Header Ads
Showing 111001 words to 114000 words out of 155363 words

Chapter 38 - SARAUNIYAR KYAU_Takun Farko _cmplt. By The Nainarh Kd -2-1.txt

Ads the beginning of article before Image

Nanah Kd   

14 Jun 2024

1030

Ads at the middle of Article

abin da ya hana ta buɗe fuskar ta a gaban Rafi'at shi ne, ba tasan da wani ido zata kalla Rafi'at ba, sannan kuma ba tasan wani kalar kallo Rafi'at zata ma ta ba, kallon mayaudariya na miki alkhairi kin sakamin da Auren miji?, ko kuwa kallon nagode da kika Aura mijina?.

Tasan dai Auren ta da Abubakar Wanda yake matsayin miji a gareta, wani ikon Allah ne kawai domin kuwa cikin wata biyar komai ya faru tun daga rescue nata da suka yi, da kuma komawar ta Jigawa State wurin su Hajiya Zuwairiya da zaman ta a can.
Dama Auran ta da Abubakar da ya biyo baya komai a cikin watanni biyar kacal ya faru.





Rafi'at mata ga Abubakar Mai Kyau kuma uwar gidan sa, ganin da tayi kowa ya watse an barta, gashi har wuraren goma Abubakar bai shigo gidan ba, to koma ya shigo bata sani ba.

Yasa ta kwashi Yaranta gaba ɗaya da suka yi bacci a nan palon ta shige bedroom ɗinta dasu ta rufe ƙofa.



Washe gari ma tunda ta fito da asuba ta girka ma Yaranta abincin da zasu ci ta kwashe a kula ta koma bedroom ɗin ta, ta kuma rufo ƙofa bata kuma buɗewa ba har wuraren sha biyu na Rana, tana jiyo hayaniyar su Jawaheer sama sama da alama suna shirin komawa Jigawa State ne.

Amma ko fita bata yi ba, har tayi baccin da bata samu tayi ba, a daren jiya, ta tashi taga Yaran gaba ɗaya suma baccin wahala suke yi saman bed ɗin kusa da ita, amma banda Abdulmaleek da Yake can gefe Yana wasa da Teddy Bear abin shi.




A hankali ta sauko daga saman gadon tana ji cikin ta Yana ma ta ƙugin Yunwa domin kuwa Rabon ta da taci wani abu, tana ganin takai kwana biyu, tana shirin shiga bathroom taji muryar Abdulmaleek Yana kiran sunan ta, juyowa tayi tana kallon sa kana ta ɗaga masa kai alamar "Menene."








___*💋 SARAUNIYAR KYAU 💋*_________ƚαƙυɳ ϝαɾƙσ__________________________________________________________💥👑𝑻𝒉𝒆 𝑮𝒍𝒂𝒎 𝐐𝐮𝐞𝐞𝐧👑💥____________________𝑩𝒚:𝑻𝒉𝒆 𝑵𝒂𝒊𝒏𝒂𝒓𝒉 𝑲𝒅____𝑲𝒉𝒂𝒅𝒆𝒆𝒋𝒂𝒓𝒕𝒉. 𝑺𝒂𝒃𝒊'𝒖. 𝒀𝒂𝒉𝒚𝒂𝒉🤙


☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆
💦𝑳𝒂𝒇𝒂𝒛𝒊 𝑾𝒓𝒊𝒕𝒕𝒆𝒓'𝒔 𝑨𝒔𝒔𝒐𝒄𝒊𝒂𝒕𝒊𝒐𝒏💦🤙

☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆




Page *73&74*


Gimtse kyakyawar fuskar sa yaron ya yi sannan yace

"Momy melaca kika kulle mu a bedroom, bayan Daddy ya yi Mana cabuwar Auntie?."🤔.



Cike da maɗaukakin mamaki Rafi'at take kallon Yaron nata, tana mamakin kaifin tunani irin nasa.
Ashe duk wannan abin da ake ciki yana kula da komai duk da cewa cikin qwarancin sa na yara ya yi maganar amma ta fahimci komai.


Ajiyar zuciya ta sauke sannan ta koma ta zauna a saman bed kana ta masa alama da hannunta naya ƙariso.


A je Teddy ɗin ya yi a gefe sannan ya ƙarisa wurin ta.

Kallon sa tayi kana ta fara magana cikin ɗaure fuska

"Buddy Mine, faɗa min tsakanin ni da Daddyn ku waye kafi so?."


Da sauri Yaron ya kalleta jin abin da ta ce Duk da cewa shiɗin Yaro ne, amma ya fahimci wani abu daga cikin maganar ta, dariya ya yi sannan yace


"Momy ke can ai nafi con Daddyn a kanki." 🤪




Ɗiif wutar Rafi'at ya ɗauke na wani lokaci kana da kyar ta iya furta

"Saboda me kafi son Daddyn ku a kaina?."

Har Yanzu Yaron dariya yake sannan cikin qwaranci yace

"Caboda cima Daddy yana cona kuma baya min faɗa idan nayi wani kuch kuye cai dai ya min nasiha kuma ya bani chakuleti da yawa kuma yana kula dani cocai cocai."



Shiru Rafi'at tayi tana kallon Yaron a kullum kaifin basirar sa ƙara nin kuwa yake Yaron brain ɗin sa tana ja sosai.




Ajiyar zuciya ta kuma saukewa sannan ta ce
"Saboda haka ne kawai kafi son Daddyn ku a kaina ko?."


Girgiza ma ta kai ya yi alamar "Eh," murmushin mugunta tayi kana tana faɗin

"Yanzu idan ni ma na dena maka faɗa, sai dai nasiha kuma ina kula da kai sosai, ina baka chakuleti cikin basket da komai da komai zaka soni fi ye da Daddyn ku, kuma zaka dinga jin magana ta?."





Abun ka da ƙaramin Yaro yaji maganar chakuleti cikin basket, Aikuwa da sauri ya shiga girgiza ma ta kai alamar "Eh, ya amince.
Murmushi tayi nan dai ta ci gaba da janshi da fira, tuni ta manta da wata Yunwa.








**
Wuraren ƙarfe Takwas na Daren Ranar Rafi'at tana zaune a palon dake ɓangaren ta Yaranta zagaye da ita suna ma ta qwaran cin su na Yara tana biye musu.



Abubakar Ya yi sallama yana shiga ciki, da kyar ta iya amsa masa sallamar dan ma kawai tasan matsayin ta ne a Addini shiyasa.

Ƙarisa shigowa ya yi sannan ya sama wuri ya zauna kusa da ita, aikuwa da ganin sa Yaran gaba ɗaya suka dawo wurin sa cike da farin cikin ganin sa, shima dai nan ya shiga nuna musu Kalar ƙaunar da yake musu.





Sai faman satar kallon sa Rafi'at take yi ta ƙasan ido. Ƴan kwanakin da tayi bata gansa ba, sai taga kamar anƙara masa wani kyau na musamman fi ye da Wanda ta sansa dashi a baya.



Ajiyar zuciya ta sauke tana danne kishinta a kansa tuno wai a halin Yanzu ba ita kaɗai bace matar sa akwai wata a gefe.🤨




"Matar Mai Kyau ina ga da kin dena satar kallona, domin ni ɗin gaba ɗaya naki ne, gwara ki fito fili ki kalleni san ranki, dan bamai hanaki kinji tawan."😅



Duk wannan maganar Abubakar Mai Kyau ne yake antayo ma Rafi'at a lokacin da ya juyo da kallon sa a kanta.

Ɗan murmushi tayi ko banza taji daɗin abin da ya faɗa wato hakan na nufin ke nan mijinta har yanzu yana ƙaunar ta duk da bai taɓa fitowa fili ya faɗa ma ta ba, ta fahimci Abubakar shiɗin na musamman ne a cikin mutane, domin kuwa baya bayyana abu da baki sai dai ya yi shi a aikace.



"Kodai matar Mai Kyau tana azumin magana da mijin nata ne. Yana ta magana babu amsa."


Abubakar ya kuma faɗa cike da Zoyala, murmushi tayi kana ta ce

"A'a kawai dai matar Mai Kyau tayi kewar My Lawful ɗin ta ne obaaa."





"To gashi ya dawo sai matar mai kyau ta kwantar da hankalin ta domin kuwa Lawful ba inda zai ƙara tafiya Yabar matar mai kyau ita kaɗai."

Wannan karon murmushin da ya bayyana fararen haƙoranta tayi, wato dai su maza a kullum sun san takan mace ko. 😡




Ganin Yaran gaba ɗaya sunyi bacci ne, yasa ta miƙe ta ɗauka Nainarh tana faɗin

"Please My lawful taimaka min da Buddy ya cika nauyi wasu lokutan."



Tayi maganar a lokacin da take ƙoƙarin ɗaukar Nailah ita ma, da sauri Abubakar ya miƙe tsaye kana ya karɓa Nailah daga hannunta Yana faɗin


"Kudai mata akwai ku da kasa da. Yanzu idan kika yar da ita Nainarh wajen ɗaukar Nailah fa, wato saboda qwiuya zaki haɗasu duka, salon ki yarda ɗaya ko?."


Ya yi maganar ne shima Yana saɓa Nailah a kafaɗa sannan kuma ya ɗauki Abdulmaleek ya haɗa su ya nufa bedroom dasu.🤭.



Baki sake ta bisa da kallo tana murmushi, wato ya ma ta faɗa akan ɗaukar Yara biyu a haɗe, shikuma ya ɗauka ko?.🤓

Girgiza Kai tayi cike da nishaɗi kana tabi bayan sa ita ma kafaɗarta saɓe da Nainarh.






Shimfiɗe Yaran su kayi, Abdulmaleek bed nasa daban, haka su Nainarh da Nailah da suke ƙanana aka haɗasu a bed ɗaya da yake gadon Babba ne.



Lulluɓa musu blanket tayi gaba ɗaya kana ta rage gudun Air condition sannan ta juya zata bar bedroom ɗin, harta kai ƙofa taji yo muryar sa yana kiran sunanta.

Ɗan dakata wa tayi amma kuma bata juyo ba.

Murmushi ya yi daga inda yake tsaye kana Yace

"Please matar mai kyau, ki a je komai a gefe kizo ɓangarena akwai maganar da nakeso na muku da Ƴar uwar zaman ki H..."
Ya yi maganar ne domin a tunanin sa zuwa yanzu Rafi'at tasan wacece Abokiyar zaman da ya ƙara ma ta. 🤭🏃






Bata Jira ya kuma cewa komai ba, ta fice daga bedroom ɗin, kai tsaye bedroom nata ta wuce, zuciyarta tunani fall, wato dai farkon sunanta 'H', ne tunda taji ya faɗa hakan, da shigar ta ɗakin kasa zaune tayi bare tsaye, sai faman safa da marwa take yi, ta rasa mai zatayi tunani take akan taje ko kuwa karta je komai zai faru ya daɗe bai faru ba.






Ajiyar zuciya ta sauke abin da zuciyarta ta raya ma ta, shi zata aikata saboda haka ta yanke shawarar zuwa tayi.


Da sauri ta ƙarisa jikin Dressing mirror tana kallon kanta, murmushi tayi kana a fili ta ce

"Dan Allah dube ni Like a SARAUNIYAR KYAU, amma Abubakar ya rasa mai zai min sai kishi..."

Kasa ƙarisawa tayi saboda girman kalmar a wurin ta.





Mayafi ta ɗauka milk color shigen Arabian gown dake a jikinta, kana tayi rolling kanta dashi, sannan ta fito daga bedroom ɗin, kai tsaye part ɗin sa ta nufa zuciyarta na har bawa na Rashin dalili.






A hankali takai hannunta na dama ta tura ƙofar sannan ta shiga ciki bakinta ɗauke da sallama, sai dai kuma ba kowa a palon, dan haka ƙarisa shiga ciki tayi, sannan ta sama wuri ta zauna a saman 3sieter ta ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya tana karkaɗawa tana jiran ƙarisowar Ango da Amaryar sa.


Ta ɗan daɗe zaune a haka, sai kuma can taji alamar shigowar mutane wurin, bugun zuciyarta ne ya ƙaru a lokacin da suke ƙara matsowa wurin da take, da yake ta basu baya shiya sa har suka ƙariso wurin suka zauna fuskar Amaryar kamar yadda ta saba ganin ta lulluɓe da mayafi.



Taɓe baki tayi ƙasa ƙasa yadda ita kaɗai zataji ta ce
"Wannan kodai munafuka ce ita sai haka, idan ba tsaban munafunci ba, ta Aure min miji shi ne hadda wani rufe fuska?."



Taja tsaki ƙasa ƙasa ta gyara zamanta tana binsu da kallo.


Buɗe Taron Abubakar ya yi da addu'a sannan ya fara musu nasiha a kan zaman lafiya da sauran su, yana ta yi dai kuma har zuwa lokacin Amarya bata buɗe fuskar ta ba, a domin uwar gida ta gani.😏

Gyaɗa kai kawai Rafi'at take yi yayin da tarin nasihohin da Abubakar yake antayo musu kamar wani Babban Malami Suke shiga kunenta na dama su fita ana hagu.





Shiru Ya yi Bayan ya gama faɗar Abin da zai iya.

Jin Ya yi shiru da kwararo Ayoyi da hadisai Yasa Rafi'at tayi gyaran murya sannan ta kalla matar dake zaune suna fuskan tar juna da ita fuska rufe da mayafi ta ce.



"Umm gashi ƙanwar tawa naga kamar rowar fuskarta take min domin kuwa har yau kuma dai dai wannan lokaci ban samu na kalla kyakyawar fuskar ƙanwar tawa ba wata ƙila rowar kyakyawar fuskar take min ban sani ba."😐





Ta yi maganar ne cike da zoyala kamar ba ita ba.



Yayin da Abubakar Yaji maganar nata kamar ya ya ke nan dai har Yau Rafi'at bata san wacece ya Auro ba aikuwa akwai matsala.




Ta ɓangaren Amarya Hajarah kuwa murmushi tayi kana cikin nutsuwa irin na ta takai hannayenta duka biyun masu ɗauke da zanen jan lalle gunin burgewa tana Ya ye mayafin da ya Rufe ma ta fuska a hankali a hankali harta Ya ye shi tas duka kyawawan idanunta suka yi taho mu gama da kyawawan idanun Rafi'at .🏃.





Cak maganganun dake ƙoƙarin fitowa daga Bakin Rafi'at suka tsaya cak kamar Yadda Brain ɗin ta Ya tafi hutun Rabin lokaci.🙆





This is emotionality blackmail, da sauri takai hannu tana murza idanunta tana zargin kodai ba dai dai suke gani ba, tabbas idanunta dai dai suke, domin kuwa fuskar da ta gani da Farko ita ta kuma gani yanzu bayan ta murza idanunta, da'ace ta Yadda da tsafi ko sihiri tofa zata ce Hajarah dake zaune Yanzu a gabanta matsayin kishiya a gareta, Magic tayi ta Aura mijinta Abubakar sai dai kash. ☠️



Da wani irin sauri ta miƙe tsaye tana kallon Hajarah hannunta na rawa kamar yadda bakinta yake rawa ta nuna Hajarah tana faɗi cikin rarrabewar harshe.



"Ke,! Ke Hajar me ki-ka-zo anan?..."

Kasa ƙarisa maganar tayi saboda tsananin tashin hankali da ƙunar da zuciyarta take ma ta a lokacin ji take gwara ta harbe Hajarah ko kuma ta caccaka ma ta wuƙa a ciki ta mutu sai dai ta ƙare Rayuwar ta a matsayin PRISONER a Babban PRISON dake Lagos.






Batare da da Tunanin komai ba ta nufi glass center table dake a tsakiyar palon, iya ƙarfinta ta dage ta ɗauki wannan glass center table ta nufi Hajarah dashi zata buga ma ta.

Ai in 360 Hajarah tayi wani super sai gata a bayan Abubakar tana neman a gajin shi.





Kece wa Rafi'at tayi da wata kalar dariyar bosawa ba tunanin komai tabi bayanta tana ƙoƙarin buga ma ta, ai nanfa aka shiga zagaye palo domin kuwa duk yadda taso ta bugawa Hajarah wannan glass ɗin Abubakar ya hana faruwar haka, ita kuma taƙi haƙura gashi ya kasa kwace center table ɗin a hannunta, duk yadda yaso.


Gaba ɗaya sunbi sun hargitsa palon curtains duk sun faffaɗo hatta plasma tv bata gyale ba sai da ta ma ta raga raga, sai faman zagaye ƙaton palon suke yi duk tabi ta haɗa uban zufa, amma taƙi haƙura ta ɗauki ƙaddara tunda aikin gama ya riga da ya gama.


Da Allah ya ba Abubakar sa'a ya damƙe hannun ta da ƙarfin gaske, aikuwa ba shiri ta saki glass ɗin.

Sai kuma ta shaƙo Neck ɗin sa cikin kururuwa tana zage zage.

Duk Yadda yaso ya fin cike ta daga Riƙon da tayi masa kasawa ya yi, hakan ne Yasa ba tare da ya san lokacin ba yasa yatsun sa guda Biyar ya bata wani lafiyayen mari, wanda yasa sai da taga wulgawar wasu taurari a kanta domin kuwa ba kaɗan ba marin ya shige hannunta dake faman Rawa takai ta dafa fuskar ta dai dai sai tin da ya mara tana binsa da wani mugun kallo.



Sai a lokacin yaji Da ya sani marinta da Ya yi, domin kuwa Namiji mai duka ko Marin mace bai cika Namiji ba confirm that's Right.🤜🤛



Da sauri ya ƙarisa kusa da ita yana ƙoƙarin kamo fuskar ta da Shedan Yatsun hannun sa suka kwanta dama abun ka da farar fata take fuskar ta tayi jajir.




A mugun fusace taja baya tana binsa da wani matsiyacin kallo Sannan ta ce



"Abubakar ke nan kayi min Abin da duk duniya babu Wanda ko da gi-gin wasa ya taɓa ƙoƙarin aikata hakan, ka mareni HHhH, mu bar wannan zancen Marin. Abubakar kayi min dafin da bazai taɓa goguwa a Brain ɗina ba, saboda tsaban cin amana ka rasa wacca zaka Auro min a matsayin kishiya sai Hajarah, toh wallahi tallahi kasani, ka siya wa gidan ka ticket na kallon YAƘIN DUNIYA NA UKU, a cikin gidan ka domin kuwa na Rantse da Allah mai girma sai na ɗauka fansar cin Amanar da kamin wallahi tallahi ka rubuta ka a je."




Tana maganar ne tun daga ƙasan zuciyarta kuma cikin kururuwa sannan kuma tana kuma tabbatar masa da Abin da take faɗa...☠️




Tofah Tun daga wannan Ranar wannan Daren wannan Lokacin salon zaman gidan Abubakar Mai Kyau Ya canza tsakanin sa da matarsa domin kuwa zama ake na ba Ruwan wannan da wancan, domin kuwa tuni Rafi'at ta koma Bakin aikinta suka ci gaba da gudanar da Rayuwa sati ɗayan Hajarah Yana ƙarewa ba tare da musu ba Rafi'at ta amshi girki.



To dai haka Rayuwar gidan ta ci gaba da gudana domin Rafi'at a kullum da Hanyar da take fitowa na takalar Hajarah da bala'i.



Sai dai kuma mugun wayo ne da Hajarah domin duk Hanyar da Rafi'at zata fito dashi na janta da fa ɗa ko wani Abun.


Bata taɓa yadda ta biye ma ta su bar Abin kunya, domin kuwa kyar Hajarah take kallonta ita da ta Karanci psychology ma'ana ilimin Tunani, ai ba abin da Rafi'at zata nuna ma ta domin tsaf take karantar tunanin ta.



Haka suka ci gaba da gungura Rayuwar daga ƙarshe da-dai Rafi'at taga ba sarki sai Allah, tuni ta zubar da makaman Yaƙinta.

Suka ci gaba da lula Rayuwar gidan, sai dai kuma na ciki fa Yana ciki eheee.







Tuni Yaran suka koma wajen Hajarah da zama gaba ɗaya domin kuwa mahaifiyar su Rafi'at bata cika zama ba, saboda yanayin aikinta hakan yasa ba wani kulawa ta uwa da take basu sosai.





Tuni Mai gidan da Jama'ar gidan suka miƙawa Hajarah kambun mulkin gidan gaba ɗaya, domin kuwa wata kalar soyayya mara misaltuwa Abubakar yake ma Hajarah, a saboda kyawawan halayenta a garesa daɗi da ƙari itaɗin ta musamman ce a cikin ma ta, ta kasance mai sa'a a cikin masu sa'a.





Komai Yana tafiya dai dai bisa tsari a gidan Mister Mai Kyau, Rayuwa ake na fahimtar juna da kuma ƙaunar juna.






Auren Abubakar da Hajarah nada watanni huɗu, ciki ya bayyana a jikin Hajarah, aikuwa kuzo kuga murna da Farin ciki wurin Abubakar, jinsa Yake Tamkar bai taɓa haihuwa ba, sai kanta wani kalar ƙauna mara misaltuwa Abubakar yake yiwa Hajarah da cikin jikinta.

Sai dai kuma duk da haka bai dena kulawa da matarsa Rafi'at ba, da kuma Yaran sa uku Abdulmaleek da kuma twin's Nainarh, Nailah.




Cikin Hajarah nada watanni biyar a duniya ciki ya bayyana a jikin Rafi'at Ita ma.

Ashe dama can tana da ciki bata faɗawa Abubakar ba, aikuwa koda ya gano haka saiya haɗasu gaba ɗaya yana kula dasu da cikin jikin su.


This novel Book 2 will be paid book fa, a next post zan faɗi nawa ne payment ɗin_Karku damu sosai zan muku discount_-_😇


*For More Enquires*
08081129487
_-_💓The Nainarh KD💓_-_







___*💋 SARAUNIYAR KYAU 💋*_________ƚαƙυɳ ϝαɾƙσ__________________________________________________________💥👑𝑻𝒉𝒆 𝑮𝒍𝒂𝒎 𝐐𝐮𝐞𝐞𝐧👑💥____________________𝑩𝒚:𝑻𝒉𝒆 𝑵𝒂𝒊𝒏𝒂𝒓𝒉 𝑲𝒅____𝑲𝒉𝒂𝒅𝒆𝒆𝒋𝒂𝒓𝒕𝒉. 𝑺𝒂𝒃𝒊'𝒖. 𝒀𝒂𝒉𝒚𝒂𝒉🤙





Page *75&76*
_-_Still free page's muke_-_


______**

Rayuwa ta ci gaba da tafiya cike da tarin nasarori sannan kuma ta gefe guda Abubakar yana kula da matan sa duka da cikin jikin su, a lokacin da cikin jikin Hajarah yakai watanni bakwai shima na Rafi'at dai dai lokacin yakai watanni bakwai, ganin haka yasa Abubakar ya samo wata Dattijuwa tana kula dasu gaba ɗaya.





A Ranar wata lahadi da Yammaci Hajarah ta fara naƙuda sai dai kuma da yake haihuwar fari ne, batasan kan abin ba, shiru tayi bata faɗawa kowa ba, gashi kuma Abubakar baya ƙasar ya tafi ƙasar jamus a kan harkar kasuwancin sa.




Har gari ya waye ba wanda yasan Hajarah tana naƙuda, sai ita kaɗai wani Abin mamaki kuma a Ranar Rafi'at wuraren ƙarfe sha ɗaya na safe ta santalo jaririyarta da taimakon wannan Dattijuwar mata dake gidan, a lokacin Hajarah tana can ɓangaren

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads