Header Ads
Showing 102001 words to 105000 words out of 155363 words

Chapter 35 - SARAUNIYAR KYAU_Takun Farko _cmplt. By The Nainarh Kd -2-1.txt

Ads the beginning of article before Image

Nanah Kd   

14 Jun 2024

1021

Ads at the middle of Article

tanaso ta taimakawa budurwar da ta hango cikin jini, wacca ko fuskar ta bata hango sosai ba.






Tsayar da Motar Ya yi a dai dai sai tin budurwar dake kwance cikin jini kayan jikinta da suke farare suma sun koma ja saboda tsananin jinin da ta zubar.






Fitowa suka yi shi da Rafi'at daga cikin Motar suka bar Abdulmaleek da Nainarh.

Rafi'at ta Riƙo Nailah a hannunta sannan cikin sauri gaba ɗaya suka ƙarisa gaban budurwar dake kwance.




Sai kuma lokacin tsoro ya fara kama Rafi'at, wannan tsoro bana komai bane saina ganin wani kalar masifaffen kyau da wannan budurwa wacca ta gama yin kaca kaca cikin jini duk da cewa cikin jini take amma wannan bai hana Rafi'at hango tsantsan kyau na musamman da wannan budurwa ke da shi ba.


Cikin zuciyarta tana mai tabbatar wa koda za'a bar wannan budurwa a haka ba tare da tayi wani kwalliya ba a haɗasu Gasar kyau Rafi'at tana da tabbacin duk da itaɗin tana da masifar kyau tofa wannan budurwa sai tayi ma ta zarra.








A fili Abubakar ya furta kalmar


"Masha Allah."


"Allah mai hallita yarda ya so..."


Ya yi maganar yana kuma ƙarewa kyakyawar fuskar ta kallo domin kuwa zai iya cewa tunda Yake a duniya bai taɓa ganin macen da kyau ya yi mata kyau ba sai wannan budurwa dake kwance gaban sa, cikin jini ga idanunta a rufe da alama suma tayi.

Ita ɗin mai kyau ce cikin masu kyau. 🤠🏃👑




Ganin Yadda mijinta Abubakar mai kyau ya tsuguna yana ƙarewa wannan budurwar dake kwance cikin jini dake gabansu kallo, ya sa Rafi'at jan ɗan ƙaramin tsaki cike da jin haushi na Rashin dalili ta ce

"Malam Mai Kyau ka taimaka mu kamata a sakata a mota domin a kai ta Asibitin saboda naga jini take zubarwa fa."


Rafi'at tayi maganar cikin ƙunƙuni ganin kamar bai jita ba yasa ta dage iya ƙarfinta ta ɗaka masa duka a baya tana kuma maimaita masa abin da ta faɗa.



A maimakon taga Yaji haushin dukan da tayi masa, a'a sai ma tsadadden murmushi Ya yi ma ta kana ya miƙe yana gyara hannun rigar sa, ganin haka yasa ta aje Nailah a gefe ita ma ta fara kici kicin gyara mayafin kanta.




"Ke kuma mai zakiyi?."


Taji Abubakar ya tambaye ta, murmushi tayi kana ta ce

"Zan tayaka ne mu cicciɓeta a kaita Asibitin ai."


Tayi maganar tana dariya.🤣


"Saboda kin mayar dani Rago ko me?."


Ko kafin ta nema amsar da zata bashi tuni taga ya ɗauki wannan budurwa da duka ƙarfin da Allah ya bashi ya nufa motar shi da ita🧐.



Baki wangame 😨 Hanci sake 👃 ido warwaje 👁️👁️fuska ɗauke da matsanancin mamaki 🤔 Rafi'at tabi mijinta Abubakar da kallon ikon Allah.




Ai bata tsaya tunanin komai ba ita ma ta mara masa baya, har ta kusa motar, ta jiyo kukan Jaririyarta Nailah da sauri ta juya Ashe wai saboda tsananin mamaki da matsanancin kishi ne yasa ta manta da jaririyarta a wurin.🤣





Fin ciko Nailah tayi saboda baƙin kishi ko gabanta bata gani da sauri ta ƙarisa jikin motar tana haki, shikuma Abubakar daidai lokacin ya gama daidai ta ma wannan budurwa kwanciya a back seat kusa da Yara.




Fito da kansa Ya yi daga cikin Motar kana Ya kalleta cikin murmushi Yace


"Ina trolley ɗin ta dana gani gefe kin ɗauko kuwa?."




Cike da takaici Rafi'at ke kallon mijinta Abubakar Mai Kyau saboda takaici da kishin da ya zo ya danne ma ta maƙoshi, ta rasa amsar da zata bashi, sai kawai ta tsinci kanta da faɗin!


"A'a ban ɗauko ba dama umarni nake jira a bani aii 😬."




Murmushi ya yi baima kula da Yayin da take ciki ba. To koya kulama Sharewa Ya yi sannan Ya ce

"Okay to your lawful ya bada umarni maza Kije ki ɗauko ma ta trolley ɗin wata ƙila akwai abubuwan ta masu muhimmanci a ciki."





Murmushin yaƙe kawai Rafi'at take yi cikin zuciyarta kuwa tana jinjina wannan ƙarfin hali na Abubakar wai ɓarawo da sallama.

Amma banda ya Raina ma ta wayo wato ita ce zata je ta ɗauko trolley ko ba komai ae.




Ajiyar zuciya ta sauke kana ta gyara Riƙon da tayima Nailah ta nufa wajen da trolley ɗin yake ta ɗauko kana ta dawo, ko kallo Abubakar bai isheta ba taje ta buɗe boot ta saka sannan ta dawo ta buɗe Motar gidan gaba ta shige ta zauna tana faman huci da hura hanci.






Shigowa shima Abubakar Ya yi sannan ya tayar da Motar suka ɗauki hanya firan da sukeyi ɗazu ma ko shi ba'ayi Yanzu. Tafiya suke tsit Abubakar ne ma da ya gaji da tsit ɗin ya kunna karatu a Radio na Motar.

Su kuwa Yaran tuni sunyi bacci amma banda Abdulmaleek da ya zubawa wannan budurwa ido yana kallo kamar ya sama TV.


Rafi'at tana lura dashi ta madubin mota qwafa taja tana kuma tamke fuska.





Wani emergency suka iso da ita ba tare da da ɓata lokaci ba Abubakar bayan ya fito ya buɗe back seat ta ɓangaren da ya kwantar da wannan budurwa sannan ya fito da ita.

A lokacin wasu Nurses biyu sun turo gadon ɗaukar marasa lafiya, dan haka cikin sauri ya kwantar da ita saman gadon sannan aka ja suka nufa ciki tare da shi.






Ita kuwa Rafi'at zama ta gyara a motar tana jan tsaki.


Abubakar ya daɗe ciki bai fito ba sai da ya kammala duka abin da ya kamata dan ma shiɗin sananne ne daɗi da ƙari ga Naira shiyasa ba tare da wani ja'inja ko ɓata lokaci ba likitocin suka karɓa budurwar, sai da ya tabbatar da an shiga da ita ɗakin hutu bayan likitoci sun gama bata taimakon da ya kamata sannan ya fito da niyyar zuwa anjima idan ta farfaɗo sai su dawo ganin ta da yake lokacin dare ya fara kawo kai.





Tana zaune harta fara gyan-gyaɗi ta hangoshi Yana nufo motar, ajiyar zuciya ta sauke ta ƙirga a dadin lokacin da ya ɗi ba a ciki kusan awanni biyu.

Gyara wa Nailah kwanciya tayi a saman jinyarta sannan Ita ma ta sai ta zaman ta kana ta rufe idanunta kamar mai bacci.




Buɗe motar Ya yi sannan ya shiga bayan ya kammala abin da ya kamata ya tayar da Motar suka bar emergency ɗin sannan ya ɗauki hanyar gidan sa.




A hanya jin shiru taba yi masa magana ba, yasa ya ɗan juyo da fararen idanun shi yana kallonta duk a tunanin sa tayi bacci ne.

Ya yi murmushi a fili Yace

"Mata iyayen kishi."



Tana jin sa tayi muluqwiii kamar mai bacci.



Har suka ƙariso gida Ya daidaita faker motar a wurin da aka tanadar domin yi bayan gate man ya wangale masa gate.




Bata koyi motsi ba, hakan yasa Abubakar ɗan bugun kafaɗunta yana kiran sunan ta.

Ƙin motsi tayi shi kuma yaƙi denawa haka ba yadda ta iya, ta buɗe idanun ta tana hamma ta Kalle sa cike da ƙissa ta ce


"Oh My Lawful am sorry har mun ƙariso gida ban samu na tayaka fira ba bacci ya yi gaba dani."





Murmushi Abubakar ya yi ma ta sannan yace


"Aah karki damu kinji, matar mai kyau, nasan akwai gajiya fa sosai."




Fitowa suka yi gaba ɗaya shiya taimaka ma ta wajen kwashe Yaran suka shiga ciki.
Shi Maleek aka kai shi ɗakinshi Yayin da suma sauran ta wuce dasu nata bedroom ɗin, shima Abubakar ya wuce nasa dukanin su a gajiye suke over.






___*💋 SARAUNIYAR KYAU 💋*___________________________________________________________________💥👑𝑻𝒉𝒆 𝑮𝒍𝒂𝒎 𝐐𝐮𝐞𝐞𝐧👑💥____________________𝑩𝒚:𝑻𝒉𝒆 𝑵𝒂𝒊𝒏𝒂𝒓𝒉 𝑲𝒅____𝑲𝒉𝒂𝒅𝒆𝒆𝒋𝒂𝒓𝒕𝒉. 𝑺𝒂𝒃𝒊'𝒖. 𝒀𝒂𝒉𝒚𝒂𝒉🤙


Page *65&66*




*WASH£ GARI*






Tana tsaye a kitchen sanye cikin kayan shan iska ta ɗaura apron saman kayan tana haɗa musu Breakfast cikin nutsuwa take komai abinta.



Alamar taku da ta jine yasa ta tsaya da abin da take yi sannan ta juyo.

Da tsananin mamaki take kallon mijinta dake tsaye gabanta sanye cikin doguwar jallabiya Brown tunani take shin ko ya yi makuwa ne ko me, amma in banda haka mai zai kawo shi kitchen bayan tunda suka yi Aure shekaru wajen nawa ko tunanin shiga baya yi, ko irin yace zai taya ta girki, a'a sai dai wani ba Abubakar sai dai ta girka yaci ba godiya balle 🥰....




A je tunanin tayi a gefe sannan cikin murmushi ta ce

"Barka da safiya My Lawful Fatan dai ba neman wani abu bane ya kawo Babban mutum kamar ka kitchen, kai da kanka baka nema wannan servant naka ba a domin ka bata umarni ba."



Murmushi Abubakar Mai Kyau Ya yi sarai ya fahimci abin da take nufi wato dai gatse tayi masa ko ba damuwa, gyara tsayuwar sa ya yi kana Yace


"Ko ɗaya dama nazo ne na faɗa miki ki girka abinci daban saboda..."

Da sauri ta katse shi da faɗin

"Baƙi zamuyi hala, ai karka damu Yanzu zan kammala sai na saka a kuloli, kaje kayi shirin office kawai oga."


Tayi maganar tana juyowa ta ci-gaba da aikin da take yi, bai kuma cewa komai ba ya fice shima daga madafar.





__*

Wuraren ƙarfe Takwas da Rabi a Ranar tana zaune saman mattress bayan sun kammala breakfast ne tayi wanka tayi shirin zuwa asibiti, shi ne ta zauna a gefan mattress tana jiran shigowar mijinta Abubakar ɗakin.




Jin shiru bashi ba labarin sa yasa ta miƙe sannan ɗauki lab-coat ɗinta da kuma jakar ta dama tuni ta yafa mayafin ta.



Fitowa tayi kai tsaye ta wuce bedroom ɗin sa tura ƙofar tayi bakinta ɗauke da sallama daga can ta hango sa tsaye sanye cikin shigar alfarma na manyan kaya.

Ɗan dafe kanta tayi ita ta manta Yau Laraba wacca ta kasance first October babu aiki sam.


Ajiyar zuciya ta sauke sannan ta ƙarisa shiga ciki tana faɗin

"Oh amma a gaisheni, gaba ɗaya na manta da cewa Yau ɗin a Free muke Ranar zagayowar Ƴan cin ƙasarmu abin alfaharin mu."


Tayi maganar tana dariya.
"Karki damu kinji kin kusa samun Abokiyar zama kinga saita dinga tayaki wasu ayyukan inaga idan kika sama Abokiyar zaman zaki rage samun tention da yawa ko kuwa?.."


Tunda Abubakar ya fara maganar Rafi'at take faman antaya masa harara.

Lura da hakan da ya yi ne ya shi canza topic ɗin ba shiri.🤣




Murmushi Abubakar Mai Kyau Ya yi sannan Yace


"Okay to ai babu damuwa a haka ma Yadda kike zaki iya Rakani izuwa unguwa tare da Yara."



"Unguwa kuma to wurin wa."


Rafi'at ta tambaya cikin suɓutar baki.



"Kedai kawai ki shirya zaki gani ai."


Abubakar ya bata amsa, bata kuma cewa komai ba ta miƙe tana kallon sa sannan ta ce

"Ka bani mintuna biyar Yanzunnan zan shirya shaf-shaf."


Tayi maganar tana nufar ƙofa ta buɗe sannan fita.



Tana fita bedroom ɗin ta ta wuce tana shirya wa tana tauna maganganun Abubakar wato Abokiyar zama, kuma ita hmmm, murmushin Takaici tayi a fili ta ce

"Rafi'at Rafiq Rayyan tafi ƙarfin ayi ma ta kishiya har duniya ta naɗe forever Wallahi."




Tsaf ta gama shirinta sannan ta ɗauki jakar ta da mayafinta ta fito waje har lokacin bata gama dawowa dai-dai ba domin kuwa har wani zazzaɓine taji Yana shirin kamata jin maganar kishiya, wai danma da wasa ya yi ma ta maganar, imagine take yi to da'ace da gaske Abubakar Yake wannan maganar ya zatayi ke nan."


A fili ta ce "Sai dai idan bani a duniyar."





Downstairs ta sauko daga can saman kujeru ta hango mijinta Abubakar ga Yaranta suma a shirye cikin shigar alfarma suna fira da mahaifinsu Abin gunin ban sha'awa.


Murmushi kawai take yi tuni ta manta da maganar wata banza kishiya, hango mijinta da tayi da Yaranta cikin farin ciki.



Sai ita ma ta tsinci kanta a cikin matsanancin Farin ciki taji gaba ɗaya baƙin cikin da Abubakar ya ƙunsa ma ta na maganar kishiya ya gudu.



Qarisowa wurin tayi fuska ɗauke da ƙayataccen murmushi tana faɗin

"Oh My Lawful ayi haƙuri dani na ɓata muku lokaci daya wa ko?."


Tayi maganar cike da ƙissa, murmushi Yayi Yace

"Oh no Yaranki sun qwace ki saboda sun zagaye mahaifin su suna masa tatsuniya."



Tana dariya ta ce "Ai haka ake so."


Abdulmaleek Yaron da bazai wuce shekaru huɗu da watanni ba a lokacin ya kalla mahaifiyar sa kana ya mayar da kallon sa akan mahaifin nasa dariya ya yi cikin qwaranci irin na sa Yace


"Daddy! Mommy!!."


Gaba ɗaya suka juyo suna kallon shi Yace
"Momy Daddy Yafi ki kyau cocai cocai."🤣



Dariya suka yi baki ɗaya kana Rafi'at ta ce

"Aha ai kowa ma haka ake cewa harni ma na sani saboda shiɗin kyakyawane a cikin kyawawa."


Tayi maganar cike da nishaɗi, miƙewa suka yi ita ta riƙe Nailah Yayin da Abubakar Ya ɗauki Nainarh sannan Ya riƙe hannun Abdulmaleek suka fita waje, motar sa suka shiga baki ɗaya sannan ya tayar da Motar, gate man ya wangale masa gate ya fita sai unguwa🚗..../This is the happiness family/....🚗







***





Cak murmushin dake akan kyakyawar fuskar ta ya gushe fuskarta ta koma Tamkar bata taɓa murmushi ba, saboda tsaban mamakin wurin da taka mijinta Abubakar ya dawo dasu "this is unbelievable."

Wato shiyasa taka jiya da dare ya fita bai dawo ba sai wuraren sha ɗaya Abin da bai taɓa ma ta ba.


Kallon sa tayi dai dai lokacin da shima ya juyo da kallon shi akanta, cike da tsaban takaici ta ce

"Haba My lawful yana ga ka dawo damu wannan emergency kodai wani ne aka kwantar ban sani ba?."


Tayi maganar cike da sa ran ya bata amsa ba kalar wanda take tunani ba.




Gimtse kyakyawar fuskar sa ya yi alamar ba wasa kana ya ce

"Wurin Ƴar uwanki muka zo domin tafiya da ita gida."


Ya mutsa fuska tayi cike da alamar tambaya take kallon sa sannan ta ce


"Wacca Ƴar uwata kuma Sailuba ba ko wa?."





Girgiza ma ta kai ya yi alamar a'a kana Yace


"Fito mu shiga zakiga ko wacece ai."


Babu musu ta buɗe motar ta fito shima bayan ya fito suka riƙe Yaran sannan suka nufa ciki Yayin da wasu Nurses ma ta ke bin bayan su da kulolin abincin da suka zo dasu.





Ita dai Rafi'at tafiya take kawai amma gaba ɗaya hankalin ta baya a jikin ta tunani take shin ko wurin waye haka Abubakar ya kawo su, ita ko kaɗan bata kawo wannan budurwa da suka taimakawa jiya a tunanin ta.


To akan me ma zatayi tunanin ko ita ce bayan cewa taimakon ta kawai suka yi bawai zasu kasance da ita bane.






Har suka ƙariso Ward ɗin bata ankara ba, har sai da taga waɗanan Nurses dake gabansu sun shiga wani Room kana ta fahimci nanne Room ɗin da wacca suka zo wurinta take.



Tura ƙofar Room ɗin Abubakar ya yi ya shiga Bakin sa ɗauke da sallama yayin da ita ma Rafi'at ta take masa baya.





Zaune take a saman gadon marasa lafiya jikinta sanye da kayan asibiti gaban ta kuma tufa ne take ci a hankali, kanta a duƙe tana kallon ƙasa, sai da ta cinye Wanda yake a bakinta sannan ta amsa sallamar da taji anayi a daidai lokacin da ta ɗago da kanta tana kallon mutanen dake shigowa ɗaya bayan ɗaya take binsu da kallon Rashin sani.





Wani irin bugawa ƙirjin Rafi'at Ya yi ganin kyakyawar fuskar budurwar dake a ɗakin zaune saman bed.



It's unbelievable menene kuma haka me yasa Abubakar ya dawo dasu wurin wannan to su mata Mene?.





Ajiyar zuciya ta sauke sannan ta sama wuri ta zauna a saman wata farar kujera kusa da mijinta Abubakar da shima ya zauna.




"Sannun ku fa please Mister and Mrs kune kuka taimake ni. In Yesterday?."




Budurwar ta musu tambayar fararen haƙoran ta duka a waje saboda murmushin dake akan kyakyawar fuskar ta.



Har Rafi'at ta buɗe baki zata bata amsa ke nan, likita ya turo ƙofar room ɗin ya shigo yana mai musu sallama.




Shiru Rafi'at tayi kamar mai tunani tana ji lokacin da su Abubakar da wannan budurwa suka amsa masa sallamar amma ita tafasar da zuciyarta take bai bari ta amsa ba.




Bayan wannan likita da Abubakar sun gaisa ne, budurwar ta kuma antayo musu tambayar ɗazu.


Murmushi likita ya yi sannan yace


"Kedai Wannan patient nawa kinaso ki gano mutanen da suka taimake ki ko to ai sune waɗannan a gaban ki."




Dariya tayi cike Farin ciki ta kalla su Rafi'at da kyawawan Yaran dake a gaban su ta ce


"Barkanku dai."


Amsa ma ta suka yi da faɗin


"Yauwa kema barka."



Nan kuma suka shiga gaisawa da ita tana musu godiyar taimakon ta da suka yi.


Rafi'at murmushin yaƙe kawai take bin wannan kyakyawar budurwa dashi amma na ciki na ciki.




Kallon kyawawan Yaran tayi cikin shauƙi ta miƙawa Nainarh hannu alamar tazo, aikuwa Yarinyar ta ɓangale baki kana ta ɓanɓare hannunta daga cikin na Rafi'at ta rarrafa da saurinta irin na Yara, ta ƙarisa bakin gadon da budurwar take zaune sannan ta kama gadon tana kici kicin hawa.



Dariya kawai gaba ɗaya suke ma Nainarh wato shi dai Yaro ba Ruwan shi ƙaunar kowa Yake ba abin da ya dame shi.




Da sauri budurwar ta kamo hannun Nainarh tahau da ita saman gadon tana ma ta wasa, aikuwa ganin haka suma Nailah da Abdulmaleek suka ƙarisa wurin da saurin su aikuwa duka ta haɗa tana musu wasa da alama tana ƙaunar Yara sosai obaaaaa.



Kallon Abdulmaleek tayi da yake Babban cikin su sannan ta ce


"My friend please Tell me, what is your name?."


Dariya Yaron ya yi sannan cikin qwarancin sa na yara Yace



"Body."

/Buddy/

Dariya tayi cike da nishaɗi ta ce "Okay wato dai 'Buddy' kake so kace ko?."



Girgiza ma ta kai Yaron ya yi alamar "E," yana dariya.

Ta kuma cewa "To ai na gaskiyar nakeso ka faɗamin."




Ɗan shiru ya yi kamar mai tunani sai kuma can Yayi dariya yace "Abdulmaleek naji Aya Aleem iya kiyana."




"Oh suna mai daɗi."🙂


Ta faɗa tana dariya.

'Kema Menene sunan ki, ko baki da suna ne?."



Yaron ya antayo ma ta tambayar wacca tasa ta yin murmushi sannan ta bashi amsa da


"Maleek ke nan ai kowa yana da suna a duniya kamar nima dai suna na, suna na...."


Shiru tayi kamar tana tunani sai da kyar ta iya faɗi cikin in'ina

"Suna na Ha-Ja-ah..."

Tayi maganar tana dafe qwoqwon kanta da taji kamar zai rabe gida biyu saboda raɗaɗin da yake ma ta.





"HAJARAH."

Rafi'at ta maimaita sunan cikin ranta tayi murmushi a fili ta ce


"Sunan ki mai daɗi kuwa?."


Murmushin ƙarfin hali budurwar mai suna Hajarah tayi tana kuma dafe kanta ta ce da kyar


"Nagode."




"Ah ah kodai kan yana miki ciwo ne, naga kina riƙewa?."


Rafi'at tayi ma Hajarah tambayar a yayin da take ƙarisawa wurin da take zaune saman bed.


"Eh Auntie sosai yake mugun rasamin jina nake kamar bani ba."


Hajarah ta bata amsa tana rumtse idanun ta.



Jin haka yasa likita ya yi ma Abubakar alama da su fita.

Ba

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads