Showing 96001 words to 99000 words out of 155363 words
Chapter 33 - SARAUNIYAR KYAU_Takun Farko _cmplt. By The Nainarh Kd -2-1.txt
/Ⴆαƚσσʅ ƙαɱႦα/
5:ʂαɾαυɳιყαɾ ƙყαυ
ɳα
Khadeejarth Sabi'u Yahyah
/ƚԋҽ ɳαιɳαɾԋ ƙԃ/
Page *57&58*
_____*
Rayuwa ta ci gaba da tafiya yau da daɗi gobe a kasin haka, to dama haka duniyar take, ba koda yaushe ake cikin jin daɗi ba.
Auren Abubakar Sadeeq Sameer Lamiɗo da Rafi'at Rafiq Rayyan nada wata biyu Rafi'at ta koma bakin aikin ta, zuwa lokacin sunje Jigawa State sun duba su Dr_Raheemah dasu Hajiya Harirah, Hajiya Zuwairiya daga nan suka wuce wurin Zuwaira, Jawaheer, Jummai, duka anan Jigawa State ɗin, daga nan kuma Adamawa State suka yi wurin Sakeenah nan ma suka sha murnar ganin juna, basu yi ƙasa a gwiwa ba, suka wuce Mai Duguri wajen Yusuf da matar sa Yusra, daga Mai Duguri kuwa Lagos suka antaya wajen Sameen da matar sa Sadiya.
Bayan sun kammala ziyarce ziyarce suka dawo Abuja City, waɗanda kuma basa a ƙasar sai dai ta waya suka gaisa, zuwa lokacin Yunus dake a ƙasar France ya zama ambassador na ƙasar.
Auren su nada watanni uku Rafi'at ta fara laulayin ciki, aikuwa koda aka gwada a kaga ciki ɗan wata biyu da satikai nanfa sabuwa, domin kuwa gaba ɗaya kulawar Abubakar akan Rafi'at ada da yake baifi kashi Ashirin cikin ɗari ba, albarkacin cikin dake jikinta kulawar da yake bata sai ta ninku ta koma kashi sittin cikin ɗari.
Rayuwa ta ci gaba da tafiya cike da nasara a ta kowani ɓangare, amma banda ɓangaren Haleesat Rashid Rayyan, domin kuwa Rayuwa tayi ma ta zafi musamman ma da ta fahimci Rafi'at suna zaune lafiya da mijinta Abubakar Mai Kyau, ta taya Rafi'at murna sosai domin kuwa ba Burin ta raba su ba, amma kuma ta yanke ba ita ba aure har duniya ta naɗe, domin kuwa zuciyarta ɗaya ce kuma ta riga da ta mallakawa wanda yafi cancanta a gareta, sai dai kuma tasan koda zata mutu ta dawo Abubakar Mai Kyau ya yi ma ta nisa, saboda yana Auren ƴar uwanta Rafi'at, tana ƙaunar ƴar uwanta, ba zata so suyi zaman kishi ba, a dalilin haka ta sadaukarwa da Rafi'at Rafiq Rayyan duka soyayyar da take yiwa Abubakar Sadeeq Sameer Lamiɗo har qarshen duniya kuwa ta haƙura dashi.😰
__*BAYAN WATANNI HUƊU*
Cikin Rafi'at Rafiq Rayyan ma ta ga Alhaji Abubakar Sadeeq Sameer Lamiɗo nada watanni bakwai kenan.
**
Ɓiit! Ɓiit...!!!
Haka sautin yake tashi gaba ɗaya yankin a yayin da jerin motocin suke buga horn a ƙofar ƙerarren gidan.
Da sauri gate man ya ƙarisa bakin gate sannan ya wangale gaba ɗaya, sannu a hankali motocin suka shiga gidan, sannan a jere suke tafiya har suka ƙarisa wajen da aka tanadar domin ajiyar motoci, shikuma gate man ya mayar da gate ya rufe.
A hankali ya zuro ƙafarsa waje daga cikin Motar kana ita ma ɗayar ta biyo baya, daga ƙarshe kuma gaba ɗayansa ya fito daga motar, kamar yadda yasa ba sanye cikin Business suit black and White color.
Tafiya ya fara sannu a hankali a yayin da da escort service nasa suke take mishi baya, wasu kuma suka tsaya suna ciro trolleys a boot na Mota.
A dai-dai bakin ƙofar palo escort ɗin suka dakata, shikuma ya shige ciki yayin da waɗanda suka ɗauko jakunku nan na tsaraba suka biyo bayan shi a palo suka jere wuri ɗaya sannan suka fice abun su.
Staircases ya hau yana qwalawa matar sa kira, amma yaji shiru shi dai yasan yana dawowa zai sameta a Palo tana jiransa amma yau tsit kakeji, babu ita babu alamar ta.
Qara ɗa ga muryar sa ya yi yana kiran sunan da ya raɗa ma ta
"Matar Mai Kyau.!"
"Matar Mai Kyau.!!"
Still shiru dai, da sauri ya tura ƙofar bedroom nata ya shiga tun daga kan mattress bathroom wardrobe babu inda bai duba ba, amma ba Rafi'at ba labarin ta, da sauri ya kuma fitowa wannan karon bedroom nasa ya nufa yana tunanin ko tana can ne bacci ya ɗauketa shi yasa bata fito ba.
Sai dai abin mamaki bedroom ɗin nasa ma, ba inda bai duba ba, still dai babu Rafi'at.
Zuwa lokacin fa hankalinsa ya fara tashi danma shi ɗin Namiji ne.
Fitowa ya kumayi ya shiga duba gaba ɗaya gidan, amma ba Rafi'at ko alamar ta
Zuwa lokacin ya fara gajiya da nemanta domin kuwa shi ba Engine bane.
Dawowa palon ƙasa ya yi ya zauna ya zuba uban tagumi yana kallon tilin kayan wasan yara da ya bada ordered ɗin su aka kawo.
Can gefan zuciyar sa kuwa tunani yake wai shin yaushe ya fara son Rafi'at Rafiq Rayyan ne da zai damu haka da rashin ta?.
Ko dai ya manta ita ɗin Likita ce wata ƙila ma tana can anyi ma ta kiran emergency shi yasa ta fita ba tare da ta faɗa masa ba.
Wani ɓangare na zuciyarsa kuma cewa yake
"To dama kasan da haka shine zaka dama kanka kodai ka fara son matar mai kyau ne?."
Da sauri ya ba kanshi amsa da faɗi a fili "A'a ba sonta nake ba, unborn ɗina dake a cikinta nake so, ba ita ba, zuciya ta ɗaya ce, kuma na riga na mallakawa wacce ta cancanta da samunta..."
Shiru ya yi daga hakan. Ya daɗe zaune a palon yana tunane tunane a cewarsa ba Rafi'at yake jira ba.
A kalla yakai mintuna talatin da biyar a wurin yana jira, can ɗa go kansa da zayyi suka yi ido huɗu da ita, a Yayin da take ƙoƙarin wuce shi, da alama bata lura dashi ba.
Da sauri ya miƙe ya ƙarisa wurin ta yana kiran sunan ta
"Rafi'at.! Rafi'at..!! Lafiyarki kuwa daga ina kike haka?."
Tambayar yake hankali a ɗan tashe, ganin kamar ba'a cikin hayyacinta take ba yasa ya ɗauketa gaba ɗaya bai damu da cikin dake jikinta ba, ya wuce sama da ita.
A ranar Rafi'at gaba ɗaya jikinta kamar a sanyaye yake, saboda haka Abubakar bai takura ta da tambayar inda taje ba, saboda yasan yana yin aikinta daɗi da ƙari kuma ita ɗin mace ce mai ɗauke da juna biyu.
Wata ƙila a can Asibitin da take aiki ne taga abin da ya firgita ta saboda haka ya yanke shawarar ba zata ƙara zuwa wajen aiki ba har sai ta haihu.
Koda ya sameta da maganar bata wani damu ba saima cewa da tayi "Allah yasa hakan shine mafi alkhairi."
Zuwa daren Ranar kuma ta ware kamar ba ita bace jiki sanyaye da rana.
__*GAB@ KWANAKI BIYU*
{_TWO DAYS LATER_}
Suna zaune a palo Rafi'at kwance saman 3sieter Yayin da Abubakar yake zaune gefanta yana karanto mata wani £nglish story.
THE MOST BEAUTIFUL HEART.
Gaba ɗayan su labarin yana ƙayatar dasu yadda ya kamata.
Wayar Rafi'at dake gefe ne ta farayin ƙara alamar shigowar kira.
Da sauri takai hannu ta ɗauka, sannan ta tashi zaune da taimakon mijinta, kara wayar tayi a kunne bayan tayi picking.
Shiru tayi tana sauraron abin da ake faɗa ma ta ta ɗayan ɓangaren.
Ko ƙaramin motsi ta gaza yi da alama ta fita daga hayyacinta, ganin kamar bata hayyacinta yasa Abubakar tambayar ta Abin da ke faruwa.
Kallon sa tayi kamar wata zautacciya batasan lokacin da ta saki Wayar hannunta ba, aikuwa ta faɗi a ƙasan tiles ba ta tarwatse.
Da sauri Abubakar ya janyo ta jikinsa yana rarrashi, ganin yanda hawaye yake zuba daga idanunta tamkar an buɗe famfo.
Sai da ya tabbatar ta sama nutsuwa sannan ya sake ta yana tambayar abin da yake faruwa.
Cikin shashsheƙar kuka Rafi'at take faɗin
"Haleesat Rashid Rayyan."
"Haleesat....
Haleesat ce wai wai ita ce..."
Sai kuma tayi shiru tana kuma fitar da siraran hawaye.
A mugun tsorace Abubakar yake kallonta sannan cikin tsananin matsanancin tashin hankali da murya wacca bata fitowa sosai saboda rarrabewar da takeyi wajen furta maganar yake faɗin
"Haleesat Rashid Rayyan. Kuma to Menene abin da ya sameta, ki faɗamin mana kinji Rafi'at Please..."
Ya yi maganar yana jijigata tamkar ta faɗa mishi Haleesat ɗin rasuwa tayi.
Cikin tsananin kuka Rafi'at ta ci gaba da cewa
"Haleesat ce wai aka sace ta tun kwanaki huɗu da suka wuce shine, Sailuba ta kirani tana faɗamin...."
Bata ƙarishe maganar ba ta kuma fashewa da matsiyacin kuka kamar zautacciya.
Shi kuwa Abubakar za'a iya cewa suman zaune ya yi jin abin da Rafi'at take faɗa Tamkar shock na wutan lantarki haka maganar tazo mishi a ba za ta sannan kuma ta dake shi yadda ya dace.
Sun ɗauki tsawon lokaci a haka ba wanda ya iya qwaqwqwaran motsi cikin su.
Sai can Abubakar da yake Namijin gaske ne, ya kalla Rafi'at bayan ya dawo hayyacinsa daga duniyar tunanin da ya lula yana faɗin
"Ki kwantar da hankalinki in Allah ya yarda za'a ganta nanda bada ɓata lokaci ba, kinji. bata bashi amsa ba, sai ma faɗawa jikinsa da tayi tana kuma fashewa da kuka.
Da yake a lokacin wuraren ƙarfe shida na yamma ne.
Yasa sai da aka kira sallar isha'i sannan suka shirya suka wuce gidan su Rafi'at.
Can ma dai banda kuka babu abin da Rafi'at take yi gaba ɗaya Ahalin Alhaji Rafiq Rayyan sun taru anata faman addu'o'i ana fatan bayyanar Haleesat Rashid Rayyan cikin gaggawa daga hannun wa'innan kidnappers da ake tunanin sune suka sace ta.
Sai can cikin dare wuraren ƙarfe sha ɗaya sannan Abubakar ya ɗauki Rafi'at suka koma gidan su, gaba ɗaya jikin ko wannensu a mugun sanyaye.
🎀🎀ϝιʋҽ ʂƚαɾ'ʂ ɯɾιƚҽɾ'ʂ🎀🎀
💦💦ɯҽ αɾҽ ƚԋҽ ρҽɾϝҽƈƚ ɯɾιƚҽɾ'ʂ💦💦
✍️αʅƙαʅαɱι ყαϝι ƚαƙσϝι🤙
_https://chat.whatsapp.com/DP2UrllaLb34m7nsvgeNEd
__*💋 SARAUNIYAR KYAU💋*___________________________________________________________________💥👑𝑻𝒉𝒆 𝑮𝒍𝒂𝒎 𝐐𝐮𝐞𝐞𝐧👑💥____________________𝑩𝒚:𝑻𝒉𝒆 𝑵𝒂𝒊𝒏𝒂𝒓𝒉 𝑲𝒅____𝑲𝒉𝒂𝒅𝒆𝒆𝒋𝒂𝒓𝒕𝒉. 𝑺𝒂𝒃𝒊'𝒖. 𝒀𝒂𝒉𝒚𝒂𝒉🤙
☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆
💦𝑳𝒂𝒇𝒂𝒛𝒊 𝑾𝒓𝒊𝒕𝒕𝒆𝒓'𝒔 𝑨𝒔𝒔𝒐𝒄𝒊𝒂𝒕𝒊𝒐𝒏💦🤙
☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆
Page *59&60*
__*
Rayuwa ta ci-gaba da tafiya kwanaki suna ja yayin da gaba ɗaya hankulan Ahalin Alhaji Rafiq Rayyan yake a tashe na Rashin Haleesat Rashid Rayyan babu ita babu labarin ta.
To abin ma haka ne ta ɓangaren Rafi'at Rafiq Rayyan da mijinta Abubakar Mai Kyau gaba ɗaya sun ɗauki damuwar duniya sun ɗaurawa kansu.
Har takai ta kawo ma Rafi'at bata iya cin abinci sai dai idan Abubakar yana gidan ne, to shine yake takurawa sai taci kodan unborn ɗin su, wani lokacin sai dai ta saka masa kuka tana bashi labarin kyawawan halaye irin na Haleesat Rashid Rayyan gata da haƙuri ga son mutane.
Kwanaki sun ci gaba da tafiya har ya kasance an ɗauki tsawon sati biyu da sace Haleesat Rashid Rayyan amma har yau waɗannan masu kidnapping basu kira sun faɗi abin da suke buƙata ba, zuwa lokacin jikin kowa ya kuma yin sanyi lakwas, wasu ma sun fara tunanin kashe ta aka yi yayin da har zuwa lokacin wasu basu cire rai ba, domin kuwa INDA RAI DA RABO.
____
Zaune yake a tsakiyar palon, saman tattausar carpet sanye cikin jallabiya fara ga hula ita ma fara akan shi hannunsa riƙe da alqur'ani mai girma yana karantawa, daga gefansa kuma Rafi'at ce ita ma zaune saman lallausar carpet ita ma sanye cikin Arabian gown white color ga mayafi fari shima tayi rolling kanta dashi, hannunta riƙe da alqur'ani mai girma ita ma tana karantawa.
Sun ɗauki tsawon lokaci a haka sannan a tare suka kai aya, kana suka rufe alqur'anan dake a hannun su.
Wanda hakan Ya yi dai dai da shigowar kira a Wayar Abubakar dake gefansa cikin nutsuwa irin nashi yakai hannun daman sa ya ɗauki wayar kana ya yi picking, a tunaninsa wata magana ce akan ɓatar Haleesat Rashid Rayyan da yasa ana binkcike na musamman, shiyasa bayyi tunanin komai ba ya saka Wayar a free sannan ya a je gefe ta yanda zasu ji abin da mai kiran zai faɗa.
Sallama suka ji mai kiran ya farayi, amsa masa Abubakar ya yi sannan Wanda ya yi kiran cikin girmamawa yake cewa
"Mister Mai Kyau wannan budurwa mai suna Haleesat Rashid Rayyan da aka bamu report na ɓatar ta ita ce aka samu can cikin forest {gandun daji} yayin binkcike, a halin yanzu an ɗauke ta izuwa Asibitin..."
Tun kafin ya ƙarisa cikin sauri Abubakar da Rafi'at har suna haɗa baki wajen tambayar sa wani Asibitin?.
Faɗa musu sunan Asibitin ya yi sannan Abubakar ya kashe Wayar basu tsaya jiran ko escort ba, ya ɗauki Rafi'at a mota ita kanta bata damu da tsohon cikin dake jikinta ba, suka bar gidan sai a hanya ne ma Abubakar ya samu damar kiran su Alhaji Rafiq a waya ya musu bayanin abin da ke faruwa, sannan ya basu Address na asibitin da aka kwantar da Haleesat Rashid Rayyan.
**
A tare Motar su Abubakar dana su Alhaji Rafiq Rayyan suka ƙari sa Asibitin da aka kwantar da Haleesat ɗin, saboda tsananin tashin hankalin da suke ciki yasa basu tsaya gaisawa ba, gaba ɗaya suka ɗunguma ciki.
Zama sukayi a kujeru amma banda Rafi'at da Abubakar domin kuwa a miƙe suke, duk yadda akaso Rafi'at ta zauna ƙi tayi, haka aka rabu da ita.
Suna Zazzaune zaman jiran tsammani sai ga wasu ma'aikatan aikin jinya mata biyu sun fito tare da wata Likita mace.
Gaba ɗayansu suka miƙe suka ƙarisa wurinta kowa da irin tambayar da yake ma ta akan lafiyar Haleesat Rashid Rayyan.
Ajiyar zuciya Dr_Salahah Gashwa, ta sauke tana kallon su cike da tausayawa sannan cikin sanyin murya take faɗin
"Mun samu an tsayar da zubar jinin da take yi, amma raunukan jikinta sune matsala, saboda haka dole akwai wani Babban Likita da muke buƙatar taimakon sa a halin yanzu..."
Shiru tayi tana kallon yadda gaba ɗaya suka yi shiru suna sauraronta.
Sannan ta ci gaba
"Please zamu iya maganar a office ɗi na kuwa?."
Ajiyar zuciya Alhaji Rafiq Rayyan ya sauke sannan yace
"Ba damuwa muje."
Da sauri Rafi'at ta ce
"Dr_Salahah zamu iya shiga nida Sailuba da Mamyn mu a domin duba ta?."
''Eh zaku iya shiga amma banda hayaniya domin ta sama bacci ne."
Dr tayi maganar sannan tayi hanyar office ɗin ta Alhaji Rafiq da ƙaninsa Alhaji Riyaz sai Abubakar suna take ma ta baya.
A hankali ta tura ƙofar ɗakin sannan ta shiga tafiya sannu a hankali irin na masu cikin da ya kusa fita.
Ƙarisawa tayi wajen gadon kana ta zauna gefan gadon a hankali Yayin da Hajiya Zinaru da Sailuba suka tsaya a tsaye suna kallon Haleesat wacca ke sanye cikin doguwar riga sky blue irin Wanda marasa lafiya suke sakawa, Baiwar Allah gaba ɗaya tayi baƙi ta rame duk tabi ta fita hayyacinta da alama masu kidnapping ɗin basu bata abinci ba, saboda yadda duk tabi tayi ƙashin wuya ga jikinta gaba ɗaya raunuka ne, da alama sosai aka gana ma ta a zaba wasu wuraren ma a jikinta shedan bulalu ne. Lallai waɗannan masu kidnapping basu barta haka ba😞
Fuskar ta kuwa abin ba kyan gani domin ko gaba ɗaya bakinta a fashe yake, idanun ta kuwa duk da a rufe suke amma ana iya ganin yadda suka kumbura ga shedan cizo ba ɗaya ba kuma biyu ba a wuyanta da fuskar ta gaba ɗaya fuskar ta a kumbure take manyan idanun ta kuwa jajir suke gasu sunyi ƙanƙanta na Rashin cin abinci.😭
Da sauri su duka suka ɗauke kallon su daga kanta gaba ɗaya hawaye suke yi, a fili Sailuba take faɗin
''Allah sarki Rayuwa tabbas INDA RANKA KA SHA KALLO a ƙasƙantacciyar Rayuwar nan da muke ciki, yanzu dan Allah dubi Auntie Haleesat, Mamy ku duba kuga inda waɗannan azzaluman mutane suka mayar da ita, ta koma tamkar wata skeleton, ina tsoron ace min Raping ɗinta aka yi domin kuwa bazan lamunta ba Wallahi..."
Gaba ɗaya maganar takeyi cikin kuka ta ci gaba da cewa in Allah ya Yadda wa'innan mutanen da suka yi ma Auntie Haleesat wannan abu sai sunga mummunar ƙarshe a Rayuwar su in Allah ya Yadda ba zasu taɓa ganin mai kyau a duniya da lahira ba. Ni Sailuba na Rasa abin da mutane suke nema ne a duniya wannan marainiyar ban san laifin da tayi musu ba, da suka saka ma ta da wannan mummunar uquba Duniyar mu da mutanen cikin ta sun koma tamkar sheɗanu saboda tsananin Rashin imani..."
Da sauri ta ƙarisa bakin gadon ta tsaguna sannan ta kamo hannun Haleesat dake saman mattress ɗin ƙara fashewa da kuka tayi tana kallon ikon Allah, wato a hannun ma ba'a Rabu da ita ba sai da aka gana ma ta wani salon a zaba.
"M_M_R_D_L."
Sune kalmomin da aka Rubuta a hannun Haleesat Rashid Rayyan da manyan baƙi sannan kuma a wawware.
Juyowa tayi tana kallon su Rafi'at da Hajiya Zinaru dake ta faman share hawaye wasu na ƙara fitowa Sailuba tayi sannan cikin kuka ta buɗe baki zatayi magana taji alamar hannayen Haleesat Rashid Rayyan dake cikin nata sun fara motsi...
🎀🎀ϝιʋҽ ʂƚαɾ'ʂ ɯɾιƚҽɾ'ʂ🎀🎀
💦💦ɯҽ αɾҽ ƚԋҽ ρҽɾϝҽƈƚ ɯɾιƚҽɾ'ʂ💦💦
✍️αʅƙαʅαɱι ყαϝι ƚαƙσϝι🤙
https://whatsapp.com/channel/0029VaEZtE15a2429vfcpf20
___*💋 SARAUNIYAR KYAU 💋*___________________________________________________________________💥👑𝑻𝒉𝒆 𝑮𝒍𝒂𝒎 𝐐𝐮𝐞𝐞𝐧👑💥____________________𝑩𝒚:𝑻𝒉𝒆 𝑵𝒂𝒊𝒏𝒂𝒓𝒉 𝑲𝒅____𝑲𝒉𝒂𝒅𝒆𝒆𝒋𝒂𝒓𝒕𝒉. 𝑺𝒂𝒃𝒊'𝒖. 𝒀𝒂𝒉𝒚𝒂𝒉🤙
☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆
💦𝑳𝒂𝒇𝒂𝒛𝒊 𝑾𝒓𝒊𝒕𝒕𝒆𝒓'𝒔 𝑨𝒔𝒔𝒐𝒄𝒊𝒂𝒕𝒊𝒐𝒏💦🤙
☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆
🎀
Page *61&62*
A can ɓangaren kuwa
Zama Dr_Salahah tayi kana suma suka zazzauna a kujerun dake Kallon wanda ta zauna shiru office ɗin ya ɗauka gaba ɗaya sun zuba ma ta ido suna jira suji abin da zata faɗa, a kalla sunkai mintuna biyar a haka.
Sannan Dr_Salahah ta ɗago daga rubuce rubucen da take yi tana kallon su, ta cire farin glass dake saƙale a fuskar ta fararen idanunta suka bayyana kana ta fara magana cikin harshen hausa yadda gaba ɗaya zasu fahimci abinda takeson faɗa musu da kyau.
"Wato Abin da Rahoton binkciken da muka gabatar akan Dr Haleesat Rashid Rayyan shi ne, akalla an ɗauki tsawon kwanaki biyar ana gana ma ta a zaba sannan binkciken mu ya nuna cewa an ɗauki tsawon kwanaki goma a kullum sai anyi Raping ɗinta sau biyu, bayan an gama kuma ana saka wani abu mai tsatsa kodai sanda ko ƙarfe ana goge duk wata alama ko hujja wacca zata nuna anyi ma ta fyaɗe.😭
Daɗin daɗawa kuma binkcike ya nuna ba iya maza ne kawai suka yi amfani da ita ba hadda ma mata sannan ta ƙarfi suke yi wanda hakan ne yasa duk taji ciwuka a jikinta da bakinta sai kuma hannunta da aka Rubuta wasu alphabet guda biyar.
"M_M_R_D_L."
Sune abin da aka Rubuta a hannun daman ta sai kuma tsakiyar hannun hagunta nan ma aka Rubuta "X" da alama ɗaukar fansa ne yasa aka sace ta ba wai saboda kuɗi ko wani abun ba."
Tana faɗin haka tayi shiru tana kallon su.
Tun lokacin da Dr Salahah ta fara magana gaba ɗaya shiru suka yi suna kallon ta Alhaji Rafiq ashe