaman makokin wahala sukai me tsayin gaske har suka sauka Nigeria ga mamakinsu motan data zo daukansu daga Lagos sun dauka masauki zata kaisu sai kawai aka Sakasu motar zuwa Yola ba jirgi ba take hankalinsu gaba Daya ya tashi anty Farha ta zame da cewan Amatu batada lafiya zasu bari ta warware zuwa da safe su biyosu.
Mum Aisha ma take tace bazata iya bin mota ba hakama Husnah Amma Kiri Kiri aka sakasu mota sunaji suna Gani Husnah Se kuka take sbd tsoro da fargaban hanyar hakama mum Aisha jininta take yafara kokarin Hawa sbd tsoron hanya,maamah ce kawai Bata damuba sbd ba shine a gabanta ba tashin hankali biyu ne suke nukurkusanta,na yanayin ciwon da Amatun keyi da Kuma halinda Abeeda ke ciki.
Anty Farha suna wucewa ticket ta Siya musu suka hau jirgi duk da Yola sukai sbd Mr Jameel ya sanar mata can Akai dasu maamah sun Dena zaman Abuja gaba dayansu har Husnah.
Koda suka is mota Mr Jameel ya aika aka daukosu suka nufo mansion din ASH na Yola din.
Akwai masu aiki already a gidan sedai main gidan a rufe yake Dan haka bayan isarsu take aka bude koina masu aiki suka hau gyara,
Amatu daqyar ta iya tsayawa aka gama gyara koina gidan yayi fes qamshi da sanyin AC suka gauraya koina.
Dakinta data taba zama lokacinda suka baro kauye bayan auren suka sauka wanka tayi da ruwa me zafi sosai sukai sallah taci abinci sosai take ta kwanta bacci ya dauketa.
Itama anty Farha wanka tayi ta Saka kaya marasa nauyi ta kwanta baccin gajiya dana Daren jiyan da Basu yiba
Su kuwa su mum Aisha na can suna bugun hanyar lagos hankalinsu a tashe da tsoron hanya.
#MAMUH#
*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070
Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#
AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar
68
*MUFEEDA'S FRAGRANCE*
*GIDAN KAMSHIII*
Munada kayan turaruka kala kala kama dasu
Turaran wuta
Turaran jiki
Turaran Kaya
Humra milk
Humra black
Kwalacca
Turaran moping
Freshener
Daidai sauran su
Ta a Very affordable price.
Zaku iya tuntubar mu a wannan
07040986690
Muna zaune ne a garin Kano da Abuja (life camp) sannan muna aika kayan mu ko ina a fadin kasar nan har ma da kasashen waje. Akwai tsarin wholesale wato sarı ga duk me bukata sai ya tuntube mu. MUNGODE
*MUFEEDA'S FRAGRANCE*
*GIDAN KAMSHIII*
**********
Bacci sosai anty Farha da Amatu suka samu Wanda ya Dan sassauta jikin Amatun Dan haka sai a lokacin ta dawo cikakkiyar hayyacinta ta tashi da asuba tayi sallah ta janyo wayarta Dan Neman maamah tajita sbd tsoro ma itama yafara shigarta na tafiyar tasu dan Koda anty Farha ta janyeta daga tafiyar Sam Bata kanta sosai Dan ko tsayuwa Bata iyayi yanda ya kamata Daman Kuma Bata cikin wainda zasuyi tafiyar mota a tsarin tafiyar.
Sam Bata samun wayar maamah duk Kiran datakeyi Dan haka ta hakura ta ajiye wayar.
Dauke wayarta anty Farha tayi tareda kashewa gaba Daya ta jefa Jakarta batareda Amatun ta saniba Dan hanata shiga ko samun Kiran da zai damar da ita Dan kuwa umarnin kukawa da Amatun datasan ko ASH be fada ba to Hakan yake expecting daga gareta.
Har dare yakuma yi su maamah Basu iso ba suna can suna dukan hanya Dan haka da wannan Daman anty Farha tayi amfani ta ringa kulawa da Amatun sosai tareda hanata shiga damuwar abinda ya faru din sedai Amatun ta kasa cire damuwar halinda ASH din yake ciki a yanxu.
Dare nayi da wuri Amatu tayi bacci anty Farha ce kawai ta rage a farke har kusan 12 na dare saiga su mum Aisha sun iso.
Securities na gidan barka da zuwa kawai sukai musu Babu Wanda ya amsar musu kayansu Kuma a napep suka iso Karan farko na rayuwar Husnah da mum Aisha dasuka hawo napep.
Gabaki dayansu su ukun Babu Wanda yake dubuwa sbd azabar hanya da yunwa da masifaffiyar wahalar dasuka sha,
Kowannensu kaman an