Showing 156001 words to 159000 words out of 188939 words
Chapter 53 - SAKAYYA Book 1 complete BY GARKUWA.txt
wallahi bamu sani ba barin idan Abbanku ya shigo zan tambaye sa muje muyi wa Umminsa jaje Ubangiji Allah ya bayyana shi Allah ya tsaresa aduk inda yake”.
Khausar kuwa kasa tsaida hawayen ta tayi cikin Muryan kuka tace.
“Ameen Mommy Ameen ya hayyu ya ƙayyum Allah ya bayyana Malam Jameel har kwana biyu kuma!?”.
Ta gumi Hajiya Bunayya tayi tare da marairaice fuska kana tace.
“Hakane kam wannan duniyar ta zama abin tsoro idan kana fama da talauci ka banu idan kayi wadata ɓarayi da ƴan Kidnapping su hanaka kwanciyar hankali da nutsuwa Allah dai ya kyauta”.
Ta faɗa tare da miƙewa ta fice ranta fess.
Baki ɗaya Wunin wannan ranan haka Mommy da Khausar suka yita cikin jimami da fargaba musamman Khausar ta gagara tsaida hawayen ta.
Moddibo kuwa yana fita daga sashen Innayi mota ya shiga tare da nufar gidan Abba yana isa ana kiran maghariba tare da Abba suka shiga Masallaci suka gabatar da sallah.
Acan ɓangaren Mommy kuwa bayan an idar da sallar Isha'i ta sanarwa da Lamiɗo suna san zuwa yiwa Ummi jaje nan yace ba damuwa ta kira Khausar da Hajiya Bunayya su fito bayan sun fito da kansa yayi Driving ɗinsu zuwa gidan Ummi.
Bayan sun isa.
Mommy ce agaba sai Khausar sai kuma Hajiya Bunayya bakinsa ɗauke da Sallama suka shiga dai-dai lokacin kuma maƙotansu suka fito.
Zaune suka samu Ummi kan 2sitter tana riƙe da Kur'ani Idanunta sun kumbura sun ƙanƙance yayin da Asma'u ke zaune gefenta hannunta riƙe da Carbi.
Cikin sauri Khausar ta ƙarasa kusa da Asma'u tare da riƙe hannun ta kana tace.
“Asma'u da gaske wai dagaske ansace Yah Jameel!?”.
Cikin zubda hawaye Asma'u ta gyaɗa mata kai kana tace.
“Khausar da gaske ansace Yah Jameel tun randa kikazo ya maida kin nan, har yanzu babu labarin sa yanzu kusan dare na uku kenan za ashiga”.
Khausar ma cikin zubda hawaye ta damƙe hannun Asma'u tare da cewa.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n”.
Kallon Ummi Hajiya Bunayya tayi tare da cewa.
“Ayyah Ummin Jameel Ashe abinda ya faru kenan toh Ubangiji Allah ya tsare Allah ya bayyana shi”.
Kai Ummi ta gyaɗa tare da faɗin.
“Ameen ya Allah Nagode”.
Mommy kuwa kafaɗar ta ta dafa kana tace.
“Ba komai Ummin Jameel kiyi haƙuri ki daina kukan nan ki riƙa yi masa addu'a Insha Allah Ubangijin zai bayyana shi”.
Cikin sauri Ummi ta share hawayenta kana tace.
“Nagode Mommyn Khausar Nagode³”.
Cike da tausayawa Mommy ke sake ƙarfafa mata guiwa.
Ahankali Khausar ta juya tare da kallon Ummi cikin Muryan kuka tace.
“Ummi Allah ya bayyanar da Yah Jameel insha Allah ba zasu samu nasarar cutar da shiba zamu tayi masa addu'a Allah ya karesa”.
Miƙewa Hajiya Bunayya tayi kana tace.
“Bari mutafi Alhj na jiran mu awaje yace a gaidaki".
Kai Ummi ta gyaɗa tare da cewa.
“Nogeda Allah ya saka”.
Sannan suka fita a coumpund suka haɗu da wasu matan sun shigo yiwa Ummi jaje bayan sun koma gida.
Baki ɗaya Khausar ta kasa nutsuwa kafin ta kwanta taje tayi alwala kana ta ɗauki Kur'ani tana ta karatu tare da tawassali dashi da niyyan Ubangiji ya bayyana M Jameel aduk inda yake.
Misalin ƙarfe goma na dare kamar lokacin da aka dauke M Jameel Moddibo dake gefen Abba ya miƙe da niyyar tafiya Akuma dai-dai lokacin wayar Abba dake gabansa ta hau ruri.
Atare Abba da Moddibo suka kalli wayar cikin sauri Abba yayi Picking call ɗin tare da kaiwa Kunnensa.
Daga ɗaya ɓangaren akace Alhj Bashiru mahaifin Jameel ko!?”.
Cikin sauri Abba ya gyaɗa kai tare da cewa.
“Eh nine nayi ta kiran layinku baya shiga”.
Cikin fusatacciyar murya Mutumin yace.
“Dama ce maka mukayi idan ka kira zai shiga?”.
Girgiza kai Abba yayi tare da faɗin.
“A'a to menene sharaɗin ku na biyu kaga ban faɗawa kowa ba!”.
Cikin bauɗaɗɗiyar murya Mutumin yace.
“Kuɗin fansa zaka biya shine sharaɗin mu na biyu”.
Kai Abba ya gyaɗa tare da cewa.
“To nawa kuke buƙata?”.
Kai tsaye mutumin yace.
“Milion ɗari biyu”.
Atsorace Abba ya dafe hannunsa aƙirji kana ya zare ido cikin tsanananin firgici yace.
“Milion ɗari biyu!?”.
Atare Hajiya Bunayya da Moddibo da maganar ya dakesu suka haɗa baki atare wajen cewa.
“Milion ɗari biyu?”.
Cike da gadara Mutumin yace.
“Toh idan ba zaka bada ba sai ka shirya karɓan gawar ɗan ka!”.
Cikin sauri Abba ya Girgiza kai tare da cewa.
“Kuyi hakuri dan Allah dan darajar Annabi kada ku kashe wayar”.
Cikin Yanayin ɓacin rai Mutumin yace.
“To ai mun riga mun faɗa muku abinda ake buƙata idan ka shirya gobe zamu sake kiran ka muji ko ka shirya”.
Yana gama fadar haka ya katse kiran...!
By
*GARKUWAR MARUBUTA*
*LITTAFIN SAKAYYAH NA KUDINE KO KIN GANSHI A WASU WURAREN DA BA CIKIN GROUPS NA DANA BUƊE NA SAKAYYAH BAto na satane, 1k ne kacal kuɗin littafin SAKAYYAH yar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci da salama babu haƙƙin kowa a kanki 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276, kiyiwa Allah da Manzonsa ku dena fidda min littafina, in dai kin san kin sayane dan ki turawa wasu, dan Allah ki gaya min in mayar miki da kuɗinki🙏🏻🙏🏻Dan Allah nace ba dan niba*
Isrnejny. Moddibo kuwa cike da mamaki da tsoro ya maimaita 200 Millions asaman laɓɓansa, he can't believe or imagine zasu iya tambayar wannan maƙudan kuɗin how cames kidnapper zasu tambayi kuɗin fansa kamar sun sace ɗan shugaban ƙasa.
Rintse idanunsa yayi tare da cije labɓansa na ƙasa lokaci ɗaya jijiyoyin kansa suka tashi sukayi ruɗu-ruɗu dasu.
Dafe kuncin Hajiya Karima tayi da hannunta duka biyu kana ta kyale baki tare da cewa.
“Ohh Allah ya kawo mu wani zamani ka haifi ɗa sannan wasu ƙartin banza da wofi su saka kasa ke sayan sa bafa Millions biyu ba, Ba ashirin ba, Ba hamshin ba, Ba ɗari ba, har Millions ɗari biyu sai kace abin Masifa ko dan sunyi zaton Jameel ɗan Aliko ɗan Gwate ne, shi, ka haifi ɗa kasha wahalar ciyar dashi shayar dashi tufatar dashi biya masa makaranta sannan ace ka sake siyan sa”.
Dafe kai Abba yayi da duka hannunsa biyu baki ɗaya ilahirin jikinsa rawa yake kar-kar-kar tamkar mazari yayin da idanunsa suka kaɗa sukayi jawur tamkar garwashi.
Dai-dai lokacin Hajiya Turai tashigo baki ɗaya tayi zuru-zuru da ita. Idanunta sun kaɗa sunyi jawur dasu ganin halin da Abba ke ciki yasa tace.
“A'a Alhj Lafiya Subhanallah”.
ta faɗa tare da nufar Bedroom ɗin sa ta da buɗe drawer ta ɗauko naganinsa ganin alamar hawan jinjinsa ne ya tashi tare da manna waya akunnenta bayan kamar second uku tace.
“Hello Dr Muktar dan Allah kazo yanzu ina ganin kamar hawan jinin Alhj ne ya tashi”.
Cikin raunin murya Abba ya ɗago kai ya kalleta tare da cewa.
“A'a ki bari ba sai Dr yazoba, ki bani maganin kawai”.
Kai ta gyaɗa kana cikin sauri ta zuba masa ruwa a glass cup ta miƙa masa tare da bara masa maganin karɓa yayi ya afasu abakinsa ya haɗiye.
Sannu a hankali ya fara maida numfashi sama-sama yana jin bugun zuciyarsa tare da sarawan da kansa keyi ya fara raguwa amma still hannunsa na dafe da kansa.
Ɗago Idanunsa yayi tare da kallon Moddibo daya zuba masa Idanu kana ya kalli gefen damansa Hajiya Turai ce durƙushe Idanunta cike da hawaye lumshe idanunsa yayi kana ya shiga tunani kwata-kwata kuɗin dake cikin account ɗinsa tsuran kuɗi, gaba da baya Million Sha biyu ne wanda yake tunanin da sun cika Ashirin zai bawa M Jameel saboda ya habɓaka Company daya bashi, da ƙarfi ya sake rintse idanunsa tare da dafe kansa tuno wa da yayi acikin Million Sha biyu ma akwai cikon kudin hajji nashi da na matansa da zai cika ta, baki ɗaya tunaninsa ya tushe ina yasan zai fara kai kadaransa asiya masa su cikin gaggawa kuma da daraja sannan abashi kuɗin cikin tsanananin tashin hankali yace.
_“Ya Ilahi ya lillahi ya mujibud da'awati ya hayyu ya ƙayyum bi rahma tika astaghisu lahaula wala ƙuwwata illa billahil aliyul azim”_.
Abin da yake maimaitawa kenan asaman laɓɓansa.
A hankali Moddibo ya matsa kusa dashi cike da tausayawa yace.
“Colm down Abba ka nutsu ka kwantar da hankalin ka everything will be fine by the grace of Allah”.
Cikin sauri Abba ya riƙo tsintsiyar hannun Moddibo tare da cewa.
“Aliyu Why should I find 2 hundred Millions?”.
Aliyu mai zan fitar in sayar dashi cikin gaggawa in Samu kuɗi?.
Aliyu bani da ko Million ashirin acikin account ɗina,kaji kuɗin da suka kira fa”.
Kallonsa kawai Moddibo keyi cike da tausayinsa Cikin raunin murya Abba ya cigaba da cewa.
“Aliyu kwanan nan na cire kuɗi na siya filin nan kuma shima gaba ɗaya filin dana siyeshi 25 Million ne da ace suna nan kaga kuɗin akwai ɗan gwaɓi ahannu na”.
Sai kuma ya sauƙe numfashi tare da sake damƙe hannun Moddibo acikin nasa kana yace.
“Ina da kadaran da zan iya sayarwa amma ta yaya awani lokaci zan samu ace ansiya se anbani kuɗina sannan na wane”.
Kasa ƙara sa maganar yayi kawai saiya janye hannunsa dake cikin na Moddibo ya rufe fuskarsa yana mai furta.
_“Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha Hasbunallahu wani'imal wakin La'ilaha Illah anta subhanaka Inni kuntu Minal zhalimin”_.
Hajiya Karima dake dafe da kuncinta ta ɗago kai tare da kallon Abba kana tace.
“Alhj ai dole dama za ayi ciniki dasu idan yaso sai anemi ragi”.
Moddibo kuwa kai ya girgiza tare da kallon ta kana yace.
“Idan da ace sunzo mana da sauƙi da kuma Imani acikin zancen zamu iya hakan amma fa kiga yanda idan sunyi magana sai su yanke mana kiran baza su tsaya suji ta bakin muba sai sun kwana ɗaya ko biyu kafin su sake kiran mu”.
Da ƙarfi ya runtse Idanunsa tare da cije labɓansa na ƙasa kana ya cigaba da cewa.
“Basa tunanin shin wani irin yanayi ko hali zamu kasance aciki ba yaya zamuyi, da wannan kuɗin da suka kira”.
Ya ida maganar cikin raunin murya.
Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe kana yace.
“Nima abinda nake tunani kenan idan nace musu babu zasu iya yiwa Jameel Illah”.
Girgiza kai Moddibo yayi tare da cewa.
“Abba kar ma kace musu babu sai muyi ƙoƙari duk yanda zamuyi mu haɗa kuɗin nan muyi ƙoƙari mu basu”.
Ahankali Abba ya furta.
“Ya Salam”.
Hajiya Turai kuwa cikin matsanancin kuka ta kalli Moddibo kana ta maida kallonta kan Abba tare da cewa.
“Ai abayar ɗin yafi Alhj duk wani abinda kake dashi ka sashi akasuwa kawai asamu asayar akarɓo Jameel meye fi maka Jameel aduniyar nan Alhj, kawai asayar da komai akai musu kuɗin akarɓo shi”.
Cikin sauri Hajiya Karima ta kalli Hajiya Turai kana tace.
“Kamar ya asaida komai Hajiya Turai kifayi tunani akan abinda kike faɗa idan aka sayar da komai muku mu murayu aya kenan?”.
Sai kuma ta maida kallonta kan Abba kana ta cigaba da cewa.
“Alhj ya za ayi ɗauki irin wannan maƙudan kuɗin amulmula abasu kaga idan wa'annan ƴan Kidnapping din da suka kinnafe Jameelu sunji dadi an basu abinda suke so to wasu kuma ai sauran ƴaƴan zasu zo su kwashe”.
Ta ida mgnar tare da sauke numfashi kana ta cigaba da cewa.
“Suma sauran ƴaƴan sai aje a kinnafesu su kuma idan kuɗin da za'a fanshe su bai rage ba ya za ayi kenan.
A gaskiya wannan ba shawara bace ace za aɗauki wannan maƙudan kuɗin abasu sai kace ba asha wahala wajen ne mansu ba”.
Ahankali Moddibo ya ɗago kumburarrun Idanun sa ya kalli Hajiya Turai dake dafe da ƙafaɗan Abba tana sharɓan kuka kana ya maida kallonsa kan Hajiya Karima data zabga tagumi.
Girgiza kansa yayi.
Sosai hankalin Abba yayi masifar tashi yama rasa wani irin tunani zaiyi Aransa ya gaza tantance abin cewa.
Sannu a hankali idanunsa suka fara lumshewa jikinsa ya saki baya yaja tare da gyara kwanciyarsa akan 3sitter tare da lumshe idanunsa Atake Bacci ya ɗauke sa sabida magungunansa da Hajia Turai ta bashi yasha sun jiƙa sunbi jininsa.
Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da miƙewa kana yai musu sai da safe tare da ficewa yashiga motarsa kai tsaye gidan Ummi ya nufa.
Awaje yayi Parking motarsa kana ya fita iska na kaɗa ko wani sashe na jikinsa ahankali ya murɗa handle din ƙofar ya tura bakinsa ɗauke da sallama ya shiga.
Idanunsa suka sauƙa akan Ummi dake zaune kan Sallaya hannunta riƙe da Carbi yayin da Malam Ahmad ke zaune gefenta yana rarrashin ta.
Ganinsa yasa Ummi ta ajiye carbin dake hannunta kana ta maida hankalinta kansa,Anutse Moddibo ya ƙara sa tare da miƙawa malam Ahmad hannu sukayi musabaha kana ya koma ya zana agaban Ummi.
Jin Sallamar sa yasa Asma'u da Bashir suka fito daga Bedroom tare da zama gefe da gefen Ummi ya zamana sun sashi a tsakiya kana cikin raunin murya suka gaishesa atare zuwa lokacin shima Bashir kuka yake sosai duk yayi zuru-zuru.
Ahankali Ummi ta zubawa Moddibo Idanu kana cikin sanyin murya tace.
“Babana ya akayi sun sake kira?”.
Kai ya gyaɗa tare da sun kuyar da kansa ƙasa kana yace.
“Eh”.
Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da cewa.
“Me suke buƙata?”.
Still Kansa na ƙasa yace.
“Ummi kuɗi suke so”.
Numfashi ta fesar kana tace.
“Kuɗi suke so?”.
Kai ya gyaɗa amma bai ce komai ba.
Cikin tsira masa ido tace.
“Kuɗi kamar nawa suke so?”.
Cikin rauni ya kalleta kana ya kalli malam Ahmad, Asma'u da Bashir ya fesar da numfashi tare da cewa.
“Ummi kuɗin suna da yawa kuɗin da suke buƙata sun wuce zatonmu”.
Gyara zama tayi kana tace.
“Toh Meye amfanin kuɗin mahaifinsa?, Meye amfanin kuɗin Babansa?,Menene amfanin duk tattalin da yake yi!?”.
Girgiza kai Moddibo yayi kana yace.
“Ummi kuɗin sun wuce tunanin mai tunani!?”.
Ɗa gowa Ummi tayi tare da tsira masa ido kana tace.
“Kamar nawa suke buƙata Babana?”.
Cikin raunin murya da alamar sarewa Moddibo yace.
“Ummi har Million ɗari biyu suke buƙata”.
Cikin wani irin yanayi mai cike da rauni, tsoro, mmki Ummi taja ajiyar zuciya kana ta maida kanta ta jingina da jikin kujeran da Malam Ahmad ke zaune tare da lumshe Idanunta kana Muryanta na rawa tace.
“Ƙarya sukeyi ba kuɗin suke so ba so suke su kashe min Jameelu lallai Mahaifinsa mai arziƙi ne amma be kai matakin da za'a matsesa lokaci ɗaya ace ya fito da Million ɗari biyuba, kawai dai yaudarace suke mana anya ma Jameelu yana raye kuwa?”.
Cikin sauri Moddibo ya girgiza mata kai kana yace.
“Yana raye Ummi ina ji ajikina J yana raye kuma na faɗa miki munyi magana dashi”.
Girgiza kai tayi tare da cewa.
“Yau da suka kira kunyi magana dashi?”.
Shiru yayi yana kallonta amma baice komai ba.
Kallonsa Ummi tayi cikin muryan kuka tace.
“Babana ka faɗa min gaskiya tsakanin ka da Allah yau kunyi magana dashi?”.
Girgiza mata kai Moddibo yayi tare da faɗin.
“Ummi ba muyi magana dashi ba, amma naji muryan J ƙasa-ƙasa yana cewa Abba abasu duk abinda suke so”.
Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare da rintse idanunsa kana tace.
“Babana ka tabbatar gaskiya kake faɗa min?”
Jinjina kai Moddibo yayi kana cikin sanyin murya yace.
“Wallahi Wa rabbul Khaba Ummi naji muryan J ƙasa. yana magana bawai sun bashi bane amma naji yana magana”.
Kuka Asma'u da Bashir suka fashe da shi atare kana lokaci ɗaya suka haɗa baki wajen cewa.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n ya Allah ka kuɓutar da Yah Jameel Ubangiji kada ka basu ikon cutar dashi ya Allah kaine gatanmu Yah Jameel shine ka wakilta da isar mana gatanmu ya Allah ka karesa da karewaka”.
Numfashi Malam Ahmad ya fesar kana cike da tausayawa yace.
“Asma'u ba kuka ya kamata kuyi ba addu'ar mu Jameelu ke buƙata idan kuna kuka ya kuke so Ummin ku tayi?”.
Cikin sheshsheƙan Kuka Asma'u tace.
“Abba Yah Jameel fa Yah Jameel yana cikin mawuyacin hali Abba kaji fa maƙudan kuɗin da suke buƙata Abba ya za'ayi mu samu irin wannan kuɗin mu karɓo Yah Jameel Abba Ina tsoron kada su cutar mana dashi”.
Girgiza kai Malam Ahmad yayi cikin sanyin murya yace.
“Insha Allah da izinin Ubangiji babu abinda zai samu Jameelu, ko wani bawa da kalar tashi ƙaddaran tun kafin a haifi Jameelu Ubangiji ya zana masa ƙaddaransa muyi masa addu'ar Allah ya sauƙaƙa mana zafin ƙaddararsa”.
Jinjina kai Moddibo yayi yana jin wani irin azabebben zafi aƙirjinsa.
Kallon Moddibo Malam Ahmad yayi kana yace.
“Moddibo mai Yakamata ayi acikin wannan al'amarin!?”.
Moddibo da kansa ke ƙasa ya ɗago ya kallon Malam Ahmad a hankali yace.
“Malam abinda yakamata kawai afara cuku-cukun neman kuɗin nan sai muga abinda zai kasance”.
Girgiza kai Ummi tayi still tana jingine da jikin kujera tace.
“Babana ina zamu samu kuɗin nan Million ɗari biyu fa da ace Million biyu suka ce koni kaina ma zan bada su”.
Ta faɗa tare da ɗaukar wayarta tayi checking balance kana tace.
“Gashi yanzu anan ina da Million ɗaya da dubu ɗari huɗu da hamsin da ɗaya sannan kuma ba matsala gobe in Allah ya kaimu zan tafi cikin.
Taraba zan kai gwala-gwalaina”.
Sai kuma ta ɗan tsaya, jin numfashin ta na yankewa, da ƙarfi ta fizgo numfashin tare da cije labɓanta na ƙasa hawaye cike da Idanunta murya na cike da rauni ta cigaba da cewa.
“Zan saida su inga nawa zan samu ajikinsu zan haɗa harda na Asma'u sannan, motata itama zan saidawa muga nawa zan samu awurina”.
Jingina kai Malam Ahmad yayi kana cikin sanyin Murya yace.
“Har gidan nan ma asashi a. Kasuwa asayar dashi”.
Kallonsa Moddibo yayi tare da girgiza kai kana yace.
“A Malam ayi haka”.
Kai Malam Ahmad ya gyaɗa kana yace.
“Asiyar Moddibo menene Jameelu baiyi mana ba aduniyar na, kasancewar sa atare damu shiyafi mana komai”.
Ahankali Ummi ta ɗago kanta tare da tsira masa ido hawaye na bin kuncinta ta sani fili dai filinsa ne halalinsa mallakinsa, amma baki ɗaya ginin dake ciki Jameel ne ya musu bayan yasa an buge tsohon ginin taɓon.
Girgiza kai tayi cikin rauni tace.
“A'a ba sai anyi haka ba bari muga abinda Mahaifinsa zai samu”.
Girgiza kai Malam Ahmad yayi tare da kallon Asma'u da Bashir da har zuwa lokacin suke kuka a hankali ya fesar da numfashi tare da cewa.
“Ni dai na sadaukar da wannan gida ga.
Jameelu wallahi na yafe masa shi duniya da lahira na amince asa shi akasuwa muddin za a samu masu siya, to asa shi akasuwa mu samu muga aƙalla dai awajen mu ace an samu Million goma kuɗin zaifi gwaɓi”.
Sun kuyar da kai ƙasa Ummi tayi hawaye masu masifar zafi suka zubo mata.
Hannunta Moddibo ya riƙe cikin sanyin murya yace.
“Ummi dan Allah ki daina wannan kukan idan kina kuka muku ma ya zamuyi Ummi babu abinda J ke buƙata awajen mu face addu'a ganin ki awannan yanayin naya sake raunatamana zuciya”.
Kai Malam Ahmad ya gyaɗa kana