Header Ads
Showing 84001 words to 87000 words out of 188939 words

Chapter 29 - SAKAYYA Book 1 complete BY GARKUWA.txt

Ads the beginning of article before Image
Ads at the middle of Article

musu da addu'o'in kana Moddibo ya gyara system ɗin sa tare da ƙara rage girms Idanunsa kana yasa lallausan tafin hannunsa ya gyara zaman microphone din dake gabansa tare dayin gyaran murya cikin sanyayyar sautin muryansa ya fara kamar haka:
_“Auzubillahi Minal Shaiɗanir Rajim, Bismillahir Rahmanir Rahim.
(10) Innalazina ya'akuluna, Amwalal yatama zhulman innama ya'akuluna fiy buɗunihim naraa,wasayaslauna sa'irah”._
Jama'ar dake wajen masallacin cikin sassarfa suka ƙaraso cikin masallacin dan basa so koda harafi ɗaya ne su rasa daga cikin karatun Moddibo saboda baiwar muryarsa.


Moddibo kuwa sanyayyar numfashi ya fesar tare da jingina bayansa da kujeran kana ya cigaba kamar haka:
_“(11)Yusikumullahu fii auladikum,Lilzikri mislu hazzil unsaynan.Fa'in kunna Nisa'a fauƙasnatayni falahunna sulusa ma tarak,Wa'in kanat wahidatan falahannisf,Wali abwayhi likulli wahidin Minhumassudusu,Mimma taraka inkana lahuu waladun,Fa'in lam yakun lahu waladu wawarisahuuu abwahu fali ummihi sulus.Fa'in kana lahu Ikhwatun fali ummihi sudus min ba'adi wasiyyatin yusi biha audayn,abaukum wa'abna ukum latadruna ayyuhum aƙrabuna lakum naf',a,Faridatan Minallah,Innalaha kana aliman hakima”._
Ya dire ayar tare da jan numfashin sa da ya riƙe.
Jinjina kai M Jameel Yayi yayinda ayoyin ke ratsa sa cikin yanayin sakewa ya lumshe idanu kana yace.
“Aya ta gaba”.


Jinjina kai Moddibo yayi kana cikin zazzaƙan muryansa mai sanyi da ratsa jiki kana da nutsuwa ya cigaba da jan ayoyin saida ya kai aya ta Ashirin kana ya tsaya.
Shi kuwa M Jameel Cike da tsantsar ƙwarewa da nutsuwa kana da sanin makaman tafsir ya fara fassara ayoyin tare da cikekken kaddima da kowa amintattun haɗisai da suka da munasaba da ayoyin harma da sababul nuzur na ayoyi, lokacin ɗaya cikin masallacin ya sake samun nutsuwa tafsirin na ratsa su.


Ƙarfe goma dai-dai suka tashi tafsir ɗin mata suka fara fita ta ɓangarensu kafin maza suka fita acikin mota Asma'u da Innayi suka jira M Jameel da Moddibo goma da kwata dai-dai suka fito suka tafi.
Acan ɓangaren Khausar kuwa yauma kamar kullum taje tafsiri ita kaɗai ta dawo duk da masallacin a ƙofar gidansu yake bakinta ɗauke da Sallama tashiga cikin falonsu Anutse ta cire hijabinta tare da nufar kichen inda take jiyo motsin Mommyta kasancewar yau itace da girki yasa ko tafsir bata jeba.


Juyiwa Mommy tayi jin motsi abayan ta ganin Khausar yasa ta maida hankalinta kan aikinta kana tace.
“Kin dawo?”.
Kai Khausar ta gyaɗa tana kallon tuƙeƙken tuwon shinkafa da Mommy ke kwashe maran ƙarshe.
Ahankali Khausar ta matsa kusa da Mommy kana tace.
“Mommy ki bari zanyi miyar”.
Kai Mommy ta gyaɗa kana tace.
“Ok to Miyar zogala za kiyi”.
Kai Khausar ta gyaɗa tare da ɗaukar.
Da fara aikin haɗa miyar zogalen.
Cikin abinda bai gaza awa ɗaya da rabi ba, duk ta haɗa ta sanya komai na buƙata kana.
Ta rufe nan danan kichen ɗin ya kaure da ƙamshin miyar sauran kayan da Mommy tayi amfani dasu ta haɗa ta wanke tare da sauƙe Miyar ganin tayi tik gwanin kyau.


Bayan ta gama ta buɗe miyar da yayi mugun kyau a ido ta ɗauki kular wani sashe ta zuba miya kasancewar babban gidana yasa kowa kaina nasa akeyi, na buɗa baki kuwa ki wacce a side ɗinta takeyi, mai girki zata sawa Lamiɗo, da Dadu, haka tsarin nasu yake.
Shigo wa Mommy tayi fuskarta ɗauke da murmushi ta kalli yanda kichen ɗin yayi fess ga ƙamshin miyar zogalan da yaki kifi da naman dariko, kallonta ta mayar kan Khausar kana tace.
“Sannu da ƙoƙari ki ɗauki na sashen Hajiya Bunayya ki kai mata”.
Kai Khausar ta gyaɗa sannan ta ɗauka kular Hajiya Bunayya ta wuce Haidar Mommy ta ƙwalawa kira bayan yazo tace ya ɗauki kular sashen Gimbiya Dadu ya kaimata dan Mommy tunda ta lura da Khausar batason zuwa yasa ta rage aikanta sashen shi kuwa Haiydar daga sashen Gimbiya Dadu ya wuce sashen Hajiya Bunayya.


Hajiya Bunayya dake zaune akan kujera ta faɗaɗa fara'ar fuskarta ganin Haiydar ta tsira masa idanu kana tace.
“Babana kaine dama yanzu nake niyyan zuwa in yi maka albishir”.
Murmushi Haidar yayi tare da zama kana yace.
“Daga sashen Gimbiya Dadu nake nace bari nazo na gaishe ki”.
Murmushi tayi masu cike da Ma'anoni tayi kana tace.
“Insha Allah bayan sallah mashin ɗinka zai zo kaga dama tun shekara biyu baya naso saya maka Abbanka yace saika ƙara girma kuma kaga yanzu aika girma”.
Jinjina kai Haidar yayi cike da tsananin farin ciki mara mistuwa ya gyara zamansa kana yace.
“Nagode Ummah Allah yarabaki da sharrin maƙiya”.
Murmushin gefen baki tayi kana tace.
“Bana son godiyar nan Babana”.


Cike da farin ciki ya miƙe ya nufi sashen su fuskarsa ɗauke da murmushi ya shiga falon zaune ya samu Mommy da Khausar.
Kallonsa Mommy tayi kana tace.
“Ina ka tsaya?”.
Zama yayi daga gefen Khausar still.
Fuskarsa da murmushi da yakasa ɓoyewa ya numfasa tare da cewa.
“Mommy Machine ɗina ya Kusa isowa fa, kinga tun shekara biyu baya Umma taso siya min shine Abba ya hanata yace saina ƙara girma ai yanzu kam dai na sake girma bazai hana ba ta saya min Machine sabo mai kyau bayan sallah zai iso”.


Khausar kuwa tunda ya fara magana ta tsira masa idanu saida ya kai aya ta sauƙe ajiyar zuciya mai zafi tare da furzar da iska daga bakinta kana babu walwala afuskarta ta kawar da kanta gefe tare da cewa.
“Kai kuma farin ciki kake ko?”.
Juyawa Haiydar yayi tare da kallon ta kana yace.
“Sosai ma kuwa kema kamata yayi kije kiyi mata godiya”.
Harara Khausar ta ɓalla masa.
Murmushi Mommy tayi kana tace.
“Rabu da ita ai ni zanje.
A yanzu kam aika girma yanda kake da tsawon ƙafan nan”.


Murmushi yayi tare da kallon Khausar kana yace.
“Sosai ma Mommy ai yanzu na girma yanzu fa shekara kusan sha shida nake nema gashi mai shekara sha takwas ɗinma na fita koda yake sha bakwai ne da yan watanni ne ko gareta”.


Jinjina kai Mommy tayi kana tace.
“Ai lallai dai kam kama cika sha shida kam Allah yasa kafara hawa asa'a.
Ubangiji ya tsareka da sharrin ƙarfe.
Allah yatsare gabanka da bayanka!.
Ubangiji ya makantar da idanun makiyan ka akanka!.
Allah ya tsare ku ga duk kan abinda zai cutar da rayuwar ku! Allah ya muku katangan ƙarfe da dukkan abin da zai zama sharri acikin rayuwarku!”.
Cike da jin daɗin Addu'ar ta Haiydar yayi Murmushi tare da cewa.
“Ameen ya hayyu ya ƙayyum Mommy na”.
Ajiyar zuciya Khausar ta sauƙe tare da kallon Mommy kana tace.
“Ameen ya Allah Mommy tunda kinyi addu'a magana ta ƙare baza'a ji tsoron komai ba babu bakin uwa akansu duk kan mai sharri zaiyi ya gama babu abinda zai sameshi da izinin Ubangiji”.


Murmushi Haiydar yayi tare da kallon Khausar kana yace.
“Aikam Addah Khausy babu bakin uwa akaina duk kan wani mai mugun nufi zai ƙare akansa”.
Murmushi Mommy tayi cike da ƙaunar ƴaƴan nata,
kallon ta ta mayar kansu tare da cewa.
“Ku tashi kuje kuyi bacci dan mu samu mu farka da wuri mu kaiwa Ubangiji bukatun mu”.
Miƙewa sukayi tare da yiwa juyawa sai da safe kana kowa ya wuce ɗakinsa ya kwantar.


Misalin ƙarfe ɗaya na dare Mommy ta farka kallon Lamiɗo daya miƙe yashiga toilet tayi sai kuma ta miƙe ahankali ta tafi side ɗinta.
ɗakin Khausar tashiga tare da kunna haske.
Idanunta suka sauƙa akan Khausar dake sharan bacci ƙara sawa tayi tare da bubbuga ƙafarta kana tace.
“Khausar ki tashi kiyi nafilla”.
Ahankali Khausar ta buɗe Idanunta cikin Muryan bacci ta kalli Mommy kana ta yunƙura ta zaune bakinta ɗauke da addu'a tace.
“Toh Mommy”,Sannan ta Sauƙa ta shiga toilet.


Juyawa Mommy tayi ta koma ɗakin Lamiɗo lokacin data shiga har ya fara Sallah kai tsaye toilet ta shiga ta ɗaura Al'wala bayan tayi ta fito tare da shimfiɗa Sallaya ta tada Sallah cikin nutsuwa ta keyi bayan tayi sujja tayi Subhana Rabbiyal a'ala³ kana ɗaura da du'inta.
“Ya Allah kayuwa ƴata zaɓin alkhairi,Ya Allah kashirya Khausar kasata ahanya madaidaiciya Ya hayyu ya ƙayyum ka tsare mata imaninta, Ya Allah ka kare min Haiydar ɗina ya Allah katsaresa daga sharrin mai sharri ya Allah ka kare min ita ya Allah kabawa Ramadan da Raudat ilimi mai albarka da yayunsu dama dukkan ƴaƴan musulmai. Ya Allah katsare min ƴaƴana daga sharrin,Mutum, aljan da kuma ƙarfe, ya Allah katse min imanina Allah ka tsaremin zuciyoyinsu, ka tsaresu da sharrin hassada, ƙeta, munafurci, da ƙyashi ya Allah ka kare min mijina kabiya masa buƙatunsa na Alkhairi dama ɗauka cin al'ummar musulmai.
Bayan ta idar da nafillah ta ɗauki Alkur'ani ta shiga Muraja'a.


