Showing 36001 words to 39000 words out of 188939 words
Chapter 13 - SAKAYYA Book 1 complete BY GARKUWA.txt
zo baki taɓa zuwa kin kwana mana ba”.
Khausar na gyara zama tace.
“Insha Allah yau zan zo mukwana”.
Murmushi Adda Adam tayi da faɗin.
“Aikam Nagode”.
Khausar ta juya tare da kallon Baffa Umaru dake sakin murmushi tace.
“Amma fa ki faɗawa jarumin mijinki ya kawo min abu mai daɗi”.
Murmushi kana tace.
“Inde wannan ne baki da matsala”.
Bayan sun gama hira tayi musu sallama ta tafi.
Da daddare bayan sun idar da Sallah Isha'i Khausar tace da Dije.
“Muje gidan Garkuwan Rugarku mu kwana”.
Dije tace.
“Toh muje”.
Sannan ta miƙe suka shiga ɗaki sukayi wa Goggo Nanne sallama.
Adda Amada dake ɗaki tana jin Sallamar su ta fito fuskarta ɗauke da murmushi tana cewa.
“Ai yanzu nake cewa zanbi sawunku”.
Khausar tayi murmushi tace.
“To aigamu ina Jarumin mijin naki?”.
“Yana nan mai zaki bashi?”.
“Babu abinda zan bashi abin daɗi da yace zai ajiye min zai bani idan kuma babu in tattara in tafi”.
Ta Ida maganar tana murmushi.
Miƙewa Adda Adama tayi tace.
“Toh ki kwantar da hankali ga abin daɗi”.
Tayi maganar tana ajiye musu karamin kwandon kaba dake ɗauke da Inabi, Tuffa, Mangoro, Ruman, da sauran kayan itatuwa sai kuma kwanon farfesun kifi yana tururi.
Murmushi mai sauti Khausar tayi tace.
“Lallai yana yina ashe wannan gara haka”.
Ita dai Dije murmushi kawai take musu.
Duka suka haɗu suka ci sannan suka kwanta ɗaki ɗaya da Adama.
Shiko Baffa Umaru yana can aɗakinsa ya kwana.
Misalin ƙarfe biyu na dare Khausar ta farka aɗan firgice sakamakon hayaniya da take jiyowa.
Dije ta gani itama zaune tana zazzare idanu ganin sukayi Adda Adama ta fice aɗakin da mugun sauri suma cikin sauri suka bi bayanta.
Da gudu Adam ta nufi ɗakin mijinta dai-dai lokacin daya fito.
Hannunsa ta riƙe cikin raunin murya tace.
“Dan Allah kada ka fita da alama suna da yawa kaji hayaniyar su”.
Da sauri ya juya ya kalleta tare da faɗin.
“Idan ban fita ba wa zai dakatar da su wannan daga ji mutanen Ƙauyen Garinga ne bamusan mai suka zo dashi ba dare dare zasu zo mana haka babu yanda za'ayi dole in fita”.
Ta girgiza kai tare da riƙe sa kana tace.
“Dan Allah kada ka fita".
Tureta yayi daga jikinsa ya fita yana fita ya hango Arnan mutanen Garinga ne wanda yawansu zai kai kimanin mutum ɗari da sauri ya nufi hanyar jejin yayin da bayansa ke rataye da kwari da baka hannunsa na riƙe da touch light mai masifar haske.
Cikin fushi da tsawa ya haskasu da touch light ɗin hannunsa mai masifar kashe ido yace.
“Menene wai ma tukun ina kuka nufa!?”.
Ɗaya daga cikinsu wanda ya kasance babban su yace.
“Ƴar mu muke nema ta ɓata”.
Duk da acikin duhu ne hakan bai hana shi watsa musu kallon banza ba yace.
“Ƴarku ta ɓata shine dare-dare haka zaku zo wajenmu nemanta?”.
Biyu Daga cikin su suka ce.
“Ai kidnapping ɗinta akayi”.
Afusace yace.
“Kuma in kidnapping ɗinta akayi sai akace muku tana nan Rugarnu?”.
Babban cikinsu yace.
“Tana nan Rugarku dama Fulanin ku ai sune suka sace ta suka kawota dan haka an saceta tana nan mu nan muke zargi”.
Cikin tsananin fushi da zuciya Baffa Umaru yace.
“Baku isa ba babu yanda za'ayi haka ya faru!”.
Babban cikinsu yace.
“Dole sai mun shiga garinku gida-gida ɗaki-ɗaki mun bincika”.
Cikin tsananin fusata Baffa Umaru yace.
“Wallahi in dai ina raye baku isa ba babu wanda ya isa yashiga garinmu yace yayi bin cike indai haka kuke so kuje kuzo da rana muyi magana”.
Babban su yace.
“Mu adaren nan muke so muyi magana”.
Baffa Umaru yace.
“Toh baku isa ba”.
Dumfaro sa sukayi da niyyar shiga Rugar gadan-gadan.
Shi kuwa baya yaja tare da jan kwari da baka yace.
“Duk wanda yake jin shi Jarumi ne kuma ya kai to ya kuskura ya shiga mana cikin Ruga yaga abinda zai faru”.
Tsayawa su kayi akuma dai-dai lokacin ne sauran mazan cikin Rugar suka fiffito mafi yawa ma sautin Baffa Umaru ne ya tashe su dan shi mutum ne mai zafin gaske musamman ma idan ransa ya ɓaci.
Acan bakin ƙofar gida kuwa sosai Khausar ta shiga mamaki sai asannan ta tabbatar da maganar Adama da tace mijinta Jarumi ne kuma Garkuwan Rugar.
Malam Liman ne yayi gyaran murya bayan isan su wajen yace.
“Tun da kunce haka yanzu ku koma da safe sai kuzo aje wajen Mai gari sai ayi magana”.
“Toh”, Babban su yace sannan suka juya suka tafi badan ransu ya soba.
Washe gari da safe bayan sunyi ta tsansu sun daddawo da hantsi Arnan garin Garinga suka zo suka haɗu aƙofar gidan Jauro.
Bayan sun gama gaisawa Jauro ya dubesu Anutse cike da kamala irin na shugaba yace.
“Mai yafaru muna sauraron ku".
Babban su yayi gyaran murya yace.
“Ƴar muce buke ce akayi kidnapping sannan muna zargin tana cikin wannan Rugar”.
Cikin danne takaicin ƙazafin da arnan ke son yi musu Jauro ya jinjina kai kana yace.
“Kun tabbatar tana cikin wannan Rugar?”.
Kai Babban su ya jinjina yace.
“Ƙwarai mun tabbatar sannan mun zo zamu shiga Umaru ya hana mu sannan Umaru shi yake sa mana Ido komai akayi bamu isa muyi magana ba sam Bama ƙaunar abinda Umaru yake mana yayi rayuwarsa muyi rayuwar mu!”.
Wani banzan kallo Baffa Umaru ya watsa musu cikin yanayin zafinsa yace.
“Ba zanyi rayuwata kuyi rayuwarku ba muddin kuna so nayi rayuwata kuyi naku to ku fita sabgarmu banga wanda ya isa ya shigo cikin Rugar mu yace zai taka mu inbar saba”.
Da sauri Jauro ya ɗaga masa hannu hakan yasa Baffa Umaru yayi shiru.
Baffa Jauro kuwa maida kallonsa garesu yayi kan yace.
“Munji mun yarda an sace muku yarinya anyi Kidnapping ɗinta”.
Sai kuma ya maida kallonsa kan Malam Liman yace.
“Ɗauko mana Bible agidanka”.
Kallon Yaya Abba Malam Liman yayi yace.
“Jeka ɗauko min asalin Bible na da acikin littatafai na”.
Miƙewa Yaya Abba yayi babu daɗewa ya dawo hannunsa riƙe da Bible ɗin ya mikawa Jauro.
Karɓa Jauro yayi tare da miƙawa Babban su yace.
“Gashi ku rantse da littafin ku tunda kuce ƴarku ta ɓata kuma tana garin nan”.
Ƙin amsa Babban su yayi.
Cikin sanyi Jauro yace.
“Inde ka tabbata ƴarku ta nan to ka karba ka rantse Inde ka rantse.
To mukuma zamu baku damar shiga sannan muma zamu rantse da Alkur'anin mu mai girma cewa ‘yarku bata nan amma duk da haka idan kun rantse zamu baku damar shiga cikin gida-gida ɗaki-ɗaki kuyi bin cike”.
Shi dai babban nasu kin rantse wa yayi sai wuƙi-wuƙi yakeyi da ido.
Ganin haka yasa Jauro ya kalli sauran na bayansa yace.
“To ɗaya daga cikin ku ya karɓa ya rantse”.
Still suma ƙin karɓa sukayi.
Afusace Baffa Umaru yace.
“Ba gashi ba basu da gaskiya Arnan nan neman fitina suke damu sam babu gaskiya alamarin su bayan sace-sacen dabbobi da kuke mana sai kun nemi fitina damu”.
Babban su ya juya ya kalli Baffa Umaru yace.
“Wani irin sace-sace kuma?".
Harara Baffa Umaru ya watsa masa yace.
“kana tunanin bamusan kune kuke sace mana dabbobin muba to yanzu ga Bible ka karɓa ka rantse da littafin ku cewa ƴarku ta ɓata duk alamun rashin gaskiya ya bayyana atare da ku kawai ku taru dare-dare kuzo mana da mugun nufi”.
Anutse Jauro yace.
“Umaru kayi haƙuri kaki”.
Yasan idan ransa ya ɓaci babu wanda zai iya shawo kansa.
Malam Liman ya dubesu yace.
“Tunda har baku rantse da littafin kuba kenan ƴarku bata ɓata ba in kuma ta ɓata to baku da tabbacin tana garinmu”.
Babban su yace.
“Shikenan babu matsala tunda zaku iya rantse wa da littafin ku munsan bata Rugarku yanzu magana ya ƙare.
Amma Jauro da malam Liman ku jawo Umaru kunne ya fita sabgarmu”.
Miƙewa Baffa Umaru yayi tare da nuna kansa da hannu yace.
“Ni ɗin nan ka ganni nan Babu wanda nake tsoro sai Allah daya hallicceni".
Ƙwafa Babban su yayi yace.
“Tun da haka kace shikenan amma zaka ga abinda kake tsoro”.
Da sauri Jauro ya juya ya kalli Babbansu yace.
“Mu ba mason fitina me kake nufi da zaiga abinda yake tsoro?”.
Babban su yace.
“Indai zai shiga sabgarmu to zaiga abu da yawa”.
Jauro yace.
“Toh bama son fitina tunda kuda kanku kun tabbatar da ‘Yarku bata cikin Garinmu sannan kuda kanku kunsan baku da gaskiya kun ƙi ku rantse, karku sake shigo mana Rugar mu haka ba maso idan kuma kuka sake to zamu haɗa ku da Sarkin cikin Gembila”.
Jin Jauro yace zai haɗa su da Sarkin Gembila yasa suka ce.
“To ayi hakuri ba zasu sake ba”.
Sannan suka juya suka tafi cike da baƙi ciki badan Umar daya hana su shiga ba adaren da sun samu damar kwasan dabbobi damar saboda haka suka ce ansace musu ‘yarsu.
Bayan kwana biyu Komai ya lafa ba fitina da hantsi Khausar da Dije da Ma'u sun ɗebo kayan marmari arafi suna fitowa daga cikin rafin suka hango wata mota fake agefen Rugar tasu sai kuma hango wasu mutane biyu ɗaya ya fito daga gefen dama ɗaya kuma daga gefen hagu da gudu suka shiga motar kafin su Dije su ƙara so sun figi motar.
Khausar kuwa sosai tsura fuskokin su ido kafin su shiga motar, sosai ta riƙe kamanninsu. sannan tabi motar da kallo lokaci ɗaya ta riƙe Number motar Dije da sauran 'yan matan kuwa mamaki suka shiga yi shin mai ya kawo masu motar garin sannan mai yasa da suka gansu suka gudu bayan sun san a irin wannan lokacin, duk mazan garin basa nan makiyaya sun tafi kiwo saura kuma su tafi jeji wa'anda ke rafi kuma sun tafi lambu jiki Asanyaye suka tafi.
Bayan kwana biyu da daddare Khausar na bacci, yayi da take ta takurewa wuri ɗaya sabida wani irin masifeffen sayin da ake tsula musu.
A hankali taja dogon numfashi kana ta fesar a hankali tayi lib.
Can cikin baccinta kuwa cikin wani ƙaton fili mai yalce da yashi fari ƙal-ƙal tana zaune bisa wani dutse tana fuskantar yamma kana daga bayanta kuma wani garden ne mai masifar kyau da girma babu kalan bishiya da sirran da baya ciki, wani irin ni'imtaccen iskane mai cike da ƙamshi furanni ke buso masu wata irin iska mai ɗan karen sanyi.
Gefen damanta ta juya ga mamakinta M Jameel ne zaune bisa wani dutse yana murmushi, da sauri ta juya gefen hagunta kuma, Adda Adama ce ta gani zaune bisa dutse tanata murmushi.
A can gabanta kuwa Mod....! *NO EDITING*
*Kuyi haƙuri sai yanzu na samu caji gashi ba editing. KUNSHA TYPING ERRORS*
By
*GARKUWAR MARUBUTA*
Moddibo ta hango zaune a gefen gabas yana fuskantar tata, bima'ana yana kallon yamma, zaune yake akan wani dutse mai masifar sheƙi kana wasu mutane biyu na tsaye gefen hagu da damansa,
Sannan da buta gabansa bisa alama Al'wala yayi domin farin yashin daya mamaye wajen daga gabansa a jiƙe yake, kana yana mai fidda wani irin ni'imtaccen ƙamshi maisa ɗan Adam lumshe ido. Baki ɗaya haske ya mamaye ilahirin filin wajen hakan yasa itada Moddibo suna fuskantar juna yayin da M Jameel da Adda Adama matar Baffan Umaru suma ke fuskantar juna.
Kana lambu dake can bayanta kuwa yake feso musu iskar yammaci dana lambun suka haɗu waje ɗaya daga sama kuma rana ne yayi Ja yana shirin faɗuwa.
A hankali ta sauƙe numfashi mai nauyi tare da lumshe idanunta.
Da sauri ta buɗe idanun nata, jin wani irin sassayan sautin dariya mai cike da shauƙi da Moddibo yakeyi.
Cike da mamaki duk suka zuba mishi idanu.
Yayinda Adda Adama ma tuni ta fara dariya mai sauti.
Ita kuwa Khausar haka nan taji jikinta yana tsuma tare da sakewa, da sauri ta juya ta kalli M Jameel ga mamakinta shima ita yake kallo, da idonshi ya nuna mata Moddibo yana mai yin lallausan Murmushi, da sauri ta maida kallonta kan Kekkyawar fuskar Moddibo, wacce tunda take a rayuwarta dashi bata taɓa ganin yayi dariyar da har haƙoransa na gaba zasu baiyana ba.
“Fatabarakallahu fih hasanil khaliƙeen”.
Ta furga a saman lips ɗinta, lokacin da ta sauƙe ƙwayar idanunta kan fuskar Moddibo, da sauri ta kuma lumshe manyan Idanunta sabida wani irin masifeffen sheƙi da ta hango sajenshi dake kwance lip-lip yanayi,
Sautin dariyarsa da har yanzu yake ne yasata saurin buɗe idanun.
“Subahanallah, tsarki ya tabbata ga Ubangiji da ya halicci wannan bawa ya kuma bashi waɗan nan haƙoran”.
Ta faɗa a fili lokacin da taga ƙyellin da haƙoransa keyi har yana ɗauke mata idanunta,
Lobgoɓar da kanta tayi bisa kafaɗarta.
Wani irin sassayan numfashi ta fesar tare da tsaida idanunta a kanshi.
Shi kuwa Moddibo dariya yakeyi mai sayyan sauti wanda yake da daɗin ji, har maƙolloton wuyanshi yana ɗan haurawa yayi sama kana ya dawo ƙasa.
Yayinda ya ɗaura tafin hannunsa kan ƙirjinsa.
Cikin tsananin dariyar ya samu ya ɗan tsagaita tare da furta.
“Astagfurillah watubu ilaik”.
Sai kuma ya ɗago ya kalli M Jameel lokaci ɗaya kuma ya sake sakin dariya mai sauti yana cewa.
“Astagafitillah Wayyo cikina”.
Cikin rage girman idanunta take kallon gashin girarsa dake kwance lip.
Jameel kuwa sai Murmushi yakeyi tare da girgiza kansa.
Yayinda Adda Adama ma dariyar takeyi harda riƙe ciki.
Ita kuwa Khausar gaba ɗaya ta kasa ɗauke idonta daga kansa.
A haka har rana tayi mudun kuyanƙi alamun yana gab da faɗuwa.
amma kafin ya faɗi saiya rabu kashi biyu.
Yayinda Khausar kuwa ke zaune tana fuskantar yamma hakan yasata ganin abin.
Atake hankalin ta ya tashi ganin yanda ranan ya rabu kashi biyu.
Ita kuwa Adda Adama hannu tasa ta dafe ƙirjinta tare da faɗin.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n yau mun shiga ukun mu ku dubi yanda ranar tayi fa!”.
Tana faɗin haka duk dariya da murmushin da sukeyi ya tsaya.
Moddibo kuwa daga inda yake zaune ya ɗaga kansa sama tare da juyawa bayanshi kana a hankali yace.
“Ya Salam ya ilahi ya mujabat da'awati meke Shirin faruwa”.
Cikin tsananin gigita da tashin hankali da firgici Khausar ɗin ta saki kuka mai cike da rauni tare da cewa.
“Innalillahi wa innailaihi raji'un, hasbunallahiwani'imanwakil, mun shiga uku”.
Sai kuma ta juyo ta kalli Moddibo da ya gyara zamanshi kana a hankali yace.
“Babu abinda zai faru wanda Allah bai sani ba, Insha Allah Ubangiji zai mana maganin duk kan abinda yayi tsanani”.
M Jameel kuwa kasa furta komai yayi sai hawaye dake kwaranya daga idanunsa.
ita kuwa Khausar ganin M Jameel na Hawaye kawai sai itama tashiga yin kuka amma ba mai sauti ba.
Cikin wani irin yanayin da bazai misaltuba Moddibo ya dubesa kafin yace.
“Haba J. Kamar ba namiji ba addu'a ya kamata muyi duk kan tsanani yana tare da sauƙi”.
Still dai M Jameel baice komai ba.
Shi kuwa Moddibo cikin sanyin jiki ya fuskanci Khausar cikin wata iriyar murya yace.
“Khausar tausayi na kike ji ne?”.
Cikin kwaranyar hawaye ta gyaɗa mishi kai tare da sakin raunataccen kuka mai cushe numfashi, lokaci ɗaya numfashin ta ya fara cushewa yana ɗauke wa, cikin yanayi wahalar neman numfashi taga Moddibo ya...!
Dai-dai lokacin kuwa ta farka daga baccin da takeyi ciki razana tare da kaɗuwa ta dafe kanta da takeji yana jujjuyawa.
Kana duk da sanyi da ake tsulawa a garin wani irin zufane ke tsastsafo mata ta ko ina.
Cikin sauƙe ajiyar zuciya, ta juya gefen hagunta ta karanta A'uziyya ƙafa uku kana ta canza hannun kwanciyar ta zuwa dama.
Sai dai sam baccin yaƙi zuwa mata, sai ta kama karatun Alqur'ani cikin sassayan sauti,
Cikin ikon Allah ta samu bacci ya kuma yin awon gaba da ita.
Baki ɗaya Wunin wannan ranan akasalance tayi koda abinci ta kasa ci haka zalika koda yawan surutu sai ta rage sosai mafarkin ya tsaya mata arai da zaran ta tuna irin mafarkin da tayi sai taji zuciyarta ta buga da ƙarfin gaske.
Da daddare cikin ikon Allah data karanta Alkur'ani mai girma tare da bin haddarta da Malam Liman ya bata sai taji sauƙin abin aranta duk da kuwa bawai ta daina jin tsinkewar zuciyar bane amma ya ragu sosai.
Da misalin ƙarfe takwas da rabi na dare Khausar suna zaune a farfajiya gidan Hajja Nana su uku ita Yaya Abba da kuma Dije suna hira jefi-jefi take sanya musu baki aciki daga ƙarshe ma ta miƙe tace zata je ta kwanta sai Dije ma ta miƙe ganin haka yasa Yaya Abba ya musu rakiya har gida.
Washe gari:Da safe still haka Khausar ta tashi bata da wani ku zari koda abinci ne ta kasa ci iyakacinta tasha Tea ko ruwan kunu sannan ta kasa faɗawa kowa irin mafarkin da tayi domin jikinta ya mutu sosai da mafarkin.
Da daddare ba kinta ɗauke da Sallama tashiga gidan Hajja Nana.
Asaman laɓɓa Hajja Nana ta amsa mata Sallamar tana binta da harara dan tunda taƙi markaɗa mata wake take jin haushi ta.
Ita kuwa khausar bata masan Hajja Nana nayi ba ta nemi waje ta zauna tare da kallon Hajja Nana tace.
“Yunwa nakeji ki bani abinci zanci”.
ta faɗa tana kallon ƙorenta dake jere guda goma sha Uku.
Harara Hajja Nana ta wurga mata tace.
“Gashi ki ɗauka ki ci”.
Kai Khausar ta gyaɗa tare da Matsawa jikin ƙoren tashiga buɗewa ɗaya bayan ɗaya tana dubawa saboda taga gidan Malam Liman anyanka kaji cikin Sa'a kuwa tana buɗe ɗayan taga Jan miyar dage-dage da kuma tuƙeƙƙen tuwon shinkafa.
Ta gyara zamanta tare da wanke hannunta ta fara cin tuwon cikin Mintuna kaɗan ta cinye tass sannan ta kuma janyo wani Ƙoren dan sosai take jin yunwa sannan bata wasa da cikinta dan ita dai ko ciwo bai cika hanata cin abinciba karo na forko kenan a rayuwarta da abu ya tsaya mata a rai har ya hanata cin abinci na kwana biyu son ta Tara yunwar shiyasa.
ta cinye ƙore biyun tas dan dama tuwon ba wani mai yawa ake samata ba tunda akwai yawan kanukan.
Hajja Nana kuwa juyawa tayi da mamaki ta kalleta kafin tace.
“Yanzu har kin cinye tuwon nan”.
Kai Khausar ta gyaɗa mata tace.
“Na cinye mana kuma yanzu ma ƙarawa zanyi dan yunwa nakeji rabo na da abinci tun shekaran jiya da daddare fa sai dai in ta Shan abu mai ruwa-ruwa”.
Taɓe baki Hajja Nana ta kuma yi tace.
“Toh bubbuga rumbu ga shican ki ƙara ki cinye duka ma in Kinga dama”.
Ta Faɗa tare da tura mata wani akoshin.
Ɗauka Khausar tayi kamar wasa ta cinye dake abincin ba wani da yawa ake sawa aƙoron ba dake sun san cewa ƙorenta da yawa mafi yawan lokuta ma loma ɗaɗɗaya takeyi ako wani ƙoren idan tayi loma sha uku ya wadatar mata a dai cikin tsohuwa ta kuma tsinci nama ta cinye to shiyasa ba'asa mai yawa.
Ita kuwa Hajja Nana ganin yanda Khausar ke cin abinci yasa tayi zaton gatse take mata ta harareta da faɗin.
“Mutum kamar jaki wannan ci haka ki cinye wannan ƙoren ki cinye wancan”.
Ta ida maganar tare da sake tura mata wani ƙoren.
Ita kuwa khausar ta