Showing 117001 words to 120000 words out of 155363 words
Chapter 40 - SARAUNIYAR KYAU_Takun Farko _cmplt. By The Nainarh Kd -2-1.txt
Page*79&80*
_____*
Rayuwa ta ci gaba da tafiya Yayin da ta gefe guda Abubakar ya kammala binkciken sa akan Ahalin Hajarah sai dai kuma wani Abin haushin shi ne.
Wai gaba ɗaya dangin sun koma ƙasar waje da zama kuma bai san wata ƙasa suka koma ba.
To koda ya sama Hajarah da zancen ba ƙaramin tashi hankalinta ya yi ba faɗa kawai take
"Shikenan ita kuma da sake haɗuwa da Ahalin ta sai dai a darrusalam inda rabo, a lokacin shima hankalin Abubakar ba ƙaramin tashi ya yi ba, jin abin da take faɗa haka ya dingi kwantar ma ta da hankali, harya samu ta dawo normal."
Rayuwa ta ci gaba da lulawa ta ko wani ɓangare abin dai sai godiyar Allah, domin kuwa ta ɓangaren Ahalin Alhaji Sameer Lamiɗo sosai suka dage suna bawa Hajarah taimakon da ya kamata.
Zaynerb Ɗiyar Hajarah nada shekaru biyu a duniya.
Wata Ranar Alhamis da Yamma wuraren ƙarfe Bakwai na dare, Hajarah ta santalo jaririyarta mace ƙatuwa mai kama da ubanta sak wannan karon, babu abin da ta rage daga jikin Abubakar komai nashi ta ɗauko abu ɗaya ne kawai na Hajarah wanda ta ɗauko wato Manya Manyan dara daran kyawawan idanu.
Daya ke wannan karon Hajiya Zuwairiya ce ta karɓa haihuwar shi yasa sai da ta kammala ba Hajarah da Jaririyarta duk Abin da ya kamata, tayiwa jaririya wanka ta shirya ta, sannan ta fito palo wurin su Abubakar da Rafi'at wacca ita ma cikin jikinta haihuwa yau ko gobe, sai Sakeenah da Jawaheer da kuma Yusra matar Yusuf da suka zo.
Fuska ɗauke da matsanancin farin ciki ga kuma jaririya ɗauke a hannunta ta ƙariso sannan ta miƙawa Abubakar Jaririyar. Bayan ya karɓeta Hajiya Zuwairiya ta ce
"Ga jaririya an sama Ɗiya mace Masha Allah, gata kyakyawar gaske duk da dai ba fara bace."
Ai da jin haka yasa gaba ɗaya mutanen palon suka ƙariso wurin suna kallon jaririyar da aka kira da baƙa bayan kuma gaba ɗaya Ahalin su ta babu baƙaƙe.😜
A je jaririyar dake sanye cikin kayan sanyi na jaririrai tana Baccin ta gunin burgewa, Abubakar ya yi a saman 3sieter aikuwa nan suka shiga kallon ta Abin gunin burgewa.
Sakeenah ta ce "Ni dai tunda nake a Rayuwata ban taɓa ganin Jaririya wacca kyanta da komai nata ya burgeni ba kamar wannan kyakyawar furanga haka, da take a gaba na, sai dai kuma wani abu ɗaya, naga kalar fatar ta shi ba fari ba, haka zalika ba baƙi ba, sai wani shaining da yake yi kamar tauraruwa cikin taurari."
Jawaheer ta amshe zancen da cewa "Ke dai bari ai jina nake kamar wannan Jaririya ta zama tawa, gata Tabarakallah Masha Allah ga kuma Kalar fatarta Wanda a turance ake kira da one in Dollars, domin kuwa kafin ki sama fata Kalar wannan to da aiki gaskiya fa."
Yusra wacca take mata wurin Yusuf ta ce "Ai Auntie Jawaheer baki kai ni ƙaunar wannan Ɗiyar ba domin kuwa jinta nake can, can a cikin ƙasan zuciyata, ga kuma fatar ta wanda iya shi mutum ya gani sai ya mance hanyar garin sa, gidan sa dama sunan sa gaba ɗaya."🔥
Dariya suka yi gaba ɗayan su, Rafi'at wacca ta ƙurawa jaririyar ido tun ɗazu ta ce
"Ummm hmm kun san menene kuwa?."
Gaba ɗayansu suka haɗa baki wajen faɗin
"A'a.'
Dariya tayi sannan tana faɗin
"Wannan Jaririyar ko, ita ake yiwa laƙani da kinfi nurul'in, Dan Allah please ku taimaka ku tayani kallon wannan haɗaɗɗiyar fatar nata wanda in banda shaining babu abin da take yi, ga manya manyan dara daran kyawawan fararen idanunta masu ɗauke da launin £ye ball's wasu masu shaining su ba blue color ba, kuma su ba green color ba, sannan kuma baza'a kirasu purple color ba, abin dai sai Wanda ya gani wallahi."
Gaba ɗaya mutanen dake palon in banda dariya babu abin da suke yi.
Hajiya Zuwairiya ta ce "Ai ina faɗa muku wannan jikar tawa, sai an dinga haɗa mata da Addu'o'i domin kuwa wannan kyan nata ko, Humm hmmm."
Gaba ɗaya mutanen palon babu wanda bai magantu ba, sannan kuma bai susuce da wannan kyau kyawu irin na na wannan Jaririya ba, tana da kyau sosai, she is so cute and so sweet so sexy and adorable, so and and so ka.!! abin ko humm Alƙalamin Nainarh Kd ya yi kaɗan wajen rubuta kyau da kyawu irin na wannan Jaririya.....ʝυʂƚ ιɱαɠιɳҽ...🥰
Abubakar da tun ɗazu ya yi shiru bai ce komai ba, amma idanun sa suna akan wannan kyakyawar furanya, ya sauke wata kyakyawar ajiyar zuciya na farin ciki sannan ya fara magana kamar haka..
"Kun san menene kuwa, jama'a?."
Dariya suka yi jin abin da yace kana suka haɗa baki wajen cewa "A'a a'a a'a...."
Yace
"Wannan kyakyawar furanya Insha Allahu wata Rana za'a wayi gari ta zama SARAUNIYAR KYAU ta duniya Insha Allahu Burina ke nan a kanta.📷💃😎
<<<{Tofah masu karatu, kundai ji Burin Mister Mai Kyau, a kan wannan Ɗiya tasa da masoyiyar matarsa son sa Hajarah ta haifa masa, shin Burin zai cika, ko kuwa dai. Akwai Ƙalubale, kudai kawai ku biyo wannan Ƙayataccen labari mai suna *💋SARAUNIYAR KYAU 💋* domin jin irin abin da yake ciki, sannan da darasin da yake tafe dashi 💃💃}>>>
Gaba ɗaya mutanen dake palon suka ɗauki sowa na farin ciki Jawaheer faɗi take
"Ina bayanka Yaya ni ma dai Burina ke nan, akan wannan Ɗiyar tamu Ahaa muje zuwa *SARAUNIYAR KYAU*
Murmushin farin ciki Hajiya Zuwairiya tayi tana cewa
"To ai sai ku bar wannan Jaririya ta Huta, ga mahaifiyar ta can baku tambaya Lafiyar ta ba, kun tsaya a kan jaririyar ko?."
Dariya suka yi sannan Sakeenah ta miƙe tsaye da sauri tana cewa
"Ni Wallahi in banda Yanzu da kikayi maganar, ni harna manta da Hajarah mai jego, kyawun Jaririyar da ta haifa mana shiya saka hakan."
Tashi suka yi gaba ɗaya suka nufa bedroom ɗin da Hajarah take ciki
Kwance suka same ta tana kwasar baccin gajiya.
Zazzauna wa suka yi suma suka ci gaba da fira sama sama suna ko ɗa kyau irin na wannan Jaririya.
Zuwa can wuraren goma na dare Hajarah ta farka aikuwa tayi kyakyawan gani gaba ɗaya mutanen gidan zazzaune suna fira ga Ɗiyarta da mijinta a gefanta murmushi kawai take yi na farin ciki.
Ganin ta farka yasa Abubakar ya yi murmushi da yake yana kusa da ita ne, a gefan gadon, cikin ƙasa da murya, yadda ita kaɗai zataji abin da zai faɗa Yace
"Nagode miki sosai da kika Haifa min wannan kyakyawar furanya, kyakkyawar Tauraruwa wacca hasken ta yake haske wuri, nagode miki sosai kin san kuwa wani suna zan saka ma ta?."
Fuskar ta ɗauke da matsanancin farin ciki na yabon da godiyar da mijinta yake ma ta ta girgiza masa kai alamar "A'a,"
Murmushi ya yi sannan ya matsa da Bakin sa dai dai sai tin kunenta ya raɗa ma ta a kunne.
Dariya tayi ba shiri wanda sautin dariyar da tayi Yasa gaba ɗaya mutanen Ɗakin juyowa suna kallon ta domin kuwa babu wanda ya lura da tashin ta.
"Ah ah kunga masoyan zahiri, wato ana jegon mah ana taɓa love ne ko?, Aikuwa Abin naku ya ƙayatar dani sosai, na ɗauki course daga Yau."
Cewar Jawaheer cikin dariya, "Wato ma saka mana ido kikayi ko?."
Hajarah ta tambaya tana jefa ma ta hararar wasa, Jawaheer ta ce "A'a nadai gani ne kawa Aha." 🤣
Habba ai nan kuma wata sabuwar fira ta ɓalle a tsakanin su, gaba ɗaya cike da nishaɗi yi suke yi kamar babu gobe, har wuraren ƙarfe goma sha biyu na dare.
Sannan ne kuma suka fara shirin komawa bedrooms ɗin su domin kwanciya bacci, gaba ɗaya suka fiffita bayan sunyi wa mai jego da jaririyarta sallama.
Suka bar Abubakar da Hajiya Zuwairiya a cikin bedroom ɗin.
Miƙewa Abubakar ya yi kamar mai neman wani abu. Da sauri ya fakaici idon Hajiya Zuwairiya ya haye saman bed ɗin.
Cikin sauri Hajarah ta kalle sa ganin abin da ya yi kana cikin ƙasa da murya ta ce
"Menene haka kuma?, in ace kaima ɓangaren ka zaka wuce, sai kuma gobe ko?."
Dariya ya yi sannan shima cikin ƙasa da murya Yace
"Na fasa anan zan kwana, tare da mata ta da Ɗiyata domin kuwa wani kalar kewar su nakeji, tun kafin na tafi na barsu."
Shiru yayi kamar mai tunani, sai can ya kalle ta kamar yadda ita ma ta ƙura masa ido tana kallo, cikin sanyin murya yake faɗin
"Kin san menene kuwa?."
Bai jira ta amsa ba, ya ci gaba da cewa,
"Jina nake kamar bani ba, ina jina gaba ɗaya jikina a sake, sannan kuma kamar wani abu mara daɗi zai faru, gaba ɗaya a sanyaye nake wallahi."
Ƙura masa ido Hajarah tayi tana kallo Sannan ta sauke ajiyar zuciya tana faɗin
"Duk wannan wasi-wasin aikin sheɗan ne kawai, ka karanto Addu'o'i komai zayyi Normalcy Insha Allah." ta ci gaba da cewa
"Ka tsaya da kyau ka saurari bugun zuciyar ka ka nutsu zaka fahimci aikin sheɗan ne kawai?."
Murmushi ya yi kana Yace
"Ina son ki sosai sosai fi ye da yadda kike sona fa."
Dariya ita kuma tayi sannan ta basa amsa da
"Ni kuma ina ƙaunar mijina abin alfaharina a kullum da ko yaushe ina ƙaunarka obaa, fi ye da ƙaunar da Lailah da Majnun suke ma juna Tabbas." Tayi maganar tana Rumgumo sa tightly.
08081129487
Via WhatsApp
For more enquires
The Nainarh Kd
___*💋 SARAUNIYAR KYAU 💋*_________ƚαƙυɳ ϝαɾƙσ__________________________________________________________💥👑𝑻𝒉𝒆 𝑮𝒍𝒂𝒎 𝐐𝐮𝐞𝐞𝐧👑💥____________________𝑩𝒚:𝑻𝒉𝒆 𝑵𝒂𝒊𝒏𝒂𝒓𝒉 𝑲𝒅____𝑲𝒉𝒂𝒅𝒆𝒆𝒋𝒂𝒓𝒕𝒉. 𝑺𝒂𝒃𝒊'𝒖. 𝒀𝒂𝒉𝒚𝒂𝒉🤙
Idan kin shirya Payment, just pay with this details.
_-_-_-_-_-_
*The Phone Number*
*08081129487*
*The Acct Number*
*8081129487*
*The Bank Name*
*Palmpay Bank*
*The Acct Name*
*Khadeejarth Sabi'u Yahyah*
Page *81&82*
Ganin dai abin nasu bana ƙarewa bane. Yasa Hajiya Zuwairiya da tun hawar Abubakar saman bed ɗin, take ankare dashi, miƙewa tsaye tana faɗin
"Toh idan an gama rashin kunyar a gaba na, sai a tashi a tafi inda aka fito, domin zan kulle ɗakin."
Da sauri suka juyo suna kallon ta su biyun, aikuwa ta galla musu harara duka.
Ƙasa da kai Hajarah tayi cike da kunya, shikuwa Abubakar ko'a jikin sa ya sauko daga saman gadon idanun sa akan Hajarah harya fi ce daga bedroom ɗin, yana yiwa Hajiya Zuwairiya dariyar ƙeta.
Ajiyar zuciya Hajiya Zuwairiya ta sauke sannan ta kalla Hajarah tana qalla ma ta harara sai dai bata ce komai ba, taje ta kulle ɗakin, ta dawo ta koma can gefe saman wata doguwar stool mai faɗi ta kwanta, domin kuwa wani kalar bacci mara misaltuwa take ji kamar Ƴar maye, Aikuwa ko mintuna biyar batayi da kwanciya ba, bacci ya yi gaba da ita.
Ajiyar zuciyar ita ma dai Hajarah ta sauke sannan ta sauko daga saman mattress ɗin, ta shiga bathroom, ta ɗauki tsawon mintuna goma a ciki.
Jiyo kukan Jaririyarta da tayi ne, yada da sauri ta kammala abin da take yi sannan ta fito, ta ƙarisa saman gadon jariran ta ɗauka Ɗiyar ta ta tana ma ta wasa, daya ke Jaririyar taƙi karɓan Breast ɗin ta, tun ɗazu kuma ba'asan dalili ba, shi yasa ma batayi tunanin bata ba.
Sai da ta tabbatar da jaririyar ta ta tayi bacci, sannan ta kwantar da ita, kana ita ma ta koma ta kwanta saman bed, bayan tayi duka abin da take yi a al'adarta kafin ta kwanta, bata daɗe da kwanciyar ba, ita ma wani bacci mai ƙarfi Ya yi gaba da ita.
*WASH£-GARI*
Wuraren ƙarfe Bakwai na safiya, Sakeenah ta fito daga bedroom ɗin da ta sauka, jikin ta sanye cikin dogon hijjab blue color har ƙasa.
Hamma kawai take yi domin kuwa baccin bai isheta ba ta tashi, amma duk da haka sai da ta makara.
Tasha mamaki sosai ganin Palon ba kowa, bata kawo komai a Ranta ba, ta wuce kai tsaye tabi ta wani korido Wanda zai sadata ɓangaren Hajarah.
Knocking ƙofar bedroom ɗin tayi, amma shiru ba'a zo an buɗe ba.
Ƙara yi tayi nan ma shiru, ganin haka yasa ta ɗan tura ƙofar da hannunta, aikuwa sai ƙofar ta buɗe.
Sallama ɗauke a Bakinta ta shiga bedroom ɗin, amma sai taji ba'a amsa ma ta ba.
Ƙarisa shiga tayi aikuwa tayi kyakyawan gani can saman doguwar stool mai faɗi ta hango Hajiya Zuwairiya tana ta faman sauke snored bacci ya yi daɗi.
Dariya Sakeenah tayi tana faɗin "Ashe dai bani kaɗai na makara ba, tunda dai ga mai jego da Hajiya suna faman sauke numfashi bacci ya yi daɗi da alama."
Qarisa wa gadon da Hajarah take a kwance tayi, sannan ta kai hannu ta fara ɗan bubbuga gadon. Tana dai yi irin idan mutum yana so ya tashi wani daga bacci.
Amma ga mamakin ta sai taji shiru Hajarah bata farka ba, ɗan waro ido tayi waje, sai kuma a fili take faɗin
"Haba Sakeenah sai kace ba mace ba, don't be shy mana haba."
Tayi maganar tana kuma ƙoƙarin tashin Hajarah daga bacci.
Sai dai kuma har lokacin ko motsi Hajarah ba tayi ba zuwa, taƙin fa Sakeenah ta fara tsorata domin ko dama can akwai ta da mugun tsoro.
Hannu na rawa takai sai tin hancin Hajarah domin taji ko tana numfashi, sai dai kuma wani ƙarin tashin hankalin shi ne ko numfashi bata ji alamar tanayi ba, izuwa lokacin zufa kawai take haɗawa, ga jikinta dake faman rawa kamar mazari.
Fa sauri ta kai kunnen ta saitin hancin Hajarah, ko dai zata ji wani alamar amma kuma har lokacin shiru.
A mugun tsora ce ta fara ja da baya, sai kuma da gudun gaske tabar wurin, ta ƙarisa wurin da Hajiya Zuwairiya da take a kwance, ta fara bugunta cikin matsanancin kuka da tashin hankali take tashin ta, ganin ko motsi taƙi yi ne yasa ta ƙarisa wurin wani ɗan madaidaicin fridge a ɗakin ta buɗe, sannan ta ciro ruwa mai sanyi a ciki, kana ta dawo ta buɗe gorar ruwan ta watsawa Hajiya Zuwairiya a fuska.
A firgice Hajiya Zuwairiya ta tashi daga zaune tana karanto duk Addu'ar dake zuwa bakinta, sai da ta ɗan dawo nutsuwar ta sannan ta lura da Sakeenah dake faman rizgar kuka tamkar ranta zai fita.
"Ke, lafiyarki kuwa, Menene ya faru kike wannan kuka kamar anyi miki mutuwa?."
Hajiya Zuwairiya ta tambaye ta hankalin ta a ɗan tashe.
Sakeenah bata tsaya amsawa Hajiya tambayar da take ma ta ba, ta kamo hannunta ta ƙarisa da ita bakin gadon da Hajarah take kwance, sannan cikin kuka da wahalar fitar numfashi taƙe faɗin
"Hajiya Dan Allah ki duba Hajarah taƙi tashi fa, tun ɗazu, tsoro nakeji kar mu rasa ta."
Da jin haka yasa Hajiya Zuwairiya ta ƙarisa wuprin Hajarah ɗin nan ta shiga duba ta cikin sauri.
A hankali a hankali ta fara ja da baya babu abin da take karantawa a bakinta sai kalmar "Inna lil lahi."
Har ƙarshe saboda tsananin tashin hankali ta ma kasa magana, a matsayinta na cikakkiyar likita ta fahimci komai saboda haka kasa magana tayi.
Ganin Hajiya ta kasa magana ne, yasa Sakeenah ta fita da gudu daga bedroom ɗin saboda tsananin tashin hankali bata ma san inda take jefa ƙafafunta ba, a dai dai tsakiyar palon ta hango Abubakar da Jawaheer da kuma Rafi'at da Yusra suna magana.
Da gudun bala'i ta ƙarisa wurin tana kuka na fitar hankali, gaba ɗaya suka yo kanta suna tambayar ta ko lafiya, tama kasa magana, sai faman nuna musu bedroom na Hajarah take yi Yayin da wasu siraran Hawayen suke biyo idanunta suka wanke ma ta fuska.
Lura da inda take nuna musu ne, yasa gaba ɗaya suka nufa bedroom ɗin cikin tashin hankali ita ma ta mara musu baya.
Can gefe suka hango Hajiya Zuwairiya tana zaune kamar bata cikin hayyacinta saboda zaman Ƴan borin da tayi, Yayin da idanunta suke akan gadon da Hajarah take kwance saman shi.
Da sauri Abubakar ya ƙarisa wurin gadon ya fara kiran sunan Hajarah, amma ina rai Ya yi halinsa, gata dai Tamkar zata amsa masa, amma ina.
"Ta mutu, ta tafi shikenan ta tafi ta barmu, da Yaranta da jaririyar ta, ta tafi gidan ta na gaskiya, ba tare da ta cika Burinta na haɗuwa da Ahalin ta ba, shikenan kuma ta faru ta ƙare, Hajarah ta tafi ta Barmu a duniya, shikenan fa munyi Rashin mace ta gari, ga kirki, ga Haƙuri, Yah Allah bazan iya jurewa ba."
Duk wannan maganganun Hajiya Zuwairiya ce take yin su a Yayin da har lokacin idanunta suke akan gadon da Hajarah take kwance saman shi.
Tamkar Saukar Aradu haka zantukan Hajiya Zuwairiya suke shiga kunnen Abubakar Wanda ya tsaya cak da ƙoƙarin Tashin Hajarah da yake yi.
Zai iya cewa tunda Yake a duniya bai taɓa shiga matsanancin Tashin Hankali ba, irin na Ranar har Ranar kuwa da Haleesat Rashid Rayyan ta Rasu, komawa Ya yi Tamkar Statue a wurin gaba ɗaya zuciyar sa da gangar jikin sa sun tafi Hutun Rabin lokaci.
Yayin da gaba ɗaya mutanen palon suka ɗauki kalmar "Inna-lilahi-wa-inna-illahir-raji'un."
Suke faɗa cikin tashin hankali, amma banda Sakeenah wacca tuni ta sume a wurin.😭
A taƙaice dai faɗin irin tashin hankalin da wannan Ahali na Alhaji Sameer Lamiɗo suka tsinci kansu a ciki Tofah Tabbas Baki ko Alƙalami Ya yi kaɗan. 😓😥
Koda mutanen Jigawa dana Kano da sauran Ahali suka zo da Farin cikin na ganin mai jego da jaririyarta, suka sama wannan mummunar Labari na rasuwar Hajarah ga kyakyawar Jaririyarta da ta Bari.
Gaza jurewa da yawa daga cikin su suka yi domin sai da suka yi kuka.
Haka Rayuwar ta ci gaba da tafiya gaba ɗaya ɓangarorin babu daɗi sam, musamman ma ɓangaren Abubakar domin kuwa Rasuwar Hajarah ba ƙaramin taɓa Ya yi ba sosai sosai.
A Ranar da Hajarah ta cika sati biyu da Rasuwa Yusra matar Yusuf ta ɗauki Jaririyar Hajarah wacca taci suna 'AFEEFAH' /Tagari/
Ta koma Mai Duguri da ita da umarnin Abubakar domin kuwa da yardansa sannan kuma da amincewar sa Yusra ta ɗauki jaririyar domin ta ci gaba da kulawa da ita har zuwa wani lokaci, Wanda kuma wannan shawarar da ya Yanke, ba ƙaramin daɗi yayiwa gaba ɗaya Ahali ba.
Yayin da ita kuma Zaynerb ta koma Jigawa State hannun su Dr_Raheemah da zama.
Wanda Hakan ba ƙaramin haushi yaba Rafi'at ba, domin kuwa a cewarta ita Yafi kamata da ya bawa riƙon Zaynerb da kuma Jaririyar domin kuwa ta kusa haihuwa sai ta haɗa da Wanda zata haifa ta kula