Khausar kuwa ƙarfe biyu da rabi bacci ya riƙa fisgarta akan Sallaya ta kwanta nan da nan bacci mai nauyi yayi nasarar ɗauke ta.
Can cikin baccinta ta fara wani mafarki mai cike da al'ajabi ganinta tayi.
Gata nan tsaye a wani ƙaton fili.
Baki ɗaya ilahirin filin ashare yake kuma , yashine malale a wurin iya ganinka sai wani irin haske mai masifar ƙyalli da ɗauke idon da ya cika wajen baki ɗaya, ahankali ta ɗaga kanta ta fuskanci gabas, da sauri ta rumtse idanunta gani wata ya fito ta gabar juyawa tayi taga yamma da sauri Still nan ya fito ta yamman sake juyawa kudu tayi still ta nan ma ya fito ahankali ta sake juyawa arewa, wani irin masifeffen karkarwa jikinta ya farayi, ganin tanan ma watan yafito duk kusurwa huɗu wata ya fito sai asannan ta lura da haskensa ne yake ɗauke mata ido.
Ahankali taga wani kyakkyawan.
Yaro fari ƙal agabanta yayinda gashin kansa ke kwance lib-lib, daga bayansa ta hango wani kyakkyawan mutum sai dai fuskarsa na kallon gefe hannunsa na kan yaron yana shafawa cikin wata.
Sanyayyar murya yake kallon yaron kana yace da ita.
“Wannan shine jininmu mahaɗinmu, wannan shine sanadin haɗayyarmu bugun zuƙatanmuuuhh”.
Ya ƙarasa jan kalmar cikin wata iriyar ƙasalalliyar murya mai cike da shauƙi.
Ita kuwa ƙoƙari take taga fuskar mutumin sai dai ta kasa sai iya fuskan kyankyawan yaron take iya kallo.
Dai-dai lokacin kuma ta buɗe Idanunta jin Muryan Mommy nacewa.
“Khausar, Khausar ki tashi zaki makara fa ƙarfe huɗu tayi bakiyi Sahur ba anjima kaɗan zaki fara ce mana kin fara jin wahalar azumi”, Ta faɗa tana buga ƙafarta da saurin Khausar ta tashi zaune tare da sakin ajiyar zuciya kana tace.
“Innslillahi wa'inna ilahi rajiu'n Hasbunallahu wani'imal wakin Astagfirullah wa'atubu ilaik”.
Sai kuma tayi addu'a ta shafa.
Mommy dake tsaye har yanzu kuwa sake taɓata tayu tare da cewa.
“Khausar kada ki koma bacci fa kitaso”.
Kai ta gyaɗa kana tace.
“Mommy na tashi bazan koma ba”.
Juyawa Mommy tayi ta fice ita kuma Khausar toilet ta shiga.
Brush tayi kana ta fito kai tsaye falon ta nufa.


Samu tayi Mommy ta haɗa mata ɗumamen tuwon jiya da Tea mai kauri ahankali ta zauna tare da kai tuwon bakinta da ƙyar ta haɗiye baki ɗaya jikinta yayi mugun sanyi da mafarkin da tayi.
Mommy dake zaune a kujeran falon ta juya ta kalleta ganin bata cin tuwon yasa ta girgiza kai tare da cewa.
“Kici abinci fa Khausar kin sanki sarai da cin abinci anjima kaɗan zaki fara cewa yunwa kike ji”.
Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da fesar da iskar bakinta kallon Mommy tayi kana cikin sanyin murya ta lumshe Idanunta tare da cewa.
“Mommy wallahi tuwon ne nakeji kamar ba zai shiga ba babu wani abu ne?”.
Kai Mommy data tsira mata Idanu ta gyaɗa kana tace.
“Kije kichen akwai indomie dana ɗaura wa Haiydar shima yace ba zai ci tuwo ba to amma ke kam nasan indomie ba wani riƙe Miki ciki yake yi ba”.


Lumshe Idanunta tayi kana ta buɗe su akan Mommy ahankali ta motsa laɓɓanta tare da cewa.
“Bari in cisa yau ɗin kam amma Mommy da kifi ne koda nama”.
Tayi tambayar ne domin bata fiye son kifi ba.


Kawar da kai gefe Mommy tayi kana tace.
“Da kifi ne idan zaki ci kici idan kuma baza kici ba ki bari”.
Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da jan siririn tsaki kana tace.
“Bari dai inci, tuwon ne naji kamar bazai ciwu ba shi ɗin ma miyar aida kifi”.
Mommy dai Bata sake cewa komai ba ahankali Khausar ta miƙe tashiga kichen ta ɗauki Plate ta ɗibi yanda zai isheta kana ta fito ta zauna tare da Bismillah ta fara ci bayan ta gama ta ɗauki tea da Mommy ta haɗa mata da bread taci.
Haiydar ne ya shigo da Sallama idanunsa akan Plate da Khausar ta gama cin indomie.
Kallonsa Mommy tayi kana tace.
“Jeka ɗebo indomie yayi sannan ka taho min da tuwo”.
“Toh",Ya amsa kana ya wuce kichen ɗin ya juye indomie sannan ya zubawa Mommy tuwon ya fito.
Khausar dai na zaune tana lumshe Idanunta tare da tuna irin mafarkin da tayi wanda ya tuno mata wanda tayi shekaru biyu baya a Jauro Yayah.


Ahankali ta saki ajiyar zuciya tare da juyawa ta kalli Haiydar da yagama Sahur ɗin ta gyara zamanta tare da cewa.
“Haiydar nikam yanzu wani surah kake?”.
Murmushi yayi kana yace.
“Ke ɗin wace surah kike?”.


Zama ta gyara tare da cewa.
“Hmmm aini nayi nisa ina Maryam kaga insha Allah zan samu sauƙa biyu”.
Kai ya gyaɗa mata tare da cewa.
“Toh ni ina Yasin Insha Allah zan samu sauƙa uku insha Allah duk azumi goma zanyi sauƙa ɗaya”.
Murmushi Mommy dake duba wani littafin addini tayi kana tace.
“Masha Allah yayi kyau Khausar ya akayi kika tsaya wasa ya wuce ki”.
Langwaɓar da kai tayi kana tace.
“Mommy kinga ai shi baya taya ki yin aiki nice ke tayaki aiki kinga shi duk lokacin daya keso zaiyi karatu.
Jinjina kai Mommy tayi kana tace.
“Eh haka ne da wannan dan wannan amma dai ki dage kema”.
Kai ta gyaɗa kana tace.
“Toh shikenan Mommy zan dage insha Allah amma Mommy ke izu nawa kikayi”.
Murmushi Mommy tayi kana tace.
“Insha Allah nima zan samu uku kaman na Haiydar”.
Ware Ido Khausar tayi tare da tura madedecin bakinta kana tace.
“Insha Allah nima zan dage duk azumi goma sai nayi sauƙa”.
Jinjina kai Mommy tayi tare da faɗin.
“Aikam da kin kyauta amma sai kin rage baccin safe”.
Jinjina kai Khausar tayi kana tace.
“Insha Allah zan rage”.
Jin kiran assalatu yasa suka miƙe Haiydar ya tafi masallaci Mommy da Khausar suka shiga ɗaki suka ɗaura alwala kana suka gabatar da sallah bayan sun idar Khausar ta zauna tayi Azkharul sabah tana gamawa ta mike ta dawo falo ta gyara tare da sharewa kana ta fita zuwa kofar sashen nasu ta gama share ko ina sannan ta wuce Bedroom ta kwanta kasancewar akwai mai yi musu wanke-wanke tun kafin su shiga Sallah ta zo ta kwashe kayan ta wanke.


Ahankali azumi ya cigaba da tafiya kwanaki suna tafiya lokaci yana ja cikin ikon Allah har angama goman farko goma na marmari inji hausawa ko?. Har an shiga goma na biyu, goma na wuya ko? Yau an kai azumi na goma sha biyu.


Yayin da Aɓangaren Moddibo da M Jameel sunyi nisa acikin tafsirin Suratul Nisa sun fassara har zuwa ayoyi na tamanin da tara zasu tashi akan aya na Casa'in


Da daddare Misalin ƙarfe tara M Jameel da Moddibo ne zaune acikin masallaci gaban ko wannensu ɗauke da system da kuma roban Swan water mai sanyi Moddibo na cikin shigarsa as Usual kamar ko yaushe Jallabiya Neavy blue kansa ɗaure da Hirami M Jameel kuwa sanye yake cikin gezner blue da babbar riga.
Cike da nutsuwa M Jameel Yayi gyaran murya tare da hura Microphone ɗin kana yace.
Ya buɗe da addu'a kamar ko yaushe.


Lokaci guda masallacin ya kaure da kabbara tamkar zasu tsaga masallacin saboda yanayin zafin jinjinsa da kwarjininsa cike da sakin fuska.
Ya cigaba da cewa.
“Anma ba'ad faya Ikhwatul musulmi Assalamu alaikum warahmatullah wabarkatuhu”.
Atare suka hada baki wajen cewa.
“Wa'alaikum Salam warahmatullah wabarkatuhu”.


A hankali ya numfasa tare da sauƙe nan-nauyan ajiyar zuciya kana ya dubi ɗumbin jama'ar dake zaune acikin masallacin cikin tsantsar nutsuwa ya juyo da system ɗin gabansa kana yace.
“Acigaba da tafsirin Alkur'ani mai girma Amasallacin. Juma'a dake ƙofar gidan Mai martaba Sarki Gembulan Lamido Bashiru zamu cigaba da tafsirin Alkur'ani mai girma acikin Suratul Nisa'i zamu tashi a aya ta cassa'in”.
Sai kuma ya juya ya Kalli Moddibo kana yace.
“Aramma Bismillah”.


Jinjina kai Moddibo yayi tare da gyara zamansa kana ya ɗan jingina bayansa da jikin kujeran cikin Sanyayyar muryarsa mai cike da nutsuwa da zaƙi yayi basmala kaya ya fara karanta ayoyin kamar haka;
_“(90)Illallazina Yasiluna Ilaƙaumim Bayna Kum wa Bayna hum misaƙun Auja,Ukum hasirat suduruhu an yuƙatalalukum.Walau sha Allahu lasallaɗhum Alaikum falaƙatalukum.Fa'in'itazalukum falam yuƙatilukum Wa'alƙau Ilaikumussalama fama ja'alallahu lakum Alaihim Sabila”._


Moddibo ya ida kai Ayar yana mai lumshe idanunsa akuma take tsikar jikinsa suka tashi yayi saurin buɗe idanunsa tare da ƙoƙarin dai-dai-ta nutsuwarsa kana ya cigaba da furta Aya ta gaba kamar haka.
_“(91)Satajidunah Akharina Yuriduna Anyamanukum Wayamanu Ƙaumahum kullamaraduu Ilalfitnatin Urkisu fiha.Fa'in lam ya'atazilukum Wayulƙau Ilaikumussalama Wayakfuru Aydiyahum Fahuzuhum Waƙtuluhum haysu saƙiftumuhum.Wa Ula'ikum ja'alnalakum Alaihim sulɗanammubina”._


Wani irin numfashi M Jameel ya saki tare da rintse idanunsa kana jikinsa ya ɗauki tsuma yana mai jin fassarar Ayar na yawo Atsakiyar kansa Atake kuma zuciyarsa ta cigaba da bugawa da kaso tamanin cikin ɗari.
Yayinda gaba ɗaya al'ummar dake cikin masallacin dama wajensa sit kakeji kamar ba mai numfashi sabida tsananin yadda sautin karatun ke ratsa musu zuƙata da ƙoƙwale.


Shi kuwa Moddibo ya kai minti ɗaya kafin ya saki gauron numfashi gaba ɗaya jikinsa yayi sanyi sabida sanin ma'anar ayoyin da zai kawo a gaba, cikin wani irin raunin tare da tsoron Allahu wahidun ƙahhar, gaba ɗaya muryarsa ta sake rauni cikin dakiya ya cigaba da Karanta Ayar Kamar haka.
_“(92)Wama kana limu'uminun An yaƙtula Mu'uminan Illakhaɗa'a.Waman ƙatala Mu'uminan khaɗa'a fatahriru Raƙbatatin Mu'uminatin wadiyyatun Musallamatu Ila'ahlihee Illah An yassaddaƙun.Fa'in kana min ƙaumin Aduwwillakum Wahuwa Mu'uminun Fatahriru Raƙbatin Mu'uminatan.Wa'in kana min ƙaumim baynakum wa baynahum miysaƙun Fadiyyatun Musallamatun Ila Ahlihi watahriru raƙbatin mu'uminatin.Famallam yajidu fasiyamu shahraini mutatabi'ayni taubatan Minallah.Wakanallahu Aliman hakima”._


Wani irin nutsuwa cikin masallacin yayi musamman ma wa'anda suka san fassarar ayoyin wa'anda basu san fassarar ba kuwa mu'ujiza ta Kur'ani ta dinga ratsasu tare da Sanyayyar sautin Muryar mai karatun.
Moddibo kuwa idanunsa ya lumshe sakamakon wasu zafafan hawaye masu ɗumi da suka cika cikin ƙarfi ya furzar da iska mai zafin gaske Tabbas kashe ran mumini baƙaramin tashin hankali bane amma baki ɗaya awannan zamanin an maida rai ba abakin komai ba.
Ya gyara zamansa tare da cigaba da karantar Ayar kamar haka.
_“(93)Waman yaƙtul mu'uminan Muta'ammidan Fajaza's'uhu Jahannama! halidan fiha wagadiballahu Alaihi wala'anahu! wa'aaddalahu Azaban! Azeeymah!!!!!”_.


Awannan lokacin hawaye ne suka ciko idanun Moddibo jin irin tsananin azaban da Ubangiji ya tana darwa duk wanda ya kashe ran mumini batare da wani hakkiba.
Walahabahu la'anar Ubangiji kana fajaza'ahun jahannamu khaleedan fiha, fa ubangiji yace kana aka ɗaura da Azaban Azeeymah!!!, Duk wannan tanadinefa da Ubangiji yayiwa mai kashen ran mumini da gangan.


Wani irin rawa jikin Moddibo keyi tamkar wanda aka konawa wuta a jikinsa cikin tsananin sheshsheƙan

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads