Header Ads
Showing 120001 words to 123000 words out of 155363 words

Chapter 41 - SARAUNIYAR KYAU_Takun Farko _cmplt. By The Nainarh Kd -2-1.txt

Ads the beginning of article before Image

Nanah Kd   

14 Jun 2024

1012

Ads at the middle of Article

dasu duka, shiru kawai dai tayi ta shanye duka ɓacin Ranta.
Don karta kuma saka mijinta cikin wani hali bayan Wanda yake ciki.





Tofah haka suka ci gaba da gudanar da Rayuwar.
Tsakanin Rafi'at da Abubakar kuma zaman nasu dai abin babu yabo balle kuma wani abu wai shi Fallasa.




- *-
-
Hajarah nada wata Biyu da rasuwa, ranar wata Alhamis ita ma Rafi'at ta haifo Ɗiya mace, sai lokacin kuma Abubakar ya ɗan fara dawowa Nutsuwar sa.
Ranar suna Jaririya taci suna Lailah, zuwa lokacin Jaririyar da Hajarah ta Bari wacca Yusra take Riƙo duk da cewa madara take sha tayi ƙiba gata da kuma yi, ga wani kyau na musamman da ta ƙara.





Aikuwa a Ranar da Yusra taje da ita Abuja a hannun mahaifinta ta wuni yana bata wani kulawa na daban, duk cewa a duk ƙarshen wata Yana tafiya can Mai Dugurin domin ganin ta sannan ya wuce Jigawa State ma domin ganin Zaynerb.





___*💋 SARAUNIYAR KYAU 💋*_________ƚαƙυɳ ϝαɾƙσ__________________________________________________________💥👑𝑻𝒉𝒆 𝑮𝒍𝒂𝒎 𝐐𝐮𝐞𝐞𝐧👑💥____________________𝑩𝒚:𝑻𝒉𝒆 𝑵𝒂𝒊𝒏𝒂𝒓𝒉 𝑲𝒅____𝑲𝒉𝒂𝒅𝒆𝒆𝒋𝒂𝒓𝒕𝒉. 𝑺𝒂𝒃𝒊'𝒖. 𝒀𝒂𝒉𝒚𝒂𝒉

*



Page *83&84*


___**

Rayuwa ta ci gaba da tafiya da sauri sauri.
Yayin da dukiyar Abubakar Sameer Lamiɗo ta ci gaba haɓɓaka ta ko wani fanni dukiyar sa ƙara nin kuwa take yi sosai.


Wanda zuwa lokacin ya buɗe makarantar Islamiya da Masallatai da kuma Orphanage, da nin yar ladar ya dinga tafiya kai tsaye ga maragayya Hajarah matar sa.






Lailah Ɗiyar Rafi'at nada shekaru biyu a duniya Yayin da Haleesat take da shekaru huɗu twin's kuma Nailah da Nainarh suke da shekaru shida, shi kuma Abdulmaleek da Yake Babba Yake da shekaru Tara a duniya.



Zaynerb Ɗaya ga Maragayya Hajarah kuma take da shekaru huɗu a duniya ita ma.
Yayin da ƙanwar ta Afeefah dake can Mai Dugurin wurin Yusuf da matar sa da Yaran su da zama take da shekaru biyu kacal a duniya.



A lokacin ne kuma Rafi'at ta kuma Haihuwa ta haifa mace again Yarinya taci sunan mahaifiyar Rafi'at da ta Rasu ba jimawa wato Zinaru Yayin da Yayyinta suka saka mata xixi suna kiranta hakan.




A lokacin ne kuma Abubakar ba kunya ya amso Ɗiyarsa Afeefah a hannun Yusuf da matar sa, amma ita Zaynerb ya barta a Jigawa State a cewar sa ita ma zai karɓe ta amma sai bayan wani lokaci.





Rayuwa ta ci gaba da tafiya tana sauri sosai, Yayin da Abubakar Yake kula da Yarinyar sa Afeefah ko sauro baya bari ya taɓa ta, to a'ina ma sauro zai ganta.🤔




Afeefah ta taso Yarinya ce mai matuƙar kaifin basira da wayau, Sannan kuma sosai take ƙaunar Ƴan uwanta duka kamar yadda suma suke ƙaunar ta musamman ma dai Lailah, amma tsakanin ta da Momy Rafi'at kuwa sai dai kallo daga nesa, ko kuma gaisuwa amma in banda wannan, babu wani abu da yake shiga tsakanin su.


Dhekarunta uku a duniya aka saka su a school ita da Lailah Yayin da suke tafiya tare da sauran Yayyin su Haleesat da Nainarh Nailah sai kuma Abdulmaleek tsakanin ta da YaYarta Zaynerb kuwa duk da cewa ba'a tare suke ba, amma shaƙuwa ce ta musamman mai zaman kanta a tsakanin su, a dalilin kuwa duk a ƙarshen wata Abubakar yake haɗa kan Yaransa suje Jigawa State ziyara wani lokacin Momy Rafi'at tana binsu, amma wani lokacin saboda yanayin aikin ta haƙura take yi, Especially ma da mahaifinta ya gina ma ta asibiti nata na ƙashin kanta sai ya zama bata cika samun lokacin kanta ba.













_****______


Shekarun Afeefah Takwas a duniya Abubakar ya ɗauko Zaynerb daga Jigawa State, ya dawo da ita Abuja cikin Ƴan uwanta.
Rayuwa ta ci gaba da tafiya da yake Zaynerb yarinya ce mai masifar wayau da kaifin tunani shiyasa bata shiri ko kaɗan da Momy Rafi'at, domin kuwa ta fahimci ba ƙaunar su take ba, musamman ma idan ya kasance da mutane a wuri to nan ne fa zata dage ta dinga nuna musu ƙauna ta musamman, amma kuma suna kasancewa daga su sai ita, wahala take basu ba kaɗan ba, domin kuwa tasha ta zane Zaynerb ba sau ɗaya ba kuma ba biyu ba, amma kuma ita Afeefah ko tayi nin yar dukan ta kasawa take yi domin kuwa Zaynerb shiga tsakani take sai dai ita a dake ta amma bata bari ko ƙuda ya taɓa ma ta ƙanwa, wacca take shalele a wurin mahaifin su, Alhaji Abubakar Mai Kyau, sai dai kuma duk da ƙiyayyar da Momy Rafi'at take yi wa su Afeefah da Zaynerb bata taɓa nuna wa a gaban Yaranta ba, ko kuma mijinta cikin taku da tsare gida take abin ta.





A wata Ranar Jumma'a ne Ahalin Alhaji Sameer Lamiɗo suka tashi da wani mummunar Labari na Rasuwar Alhaji Sameer Lamiɗo ta farar ɗaya cikin dare, wuraren uku na dare ya rasu, Yayin da kafin gari ya waye ita ma matar sa Hajiya Harirah ta ce ga garin ku nan tabi mijinta.


A lokacin ba ƙaramin Tashin Hankali gaba ɗaya Ahalin Alhaji Sameer Lamiɗo suka shiga ba, musamman ma Abubakar domin kuwa zai iya cewa wannan ne mutuwa ta uku da aka taɓa masa waɗanda ba ƙaramin Tashin Hankali ya shiga ba.

A lokacin kuma sai mutuwar masoyiyar sa Haleesat Rashid Rayyan da kuma matar sa Hajarah Ya dawo masa sabo a zuciya.




Gaba ɗaya Ahalin basa cikin walwala sakamakon Rasuwar Alhaji Sameer Lamiɗo, hatta mutanen France, Lagos, Kano, Mai Duguri da Adamawa States dama su Abubakar dake Abuja suka taru a Jigawa State jikin ko wannensu a mugun sanyaye.






Alhaji Sameer Lamiɗo da matar sa Hajiya Harirah suna da watanni Biyar da Rasuwa zuwa lokacin tuni Dr_Raheemah da Hajiya Zuwairiya suka kammala taka ba.




A lokacin ne kuma suka gaza jurewa suka kasa zama a gidan dama Jigawa State gaba ɗaya.
Bayan Raba gadon Alhaji Sameer Lamiɗon. Mai matuqar Yawan gaske ne da akayi, Dr_raheemah ta tattare ya nata ya nata ta koma Kano da zama wajen Autan ta Sagir da iyalansa.

Yayin da ita kuma Hajiya Zuwairiya ta koma Mai Duguri wajen Yusuf da iyalansa.










____**__



Rayuwar ta ci gaba da tafiya ana gungura wa.
Yayin da a kullum dukiyar Alhaji Abubakar Mai Kyau ƙara bunƙasa take obaaaaa.



A lokacin ne kuma ya buɗe wurare da Yawa. banda waɗanda ya buɗe a baya, Ya buɗe wurare kamar su.


Mai kyau Chinese Restaurant.
Mai Kyau Indian Restaurant.
Mai Kyau Korean Restaurant.
Mai Kyau Spanish Restaurant. And Mai Kyau ethiopian Restaurant. Et.c.😘


Sannan kuma Ya buɗe Company na ƙera Takalma Wanda ya yi ma laƙani da.

'MAI KYAU ABBAN FEEFAH'
A Adamawa State, kana kuma ya buɗe wani Company shi kuma na ƙera Atamfofi, materials, laces a Borno State.



Kana ya buɗe wani company again na qera wayoyi shi kuma aka saka masa suna.

Mai Kyau
Bayan haka ya buɗe restaurant daban daban da kuma companies daban daban a kowani State na faɗin Nigeria, sannan kuma hatta ƙasashen waje akwai companies nasa da Yake ƙera kaya daban daban kamar irin ƙasar.



Amsterdam, Romanian, Spain, Poland, Greece, Austria, Italy, Egypt, Sudan, Libya, Eritrea sai kuma Germany Wanda acan companies nasa sunkai uku sai kuma Malaysia. E.t.c.💫💫





______**

Rayuwa ta ci gaba da tafiya ta ko wani ɓangare cikin sauri sauri Yayin da zuwa wannan lokacin shekarun Afeefah goma a duniya Yayin da suke kai ɗaya da Lailah gasu suna masifar kama sosai Like a twin's.





A wata Ranar lahadi da safe misalin ƙarfe goma sha biyu.

Afeefah tana zaune a palon gidan ta ƙura karantun Alqur'ani a plasma tv, na palon tana sauraro sai faman karatu take yi, da yake lokacin ita da Lailah sun kammala primary school sun ma zama Jarabawar fita.



Sai faman karatun ta take Yayin da Lailah take zaune daga ƙasan carpet sai roƙon Afeefah ɗin take a kan ta kashe karatun ta kunna musu cartoon su kalla, ita kuma Afeefah tayi ma ta kunnen uwar shegu.

Su biyu ne kacal a palon.

Daya ke shi Abdulmaleek Ya kammala secondary school Ya tafi ƙasar Russian karatu.
Yayin da su kuma Nainarh da Nailah suke a Boarding school suna karatu.
Ita kuma Zaynerb da taƙi Boarding, a ranar tana saman Bene a Bedroom ɗin ta tana karatu.
Yayin da Momy Rafi'at aka ma ta kiran Emergency a hospital ɗin ta.
Shi kuma Daddyn su Alhaji Abubakar Mai Kyau kuma Ya fita company domin cike wasu Takardu, duk da cewar ba Ranar aiki Bane, da yake Yana shirin komawa ƙasar Jamus ne domin Ya qara bunƙasa Harkokin kasuwancin sa, na can.






Kallon Lailah dake faman sha re Hawaye tamkar an dake ta, Afeefah tayi tana dariya ta ce

"Allah sis kina Bani mamaki, ace ke kwata kwata bakya ƙaunar kiji an saka karatun Alqur'ani Mai Girma, a gida sai kace Ƴar maguzawa, to Indai kinaso na kashe karatun na kunna miki cartoon, sai kin Fara gogemun Ƙafata, amma idan kin yadda fa." 🌚




Da sauri Haleesat dake can Dining Room tana faman kai loma, kallon Afeefah jin abin da take cewa, sai dai da yake ita ɗin miskilar gaske ce, ba tayi magana ba, sai ma dakata wa da cin abincin da tayi, tana kallon drama ɗin su domin ganin yadda zata kaya, shin Lailah zata Yarda ta goge ƙafar Afeefah ɗin, ko kuwa?."
Ita dai Haleesat iya sanin ta da Lailah muguwar Ƴar girman kai ce, ga ta da mugun tsafta, ga aji, ga Raini ga.!! umm ummm.🧐







Ajiyar zuciya Lailah ta sauke sannan cikin murya irin na Wanda ya sha kuka Ya ƙoshi ta ce

"Idan na goge miki ƙafar zaki bani remote control ɗin, na kunna cartoon ɗin?."




Murmushi Afeefah tayi wanda ya bayyana dimples ɗin ta duka biyun ga wushiryarta Mai Kyau, tana juya manyan dara daran kyawawan fararen idanunta ta amsa ma ta

"Yeah it's okay, idan zakiyi, to ga Remote sai na baki, ki kashe karatu ki kunna cartoon."




Da jin Haka Lailah tayi murmushin murna, sannan ta durƙusa dai dai saitin fararen ƙarfafun Afeefah dake sanye cikin farar safa.
Ta cire safar sannan takai hannu ta cire hular kanta, nan take dogon gashin kanta Wanda yasha kitson kalaba ƙanana ya zubo ma ta har gadon bayan ta.

Nan naɗe hular tayi, yadda zata ji daɗin goge ƙafar, sannan ta kamo ƙafar Afeefan ta ɗaura akan cinyarta, tana goge hawaye.
Yayin da Afeefah take dariyar murna, Lailah har takai Hannu ke nan zata fara goge ƙafar Afeefah ɗin, taji anyi sama da ita sannan an jefa ta saman 3sieter.



Da sauri gaba ɗayan su tun daga kan Haleesat dake zaune a Dining,nda Lailah da aka yi wurgi da ita saman 3sieter Like a Little kid, da kuma Afeefah wacca take saman 1sieter suka ɗago kansu a tare domin ganin mutumin da ya yi wannan aiki.





Momy Rafi'at ce tsaye sai Faman huci take yi, ga yarinyar ta xixi mai shekaru Takwas a duniya tsaye gefe.
Ashe tun lokacin da Afeefah taba Lailah zabi a kanta goge ma ta ƙafa sannan ta bata remote.
Momyn ta shigo ta tsaya ne domin ganin shin Lailah zata gogewa Afeefan ƙafar ko kuwa.





A mugun fusace Momy Rafi'at tayo kan Afeefah bata tsaya jiran komai ba, tasa Yatsun hannunta duka guda Biyar waɗanda Allah ya azurta ta dasu ta bawa Afeefah lafiyayen mari. Wanda sai da taga wuta tsaban azabar da ya ziyarci duka fuskar ta dama gangan jikinta.

Sannan ta fin ciko ta daga saman kujerar, nan ta shiga dukan ta kamar Allah ya aiko ta, tana dukanta tana Marin ta, ita kuwa Afeefah in banda kuka babu abin da take yi saboda tsananin azaba har muryar ta, ta dashe, da kyar ake iya jiyo kukan da take yi.



Lailah kuwa sai faman dariya take yi tana faɗin

"Ƙara ma ta, Momy ƙara ma ta."


Yayin da Haleesat dake Dining Room tayi shiru tana kallon ikon Allah cike da mamakin dukan da Momy take wa Afeefah, ita fa bata ga abin duka ba anan, sai dai bata ce komai ba, haka zalika bata miƙe ba a domin ta taimakawa Afeefah ɗin, sai dai ta ji babu daɗi a zuciyarta.




Da gudu Zaynerb ta fito daga bedroom ɗin ta jiyo kukan Ƴar uwanta da tayi, saboda tsananin saurin da take yi ga tashin hankalin da take ciki, yasa da uku uku take tsallake staircases ɗin, tana saukowa Down, Aikuwa garin saurin da take yi ƙafarta ɗaya ta gurɗe gaba ɗayanta tayo ƙasa tun daga saman bene har sai da ta yo Down.

Aikuwa tasha azaba sosai, ga Bayanta da ya riƙe dama abu ga mara ƙiba, amma duk da hakan bata dan dara ba.



Da a zamar ta ta miƙe tsaye, sannan ta ƙarisa tsakiyar palon inda Afeefah take kwance kamar gawa ga Momyn har Yanzu bata haƙura ba, sai Faman dukan ta da marinta harda hamɓarinta take yi.




Tsuguna wa Zaynerb tayi a gaban Momyn tana bata haƙuri, amma ina Momy tayi nisa, bata jin kira da ta gata hakan ma bai isheta ba, sai ta ƙarisa wajen kayan wuta na Palon, ta ɗauko wayar wuta, sannan ta dawo ta haɗa da Zaynerb da Afeefah ɗin tana duka.
Gaba ɗaya tabi ta farfasa musu jiki da duka, ko gajiya ba tayi ga Zaynerb sai faman kuka da kururuwa take tana ka re Afeefah ita dukan yake samu.



Ganin dai Momyn nasu zatayi kisa ne, Yasa Haleesat tashi da sauri ta ƙarisa tsakiyar palon tana kare su, sannan kuma cikin tsawa da ɗaga murya take faɗin

"Momy.! Momy! Are going to crazy or what?, ki barsu haka mana zasu mutu fa, wai Menene ma abin duka anan ne, wannan zalunci ne fa."






Kallon Haleesat Momyn tayi ita ma cikin tsawa da huci ta ce.



"Ki barni Haleesat ki barni na daka wannan shegun, in banda tsaban Rashin mutunci har Afeefah ce zata ce Lailah ta goge ma ta ƙafa, ita har wacece hakan, Wacece ita iye, How Dare Her?, ki matsa ko kuma na haɗa dake, duka dasu na daka."


Ƙin matsawa Haleesat tayi sai ma ƙara rufe su tana ka resu da tayi.


Ganin haka yasa Momyn dage wa iya ƙarfinta, ta ɗauke Haleesat da mari mai zafi.


Da sauri Haleesat ta dafe kun cinta cike mamaki take kallon Momyn, gaza jurewa tayi da sauri tabar wurin ta haye sama da sassarfa.




Ita kuma Momyn ta ci gaba da dukan su Zaynerb da ko motsi ba sayi zuwa Lokacin. 😭


For More Enquires
08081129487
The Nainarh Kd




___*💋 SARAUNIYAR KYAU 💋*_________ƚαƙυɳ ϝαɾƙσ__________________________________________________________💥👑𝑻𝒉𝒆 𝑮𝒍𝒂𝒎 𝐐𝐮𝐞𝐞𝐧👑💥____________________𝑩𝒚:𝑻𝒉𝒆 𝑵𝒂𝒊𝒏𝒂𝒓𝒉 𝑲𝒅____𝑲𝒉𝒂𝒅𝒆𝒆𝒋𝒂𝒓𝒕𝒉. 𝑺𝒂𝒃𝒊'𝒖. 𝒀𝒂𝒉𝒚𝒂𝒉🤙


☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆
💦𝑳𝒂𝒇𝒂𝒛𝒊 𝑾𝒓𝒊𝒕𝒕𝒆𝒓'𝒔 𝑨𝒔𝒔𝒐𝒄𝒊𝒂𝒕𝒊𝒐𝒏💦🤙

☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆

*




Page *85&86*


"Rafi'at. Rafi'at. Ke Rafi'at.!!"



Duk wannan kiran Alhaji Abubakar Mai Kyau ne Yake ƙwalawa Momy Rafi'at Yayin da yake ta kowa palon hankali tashe, ganin irin dukan mutuwar da take yi wa marayun Yaransa.



Aikuwa Yana ƙari sawa shima bai tsaya komai ba. Ya yasa kyawawan Yatsun hannun sa. Ya bata zazzafan maruka a kumatu, bai tsaya ba ya kuma ƙara ma ta, ya ƙara, ƙara ma ta, har sai da ya ma ta sau Biyar ta ko'ina, sannan ya dakata cikin huci da ɓacin rai yake kallon ta yana faɗin.



"Rafi'at akan wani dalili kika daki waɗannan marayun Yaran?, dama Haka mukayi dake zaki dinga duka min Yara Iyyyee?."


Ya yi ma ta Tambayar ne damma bayaso ya yanke Hukunci kai tsaye.


Tana huci ita ma take basa amsa da faɗin

"A kan na isa na taɓa su, nace saboda na isa dasu ne, kuma sunyi min laifi mai girma, shiyasa idan kuma akwai abin da zaka iya kayi kai tsaye ina jiran ka Malam Abubakar."



Tayi maganar cikin tsawa da kururuwa tamkar batasan wanene tsaye a gabanta ba.


"Okay haka kika ce ko?."


"Eh Abubakar Sameer Lamiɗo haka na faɗi kayi duk abin da kaga zaga iya."



Cikin Huci shima Yake faɗin

"It's okay a baya banso na yanke wannan tsatsaurar Hukuncin a kan ki ba, amma kuma tunda hakan kika zaɓa ki kwashi yaran ki, kije ni Abubakar Sameer Lamiɗo na sakeki, saki ɗaya ni Abubakar Sameer Lamiɗo na sakeki saki biyu..."😐




🔥🔥Kan Bala'i 😝 Taɓɓ, Tashin sense Wanda ba'a saka masa lokaci, Balle kuma Rana 🔥🔥 }






Cak... Momy Rafi'at ta tsaya galala tana kallon mijinta Abubakar wanda ya dan ƙara ma ta saki har biyu lokaci guda, gaba ɗaya wutarta ta tsaya cak, saboda tsananin tashin hankali, tama kasa magana, sam bata yi tunanin wannan tsatsaurar hukuncin Abubakar zai yanke a kanta ba, a tunanin ɗauke Yaransa zai yi daga gidan ya kaisu can wurin mahaifiyar sa ko kuma Ƴan uwansa.




Kallon Lailah da tayi tsuru tsuru da ita a saman 3sieter inda Momy Rafi'at ta jefa ta, Alhaji Abubakar Mai Kyau ya yi kana Ya daka ma ta wani uban tsawa Yana faɗin
"Tashi ki wuce wurin uwarki tun kafin na ya galgalaki a anan wurin... Wato ke ce mai cewa a ƙarawa Shalele ta ko?, zaku sani daga ke har uwan taki, sai nayi maganin ku."



Da gudu ta sauko daga saman 3sieter ɗin har tana tun tuɓe, ta ƙarisa wurin uwarta wacca ta zama Tamkar statue a wurin. 😹





Qari sawa wurin da Yaran nasa suke ko wacce a sume. Ya yi sannan ya kamo hannun Zaynerb ya ɗa ga ta ya saɓata a kafaɗa sannan Ita ma Afeefah da jini duk yabi ya ɓata rigar Ƴar kanti dake jikin ta.

Ko kallon wurin da Momy Rafi'at take bayyi ba, ya fi ce dasu kai tsaye parking lot ya nufi.




Da hango Mister Mai Kyau tafe, ga Yara jiki duk jini, driver Jacob ya tabbatar da babu lafiya.
Da saurin sa ya ƙarisa wajen da motocin gidan suke a fake, sannan ya buɗewa ogan nasa motar ya saka Zaynerb a back seat, sannan ita ma Afeefah ya sakata, kana shima ya shiga, ganin haka shima Jacob ɗin ya shiga sannan ya tayar da motar, da gudu suka bar gidan bayan gate man ya wangale musu gate.






Wani Emergency dake a nan kusa da yankin Jacob ya ƙarisa da su bisa umarnin Mister Mai Kyau.




Da sauri ya fito daga motar sannan ya fito da Zaynerb aka aurata bisa Stretcher sannan aka shiga ciki da ita. Yayin da ita ma Afeefah aka ɗaura ta bisa gadon ko numfashi bata yi, gaba ɗaya a kayi ciki da su domin basu a gajin gaggawa.
Yayin da Alhaji Abubakar ya yi ma Jacob umarni da ya koma can gida da motar.




Sannan ya shiga cikin emergency ɗin da yake Babban mutum ne kuma sananne a duniya, shiyasa ba tare da ɓata lokaci ba ko bincikan lamarin aka fara basu taimakon gaggawa.



Tuni Zaynerb ta dawo Hayyacinta sai dai kuma a dalilin faɗowar da tayi daga saman bene ta sama gocewar ƙashi a hannun ta na dama.



Sai dai kuma duk yadda aka so Afeefah ta dawo Hayyacinta Abu dai ya cutura, domin kuwa ba ƙaramin wahala ta sha ba. Wanda dalilin haka ne ma

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads