Header Ads
Showing 114001 words to 117000 words out of 188939 words

Chapter 39 - SAKAYYA Book 1 complete BY GARKUWA.txt

Ads the beginning of article before Image
Ads at the middle of Article

kana cikin narkar da murya yace.
“Naga yau kina cikin farin ciki?”.
Kai ta gyaɗa masa tare da cewa.
“Sosai ma kuwa Uncle Naseer”.


Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da narkar da murya kana yace.
“Nima ki sani cikin farin ciki mana”.
Tana wasa da yatsun hannunta ta ɗago kanta tare da cewa.
“Toh me kake so in yimaka?”.
Karyar da murya yayi tare da faɗin.
“Ki cika min alƙawarin da kika ce zaki yimin, kince sai kinyi shawara nan da kwana biyu amma yau kusan kwana goma kenan da yin maganar mu kullum idan na tambayeki, sai kice baki yi tunani Ba dan Allah yau dai kiyi min”.
Cike da farin cikin kammala karatun ta da kuma nasaran data samu ta kallesa tare da cewa.
“Nayi alƙawari Uncle Naseer duk abinda kake so zanyi maka matuƙar bai saɓawa addinin Musulunci ba”.
Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da gyara zamansa kana yace.
“Naji daɗi My Khausi, Khausar ɗina ina sonki My life is nothing without you, you are my World”.
Kallonsa kawai take Amma batace Komai ba.
Ahankali ya sanya hannunsa acikin aljihu tare da ciro wani farin ƙyalle fari ƙal yana fitar da wani irin ƙamshi mai masifar hawa kai tare da birkita lissafi, ƙyallen ya miƙa mata ba tare da ta karɓa ba ta tsaida Idanunta akansa kana tace.
“Wannan kuma na menene?”.
Langwaɓar da kai yayi tare da cewa.
“Ki karɓa mana”.
Girgiza kai tayi tare da faɗin.
“Toh ka faɗa min na menene sai na karba”.
Marerece Murya yayi kana yace.
“Ki karɓa mana zan faɗa miki ai ba dai kinyi al'ƙawari ba?”.
Kai ta gyaɗa tare da karɓa..
Murmushi yayi tare da shafa sajensa kana yace.
“Ki shin shina ƙamshin mana”.
Kai ta girgiza tare da jan siririn tsaki asaman laɓɓanta kana tace.
“Haka ma yayi dan inajin ƙanshin yana hawa kai!”.
Zama ya gyara tare da cewa.
“Allah ko?”.
Matsar da ƙyallen tayi daga jikinta saboda irin ƙamshin da yake fitarwa mai masifan hawa kai.
Anutse ta ɗago manyan Idanunta dake lumshe ta kallesa tare da cewa.
“Toh Uncle Naseer mai zan maka da wannan ƙyallen?”.
Matsowa kusa da ita yayi har gwiwan ƙafarsa na taɓa yatsun ƙafa ta cikin wata siga ya karya murya tare da faɗin.
“Khausar kinyi min al'ƙawari ko?”.
Kai ta gyaɗa tare da cije lips ɗin ta kana tace.
“Eh nayi al'ƙawari”.


Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da kallon ƙofan falon kana yace.
“Kuma na faɗa miki cewa sirrine tsakanin mu dake”.
Kallon farin ƙyallen tayi tare da juyawa ta kallesa kana tace.
“Eh nasani”.
Sauƙe numfashi yayi tare da fesar da iska daga bakinsa kana yace.
“Sannan kinsan na faɗa miki cewa ci gaban mu ne. Ni dake da kuma ƴaƴan da zamu haifa?”.


Jinjina kai tayi tare da cewa.
“Eh nasani ka faɗa min mana”.


Langwaɓar da kai yayi tare da narkar da murya kana yace.
“Zan faɗa miki amma da farko ina so ki.
Sirrinta min dan nasan duk duniya babu wanda zan roƙa ya min inba keba”.


Aƙage ta kallesa tare da faɗin.
“Toh ina jinka ka faɗa min menene?”..
Kallon fuskarta yayi tare da sakin ajiyar zuciya kana ya sunkuyar da kansa.
Idanu Khausar ta zuba masa tare da kallon yanda ya sunkuyar da kansa ƙasa sannan tace.
“Ka faɗa kawai”.
Ɗago kansa yayi cikin sigar rauni yace.
“Kinyi al'ƙawari ba zaki faɗawa kowa ba ko?”.
Jinjina kai tayi tare da cewa.
“Nayi al'ƙawari bazan faɗa ba”.
Sauƙe Ajiyar zuciya yayi tare da faɗin.
“Kin tabbata?”.
Aƙage ta gyaɗa masa kai batare da tace komai ba dan tagaji da wannan tambayar tasa.
Iska ya furzar daga bakinsa kana yace.
“Khausar nasan dai tuntuni kin daɗe da fara period ko?”.


Cikin sauri tayi ƙasa da kanta cike da mamaki da kuma kunyar tambayarsa.
Ya shafa ƙyeyarsa tare da karyar da murya kana yace.
“Ya kikayi shiru?”.
Girgiza kai tayi tare da cewa.
“Babu komai”
Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da tsira mata idanu kana yace.
“Ki faɗa min gaskiya tsakanin ki da Allah nasan dai kin daɗe da farawa?”.
Ƙin cewa komai tayi sai ƙasa data sake yi da kanta.
“Ki faɗa min gaskiya kiyi haƙuri na haɗa ki da Allah”.
Still Nan ma shiru tayi Zuciyarta na bugawa.
Zama ya gyara tare da faɗin.
“Nasan dai kin fara tabbas”.
Ataƙaice ta gyaɗa masa kai.


Zare Ido yayi tare da cewa.
“Yauwa Alhamdulillah
kin fara period din ko?”.
Kai ta gyaɗa fuskarta babu walwala tace.
“Eh”.
Sajensa ya shafa tare da cewa.
“Alfarma to nakeso kiyi min”.
Gyara zamanta tayi tare da ɗago kanta kana tace.
“Toh wace iriyar alfarma ce zanyi maka?”.


lumshe idanunsa yayi tare da buɗe su akanta kana yace.
“Bance ki bani kuɗi ba, ban kuma ce kibani ranki, ko lafiyarki ba, kuma bance ki mallaka min kanki ba, kawai abinda nake so ki sammin Period ɗin ki”.
Atsorace ta zare Idanunta tare da ɗago kanta kana cike da mamaki tace.
“In san maka Period Kuma Uncle Naseer? Kamar yaya ban gane ba”.
Tayi mgnar jikinta na rawa kana ta miƙe cike da tsoro tana ja da baya.


Da sauri ya ɗaga mata hannunsa cikin sassauta murya yace.
“Karki manta fa kinyi al'ƙawari zaki sirranta min maganata, kuma shiyasa na faɗa miki dan nasan cewa zaki siririn ta min ki zauna mana kiji”.
Ya ƙare mgnar yana kuma yin mgnar zuci.
“Wannan yarinya sirri baya kamata da wuri, duk da ta shaƙi ƙamshin turaren nan amman ga yadda take min gardama”.
Yayi mgnar cikin ƙoƙon zuciyarsa dan baiyi zaton zata iya musa mishiba.
Ita kuwa Khsusar kallonsa tayi jikinta na rawa ta girgiza kai tare da faɗin.
“Toh ai ban fahimci mai kake nufi bane! wannan wace iriyar magana ce? me hakan yake nufi kenan?”.
Marerece Murya yayi da alamun damuwa yace. “Dan Allah dan darajar Annabi Muhammad (S.A.W) kiyi shiru kar kuyi magana da ƙarfi kiyi magana ahankali zaki fahimceni”.
Lokaci ɗaya tashin hankali ya bayyana afuskarta cike da tsoronsa tace.
“Toh mai zanyi maka?.
Kai ya langwaɓar tare da karyar da kai tamkar mai shirin fashewa da kuka yace.
“Nasan kina Period”.
Cikin fusata da yanayin tsoro tace.
“Ni ka daina maimaita min wannan maganar”.
Matsota yayi tare da cewa.
“Dole in maimaita Miki wannan maganar tunda abinda nake sone kuma kikayi al'ƙawarin zaki yimin!”.
Girgiza kai tayi still jikinta na rawa tace.
“A'a ai ko al'ƙawari idan abu yafi ƙarfin ka ba zaka yiba zaka janye sa”.
Cikin sauri ya kalleta tare da cewa.
“No baifi ƙarfin kiba Khausar bafa cewa nayi kiyi min komai ba, idan Period ɗinki yazo kika fara kawai zaki ɗauki ƙyallen ne sai kisa shi agabanki madadin kisa Pad Idan yayi awa ɗaya sai ki cire kisa min aleda zanzo in karɓi abuna shine kawai abinda nake so Khausar abinda kaɗai nake sofa”.
Ya ida maganar cikin yaudara murya tamkar zai fashe da kuka.
Ya cigaba da cewa.
“Kuma kada ki manta al'ƙawari kika yimin kuma baifi ƙarfin ki ba sannan ba kanki nace kibani ba”.
Cike da mamaki take Kallonsa cikin yanayin damuwa da alamun tsoro ta zare Idanunta kana tace.
“To me zakayi dashi Uncle mai zaka yi dashi wannan wani irin abune?, Wannan wace iriyar magana ce zaka ce min haka Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n”.
Cikin sauri ya riko tsintsiyar hannunta tare da Marerece fuska kana yace.
“Ki yiwa Allah da Annabi ki nutsu Khausar kar ki manta cewa kinyi min al'ƙawari.
Kuma wallahi idan kika faɗawa wani zan miki abinda ba kiyi tsammani ba!”.


Cike da fushi da kuma tsoro tace.
“Toh me zaka yimin tukunna?”.
Karyar da murya yayi tare da saurin dai-dai-ta nutsuwarsa kana yace.
“Zanyi fushi dake”.
Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da sakin murmushi har tayi zaton ko wani mugun abu zai mata tura madaidaicin bakinta tayi tare da cewa.
“Nidai gaskiya banyi al'ƙawari ba Uncle tsoro nakeji, amma tukunna mai zaka yi dashi?”.
Ɗan hararanta yayi tare da cewa.
“Ke dai me ruwanki? Maganin abu zanyi da shi maganine ance sai na samu Period ɗin zanyi maganin?”.
Kallonsa tayi still zuciyarta na cigaba da tsinkewa tace.
“Wani irin maganine wannan wanda saida period ɗin mace za'ayi shi?”.
Wani irin kallo ya watsa mata kafin ya sauƙe ajiyar zuciya tare da cewa.
“Magani ne kawai nace miki magani zan haɗa amma kamar baki yarda dani ba inada matsala ne ke dai in Zaki yimin in samu lafiya in kuma baza kiyi min ba shikenan dama can aikinsa inada ciwon kai ko?”.


Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da jinjina kai kana tace.
“Eh nasani toh shine ake cemin saina samu yanzu idan kika samin a farin ƙyalle, da daddare in zan kwanta ne zangoga shi asaman goshina ance insha Allah daga ranan na rabu da shi kenan”.


Sanyayyar Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da lumshe Idanunta kana tace.
“Tsakaninka da waye?”.
Ahankali yace.
“Tsakanina da Allah Wallahi dagaske na faɗa miki. My Khausi Magani zan haɗa kuma kinsan duk sanda ciwon kan nan ya tashi kamar zan mutu”.
Khausar kuwa jinjina kai tayi tare da sauƙe ajiyar zuciya kana tace.
“Toh shikenan ba damuwa insha Allah zanyi maka”.
Ta faɗa tare da juyewa ta fice bayan ta dauki ƙyallen.


Tun da Khausar ta koma ɗaki ta rasa meke damunta baki ɗaya ƙamshin ƙyallen na damunta ahankali ta buɗe drawer ta ɗauki leda ta jefa ƙyallen aciki sannan tasake saka wani ledan saida ta ninka masa laida biyar sannan ta fita bakyard ta ajiye sai asannan ta samu nutsuwa baki ɗaya ƙamshin ɗaga mata hankali yake.


Bayan kwana biyu Ya kama yau ne ake sunan Aunty Asiya misalin ƙarfe goma Mommy, Hajiya Bunayya, Amina, Raudat, Ramadan duk suka tafi sunan Aunty Asiya gidan ya rage saura Khausar ita kadai kasancewar. Mommy tace da ita dai idan ta dawo zata je dan kada abar gidan.


Khausar dake zaune a Bedroom ɗin ta tayi saurin miƙewa jin muryan Asma'u afalo atare Asma'u da Haiydar suka shigo falon da alama daga koyon Machine ya dawo saboda hannunsa dake riƙe da ƙaton L, kwanciya yayi akan 3sitter tare da kunna TV bayan sun gaisa da Asma'u, Khausar kuwa cike da farin ciki ta rungume Asma'u.
Ahankali Asma'u ta janye jikinta daga na Khausar kana tace.
“Ya naji gidan shiru kamar ba kowa?”.
Kai Khausar ta jinjina cikin sanyin murya da alamun damuwa atare da ita tace.
“Eh babu kowa sunje gidan Aunty Asiya yau sunanta, nima so nake inyi wanka sai Inje in duba su. Mommy nake jira baya ga haka ma jikina duk amace yake”.
Ta ida maganar lokacin da suka shiga ɗakin ƙaramin fridge dake ɗakin Khausar ta buɗe tare da ciro Friut ta ɗauki Plate akai ta zuba mata kana ta ajiye mata agabanta.


Cike da kulawa Asma'u tace.
“Khausar ya dai na ganki Asanyaye kamar akwai abinda ke damunki?”.
Girgiza kai Khausar tayi tare da cewa.
“Babu komai Asma'u kici Fruit”.
Kallonta Asma'u tayi tare da girgiza kai kana tace.
“A'a Taya zan sha Friut baki faɗa min abinda ke damunki ba?".
Ajiyar zuciya Khausar ta sauƙe tare da faɗin.
“Wallahi Asma'u wani Abu ke damuna, yake kuma bani tsoro nasha faɗa miki al'amarin Uncle Naseer.
Yana bani tsoro kince ba haka ba ko to kinji abinda ya faɗa min kwanaki”.
Atake ta kwashe dukan yanda sukayi da Naseer ta faɗa mata“.
Atsorace Asma'u ta dafe ƙirjinta tare da cewa.
“Kai Khausar kada ki yarda ki sanya Period ɗinki akan wannan ƙyallen ki bashi muka san mai zaiyi dashi ke har kin yarda dashi”.
Girgiza kai Khausar tayi cike da damuwa ta langwaɓar da kai kana tace.
“Nasan yana da ciwon kai, amma baki ɗaya ban yarda cewa maganin ciwon kai zaiyi dashi ba”.
Ajiyar zuciya Asma'u ta sauƙe kana tace.
“Gaskiya kar ki yarda ki kiyaye”.
Cike da damuwa Khausar tace.
“Toh yanzu ya zamuyi?”.
Gyara zama Asma'u tayi tare da faɗin.
“Gaskiya dai kam Khausar kada ki yarda kisa jininki akan wannan ƙyallen, hakan ma bazai yuba mukasan me yake nufi dashi, kika san me zaije ya aikata dashi ai haka baza ta yuba?”.
Lumshe idanu Khausar tayi kana tace.
“Toh shikenan ai dama bazan saba”.
Mommy ce tashigo tare da ɗaga labulen bayan tayi sallama.
Amsawa suka yi kana cike da ladabi Asma'u ta gaishe da Mommy.
Cikin sakin fuska Mommy ta amsa tare da tambayarta yasu Umminta.


Kallon Khausar Mommy tayi tare da cewa.
“Khausar ki ɗauki Plate da Spoon ki Kai gidan Aunty Asiya”.
Kai Khausar ta gyaɗa tare da cewa.
“Toh”,Juyawa Mommy tayi ta fice.
Miƙewa Khausar tayi tare da cewa.
“Asma'u muje ki rakani”.
Kai Asma'u ta gyaɗa tare da miƙewa direct kichen ta nufa ta tare da ɗaukar Plate da Spoon suka fita kai tsaye gidan Aunty Asiya suka nufa.


Ahankali Asma'u ta zubawa raguna biyu dake rataye a coumpund ɗin ido, da alama na suna ne duk angama gyarasu an cire kayan cikinsu ana jiran su tsantsame.
Har suka shiga cikin gidan suka kai Plate ɗin baki ɗaya hankalin Asma'u na kan ragunan dake coumpund ɗin bayan sun fito Asma'u ta kalli ragunan cikin sanyin murya ta kalli Khausar tare da cewa.
“Khausar ga dama ta samufa”.
Da sauri Khausar tace.
“Wacce damar”.
Cikin yin ƙasa da murya Asma'u tace.
“Dauko ƙyallen nan zamuyi muzo musaka jinin wuyan ragon nan”.
Jinjina kai Khausar tayi cike da gamsuwa tace.
“Ƙwarai kuwa Asma'u muje mu ɗauka”.
Cikin sauri suka fice cikin sa'a koda suka shiga basu samu Mommy a falon ba tana toilet. Haiydar kuwa baya nan kai tsaye backyard suka nufa Khausar ta ɗauki ƙyallen a inda ta ajiye sannan ta since.
Da sauri Asma'u ta kawar da kanta gefe jin yanda ƙamshin jiki ya bugeta.
Cikin ya mutse fuska tace.
“Kai Wannan wani irin ƙamshine mai tada hankali ba daɗin ji”.
Baki Khausar ta taɓe kana tace.
“Hmm nima dai haka naji”.
Ahankali suka juya suka fita kai tsaye gidan sunan suka nufa Baba Mai gadi dake zaune yace da.
“Hajiya Khausar ya gida?sai yanzu kika leƙo?.
Murmushi tayi tare da cewa.
“A'a ɗazu ma nazo bamu ganka bane”.
Kai ya jinjina tare da cewa.
“Ayyah wataƙil na zagaya ne”.
Cikin sa'a babu kowa a coumpund ɗin kallon Khausar Asma'u tayi cikin ƙasa da murya tace.
“Kinga mai gadi na kallonmu sai munje dai-dai wajen ragon zan durƙusa kamar takalmina ya tsinke ke kuma saikiyi saurin daddalan jinin ajiki”.
Kai Khausar ya gyaɗa suna isa wajen Asma'u ta tsugunna tana taɓa ƙafarta.
Khausar kuwa cikin sauri ta matsa jikin ragunan ta ciro ƙyallen cikin leda sannan ta manna ƙyallen ajikin wuyan ragon dake ɗigar da jini kaɗan-kaɗan sannan ta sake dan dala tayi haka har sau uku ajikin wuyan ragon cikin sauri tace.
“Asamu'u nayi mu tafi”.
Miƙewa Asma'u tayi suka nufi ƙofa,Baba mai gadi yace.
“Ya dai Asma'u ta kalmin tsinkewa yayi ya kuka tafi baku shiga ba?”.
Murmushi Asma'u tayi tare da cewa.
“A'a kawai dai na ɗan gurɗene naji ƙafar na yimin ciwo sannan mun manta ɗauko abinda Mommy ta aiko mu mukawo”.
Daga haka suka fice daga gidan.
Kai Baba ma gadin ya jinjina musu,
Tare da juyowa, cikin gidan,
Wani irin zazzaro idanu waje yayi cike da tsanani tsoro da mamaki Baba Mai gadi ya buɗe baki da ido da hanci duka gani, cikin raguna biyu dake rataye ɗaya ya ɓace ɓat......!








*Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci da salama babu haƙƙin kowa a kanki littafin SAKAYYAH 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276,*








*By*
*GARKUWAN MARUBUTA*
SAKAYAH


21


🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇




Isreg'o. Cikin tsananin tsoro da mamaki Baba mai gadi ya juya gabas da yamma,r kudu da arewa acikin coumpund ɗin gidan amma babu mutum babu dalilin mutum, cikin tsananin kaɗuwa da ganin wannan abin al'ajabin yace.
“Innalillahi wa'inna Ilahi rajiu'n. Cikin abinda bai wuce second ɗaya ba ace babu rago babu dalilinsa, kuma abu ayanke bawai da ransa ba bare ace ya gudu”.
Cikin kaɗuwa ya nufi cikin gidan tare da cewa.
“Ya Ilahi mai ya faru”.
Duk ya burkice ganin abin yake tamkar mafarki dai-dai lokacin da mai gidan ƙanin Lamiɗo yake fitowa.
Aruɗe Baba mai gadi yace.
“Alhaji ragunan biyu suna ɗaure amma yanzu naga ba ɗaya”.
Kallon Mamaki Alhj Musa ya masa tare da cewa.
“A'a ragunan biyu yanzu kuma babu ɗaya ƙafa ragon yake dashi Malam Idi?.
Aruɗe Malam Idi yace.
“Wallahi tallalahi Alhj da gaske yanzu-yanzu ragonan yana nan amma yanzu ya ɓace babu shi babu dalilinsa”.
Tsayuwa Alhj Musa ya gyara tare da cewa.
“Toh ragon ƙafa zaiyi ina zai shiga?”,.
Malam Idi daya gama shiga tashin hankali yace.
“Wallahi da gaske Alhj”.
ya faɗa tare da juyawa ya fice daga gate ɗin ganin su Khausar basu yi nisa ba yasa ya saki Ajiyar zuciya tare da cewa.
“Khausar!, Khausar!! Kuzo”.
A tsorace Khausar da Asma'u suka jiyo atare kana suka haɗa baki wajen faɗin.
“Ya dai Baba mai gadi”.
Hannu ya ɗaga musu tare da cewa.
“Kuzo dai”.
Cikin rawan jiki da tsoro Khausar tace.
“Lafiya?”.
Cikin ƙasa da murya Asma'u tace.
“Mun shiga uku kad dai ya gane?”.
Da ƙarfi Khausar ta haɗiye wani abu mai ɗaci tare da cewa.
“A'a Insha Allahu ma bai gane ba”.
Suna isa bakin gate ɗin yace.
“Khausar kushigo”.
Ƙara sa shiga sukayi zuciyar su na bugawa da mugun sauri.
Kallonsu Baba mai Gadi yayi tare da kallon Alhj Musa kana yace.
“Dan Allah dan Annabi ba ragunan biyu suna nan ba, har kuka tsaya kusa dasu suna ɗaure ba?”.
Atsorace Khausar ta gyaɗa masa kai kana Muryanta na rawa tace.
“Eh”.
Da sauri Baba mai gadi ya sake kallon wajen tare da cewa.
“Kawai ina zaune fa kamar abin wasa kamar amafarki kamar a Tv naga rago ɗaya ya ɓace”.
Khausar da jikinta ya fara rawane tace.
“Ya ɓace kuma?”
Cikin tashin hankali Asma'u da Idanunta sukayi zuru-zuru ta dafe ƙirjinta tare da faɗin.
“Ya ɓace kuma dai?”.
Jinjina kai Baban mai gadi yayi tare da cewa.
“Wallahi kuwa kun fita kenan ina juyawa naga ragon nan ya ɓace Khausar abin nan abin mamaki fa ina kuma kun gansu?”.
Shi dai Alhj Musa na tsaye ya harɗe hannunsa aƙirji yana sauraransu cike da al'ajabi.
Cikin tsananin tsoro mamaki da al'ajabi da kaɗuwa gami da kiɗima Khausar ta kalli Alhj Musa kana tace.
“Wallahi kuwa Baba ƙarami muma munga ragunan nikam mafa akusa dasu na tsaya. Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n yau mun shiga uku Meye faru ya akayi haka?”.
Jin hayaniya yasa mata dake cikin gida suka fara fitowa suna tambayar abinda yafaru duk wanda yaji rago ya ɓace sai yashiga cikin mamaki da al'ajabi.
Baba mai Gadi da abin ya tsaya masa arai ya kalli mutanen dake wajen tare da cewa.
“Wallahi ganin Idona ragon nan ya ɓace ɓat kamar a Film kuma babu kowa a farfajiyar gidan Khausar suna fita abin ya faru ina juyawa naga sun ɓace ɓat!”.
Atsorace Khausar ta jinjina kai tare da cewa.
“Wallahi kuwa Muma yanzu muka gansu mun samu ragu nan nan aɗaure”.
Ana haka Mommy tashigo nan ta samu labarin rago ya ɓace nan suka shiga jajantawa.


Khausar kuwa hannun Asma'u taja suka fice bayan sun fita Asma'u ta juya ta kalli Khausar tare da cewa.
“Khausar”.
Juyawa Khausar tayi tare da haɗiye wani abu mai Masifar ɗaci tace.
“Asma'u”.
Asma'u taja

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads