Header Ads
Showing 75001 words to 78000 words out of 155363 words

Chapter 26 - SARAUNIYAR KYAU_Takun Farko _cmplt. By The Nainarh Kd -2-1.txt

Ads the beginning of article before Image

Nanah Kd   

14 Jun 2024

1025

Ads at the middle of Article

gefanta tayi ƙara alamar shigowar kira, gaba ɗaya suka sauke ajiyar zuciya na dawowa hayyaci hadda ita.


Ganin bata da niyyar picking call ɗin yasa Auntie cewa.


"Ki ɗa ga mana ko dai ba kiran ki ake ba, ajiyar zuciya Humaira ta kuma saukewa a karo na bar ka tai sannan ta ɗauke kallonta daga kansu ta mayar kan wayarta dake faman sowa.


Murmushi tayi ganin Abokiyar aikinta Hameeda Sagir ce mai kiran nata, da sauri tayi picking sannan ta kara a kunenta bakinta ɗauke da sallama, daga can ɓangaren Hameeda Sagir ta fara magana.


"Ke Komai Naka Girl, aje sallamar nan a gefe kiji abin da zan faɗamiki."

"Okay inaji ai."

Humaira ta bata amsa tana saita nutsuwarta, Hameeda Sagir ta ci gaba da cewa.
"Yanzu yanzu ki kunna T.v domin sanin halin da Birnin Kano Najeriya take ciki, dan da alama baki kunna ba, kuma baki sani ba."


Da sauri Humaira ta tambayeta "Menene yake faruwa ne, a garin haka da na ji ki So Anxiety ne?"


Hameeda Sagir ta ce "Kedai kawai ki kunna T.v zaki ga komai." Da faɗar hakan tayi rejected.


Ganin yadda Humaira take bin wayar da kallo batayi magana bane yasa Jiddarh tambayar, "Lafiya kuwa Humaira meke faruwa ne, wacece ta kiraki, kuma mai ta faɗa miki."


Kallonta Humaira tayi ta ce "Hameeda Sagir ce Abokiyar aikina ta kirani."



Auntie ta ce "Oho Hameeda dai nan Neighbor ɗin mu ko, to menene ta faɗa miki.?"

Humaira ta bata amsa da, "Cewa tayi wai na kunna T.v zanga wani abu fa."



Tun kafin ta ƙarisa Jiddarh ta ɗauki Remote Control ta kunna T.v dake a palon gaba ɗaya suka zuba ma T.v ido domin ganin abin da zai faru."




ᴀʙɪɴ ᴅᴀɪ sʜɪ ɴᴇ.
Da farko hoton Asibiti aka fara nunawa sannan kuma aka nuna wannan Shararriyar ƴar jaridar da tasan makamar aiki, wato Hameeda Sagir.
Magana take kamar haka.



"Assalamu alaikum jama'ar duniya masu kallon mu da sauraron mu, kamar yadda kuka sani sunana Hameeda Sagir ina tare da Abokin aikina mai ɗaukar bidiyon abin da ke faruwa, wato Omar Uthman Gaya, yau muna tafe muku da wani rahoto ne, akan wannan dai budurwar Gasar SARAUNIYAR KYAU matakin jaha, da ta faɗi a lokacin da ake tsakiyar gudanar da Gasar SARAUNIYAR KYAU na jahar Kano, ana tsaka da Gasar."


A halin yanzu muna cikin Asibitin da aka kwantar da ita, kamar yadda kuke gani zamuji ta bakin ita wannan budurwar mai suna Juwairiya Jabir Bici.
Domin sanin dalilin da ya sa ta faɗi a tsakiyar filin Gasar a sume."


Ƴar jaridar Hameeda Sagir tayi maganar tana nufar cikin Ɗakin da aka kwantar da Juwairiya Jabir Bici yayinda mai ɗaukar bidiyo yake take ma ta baya.

Kyakyawar budurwar tana daga kwance saman Bed irinna na masu jinya jikinta sanye da kayan marasa lafiya ana ma ta ƙarin ruwa.


Zama Hameeda Sagir tayi daga gefanta sannan taba mai ɗaukar bidiyon damar mayar da na'urar ɗaukar akan Juwairiyar.


Murmushi Hameeda Sagir tayi ma Juwairiya Jabir Bici, ita ma ta mayar ma ta sannan Hameeda ta fara magana.


"Sunana Hameeda Sagir kuma niɗin ƴar jarida ce, sannan ga Abokin aikina Omar a halin yanzu wannan ɗaukar da kikaga anayi ta kai tsaye ne. Don haka Malama Juwairiya Jabir Bici zaki iya faɗa mana muda ɗumbin mutanen da suke kallo ainihin abin da ya saka kika suma a tsakiyar filin Gasar.?"

Hameeda Sagir tayi ma ta tambayar tana mayar da abin maganar dake hannunta a sai tin fuskar na Juwairiya.



Miƙewa Juwairiya tayi ta zauna da kyau, sannan tayi gyaran murya kana ta fara magana kamar haka.



"Da farko dai,
Sunana Juwairiya Jabir Bici.
Mahaifina Alhaji Jabir cikakken ɗan garin Bici ne ta jahar Kano.
Mahaifiyata kuma Asalinta ƴar Nijar ce, a maraɗi, zaman aure ya kawota Najeriya kuma Kano, mu biyar ne a gurin iyayen mu yayyina uku duka maza, sai ƙanwata mace Auta kenan, sai kuma ni.
Tunda na taso a rayuwata burina ɗaya ☝, shine naga wata rana an wayi gari na zama SARAUNIYAR KYAU koda kuwa ta jaha ce.
Ko'a Makaranta ne aka tambaye ni abin da nakeso na zama a rayuwa sai nace burina ɗaya shine na zama SARAUNIYAR KYAU, haka ƴan class ɗin mu zasuyita min dariya, suna cewa tayaya zan zama SARAUNIYAR KYAU bayan kuma ni baƙace?.😭

A lokacin sai dai kawai nayi murmushi nace musu, ai abin ba haka yake ba, zama SARAUNIYAR KYAU, ba dole sai farar fata ba, baƙaƙen fata ma zasu iya zama."👍





Shiru tayi sannan tayi murmushi tana goge siraran hawayen da suka zubo ma ta, ta kalla Hameeda Sagir da tayi shiru tana kallonta, murmushi Juwairiya ta kuma yi sannan ta tambayeta da.



"Kinsan wani abu kuwa?."


Girgiza kai Hameeda tayi alamar a'a.
Juwairiya ta ci gaba da cewa "Akwai wani lokaci, wata rana da bazan taɓa mantawa da ita ba tsawon rayuwata, a lokacin na kammala Secondary School, ina shirin shiga University, a ranar da ta kasance Lahadi kamar yadda yake a al'adata ina zaune a palo ina abin da na saba, wato bincikar yadda ake gudanar da Gasar SARAUNIYAR KYAU. da kuma irin abuwawan da ya kamata wacca ta shiga Gasar tayi.
A Laptop nayi nisa sosai akan abin da nakeyi, najiyo muryar Yayana abin alfarina wanda kaf gidan mu shikaɗaine yake bin bayana akan ra'ayina na zama SARAUNIYAR KYAU.

Yana qwalamin kira tun daga waje, da sauri na miƙe tsaye na fita waje gurin shi, ina tambayar shi abin da yake faruwa, a lokacin cike da farin ciki Yayana yake faɗamin abin da na daɗe ina jiran ji a rayuwata.

Cewa an saka sunana acikin jerin ƴan matan da zasu shiga Gasar SARAUNIYAR KYAU matakin jaha na shekara.

A lokacin na shiga farin ciki da zaquwa kalar wanda ban taɓa shiga ba, tsayin rayuwata haka zan zauna na dinga qwada kaya kala kala ina neman kalar da zansaka ranar Gasar.


Haka rayuwa ta ci gaba da tafiya har akazo saura kwana ɗaya a gudanar da Gasar ranar ko bacci na kasa, saboda zaquwa a saman sallaya na sallah na kwana ina jira gari ya waye mutafi wajen Gasar.


Haka ma da gari ya waye ko abinci ban ci ba saboda ƙosawar da nayi.

A TUNANINA idan mutum yana da wani buri nashi, mutanen gidansu sune first waɗanda zasu fara qarfafa mishi gwiwa akan burin shi kafin mutanen waje.

Amma ni banyi wannan sa'ar ba, domin kuwa kaf gidan mu ba mai ƙarfafa min gwiwa akan burina, sai Yayana abin alfarina shikaɗaine yake son abin da nakeso.

Babban abin da ya sanyaya min jiki a karo na farko shine.
A Ranar da zamuje Gasar ko mutum ɗaya daga cikin ƴan gidan mu babu wanda yazo domin ganin yadda Gasar zai kasance, sai Yayana shikaɗai.

Haka mukaje wajen Gasar gaba ɗaya jikina a sanyaye, sai dai kuma wani Babban abin da ya ƙara kashemin jiki shine.

A lokacin da akayi Gasar nayi rashin Nasara, domin kuwa koda ta Uku kasa zuwa nayi.
Haka muka koma gida jiki ba qwari, amma ko mutum ɗaya a gidanmu an kasa samu wanda zayyimin koda tambayar yadda Gasar ta kasance.




Sai Yayana shikaɗai a kullum yake ƙara ƙarfafamin gwiwa akan nayi hakuri akwai shekara mai zuwa, karna damu kaina domin haka rayuwar take.

Rayuwa ta ci gaba da tafiya harna shiga University na fara karatu shekara ta zagayo.
Haka wannan shekarar ma Yayana yayi ƙoƙari ya samu aka saka sunana a cikin ƴan matan Gasar.

Haka cike da farin ciki yazo yake faɗamin, sai dai wannan karon na rage zaƙuwar, dan lokacin da ya faɗamin ma ban wani nuna farin ciki na sosai ba, kawai dai cewa nayi Allah ya kaimu lokacin.
Na cigaba da aikin da nakeyi, a lokacin sam Yayana baiji daɗin abin da nayi ba, amma bai ce dani komai ba.
Sai washe gari ya sameni yamin nasiha sosai akan yadda da ƙaddara.

A lokacin jikina yayi sanyi sosai kuma na ƙarajin ƙaunar Yayana sosai fiye da baya, sannan fiye da komai a Duniyata gaba ɗaya 💓


Haka rayuwata ta ci gaba da tafiya har akazo ranar Gasar a ranar nida Yayana mun fito harabar gidanmu zamu shiga mota mu tafi, saiga ƙanwata ta ƙariso gurin da gudunta, gaba ɗaya muka juyo muna kallon ta, Yaya ne ya tambaye ta abin da ya sakata gudu, sai cewa tayi tanaso ta rakamu gurin Gasar ne.🙂

Umma bataso Ummanmu ta sani saboda zata hanata🙃.
Duk da jikina yayi sanyi amma haka na daure nace ma ta ta shiga mota mu tafi, haka muka tafi da ita ba tareda Ummanmu ta sani ba, muka tafi wajen Gasar."








Shiru Juwairiya ta kuma yi tana kallon Hameeda Sagir, kamar yadda ita ma Hameedar ta zuba ma ta ido tana kallo cike da tausayi.

Sai da tayi mintuna biyar a haka sannan ta sauke ajiyar zuciya ta ci gaba cewa.

"Muka ƙarisa gurin Gasa an fara gudanar da Gasar nayi Round ɗina nima cike da gwarin gwiwa irin wanda bantaɓa samun kaina a ciki ba.

Ba komai ya ƙaramin gwarin gwiwa ba sai ganin yadda ƴan uwana har uku sun zo kallon Gasa na domin kuwa ɗayan Yayan nawa yazo shima.



Anyi Gasa an gama gaba ɗayanmu ƴan matan Gasa mu goma muna daga saman floor muna jira muji waɗanda suka ci Gasar, wato sama Nasarar zama winner's na shekara.


Haka munaji aka kiran wacca tazo ta ɗaya aka kira ta biyu, haka ma aka ta uku amma ba'a kirani ba.

A lokacin kasa jurewa nayi, domin ni macece ina da rauni sosai musamman ma akan abin da nakeso, kuma na sanya a gaba.
A lokacin zuciyata tamin nauyi na gaza jurewa.
Dalilin ne yasa na zube a gurin a sume, sai farkawa nayi na ganni a gadon Asibiti, That's All."


Ta ƙarishe maganar tana kuma goge hawayen fuskarta, Hameeda Sagir harta buɗe baki zatayi magana, Juwairiya ta rigata da kuma faɗar.

"Sai dai kuma yanzu komai yazo ƙarshe na haƙura da zama SARAUNIYAR KYAU, a baya idan mutane suna cewa bazan taɓacin Gasar SARAUNIYAR KYAU ba, saboda ni baƙace bana yadda amma yau na yadda ɗari bisa ɗari 100% baƙaƙen fata basa samun Nasara a Gasa sai dai fararen fata amma yanzu na fahimci komai."



Ta rufe da faɗar

"Inayiwa sauran ƴan matan da suka sama Nasarar lashe wannan Gasar na SARAUNIYAR KYAU matakin jaha fatan Nasara.

Sannan ina taya ira irena waɗanda suka faɗi a Gasar baƙin ciki da jaje."


Tana faɗin haka tayi shiru, gaba ɗaya ɗakin ya ɗauki shiru ana kallon kallo tsakanin juna.



Can ƴar jarida Hameeda Sagir ta katse shirun da ɗakin ya ɗauka da faɗin "Malama Juwairiya Jabir Bici nida sauran jama'ar dake kallo da sauraro muna tayaki jin babu daɗi, akan wannan al'amari kuma muna fata hakan ya zama mafi alkhairi a gareki dama sauran waɗanda suka sama failure a Gasar."


Tana gama faɗin haka ta juyo tana fuskan tar na'urar ɗaukar bidiyon, sannan ta ci gaba da cewa "Yanzu dai mutane gaba ɗaya munji dalilin da ya saka Malama Juwairiya ta faɗi a gurin Gasar daga bakinta, dama Hausawa sukace magana daga bakin mai ita tafi sugar."😋




Ta ci gaba da cewa "A halin yanzu muna jiran ƙarisowar Madam Miracle wato ɗaya daga cikin manyan alƙalan Gasar, domin muji ta bakinta akan wannan al'amari mun sama labarin yanzu yanzu tana akan hanyarta zata ƙarisowa wannan Asibiti domin duba jikin Malama Juwairiya Jabir Bici, sannan kuma ta amsa mana wasu ƴan tambayoyi."




Tana kai maganar suka turo ƙofar room ɗin suka shigo, securities ne mata guda biyu ɗirka ɗirka dasu, suka fara shigowa sai Madam Miracle sai kuma wasu matan biyu suna take ma ta baya.


Da sauri ɗan jaridar mai ɗaukar bidiyon ya mayar da na'urar akan Madam Miracle da ta zauna akan wata farar kujera kusada Juwairiya Jabir Bici tana ma ta ya jiki, cike da farin ciki Juwairiya take amsawa.



Sai da Madam Miracle ta kammala duba jikin Juwairiya Jabir Bici, sannan ta juyo da kallonta akan Hameeda Sagir ƴar jarida dake zaune a gefanta saman wata farar kujera hanunta riƙe da abin magana.




Murmushi Madam Miracle tayi sannan ta ce ma kyakyawar ƴar jaridar dake zaune a kujerar kusada ita.

"Go ahead."

Sai ta abin maganar ƴar jarida Hameeda Sagir tayi shima mai ɗaukar bidiyon ya sai ta nashi akansu, su duka ukun hadda Juwairiya Jabir Bici.


Gyaran murya ƴar jarida Hameeda Sagir tayi sannan ta kalla sai tin na'urar ɗaukar bidiyon ta ce 'Barkanku dai masu kallon mu da sauraron mu, kamar yadda kuke gani ga Madam Miracle ta ƙariso fa."


Dawo da kallonta tayi kan Madam sannan ta ce "Barka dai Madam Miracle fatan kin ƙariso lafiya.?"

Madam ta amsa da "Yauwa barkanki dai, lafiya ƙlau."

Ƴar jarida ta ci gaba da cewa "Masha Allah, shin Madam zamu iya sanin ainihin dalilin da yasa ba'a zaɓi Malama Juwairiya Jabir Bici ba a Gasar SARAUNIYAR KYAU matakin jaha?, ko kuwa dai kamar yadda ita Malama Juwairiya ɗin ta faɗane, cewa ba'a zaɓan baƙaƙen fata sai farare?."



Murmushi Madam Miracle tayi sannan ta gyara zaman Medical glass dake fuskar ta kana ta ce "naji duka tambayoyin ki Malama Hameeda Sagir amma mudai a tsarin Gasar SARAUNIYAR KYAU na ko wani mataki ba'abin hasken fata, domin kuwa ba'akan haka aka gina Gasar ba.
Sannan da kika tambaya akan Miss Juwairiya.
Yes baƙar fatace ita. Amma ba wannan dalilin ne ya hana a zaɓeta a Gasar ba ae.'

Cikin sauri Hameeda Sagir ta kuma tambaya, "Shin Madam zamu iya sanin dalilin da ya sa ba'a zaɓeta ba kuwa."

"Of course, zaku iya sani ae, babu damuwa "

Cewar Madam Miracle.

"Babban dalilan da suka saka ba'a zaɓa Miss Juwairiya ba, guda biyu ne zuwa uku, na farko shine batada idanu😳

Ma'ana dai idanunta sunyi ƙanana da yawa wanda hakan yasa ba'a zaɓeta ba.
Na biyu kuma shine tsayinta bai kai yadda akeso ba."


Da mamaki Hameeda Sagir take kallon Madam sannan ta ce Madam bamu fahimci abin da kike nufi ba?. Kenan dai har tsayi ana dubawa wajen Gasar. Ko ince ana buƙata ko?."

Murmushi Madam Miracle tayi kana ta bata amsa da "Sosai ma, ana duba tsayi. Misali ita Juwairiya Jabir Bici, it's her Height is _1.49m take, kinga kuwa babu yadda za'ayi tayi Nasara."

Hameeda Sagir ta ce "Okay, Madam ko zaki iya faɗamana yadda akeso tsayin ya kasance?."




Madam ta ce "anaso ya kasance kamar_1.55m zuwa sama da hakan."



Hameeda ta ce "Madam tambayoyi biyun ƙarshe please. Na farko shin zaki iya faɗamana dalilin da yasa kikazo duba lafiyar Juwairiya Jabir Bici?."

"Na biyu shin zaki iya faɗamana dalilin ki naba budurwar da ta lashe Gasar tazo ta ɗaya kyautar tsadadden Diamond Ring?. Domin mutane da yawa suna so susan dalilin ki nayin hakan."


Wannan karon dariya Madam Miracle tayi har farare jerrarun haƙoranta suka bayyana sannan ta bata amsa da "Duka waɗannan tambayoyin naki Miss Hameeda Sagir amsa ɗaya ne dasu, wannan amsar kuma ita ce saboda naji ina ra'ayin hakan ne, cause it's the personal secret thing."




Hameeda Sagir zata kuma magana, Madam Miracle ta miƙe tsaye tana faɗar



"It's okay, lokaci yaja zan tafi."


Miqewa ita ma ƴar jarida Hameeda Sagir tayi tana faɗin "Okay Madam Miracle sosai munji daɗin wannan taƙaitaccen firan da ya gudana tsakanin mu, muna fatan nan gaba zamu sake zama domin firar kalar wannan?."


Murmushi Madam Miracle tayi sannan ta ce "Babu damuwa, domin a koda yaushe ina mai maraba daku, na barki lafiya."


Juyowa ƴar jaridar Hameeda Sagir tayi tana fuskan tar na'urar ɗaukar bidiyon tana faɗin "Toh jama'a masu kallon mu, da sauraron mu, kamar yadda kuka gani mun tattauna da Madam Miracle kuma munji dalilin da yasa ba'a zaɓi Miss Juwairiya Jabir Bici ba a cikin Gasar SARAUNIYAR KYAU matakin jaha ba."





# MASU KARATU, IDAN BAKU MANTA BA, DUK WANNAN TATTAUNA WAR KALLON SHI SU JIDDARH SUKEYI A TV.




Kashe T.v ɗin Jiddarh tayi sannan ta kalla su Humaira tana faɗin "Abin akwai ban tausayi fa, ace mutum bai samu ya cika burin da ya sama rai ba, a gaskiya yarinyar ta bani tausayi ba kaɗan ba."

Ajiyar zuciya Humaira ta sauke tana mai faɗin "Ni ma dai hakan ne, amma ya zatayi wannan ita ce ƙaddarar ta gashi abin ya yayatu a social media ta ko'ina maganar ta akeyi fa."

Auntie ta ce "ai kunji irin matsalar yanzu tajama kanta da iyayenta tonon qwaqwaf kenan fa."

Ci gaba da tattaunawa akan lamarin sukayi gaba ɗaya jikin Jiddarh yayi laqwas duk tausayin budurwar yabi ya addabeta a zuciya.



Suna cikin haka sai ga Bilki ta shigo bugujin bugujin da ita ga yarinya a hannunta tana tsotsar madara a fida.

A tsakiyar palon ta zube sannan ta kalla Jiddarh tana faɗin "Sannu SARAUNIYAR KYAU ta jahar Kano, gaskiya ina tayaki murna sosai."

"Ke tayaya kika san ita tayi Nasara a Gasar bayan kuma bakije Gasar ba?."

Auntie ta tambaya tana kallonta, dariya Bilki tayi ta ce "Hajiya kenan Auntien mu kin manta ina da waya ne.?"

Humaira ta saka baki, "Malama Bilki mai raino, to ya ya yarinyar taki take,?"

Bilki tana washe baki ta ce "Ga yarinyar bata da rigima sam, inajin daɗin wannan yayen da nakeyi, ni dama mutane zasu gane su dinga kawomin raino ai dana zama Auntyn Yara."


Jiddarh ta ce "Aikuwa zaki dace da Autyn Yaran highly."

Bilki ta bata amsa da "Kedai bari ai abin ba'a iya cewa komai wallahi."

Jiddarh ta kuma cewa "To ya zakiji idan akazo tafiya da Khausar ranar da kika gama rainonta?."

Bilki ta ce a gaskiya abin babu daɗin faɗa ko'a baki, dan zanyi kewar ta sosai banama fatan ranar da zata zo karɓanta tazo, dan idan tazo sai nayi zazzaɓin yini ɗaya yasin."

Tayi maganar tana zuba uban tagumi.
Humaira ta ce "Ba kewar ta zakiyi ba kenan, tunda dai zazzaɓin yini ɗaya zakiyi kacal?."

Bilki ta amsa da "To ai na yini ɗayan yafi daɗin faɗane a baki fa, shiyasa nace hakan."

Dariya sukayi jin irin wautar Bilki fira suka ci gaba dayi sama sama Bilki tana basu dariya da shirmen ta.





*SARAUNIYAR KYAU* 💓

_(The Glam Queen)_ 👑

```Takun Farko```

Story & Written By:

*_The Nainarh KD_*

_In dedication to my dear Classmate Science G.S.S.S BELE ROAD._







*THE ONGOING BOOK'S*


1. *SONKI NE ƘADDARA TA*

MALLAKAR
FATIMA ABDULLAHI
_Batool Kamba_





2. *ZAN JIRA KA*

MALLAKAR
A'ISHA ALƘALI

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads