Showing 81001 words to 84000 words out of 155363 words
Chapter 28 - SARAUNIYAR KYAU_Takun Farko _cmplt. By The Nainarh Kd -2-1.txt
yarinya kam da wani pretending."
Qara rufe fuska Deejarh tayi ta ce 'Kai Auntie Lailah Allah kina bani kunya da yawa fa "
Dariyar mugunta Lailah tayi "Ashe dai kinada kunyar."
Dawowa wurin Afeefah tayi hanunta riƙe da hular bat sky maroon, miƙawa Deejarh tayi tana faɗin
"Oya saka mu tafi."
Amsar hular Deejarh tayi ta saka, Lailah ta kuma gyara ma ta gashinta da ya sauko har gadon bayanta sannan suka fita a tare.
Tun kafin su ƙarisa palon ƙamshinsu ya isa hancunan mutanen da ke zazzaune a palon.
Habba ae nan kallo ya koma sama wai shaho ya ɗau giwa.🤐
Gaba ɗaya mutanen palon suka juyo suna kallon su fuskar ko wannensu su cike da fara'a da walwala, wata daga cikin ƴan matan ce tayi magana
"Amazing kunga *SARAUNIYAR KYAU* ta iso tana baza ƙamshi."
Gaba ɗayansu su ukun suka sama wuri a 3sieter suka zazzauna nan suka shiga gaisawa da mutanen palon cike da farin ciki suke amsawa amma yawancinsu idonsu yana akan Deejarh wacca take zaune kusada Afeefah tayi tsumu da ita kamar tsumma a randa 🤓
Afeefah ta lura da irin kallon neman ƙarin bayanin da mutanen n palon sukeyiwa Deejarh, amma ta sha re suka ci gaba da fira yayinda Deejarh take buga game na *Streetchaser* da wayar Afeefah.
Suna zaune sai ga mazan sun shishshigo dama can suna part ɗin Daddyn ne gaba ɗaya suma suka sama wuri suka zazzauna dayake palon Babba ne sosai kuma kujeru set biyu ne, yasa duk ya ishesu suka zazzauna nan suka shiga sabon gaisha gaishe yayinda Deejarh take buga game ɗinta hankali kwance tunda ta gaishesu suka amsa.
Wata ce daga cikin ƴan matan ta gaza haƙuri ta kalla Haleesat tana tambayarta
"Wai Leesat a'ina kuka samo wannan Beautiful Baby ɗin, ƴar Kyakkyawa da ita?."
Tayi tambayar tana nuna Deejarh sai kuma hankulan gaba ɗaya mutanen palon ya dawo kan Haleesat ɗin suna jira suji mai za ta ce, ganin ta kasa magana ne sai dai ta kalla Deejarh ta kalla mutanen palon.
Yasa M.m.k gyaran murya sannan yace "Ɗiyata ce sunanta Khadeejah."
Kallon Afeefah yayi yana murmushi yace "Shalele yima ɗiyata Khadeejah bayanin kowa da kowa."
Cike da taikaci Momy Rafi'at take jefawa Daddyn hararar ƙasan ido, tana jan qwafa wato dai Hajarah ta mutu ga Ƴarta ta gaji sarauta ko, yanzu fisabilillah gata zaune a palon, amma ya tsallaketa yace ma wannan yarinyar mai kamada uwarta wani wai shalele yima ta bayanin kowa da kowa, ta kwaikwayi muryar Daddyn a zuciyarta cike da haushi qwafa ta kuma ja sannan ta mayar da kallonta kan Afeefah kamar yadda duka sauran jama'ar palon suke kallonta.
Murmushi Afeefah tayi Sannan ta kalla Deejarh ta ce "Dama ba kinaso kisansu ba ko?."
Dariya Deejarh tayi ta ce "E, mana Balarabiyar India,"
Afeefah tayi dariya sannan ta ce "Yauwa to yanzunnan zakisan kowa da kowa Insha Allah."
Tayi maganar tana kuma kallon jama'ar palon.
Sannan ta nuna wata kyakyawar mata ta ce "Sunanta Mamy Zuwaira tana aure a Jigawa State yaranta huɗu maza biyu, mata biyu ga matan anan ta nunasu, Zakiyya da kuma Fateemah, mazan kuma Zaid da Yusuf, amma basu zo ba.
Gyaɗa kai kawai Deejarh take alamar tana ganewa sannan ta kalla matar da aka kira da Mamy Zuwaira ta ce "Sannu Mamyn mu."
Hajiya Zuwaira tana murmushi ta ce
"Yauwa sannu Khadijatu."
Kallon Zakiyya da Fateemah ta kumayi ta ce "Barkanku dai yayyina."
Suma suna murmushi suka amsa ma ta da
"Yauwa kema barkanki."
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.}``` ✏️
____________(✪)______________
https://www.facebook.com/profile.php?id=100069755834980
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*SARAUNIYAR KYAU* 💓
_(The Glam Queen)_ 👑
```Takun Farko```
Story & Written By:
*_The Nainarh KD_*
_In dedication to my dear Classmate Science G.S.S.S BELE ROAD._
*THE ONGOING BOOK'S*
1. *SONKI NE ƘADDARA TA*
MALLAKAR
FATIMA ABDULLAHI
_Batool Kamba_
2. *ZAN JIRA KA*
MALLAKAR
A'ISHA ALƘALI
_Mrs Aysib_
Page *45&46*
.
Afeefah ta ci gaba ta nuna wata matar dake hakimce saman kujera ta ce "Sunanta Mamy Jawaheer ita ma tana aure a Jigawa State ne, yaranta uku maza biyu mace ɗaya, sannan ta nuna wasu kyawawan matasan samari da suke zaune kusada Daddy tana faɗin "Gasu nan da Yaya Omar da kuma Yaya Umer, sai ta nuna wata matashiyar budurwa dake zaune gefan Zaynerb ta ce "Sai wannan sunanta Husnee."
Deejarh ta gane budurwar ita ce wacca suka haɗu da zata shiga Bedroom na Afeefah ɗazu, dan haka cikin sakin murmushi ta musu sannu duka suma suka amsa.
Ci gaba da magana Afeefah tayi Bayanta nuna wata matar
"Sunanta Mamy Jummai ita ma dai aure take a Jigawa State, yaranta uku duka mata ga ɗaya anan wacca taci sunan Mamy Jawaheer muna kiranta da 'Ƙarama' sauran biyun kuma suna karatu a Abroad.
Sai kuma Mamy Sakina tana aure a mai Duguri amma ita bata sama damar zuwa ba, gadai wakilanta wato yaranta su biyu Yaya Salim da kuma Saleemarh."
Suma suka gaisa da Deejarh cikin sakin fuska abunka da ƴan boko wayayyu.
"Sai kuma Uncle Yusuf."
Ta nuna wani magidanci da yake zaune kusada da Daddyn sannan ta nuna wata mata da yara biyu mata ta ce "Ga matarshi Auntie Yusra da yaranshi Yasira da Yasmin, akwai Yaya Yasir amma shi baizo ba yana ƙasar Australia yana karatu, suna zaune a Adamawa State ne."
Suma suka gaisa da Deejarh tana washe baki.
Afeefah ta ɗanyi shiru sai can ta ce "Akwai Uncle Saminu yana zaune a Lagos da iyalansa, amma suma basu sama damar zuwa ba, sai kuma Uncle Yunus yana zaune a ƙasar France shida iyalansa."
"Sai wannan da kike gani Mamy Suwaiba matar Uncle Sagir ce."
kana ta nuna wasu kyawawan ƴan mata biyu da wani saurayi tana faɗin
"Yaranta ne Haseeya da Mah'eesha sai Yayah mahfuz."
Ajiyar zuciya Deejarh ta sauke tana kallonsu su duka a zuciyarta tana mai faɗar "Lallai ma, wato su kowa yanada twin's ne a familynsu?, babu inda basu ko'ina suna nan."
Ta kalla Afeefah ta ce "Lah Balarabiyar India.! Baki faɗamin garin da suke ba, dukansu."
Afeefah ta bata amsa da "Ki cin ka mana."
Ɗan shiru Deejarh tayi tana kallonsu kana ta ce
"Ina ganin Kano ne ko?."
Afeefah ta amsa ma ta da "E, haka ne."
Da sauri Deejarh ta ce "To wai ina Ammah ne, naga basu zo da ita ba?."
Wannan karon Zaynerb ce ta ce "Kedai Deejarh rabu da Amman nan rigima take ji taƙi zuwa, wai sai dai mu muje can fa."
Nainarh ta karɓe da faɗin "Ai ni nayi fushi da ita, tunda taƙi zuwa a taya Afeefah murna da ita."
Nailah ma ta ce "Mu ai sai muje can mu sa me ta, idan mun tashi tafiya gida ko?."
Deejarh ta kalla Afeefah ta na faɗin "Balarabiyar India kema zakije na bi ki?."
Kafin Afeefah tayi magana wata daga cikin ƴan matan wacce Afeefah ta kira da suna 'Husnee' ta ce
"Ni fa ina da tambaya?."
Kallonta sukayi Haleesat na cewa "Muna jin ki, go ahead."
Husnee ta ce "Wai meyasa naji wannan yarinyar..." ta nuna Deejarh. "Tana kiran Afeefah da Balarabiyar India ne?."
Lailah ta bata amsa da "Muma hakan muke ce ma ta ai wasu lokutan."
Wannan karon Umer ne yayi tambaya da faɗin "To saboda me kenan?."
Deejarh ta amsa "Saboda ita kyakyawa ce."
Yasira ta ce "To amma ae naga babu Larabawa a Indai ko?."
Yasmin ce taba Yasirar amsa da "Kika sani ko akwai su, kece baki sani ba?."
"Ni dai nasan ba wasu Larabawa a ƙasar India, dama dai Qatar ta ce ko kuma Sudan ko Egypt da dai sauransu dai, dana yarda."
Cewar ƙarama. Ɗiyar Mamy Jummai.
Deejarth ta ce "Ai saboda babu Larabawa a India ne, yasa nake ce ma ta Balarabiyar India fa."
"Because of what?."
Haseeya ta tambaya
Deejarh ta ce "Saboda duka Indiyawan tafisu kyau."
Dariya aka saka Mahfouz yana faɗin "Ni dai banga laifinta ba, ai gaskiya ta faɗa, domin Afeefah kyakyawa ce, ni ma daga yau Balarabiyar India zan dinga kiranta dashi gaskiya."
Nan ma aka kuma saka dariya Mamy Zuwaira ta ce
"Nima dai hakan."
Fateemah da Zakiyya suka haɗa baki wajen faɗar
"Muma haka gaskiya."
Nanfa kowa ya shiga faɗin shima haka, daga haka dai aka dasa sabuwar fira a tsakanin familyn cike da farin ciki da fahimtar junan su, suke firan nasu gunin burgewa abin nasu.😎
Can suna cikin fira sai ga Elina da Ummi ma'aikatan gidan masu girka lunch suka ƙariso wurin sanye cikin kayan ma'aikata, sun ɗaura apron blue a saman kayan jikin su, wurin Momy Rafi'at Elina ta ƙarisa cike da ladabi ta ce
"Madam the lunch is ready, shin a jeresu a Dining Room ne, ko kuma a kawo nan?."
Tayi maganar cikin harshen turanci, tana jira a bata amsa, ɗan murmushi Momy Rafi'at tayi sannan ta amsa da
"Ah inaga a kawo nan kawai domin za'a fi enjoying da kyau."
Cike da ladabi Elina ta amsa ma ta, sannan ta juya ita kuma Ummi ta shimfaɗa lodojin cin abinci daga can gefe a wuri biyu ma'ana da wurin maza dana mata mabanbanta.
Cikin ƙanƙanin lokaci suka kammala jere komai akan lodojin, sannan Elina ta dawo ta faɗawa Momy Rafi'at sun kammala, kana ta koma ciki.
Magana Momy Rafi'at ta musu gaba ɗaya mutanen palon suka tashi suka nufa wurin cin abincin, kowa ya zauna a wurin da ya dace dashi, yayinda Ummi take binsu ɗaya bayan ɗaya da roba da ruwa a hannunta suna wawwanke hannayensu a ciki, sai da suka kammala tsaf sannan ta koma ciki.
Su kuma suka fara ɗu'amun sannu a hankali cikin nutsuwa.🥳
A hankali Deejarh dake zaune gefan Afeefah, ta matsa da bakinta sai tin kunnen Afeefah ɗin tana faɗin "Balarabiyar India, shin zan iya tambayar ki wani abu?."
Afeefah ta ce "Inajin ki."
Deejarh ta ce "Waɗannan matan da suka raba abinci, su kuma daga ina suke?, Naga ma harda arniya a cikin su😏."
Murmushi Afeefah tayi dama tuni ta rubuta ta aje cikin zuciyarta sai Deejarh ta ma ta wannan tambayar. Ita ma cikin ɗan ƙasa da murya ta bata amsa da cewa "Ma'aikata ne su, wa'innan da kike ganin su Degree, garesu akan fannin girge_girge anan gidan namu suke aiki ana biyansu Salary mai tsoka, duk wata."
Deejarh da mamaki ya kamata ta ce "To meyasa kusan kwanana goma anan, amma ban taɓa ganin su ba sai yau kuma yanzu?."
Afeefah ta bata amsa da "Saboda sun tafi gida hutun watanni har biyu ne, yau suka dawo shiyasa bakisan su ba."
Deejarh tana gyaɗa kai alamar gamsuwa da bayanan Afeefah ta ce "Ooho kice ba'a nan garin suke ba kenan?."
Murmushi Afeefah ta kumayi, ita fa Wallahi bata gajiya da shirmen tambayoyin da Deejarh take ma ta, saima sakata nishaɗi da suke yi🤣
Ta ce "E, ita Ummi anan kusa take amma dai bansan sunan garin su ba, sai dai wata ƙila ma, anan Abuja suke zaune. Ita kuma Elina Ƴar Lakwaja ce, ita ma dai bansan sunan ainihin garin da take ba..."
"Wai kam nace gossip ɗin wa akeyi ne haka, naji anata qus qus fa?."
Cewar Husnee tana kallon su Afeefah ɗin.
Dariya Deejarh tayi ta ce "Sirri ne, tsakani na da Balarabiyar India ta."🤥
"Oh tunda haka ne, bari na barku ku ci gaba, ayi gulma da kyau guy's."
Husnee tayi maganar tana mayar da hankalinta wajen cin abincinta.
Hayaniyar da suka ji, yana tashi ne daga can waje yasa duk sukayi shiru, suna so su fahimci abin da ke faruwa.
Jin da sukayi hayaniyar ba mai ƙarewa bane, yasa ba shiri gaba ɗayansu, suka mimmiƙe suka nufa waje domin ganin abin da ke faruwar.
Gaba ɗayansu fitowa sukayi waje, don ganin komai. Daga can tsakiyar compound ɗin gidan suka hango gaba ɗaya ma'aikatan gidan sunyi curko curko dasu, ga wani saurayi ya juya baya yana zuba musu ruwan masifa kamar wanda baya cikin hankalin shi.
Da sauri suka ƙarisa wurin su duka Daddy yana tambayar Peter mai bawa flowers ruwa abin da ke faruwa. Cike da girmamawa Peter yake faɗi cikin hausar sa wacca bata gama karyewa a harshen shi ba.
Yace.
"Sir wannan ne,"
Ya nuna saurayin dake faman zabga masifa kafin ƙarisowarsu wurin amma suna ƙariso yayi tsit sannan kuma yaƙi juyowa.
"Sir tun ɗazu yake ƙoƙarin shigowa ciki, yana faɗin gidan sune wai, mu kuma bamu sanshi ba, munƙi bashi dama, shi kuma ya dage, ya dage akan sai ya shigo, har yana marin Moses fa, shi ne mu kuma muka dage muka hanashi shigowa Sir."
Peter yana maganar ne, yana gwada musu yadda saurayin yakeyi wai. { kuma dai masu karatu kunsan yadda Yare suke Especially ma idan suna so a Yarda da abin da suke faɗa 😆 }.
Ɗan murmushi Daddyn Yayi ganin yadda Peter ya dage yana bayani, bayaji baya gani, ba kuma ƙaƙƙautawa.
Sannan Mister Mai Kyau ɗin, ya mayar da kallon shi akan saurayin wanda
yake sanye cikin riga Top blue mai gajeren hannu, sai kuma wando Crazy Jean's wanda ya tsaya mishi iya gwiwa black color, ya saka p-cap black akanshi ga kuma face mask black, shima dai. Ya goya Backpack irinna na masu tafiya a bayanshi, ƙafafunnshi kuwa Boots ne blue color, ga kuma wani akwatu yashe a gefansa.
Cikin jin ɗan faɗuwar gaba, wanda baisan dalili ba, Daddyn ya fara magana kamar haka.
"Yaka ɗan saurayi, shin zaka iya jiyowa domin muga fuskarka da kyau kuwa?."
Shiru saurayin yayi kamar ba zai juyo ba, sai can ya juyo gaba ɗayanshi tare da cire face mask ɗin dake a fuskarshi nan take kyakyawar fuskarshi ta bayyana.
Tundaga kan Momy Rafi'at wacca ko'a mafarki ba za ta taɓa manta wannan kyakyawar fuskar ba...
Da Nailah wacca gaba ɗaya tsananin mamaki da ruɗani ya bayyana a kyakyawar fuskarta.
Ga Haleesat wacca ko daga bacci ta tashi ba zata taɓa mantawa da wannan fuskar ba.
Ba re Lailah wacca kullum take kwana take tashi da tunanin wannan saurayi da kyakyawar fuskarsa a kullum.
Zaynerb kuwa, ita bama za'a iya cewa komai ba, domin kuwa, she was very thither shock.
Gaba ɗaya suka haɗa bakunan su wajen faɗar
"BUDDY."
Afeefah da ƙarisowar ta wurin kenan ita da Nainarh da kuma Deejarh, taji maganar a kunnuwanta tamkar saukar adu.
Da wani irin sauri take wuce mutane harta ƙarisa gaban shi ta tsaya cak tana kallon shi kamar yadda shima yake kallonta.
Cikin sarƙewar murya da wahalar fitar numfashi take faɗin
"YaYa Maleek..! kaine kuwa..?"
Lallausar murmushi ya saki, sannan yace
"Ni ne dai Yaya Maleek ɗinki mai ƙaunar ki, yau gani na dawo gareki, shin ba za ki zo kiyi Hugging ɗina ba kamar yadda kika saba a koda yaushe?. MY sweet Blood 6ter?."
Yayi maganar yana buɗe ma ta duka hannayenshi.
Da gudun tsiya Afeefah ta nufa gurin shi, da niyyar zata rungumeshi, kamar yadda ya buƙata.
Sai dai kafin ta ƙarisa wurin sa, ta zube a ƙasa sumammiya.🤕
🔥ᴛᴀsʜɪɴ sᴇɴsᴇ🔥
Ai da wani irin sauri Maleek ya jefar da Backpack dake rataye a kafaɗunshi, Yayo kan Afeefah da gudu yana kiran sunanta da ƙarfi ya kai Hannu kenan zai taɓa ta.
Cikin mugun buga tsawa Nainarh ta dakatar dashi da faɗin
"Kar ka sake ka taɓamin Ƴar uwata da wannan ƙazamin hannun naka.🤨
Cak Maleek ya dakata da niyyar taɓa Afeefah da ya yi.
Ya juyo da rinannun idanun shi waɗanda sukayi jajir lokaci guda, saboda tsananin ɓacin rai, yana kallonta.
Qarisawa wurin Nainarh tayi tana tafa hannu ta ce
"Sai Yau?, na ce yau ne ka tuna damu Buddy?."
Nuna Afeefah dake yashe maga shiyan a ƙasa tayi da hannayenta waɗanda suke tsananin rawa tana faɗin
"Dube ta baiwar Allah yau tana cikin farin amma da zuwarka kalla yadda ta ƙare fa. Yanzu ka Faɗamin meyasa zaka zaɓa wannan ranar. This is only our glamorous Day, not yours, Amma... duba ka gani, daga zuwanka duba baiwar Allah yadda ta ƙare a sume fa."
Maganar take cikin hargowa da tsananin ɓacin rai gaba ɗaya ta manta wanda yake tsaye a gabanta, ta manta Buddy ɗinsu ne mai ji dasu, ta rufe ido tana zazzaga mishi masifa, tana fitar da duka baƙin ciki da damuwar da suka daɗe suna caccakar zuciyarta.😰
Zubewa Maleek Yayi gwiwo winshi duka a ƙasa yana zubar hawaye.
Hawayen da bai zubar dasu ba ranar da yabar gidan, Hawayen da ya daɗe yana jiran fitowarsu sai yau suka ƙari so. Saboda tsananin kuka ya ma kasa magana.
Shikuwa Daddyn su wato Mister Mai Kyau, Ashe tuni ya daɗe da yin sumar tsaye ba'a sani ba tun lokacin da Maleek ya juyo, da kuma tun lokacin da Shalelen shi ta zube a ƙasa sumammiya alamar ciwonta ne yakeso ya taso.
Ganin za'ayi to ne to ne ne, a tsakiyar gida yasa Uncle Yusuf kallonsu gaba ɗaya yana faɗin
"Ku shiga daga ciki a ƙarishe maganar zai fi."
Yayi maganar yana kamo hannun Daddyn wanda ya zama kamar mutum-mutumi, sannan ya kalla Auntie Yusra yace da ita.
"Ku kamo Afeefah ku shigo da ita ciki,"
Kallon shi ya mayar kan Maleek da har yanzu yake a durƙushe, cikin sanyin murya Uncle Yusuf Yace
"Ka ɗauko kayanka ka shigo ciki." sannan ya yi gaba.😞
{*Tofah.! masu karatu, wai shin Menene ainihin abin da yake faruwa ne, a wannan labarin, gadai Maleek ya dawo gida, kuma ga Daddyn Ya zama kamar baya cikin hayyacin shi, gefe guda kuma ga Jarumar mu tana sume cikin wani hali, shin dama akwai wani ciwo ne da Afeefah take dashi ba'a sani ba🤔 koma dai menene yanzu zamuji asalin labari }... INSHA ALLAH 💘*}
*SARAUNIYAR KYAU*💓
_(The Glam Queen)_ 👑
```Takun Farko```
Story & Written By:
*_The Nainarh KD_*
____________________________________________👑
*THE ONGOING BOOK'S*
1. *SONKI NE ƘADDARA TA*
MALLAKAR
FATIMA ABDULLAHI
_Batool Kamba_
2. *ZAN JIRA KA*
MALLAKAR
A'ISHA ALƘALI
_Mrs Aysib_
___________________________________________👑
*TH£ B£GINNING OF THE STORY*
*MAFARIN LABARI*
*SOM£ Y£ARS £ARLI£R*
*AL_HAJI SAMEER LAMIƊO*
Page*47&48*
Shararren mai dukiya ne, wanda duniya ke ji dashi, a domin kuwa ba iyaka ƙasar