Showing 42001 words to 45000 words out of 188939 words
Chapter 15 - SAKAYYA Book 1 complete BY GARKUWA.txt
kuma irin gwagwarmayar da yayi adomin kare rayukansu.
GEMBILA
Acan ɓangare makarantarsu Khausar kuwa ayaune aka gama gyara ilahirin makarantar daga nesa idan ka hango ginin ba zakayi zaton cewa a Gembila makarantar take ba koda a ƙasashen turawa ne sai ’Ya’yan wane da wane saboda yanda aka ƙawata ginin Makarantar fentin ya kasance Maroon and White haka zalika gate din Maroon anda white ne daga sama An rubuta
*Al'ANSAR ACADEMIC SCHOOL* Rubutun ma Maroon and White ne.
Acikin harabar makarantar kuwa Moddibo ne tsaye hannunsa harɗe aƙirji ya yinda manyan idanunsa ke lumshe yana kallon tsarin ginin Makarantar da akayi wani irin Up stair cycle daga cikin harabar makarantar zagaye yake flowers masu kyau da tsari.
M Jameel ne yace.
“Gaskiya Moddibo kayi ƙoƙari makarantar yayi masifan tsaruwa”.
Murmushin gefen baki Moddibo yayi wanda ke ƙarawa fuskarsa kyau yace.
“Masha Allah haka akeso”.
Ya ida maganar tare da juyewa cikin nutsuwarsa yake tafiya har suka fita acikin harabar makarantar suka shiga motarsu dake gefe afake.
Moddibo ke Driving yayin da M Jameel ke gefen mai zaman banza ƙira'an Sudai's na tashi cikin suratul Nisi'i Moddibo kuwa jinjina kai yayi ayoyin na ratsa sa.
M Jameel ya juya ya kalli Moddibo da bakinsa ke motsi alamar karatun yake bi yace.
“Moddibo kamar akwai motar dake bin mu fa”.
Kai Moddibo ya girgiza yace.
“A'a ba binmu akeyi ba”.
Kai M Jameel ya gyaɗa still yana kallon mirror bai dai ce komai.
Daga nan suka ci gaba da tafiya ganin still kamar binsu akeyi yasa Moddibo ya tsaya.
Ga mamakin su ganin su tsaya yasa wancan motar tayo kansu gadan-gadan...!
📝🍇✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️🍇
*SAKAYYAH*
_Page 8_
_NA_
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*Free page ne ƴar uwa in sun ƙare ko kinga littafin SAKAYYAH a a waje ba a cikin Groups na na SAKAYYAH ɗin da nabuɗeba, toh na satane kuma na Allah ya isane, kana na Yaseen doguwane😂 bulluƙutu kuma baƙar mutuwa... Dan haka biya ki karanta cikin Salamah yar uwa ba haƙƙin kowa kanki, littafin SAKAYYAH 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276. Sai in saki a Group ki karanta abinki Nana lfy fata lfy*
Masu son kayan Ɗa'a akwaisu Available.
Motar tayo kansu gadan-gadan.
Aruɗe M Jameel yace.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n!Hasbunallahu wani'imal wakin!! A'a su waye wannan suna da hankali kuwa!?”.
Cike da al'ajabi Moddibo ya zuba musu ido tare da ƙoƙarin yiwa motar key sai kuma ya gaza yin komai ya zubawa motar ido ganin gada-gadan fa ta nufi kansu haiƙan ƙadaran.
Sai da motar tazo gab dasu sai kuma ta kauce ta hau titi ta wuce.
Wani irin nannauyan ajinyan zuciya mai masifan ƙarfin M Jameel ya dire tare da meda kansa ya jingina da kujerar.
Shi kuwa Moddibo Idonu ya tsirawa motar cike da mamaki sai kuma ya motsa laɓɓansa a saman lips ɗinshi ya furta.
“Wannan wani irin tuƙi ne?.
Tuƙin ganganci ne ko kuwa dai da nufi ne?”.
Dalilin da yasa ya tsaya ma atunanin sa ko ɗaya daga cikin ‘Ya‘yan Malam Arɗo ne sai kuma yaga saɓanin haka.
Key yayiwa motar tare da kallon M Jameel dake lumshe da ido a hankali yace.
“J nayi zaton ɗaya daga cikin ‘Ya‘yan Malam Arɗo ne ya biyo mu shiyasa na tsaya, amma inaga basu bane wata ƙil ɗan koyon tuƙi ne”.
Ya ida Maganar batare daya ɗauki abin da muhimmanci ba.
Kai M Jameel ya gyaɗa da faɗin.
“Allah ya kyauta amma na tsorata da ganin yanda sukayo kanmu kamar da gayya suka yi sun tsinka min zuciya saura kaɗan fa su hau kanmu”.
Girgiza Kai Moddibo yayi kana yace.
“Da alama dai 'yan koyo ne!”.
Kai M Jameel ya gyaɗa tare da gyara zamansa, kana suka cigaba da tafiya.
Kai tsaye masallaci suka nufa kasancewar lokacin sallar Azahar yayi, bayan sunyi parking ne suka fito suka nufi cikin masallacin, aƙofar masallacin suka tsaya kusan tare sukay addu'ar shiga masallacin.
_“Auzubillahil Azim,Wabiwajhihil Kareem,Wasulɗanihil Ƙadiym,Minal Bismillahi Wassatu Wassalamu Ala Rasulullah.Allahummaftahliy Abwabal Rahmatik”_.
kana suka shiga.
Bayan sun idar sun fito daga masallacin M Jameel ya juya ya kalli Moddibo yace.
“Muje gida muci abinci”.
Da gefen ido
Moddibo ya kalleshi tare damotsa lips enshi zaiyi magana.
M Jameel yayi saurin ɓata fuska tare da cewa.
“Ba zakaje ba ko?”.
Murmushi Moddibo yayi tare da juyawa akalar motar zuwa gidansu M Jameel.
Yanzu ƙira'ar Sheykh Jabeer suke saurara har suka isa.
Bayan sunyi parking suka shiga Babban falon gida Adining suka zauna sukaci abincin shikam Moddibo kaɗan yaci ya bari.
Miƙewa sukayi suka fita Fitowarsu daga falon yayi dai-dai da ƙarasowar Hajiya Karima wajen M Jameel yace.
“Aunty Karima ina yini”.
Ba tare data amsa ba ta watsawa Moddibo kallon tsana tace.
“Maƙale anzo kenan?”.
Cikin ɗan sakin fuska yace.
“Ehh”.
Cike da mamakin halayensa da ƙarfin halinsa tace.
“To wai kai dan Allah ka rabu da bawan Allah nan da dukiyar mahaifinsa mana ko zai samu yayi abin kansa!”.
Cikin takaici M Jameel yace.
“Dan Allah Aunty ki ƙyale Moddibo da irin wa'annan kalaman mana, na sha faɗa miki shi ba irin mutunen da kike zato bane, ta ya zan fahimtar da ke?”.
Baki ta taɓe tare da juyawa tabar wajen kamar zata tashi sama.
Shi kuwa Moddibo lumshe idanunsa yayi tare da cije laɓaɓɓansa na ƙasa tare da kiran sunan Allah aransa.
Araunane M Jameel yace.
“Dan Allah Moddibo kayi haƙuri da abinda Aunty Karima keyi maka”.
Cikin kula Moddibo ya dubesa cikin yanayin nutsuwarsa da kuma ƙasaitarsa yace.
“J.kada ka damu inda sabo ai yaci ace na saba da halin Aunty abinda tun tasowar mu a haka nake da ita abinda tun bamu wuce shekaru shida-shida a duniya ba take min, har yanzu da muka bawa talatin baya, ai ya zama man shafawa kawai dai abu biyu ke sawa ban taɓa yi mata wonkin babban borgoba”.
Ya ƙare mgn tare da nufar ɗakin M Jameel.
Cikin jinjina kai M Jameel ya bi bayansa yana mai al'ajabi abinda Modiyke ɓoyewa tsawon shekaru da yake cewa dalilin dake hanasa taka mata birki, yayi ya gaya masa kuma sam yaƙi.
A ha dai suka isa, suna shiga ɗakin Moddibo ya kwanta bisa kujera tare da lumshe idanunsa alamun bacci zaiyi.
Acan gidansu Lamiɗo kuwa Mommy ce zaune yayin da Asma'u ke zaune daga ƙasa gefen ƙafafunta ta ɗago kanta tace.
Mommy asatin nan zamu koma makaranta gashi har yanzu Khausar bata dawo ba”.
“Wallahi kuwa gashi duk kwana biyun nan ba muyi waya ba, dan munfi sati da yin mgn”.
“Ayyah Allah Andi Meyesa”.
Cewar Asma'u
Kai Mommy ta jinjina tare da cewa.
“Kuma Idan ka kiransu ba zai shiga ba sai dai idan su suka kira ka”.
Gyara zama Asma'u tayi tare da cewa.
“Gaskiya Mommy Idan ta kira kice ta dawo tasan ana komawa za'a fara karatu gadan-gadan”.
Mommy tace.
“Inasha Allah zan faɗa mata”.
Daga nan sai suka ɗan ci gaba da hida, daga bisani sukayi
Sallama sannan ta tafi.
Acan Rugar Jauro Yaya kuwa yau sati da rasuwar Baffa Umaru baki ɗaya basu da cikakkiyar walwala duk da cewa sun dawo da sabgoginsu kamar da sai dai ciwon na nan aransu.
Khausar kuwa sosai tayi sanyi tun da akayi rasuwar bata cikin hayyacinta shiyasa bata samu ta kira Mommy ta ba.
Kasancewar jiya akayi adduo'ar bakwai Baffanta da yaransa duk sun koma bayan sunyi exchange na number ita dai ta Mommy ta basu. tare da yiwa Khausar al'ƙawarin kai mata ziyara wataran...
Anutse Khausar ta juya ta kalli Yaya Abba cikin sanyin murya tace.
“Ayyah yaya Abba dan Allah ka bani wayarka zan kira Mommy na”.
Kallonta Yaya Abba yayi cike da tausayi duk tayi wata iri yace.
“Toh shikenan amma ki bari sai gobe ki kirasu dan yau network bashi da kyau koda kin hau kan Bishiyar ma ba zaki ji magana ba”.
Kai ta gyaɗa masa kana tace.
“Toh Allah ya kaimu”.
“Amin”.
Ya amsa tare da miƙewa ya fita.
*GEMBILA*
Washe gari da safe tunda gari ya waye Malam Arɗo ke ta kiran wayar Moddibo awaya amma ba'a ɗagawa.
Shi kuwa Moddibo Anutse ya farka daga baccin daya koma tare da furta.
_“Alhamdulillahil Lazi ahyana bada amatana wa'ilaihil nushur”_
Wayarsa dake gefe ya janyo ganin Miss call ɗin malam Arɗo bar katai da yayi ne ya sashi ajiye wayar.
Kana ya miƙe ya shiga toilet.
Tare da addu'a a baki nai
Wanka yayi wanda ya ɗauke sa kimanin minti talatin kana ya fito yana mai faɗin.
_“Gufranaka”_
Suman kansa yake tsanewa da baby pink towel mai taushi.
Yayinda yake sanye da jibgegiyar bathrobe pink color mai masifar taushi wacce ya saƙale igiyoyinta a ƙugunsa.
A hankali ya zauna agaban dressing mirrow tare da,
Jona handdryer kana ya kunna tare da gyara zamansa da kyau bisa kujerar, dressing mirror ɗin tare da fara busar da sumar kansa mai ɗan karen sulɓi.
56 seconds yayi zuwa 1 minute yayi yana jujjuya kan handdryer ɗin tare da sa hannunsa ɗaya dake riƙe da madaidaicin Kum.
A hankali ya ajiye dryer din tare, da buɗe wani gora mai haɗe da man gashi na musamman, wanda Ummi ce ke haɗa musu, ɗan tsiyaya yayi kana ya murza tafin hannunsa tare da shafa.
Wani irin sheƙi da ƙyalli mai ɗaukan ido suman nasa ya farayi tare da fidda wani ni'imtaccen ƙamshi.
wani ƙum mai laushi wanda yafi na farin ya ɗauka tare da bin gashin nasa ya mishi tafiyar tsutsa,
Wow masha Allah, kamar saƙan taburma haka gashin ya kwanta da salo mai burgewa.
Goge tafin hannunsa yayi da towel ɗin dake bisa ƙafaɗarsa, kanaya
lakato lotion ɗin sa mai daɗin ƙamshi ya shafa jikinsa baki ɗaya.
idonsa ya lumshe tare da kauda kansa lokacin da yake shafawa cinyoyinsa mayin,
fuskarsa ya ɗan shafawa, mai ɗin tare da sa yatsarsa babba ya kwantar da gashin giransa na gefen dama, kana yasa babbar yatsar na hagu ya kwantar da na gefen hagun. sannan ya ɗan tsiyayi man kanshin ya shafawa tattausan sajensa dake kwance lip-lip ya shafa, wani irin sheƙi sajen keyi yana fitar da sanyayyan ƙamshi.
Anutse ya Miƙe ya buɗe durowarsa ya ɗauki jallabiyarsa mai masifar tsada da taushi Kalar Army green, kana ya zaro tattausan boxer and singlet farare ƙal-ƙal,
ɗan sunkuyawa yayi ya sanya boxer ɗin ba tare da kalli surarsa ba.
Kana ya miƙa tare da dai-dai ta zaman robor a gugunsa,
Bathrobe din ya kwance, kana ya saƙalashi bisa wata yar Kekkyawar masaƙali dake gefen drowersa, singlet ɗin ya saka, kana ya zira tattausar jallabiyar dake zuba sheƙi da ƙyalli wacce kai da ka gani kasan taja kuɗi.
baƙin hirami ya jawo, sanya kana ya naɗe kansa da hirami tare da sako jelar ɗaurin ta gefensa na hagu tsayawa yayi agaban Dressing mirrow tare da ɗaukar kwalbar turaren mai masifar ƙamshi ya feshe ilahirin jikinsa dashi wayarsa ya ɗauka tare da sanya wa a aljihun gaban rigarsa kana ya fice.
A motarsa ya shiga bayan ya buɗe gate sannan ya fice kana ya sake fitowa ya rufe gate ɗin.
Aƙofar gate ɗin gidan Malam Arɗo yayi Hong mai gadi ya buɗe masa yashiga Babban gida ne sosai sai dai kallo ɗaya zaka yiwa gidan kasan mamallakin gidan mutum nai mugun maƙo da kirta babu wani fentin arziƙi ajikin ginin gidan haka zalika ginin ɗakunan single rooms ne cikin haraban gidan kuwa koda flow babu daga can kusan ƙaramin ƙofar da zai sadaka da cikin gidan rijiya ce babba anyi masa murfin ƙarfe fitowa Malam Arɗo yayi yana murmushi.
Ɗan guntun Murmushin gefen baki Moddibo ya mayar masa tare da cewa.
“Ina kwana Malam ɗazu ka kira ina bacci”.
Ya ida maganar yana shiga ɗakin ɗaya daga cikin matan Malam Arɗo mai suna Hajiya Zainabu domin Malam Arɗo ya ɗauki Moddibo tamkar jika.
Wara ido Moddibo yayi yana kallon Hajiya Zainabu yace.
“Hajiya ina kujerun ɗakin?
Indai ba kujera Ni gaskiya bazan zauna ba”.
Sai kuma ya juya tare da kallon Malam Arɗo yace.
“Malam dan Allah asamu kujeru saboda idan sukayi baƙi su samu inda zasu zauna”.
Hararansa Malam Arɗo yayi tare da cewa.
“Ba kai bane kake lissafin duk abinda zai cin yemin aljihu kasan yanda gyaran makarantar nan ya cinye min kuɗi kuwa?.
Yanzu ma abu biyune yasa na kira ka na farko motata ta ɓaci zaka kaini Rugar Jauro yaya sannan kuma muyi magana akan ƙara kudin school fees ɗin yara dan gaskiya saina fanshe kuɗin dana kashe a school fees ɗin forko Aradun Allah.
Kai Moddibo ya jujjuya tare da yar kwaffa hana yace.
“Toh ba matsala ai ka'ida iyayen yara.
Yau kuma mai yasami motar ta lalace ne? Ko kuma sa maine bazaka iya ba”.
Yana mai laluben aljihunsa yace.
“Duka biyu, ta lalacen kuma yau du-du-du da naira ashirin da biyar na tashi”.
Kai Moddibo ya sunkuyar yana mai kallon wayarshi yace.
“Kuma har ina Rugar Jauro Yaya yake da nisa ne!?”.
Da sauri Malam Arɗo Yace.
“Koma da nisa kai zaka kaini dan badan ka matsa min akan gyaran makarantar nan ba da wataƙil in canza mota kuma da ko ban canza a ai bazan rasa kuɗin da mai ba”.
Murmushi Moddibo yayi kana yace.
“Dama wataƙil ne Malam koba ayi gyaran makaranta ba da wuya ka canza wannan motar.
Dariya Hajiya Zainabu tayi tace.
“Aikam Moddibo ka faɗi gaskiya”.
Anutse Moddibo yace.
“Koma dai menene dan Allah Malam ayi ƙoƙari asa musu kujeru dubi fa ba laida ba Capet ba kujere ba tiles sai siminti kawai dan Allah ka daure kasamu tiles da kujeru”.
Murmushi Hajiya Zainabu tayi tare da yiwa Moddibo alamar jinjina da hannu kana tace.
“Allah ya maka albarka”.
Tayi maganar yanda Malam Arɗo ba zai jiba.
Kai Malam Arɗo ya gyaɗa da faɗin.
“Naji wuce muje".
Taɓe baki Moddibo yayi kana suka fita.
Ɗakin Uwar gidan Malam Arɗo suka shiga mai suna Hajiya Ramatu,
Kwance suka same ta akan faranda ta shimfiɗa ta burma.
Gefenta Moddibo ya ɗan zauna bisa dakalin dake mazaunin Mlma Arɗo cikin mutuntaka yace.
“Ina kwana Hajiya ya jikin?”.
“Da sauƙi Moddibo ya ƙoƙari?”.
Tace tana mai kallonsa, kauda kansa yayi tare da cewa.
“Alhamdulillah”. yana miƙewa.
Yace.
“Ai dole ma sanyi yata kamaku ba Capet ba kujeru asanyin garin nan kam dan Allah Malam asamu kujeru inba haka ba zasu ta cutuwa sanyi zaita kamasu sannan ya batun fitar da ita wajen?”.
Tsaresa da Ido Malam Arɗo yayi kafin yace.
“Moddibo! Moddibo!! Moddibo Kafita idona baka iya lissafin komai ba sai lissafin yanda za'a cinye min kuɗina ko”.
Shi kuwa Moddibo kai ya karya kana cikin sanyi yace.
“Ai gaskiya ne Malam ita lafiyar nan dole aneme ta”.
Harara ya galla masa tare da faɗin.
“Ai mun gama magana da Basiru na basa kuɗin da zai isa".
Shi kuwa Moddibo kai ya jinjina yace.
Malam munyi magana da Basheer kuɗin ba zai isa ba Malam fita waje fa ba abune mai sauƙi ba”.
Saurin Kallonsa Malam Arɗo yayi yace.
“Na fahimta wato har ƙarana suke kaiwa wajenka to kaiɗin Ubana ne da zaka sani inyi!?”.
Murmushin gefen baki Moddibo yayi wanda ke ƙarawa fuskarsa kyau yace.
“A'a Malam niba Babanka bane ai shawara ce dai”.
Shi kuwa Malam Arɗo kai ya gyaɗa yace.
“Toh shikenan naji zanyi”.
Sallama Moddibo yayi wa Hajiya Ramatu sannan suka wuce ɗakin Malam Arɗo.
Kallon Moddibo Malam Arɗo yayi yace.
“Ya batun ƙara school fees ɗin yaran nan?”.
Shi ma Moddibo Kallonsa yayi kafin yace.
“Malam duk gyaran makarantar nan da akayi a asusun makaranta akayi school fees ɗin yaran yayi dan angyara makaranta baya nufin sai anƙarawa ɗalibai school fees zaka kashe makarantar ida kuɗin yayi yawa”.
Baki Malam Arɗo ya cuna har Moddibo ya ida magana sai kuma yace.
“In kashe makaranta fa kace?
Bayan na gyara makaranta sannan kuma ga lafiyayyun malamai masu ilimi yara suna samun wadataccen ilimi ko za'a samu ilimi abanza ne? zan ƙara school fees Tabbas zan ƙara”.
Murmushi Moddibo yayi yace.
“Toh shikenan kamar nawa za'a ƙara?".
Sai asannan Malam Arɗo yayi Murmushi yace.
“Za'a ƙarawa ko wani ɗalibi dubu Ashirin”.
Wara ido Moddibo yayi yace.
“Innalillahi gaskiya Malam yayi yawa inma za'a ƙara ya kama dole to bazai wuce aƙara dubu biyar biyar za'a ƙara shima saboda za’a ƙara sabbin malamai ne da kuma sabbin tsare-tsare”.
Kai Malam Arɗo ya jinjina yace.
“Toh shikenan tunda ka matsa zan barshi ahaka”.
Zama Moddibo ya gyara yace.
“Akwai kuma maganar tafiya musabaƙa na gasar hadda da za'ayi za'aje Noka”.
Kai Malam Arɗo ya gyaɗa da faɗin.
“Wannan ba matsala ashirya komai”.
Murmushin gefen baki Moddibo ya kumayi idanunsa akan Malam Arɗo yace.
“Eh badamuwa Malam wato tunda kasan wannan iyayen yarane zasu biya kuɗin motar da sungulla da komai”.
Dariya Malam Arɗo yayi yace.
“Atoh ainima dai ina ƙoƙari tunda motoci makarantar nanne ake tafiya dasu ko”.
Kai Moddibo ya jinjina yace.
“Ai Malam, Ƙarfe nawa zamu tafi can jauro yayan sannan mai zakaje yi?”.
Cikin sanyi yace.
“Wata Rugar Fulani ce amma gaskiya akwai tafiya zamu tafi da yanzu tun da kaga ƙarfe tara zuwa sha ɗaya zamu isa Insha Allah,Yawanci ina zuwa karatu can wajen wani Malam Aliyu limamin Rugar tasu sannan kuma anyi masa rasuwa shine nakeso Inje inyi masa ta'aziyya to kaga motata ta samu matsala”.
Jinjina kai Moddibo yayi da faɗin.
“Allah yajiƙan musulmi toh ba matsala muje tunda dama yanzu babu abinda nake yi, amma dai zamu dawo da wuri ko tunda kasan akwai ‘yan hadda?”.
Kai Malam Arɗo ya gyaɗa yace.
Toh ba matsala Allah dai ya kaimu lafiya”.
“Amin”. Yace
Sannan ya miƙe suka shiga mota suka fice kasancewar Ashirye suke.
Moddibo kuwa ƙira'ar Sheykh Jabeer ya kunna suna tafiya yana saurara tare da bin bakinsa tafiya mai ɗan nisa sukayi a haka.
Malam Arɗo ne ya katse shirun da faɗin.
“Gaskiya wannan tsarin ginin Makarantar yayi kyau Moddibo kayi ƙoƙari”.
Murmushi Moddibo yayi yace.
“Uhum Masha Allah”.
Haka suka cigaba da tafiya suna taɓa hira jefi-jefi wanda mafi yawan hiran Malam Arɗo keyi shi dai Moddibo daga Uhm sai um-um. Koko yace Masha Allah ko Alhamdulillah.
Suna dosan Rugar Moddibo yaga wajen kamar Rafi hayaƙi na tasowa lokaci ɗaya wani irin sanyi mai ratsa jiki ya ratsa gaba ɗaya ilahirin jikinsa Atake ya lumshe idanunsa tare da cije laɓɓansa na ƙasa.
Ahankali ya juya ya kalli malam Arɗo yace.
“Kai Malam garin nan akwai sanyi”.
Murmushi malam Arɗo yayi yace.
“Sosai ma kuwa garin akwai sanyi”.
Kai ya jinjina tare da jan numfashi kana ya fesar da huci mai ɗan karen ɗumi.
Dai-dai lokacin yayi parking a ƙofar gidan malam liman kana yana motsa laɓɓansa alamar Tasbihi yake.
“Subahanallahi”. Ya furta