Header Ads
Showing 108001 words to 111000 words out of 188939 words

Chapter 37 - SAKAYYA Book 1 complete BY GARKUWA.txt

Ads the beginning of article before Image
Ads at the middle of Article

da watsa masa wani kallo.
Tsuke fuska yayi tare da marairaice murya kana yace.
“Haba My Wife mai yasa zaki min haka kibari mana in sinsina gashinki naji wannan Sanyayyar ƙamshin da yake fita”.
Sake tsuke fuska Khausar tayi tare da tura ƙaramin bakinta kana tace.
“A'a nidai Yaya Naseer ka bari bana so”.
Langwaɓar da kai yayi kana cikin wata murya mai ɗauke da zallan shauƙi da sha'awa yace.
“Toh na bari ai yanda kike so haka za ayi hope dai kina sona?”.
Ƙasa tayi da kanta tana wasa da zara-zaran yatsun hannunta amma ba tace komai”.
Sake narkar da muryarsa mai ɗauke da zallan sha'awa kana yace.
“Dan Allah kice kina ƙaunata ko zanji daɗi kinsan na daɗe ina dakon soyayyarki azuciyata, Khausar kece rayuwata bazan iya rayuwa idan babu keba kece muradin raina, kece fitilar dake haskaka rayuwata ina miki sahihiyar ƙauna wanda bana yiwa kaina”.
Lumshe idanunsa yayi tare da kallon fuskarta zuwa ƙirjinta kana yace.
“Kece wacce zuciyata keda burin kasancewa da ita, kece farin cikina muddin ban mallakeki amatsayin matata ba bazan taɓa samun nutsuwa ba, My Khausi saboda ke nadawo Nigeria ba dan keba wlh bazan dawo ba.
Duk yawan kyakkyawawan matan dake India babu wacce ta burgeni ta kuma kwanta min arai sai ke duk kyawunsu kallon maza nake musu!”.


Ita dai Khausar batace komai ba sai wasa da take da yatsun hannunta.
Naseer kuwa karyar da murya yayi tare da lashe lips ɗin sa kana yana binta da wani shu'umin kallo ya lumshe Idanunsa tare da cewa.
“Khausar inada burin mallakar ki ke kaɗai ce zaki iya sarrafani, akan shimfiɗata sannan ke kaɗai ce zaki iya bani farin ciki akan shimfiɗa ta”.
Lokaci ɗaya Khausar ta sake haɗe fuska cike da takaici tarasa Meyesa Naseer yake mata wasu irin maganganu marasa kan gado.
Al'amarin Naseer yafi kama da irin mayaudaran mazan nan na zamani.
Shirune ya ratsa motar har suka isa ƙofar gidansu Ummi yayi Parking daga waje, Ahankali Khausar ta ziro ƙafanta da suka sha jan lalle.
Dai-dai lokacin Asma'u ta iso.
Ganin Khausar yasa ta faɗaɗa fara'ar fuskarta kana tace.
“A'a Khausisi, Lelewal tawa”.
Murmushi Khausar ta sakar mata tare da gyara zaman gyalenta kana tace.
“A'a ina kika je?”.
Asma'u na gyara wuyan hijabinta ta kalli Khausar tare da cewa.
“Wallahi kitso naje”.
Jinjina kai Khausar tayi kana tace.
“A lallai dai kam”.
Juyawa tayi ɓangaren da Naseer ke tsaye ya zuba mata ido ɗauke kanta daga garesa tayi kana ta mayar da kanta kan Asma'u tare da cewa.
“Asmeey ga Uncle Naseer”.
Sai alokacin Asma'u ta ganesa da murmushi afuskarta tace.
“Laa Uncle Naseer Mutanen India fatan kazo lafiya. Khausar tace min kadawo toh Allah yatemaka”.
Kai ya jinjina cike da Iyayi kana yace.
“Wallahi na dawo amma fa saboda My Khausi nazo, ana ɗaura mana aure kuma zan ɗauki abata mukoma can”.


Murmushi Asma'u tayi tare da kallon Khausar da ta tsuke fuska kana tace.
“Toh Allah ya tabbatar mana da alkhairi”.
Da sauri ya amsa da.
“Ameen”.
Khausar kuwa hannun Asma'u ta riƙe zasu shiga gida.
Da sauri yace.
“Ya dai haka My Khausar ba zaki tsaya mu ɗanyi hira ba?”.
Ataƙaice ta girgiza masa kai tare da cewa.
“A'a”.


Shafa kansa yayi tare da lumshe idanunsa kana yace.
“Toh ƙarfe nawa zaki koma gida sai inzo in ɗauke ki”.
Babu walwala atare da ita tace.
“A'a ba sai kazo ba Uncle Naseer zan koma”.
Wani irin zare ido yayi tare da girgiza kai kana yace.
“A'a My Khausi kar ki min haka.
Ni dai ki faɗa min ƙarfe nawa zanzo ɗaukarki”.
Ƙaramin tsaki taja aranta tare da cewa wannan mutumin ya fiye naci afili kuma juyawa tayi ta kallesa tare da cewa.
“Toh ka dawo ƙarfe shida na Yamma”.
Kai ya gyaɗa tare da cewa.
“Toh shikenan My Wife sai nazo”.
Ya ida maganar tare da shigewa motarsa yaja.


Bayan sun shiga cikin gida Khausar ta juya tare da kallon Asma'u kana tace.
“Ya dai naga kamar Ummi bata nan?”.
Kai Asma'u ta gyaɗa tare da cewa.
“Eh Ummi ta tafi gidan Innayi. Ni kaɗai ce sai Bashir dana bari yana mana gadin gidan shiyasa ma ana gama min kitson na dawo.
Jinjina kai Khausar tayi kana tace.
“Ayyah yayi kyau”.
Kai tsaye Bedroom din Asmau suka shiga fridge Asma'u ta buɗe ta kawo mata drinks da Fruit.
Kallon Friut ɗin Khausar tayi tare da zabga ta gumi.
Zama Asma'u tayi daga gefenta cike da kulawa tace.
“Ya dai Khausar tunanin me kike?”.
Ajiyar zuciya Khausar ta saki tare cire gyalenta ta ajiye kana ta kalli Asma'u tare da cewa.
“Ni wallahi lamarin Uncle Naseer ya fara damuna”.
Asma'u na ninke hijabin data cire ta kalli Khausar tare da faɗin.
“Mai yafaru?”.
Ajiyar zuciya Khausar ta saki tare da lumshe Idanunta kana tashiga zayyanewa Asma'u abubuwan daya yima tun daga zuwansa har yanzu daya kawota kana ta ɗaura da cewa.
“Asma'u Uncle Naseer yana bani tsoro abubuwan da yake gwada min sun fi kama dana mayaudara idan yana wani abun tamkar yana da wani nufi akaina, sannan yana yawan nuna zalamarsa akaina, ya rinƙa wani abu kamar maye!”.


Dariya Asma'u tayi tare da cewa.
“Wataƙil tsanananin son da yake miki ne kike ganin kamar haka, kinga tun kina ƙarama kamar da wasa ya fara ce Miki matarsa har gashi girma yazo wataƙil tsananin soyayya ne sannan kinga ya zauna a ƙasar da al'adun mu ba ɗaya dana suba kinga ƙasashen India wannan sai ahankali runguma da sumbata basu ɗauke shi abakin komai ba may be shiyasa kike ganin yake miki haka kuma kinga ai ya riƙa dole zaiso mace”.
Ajiyar zuciya Khausar ta sauƙe tare da furzar da iska mai zafi kana tace.
“Anya kuwa Asma'u abin nasa is too hight ɗazun fa agaban Mommy saura kaɗan ya rungumeni saida na kauce”.
Dafe kunci Asma'u tayi tare da kallon Khausar da fuskarta ke ɗauke da alamun damuwa kana tace.
“Toh tunda har haka ne ki kiyaye al'amarin sa”.
Ajiyar zuciya Khausar ta saki tare da lumshe Idanunta kana tace.
“Zan kiyaye insha Allah amma gaskiya ya fara bani tsoro baki ɗaya al'amarin sa azalamance yake”.
Jinjina kai Asma'u tayi tare da cewa.
“Amma duk da haka yana sonki”.
Kai Khausar ta gyaɗa kana ta buɗe Idanunta dake lumshe tace.
“Na sani Uncle Naseer na ƙaunata, amma kuma wani lokaci soyayyar tafi kama da Sha'awa”.
Girgiza kai Asma'u tayi tare da cewa.
“No Khausar kada ki fassara shi da haka, sannan kinga yanzu lokaci yayi da zaki bawa Uncle Naseer dama kinga dama ga Maganar da Hajja Nana tazo da ita cewa kina gama Secondary school za ayi batun Aurenki kinga yanzu munzo gangara koma ince mungama kawai”.
Shiru Khausar tayi tare da lumshe Idanunta tana jin wani iri azuciyar ta.


Asma'u ta cigaba da cewa.
“Sannan kin gani tayi miki maganar Yayanki Aliyu idan har baki amince da Naseer ba kika fitar dashi amatsayin wanda kike soba dole Yaya Aliyu za'a liƙa miki, kuma kinga Yaya Naseer tunda ansan Asalin sa sannan ansan komai nasa, kuma ke kanki kinsan yana masifar sonki”.
Ƙaramin tsaki Khausar taja tare da kallon Asma'u kana tace.
“Kayya Asma'u Asalin nasa har wani kyau gareshi!?
Mahaifiyarsa fa ƙanwar Gimbiya Dadu ce Uwar su ɗaya ubansa ɗaya, kuma duk ɗabi'u da hallayar Gimbiya Dadu babu wanda mahaifiyarsa ta bari, sannan kuma shine ɗan Auta wajenta Ni Wallahi tsoron su na nake ji wallahi nama fi tsoron mahaifiyarsan”.
Ajiyar zuciya ta sauƙe kana ta cigaba da cewa.
“Amma shi Uncle Naseer bashi da matsala Saboda zuciya nason mai kyautata mata, shi kuma tun ina ƙara ma yake nunawa kowa cewa. Ni ta da bance ni ta musamman ce awajensa, na ɗaukesa ne tamkar wani sashina amma banjin Uncle Naseer awani mataki na daban sannan batun Yaya Aliyu kuwa gaskiya saidai Hajja Nana tayi duk abinda zatayi, amma ni bazan Aure shiba babu ta yanda zanyi na aureshi”.
A hankali ta furzar da iska mai zafi daga bakinta kana ta kalli Asma'u da itama ita take kallo.
Idanunta ta lumshe cikin sanyi murya tace.
“Ni inaji azuciya ta ina da muradin da nake da ita na, musamman da nake buƙata inada muradin da nake so Asma'u ina da wani abun da nake so, wanda ni kaina bansan menene ba.
Amma Uncle Naseer ba irin Nature da nakeso ajikin namiji yake dashi ba dama yanada ilimi Addini kamar Yah Jameel ne to da ya tsarkaka, dama ace ɗabu'unsa irin na Yah Jameel ne da ya cikemib ko wanne gurbi”.
Ajiyar zuciya Asma'u ta sauƙe kana tace.
“Allah ko?”.
Tayi mgnar a fili yayinda zuciyarta ke saƙa wasu zantukan, ita kuwa Khausar kai kawai ta gyaɗa mata.
Cikin sauƙe numfashin Asma'u tace.
“Allah ya mana zaɓi mafi alkhairi dai”.
Cikin lumshe ida Khausar tace.
“Amin”.
Hira suka cigaba dayi, ƙarfe biyar dai-dai Khausar ta miƙe tare da ɗaukan gyalenta ta yafa kana ta kalli Asma'u tare da cewa.
“Asma'u Ni zan tafi”.
Saurin Kallonta Asma'u tayi tare da cewa.
“Toh ba kince sai ƙarfe shida zaki tafi ba?,Kuma ina Uncle Naseer zai zo ya ɗauke ki!?”.


Baki Khausar ta taɓe kana tace.
“Guduwa zanyi kafin yazo ɗin dai, ai shiyasa nace masa shida kinga yanzu biyar zan tafi”.
Murmushi Asma'u tayi tare da cewa.
“Toh idan yazo fa?”.
Ka faɗa Khausar ta ɗage tare da taɓe baki kana tace.
“Sai kice masa na tafi”.
Ta ida maganar tana ficewa da sauri.
Asma'u tabi bayanta dan yi mata rakiya.


Misalin ƙarfe shida saura kwata Naseer yayi Parking aƙofar gidansu Asma'u tare da danna Hong.
Asma'u dake sauraran zuwansa ta sanya hijabi ta fita zaune ta samesa acikin mota kana tace.
“Bata daɗe da tafiya da taga iska ya taso”.
Kai ya gyaɗa tare da cewa.
“Nagode”.
Kana ya figi motarsa yabar layin kai tsaye gidansu Khausar ya nufa lokacin daya isa ankira maghariba direct masallaci ya wuce ya gabatar da sallah kana ya wuce gidan kai tsaye sashen Gimbiya Dadu ya shiga.
Shigarsa ba daɗewa Haiydar ya shiga bakinsa ɗauke da Sallama kana ya gaishesu tare da ajiye kulan abincin Gimbiya Dadu.
Har ya juya zai fita.
Naseer ya kallesa tare da cewa.
“Please Haiydar kace da Khausi tazo zamuyi hira”.
Kai Haiydar ya gyaɗa kana yace.
“Toh Uncle Naseer sannan ya fita”.
Kai tsaye masallaci ya wuce sai Misalin takwas saura kwata ya koma sashen su bakinsa ɗauke da Sallama.


Khausar dake zaune kan 1sitter sanye cikin Neavy blue riga da wando na bacci mai santsi wanda ya sauƙa har ƙasa rigar kuma mai hannun Spaghetti ne kanta sanye da hular Net jikinta na fitar da sanyayyan ƙamshin tularen ta yayin da hannunta ke riƙe da wayar Mommy tana latsawa.
Da sauri Haiydar ya kalleta tare da cewa.
“Addah Khausar na manta ban faɗa miki ba, ɗazu kafin na wuce Masallaci Uncle Naseer yace. In faɗa miki kije ki same shi a sashen Gimbiya Dadu yana son ganinki”.
Nanda nan Khausar ta canza fuska tare da cewa.
“A falon Gimbiya Dadu kuma!?”.
Harara Mommy ta watsa mata kana tace.
“Toh cin yeki Gimbiya Dadu za tayi ko kuma me Ni nalura wani shan ƙamshi kike yiwa Naseer fa, idan kinsan bakya sonshi ki fito fili ki faɗa, sannan ki fito da wanda kike so, tun kafin kakar ki tazo ta buwayemu da batun Aurenki.
Kinga dama ta ajiye target ne kina gama Secondary school magana ya ƙare za azo ayi miki aure”.
Ajiyar zuciya ta sauƙa kana ta cigaba da cewa.
“Idan kuma kinƙi baki da hujjar da zaki ƙi Auren Aliyu, dole kibi zaɓin ta dan haka ma gwara ki tsaida zuciyarki kisan me kike ciki don in duniya duk zasu taru babu mahluƙin da zai hana batun wai kin gama secondary School za'ayi miki aure, tunda har Hajja Nana ta rantse, dan haka gwara kawai ma ki tsaida zuciyarki, ki fidda mijin da zai iya barinki kici gaba koda kinyi aure, kuma da fidda wanda kike sone, zamu samu hujjar nuna mata kinada wanda kike son”.


A hankali Khausar ta janye idonta daga kallon Mommy kana tace.
“To amma ni gaskiya ba zanje.
Falon Gimbiya Dadu ba”.
Ɓata fuska Mommy tayi babu walwala atare da ita tace.
“Maza ki wuce kije idan ita kura ce to ta cinye ki”.
Miƙewa Khausar tayi badan ranta yaso ba sai dan ganin yanda Mommy ta ɓata rai yasa ta ɗauki hijabinta dake fitar da ƙamshi sanya kana ta fice.


Acan ɓangaren su Moddibo kuwa zaune suke aɗakin Innayi shi da M Jameel bayan sun kammala cin abinci Anutse ya miƙe tare da kallon Innayi da suke magana da M Jameel ya gyara tsayuwar sa tare da cewa.
“Innayi saida safe”.
Kallon sa M Jameel da mamaki afuskarsa yace.
“Zaka je ka kwanta fa kace?”.
Kai Moddibo ya gyaɗa tare da lumshe idanunsa kana yace.
“Eh”.
Kai M Jameel ya gyaɗa tare da faɗin.
“Ok nima zan tafi gida”.
Ahankali Moddibo ya buɗe Idanunsa dake lunshe kana yace.
“Mu kwana anan mana tunda har ƙarfe takwas tayi”.
Girgiza kai M Jameel yayi tare da miƙewa kana yace.
“A'a ina so Inje gida”.
Kallon yanayin fuskarsa Moddibo yayi tare da cewa.
“Dan Allah mu kwana mana”.
Ataƙaice M Jameel yace.
“A'a tafiya zanyi”.
Ajiyar zuciya Moddibo ya sauke tare da cewa.
“Toh shikenan ni zanje in kwanta”.
Ya Ida maganar tare da ficewa.
Da kallo Innayi da M Jameel suka bisa har ya ɓacewa Kallonsu.
Moddibo kuwa yana shiga falonsa yayi saurin yarfe hannunsa tare da jan tsaki tare da jan numfashi kamar wanda yaci yaji lokaci ɗaya lips ɗin sa suka kama rawa cikin yanayin damuwa ya dafe kansa tare da cewa.
“Ya salam³,Wannan wani irin al'amari ne meke mai wuyar ɗauka haka?”.
Cikin mutuwar jiki ya wuce kichen tare da ɗaukan Cup ya ɗauraye ya zuba ruwan Tea kana ya yanka lemun tsami ya matse sannan ya zuba zuma ya kafa kansa ya shanye tass, ajiye Cup ɗin yayi ya fita zuwa Bedroom ɗin sa yana shiga ya kwanta ko minti ɗaya baiyi da kwanciya ba yayi saurin miƙewa ya zauna cikin sauri ya sake komawa ya kwanta tare dayin ruf da ciki cikin wani irin yanayi yasanya hannunsa duka biyu ya danne mararsa saboda wani masifaffen harbawa da yakeyi.


Acan ɓangaren Gimbiya Dadu kuwa cikin sanyi jiki Khausar ta buɗe ƙofar falon tare da Sallama tana shiga ta...!


*Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci da salama babu haƙƙin
SAKAYAH


20


🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇




Ujnr. Tana shiga ta sauƙe numfashi ganin babu. Gimbiya Dadu, falon shiru ba kowa sai Uncle Naseer dake zaune kan 3sitter yana riƙe da system akan cinyarsa da kuma wayarsa.
Yana ganinta yayi saurin rufe system ɗin kana ya zira wayarsa acikin aljihu tare da tsira mata idanu afili ya furta.
“Wowww Masha Allah kinsha kyau My Dear”.
Batare da tace komai ba ta ƙara sa shiga falon tare da yiwa kanta masauƙi akan 1sitter.
Tsuke fuska yayi tare da zuba mata idanu kana yace.
“Meyesa ba zaki zauna akusa dani ba My Khausi?”.
Kallonsa tayi da lumsassun idanunta kana da alamun bacci acikin Muryanta tace.
“Unclr Naseer nan ma yayi”.
ta ƙarasa maganar tana mai lumshe Idanunta.
Ido ya tsira mata yana kallon yanda ta lumshe sexy Eyes ɗin ta miƙewa yayi tare da dawowa kusa da ita ya zauna a hannun kujeran, yana shaƙan daddaɗan ƙamshin turarenta, Khausar kuwa jin alamu sa akusa da ita yasa tayi saurin buɗe Idanunta dake lumshe kana ta miƙe da niyyan barin wajen.


Cikin hanzari ya sanya tafin hannunsa dake ɗauke da zoben azurfa ya riƙe nata yana binta da wani mayataccen kallo.
fuskarta ta yamutsa cikin ɗaure fuska kana da rashin walwala tace.
“Me haka Uncle Naseer?”.
Langwaɓar da kai yayi tare da tsaida idanunsa cikin nata kana ya karyar da murya tare da faɗin.
“Guduna zakiyi?”.
Kai ta girgiza masa tare da lumshe Idanunta jin bacci na fusgarta kana tace.
“A'a ba gudunka nake ba kawai dai ai baidaceba”.
Karyar da muryarsa yayi tare da yi mata kallon Up and down kana yace.
“Toh ki zauna anan ni dodone, ko kuma cinye ki zanyi mai yasa kike min haka ne Khausar”.
Kai ta girgiza tare da gyara hijabinta kana tace.
“Bai dace bane Uncle Naseer haka baiyi ba ni ka sakar min hannu”.
Wani kallo ya watsa mata kana yace.
“Bazan sakar miki hannu ba”.
Ya ida maganar yana latsa mata hannu tare da yi mata tafiyar tsutsa.
Cikin fushi ta.
Fisge hannunta tare da galla masa harara kana tace.
“Ni gaskiya banason abinda kake min banaso sam”.
Ta Faɗa tare da juyawa zata bar masa falon.
Da sauri ya miƙe tare da shan gabanta kana ya durƙusa akan gwiwoyinsa tare dasa hannunsa duka biyu ya riƙe kunnensa cikin wata. Sanyayyar murya mai cike da lallashi ya zuba mata ido tare da cewa.
“Na tuba dan Allah kiyi haƙuri, bazan ƙara ba Insha Allah, ki gafar ceni kinji My dear.
Dan Allah Dan darajar Annabi Muhammad (S.A.W) kiyi haƙuri ki koma ki zauna naji Ni zan zauna a ƙasa”.
Jin haka yasa ta saki ajiyar zuciya tare da komawa ta zauna.
Murmushin gefen baki ya saki tare da miƙewa ya zauna aƙasan Capet mai taushi dake malale Atsakiyar falon tare da yin tagumi kana ya tsira mata Idanu, tare da saki ajiyar zuciya langwaɓar da kai yayi kana yace.
“Khausar ina sonki, ya zanyi idan har kikayi fushi dani rayuwata ba zata yimin daɗi ba. Duniyar nan zata yimin duhu matuƙar dai kikayi fushi dani, hankalina ba zai kwanta ba.
Kada ki mancefa na yarda nabi duk dokan da aka samin nacewa kada in sake inyi miki maganar soyayya har saikin kammala Secondary school, ni Kuma na kammala karatuna”.
Ajiyar zuciya ya saki tare da fesar da numfashi kana yace.
“Bisa wannan sharaɗin aka hanani koda jin Muryan kine Koda na Kira Mommy mun gaisa baza ta baki mu gaisa ba, haka nayi ta dakon soyayyarki azuciyata, duk tsawon shekarun nan da nayi a India ina ɗauke da dakon soyayyarki Khausar, Ina son ki³ kinsan tsawon shekara shida ba wasa ba I miss you, I really love you Matata, kece farin cikina kece sirrina kece duniya ta Khausar will you Marry me?”.
Ahankali tayi ƙasa dan kanta har ga Allah batasan mai zata ce dashi ba.
Kai ya jinjina tare da cewa.
“Khausar zaki Aureni!?”.
Lallausan tafin hannunta tasa ta rufe fuskarta batare data bashi amsa ba.
Shi kuwa Naseer murmushi ya saki kana yace.
“Nagode My Khausi”.
Domin shi duk azatonsa kunyarsa da kuma rufe fuskar da tayi sonsa take.


Cikin Sanyayyar murya mai taushi da kulawa ya kalleta kana yace.
“Kece Sirrina duk abinda zanyi aduniya dole ke sirrina ce, dake zanyi shi abubuwa biyu ne suka dawo dani ƙasar nan Khausar,
akwai mahaɗin abinda ya dawo dani ƙasar nan sai kuma burin mallakar ki da fatan kasancewarki mallakina na har abada”.


Cikin sanyin murya mai ratsa zuciyar duk wanda ya saurara tace.
“Uncle Naseer kace Ubangiji ya mana zaɓi msfi al'khairi, duk abinda muke so aduniya mu barwa Ubangiji zaɓi kaji ko Uncle Naseer”.
Kai ya jinjina tare da cewa.
“Naji Nagode amma ina da wata alfarma da nake so in nema awajenki shin zakiyi min shi?”.
Cikin sanyi da alamun bacci a idanunta tace.
“Eh Uncle Naseer in baifi ƙarfina ba zanyi

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads