Header Ads
Showing 66001 words to 69000 words out of 188939 words

Chapter 23 - SAKAYYA Book 1 complete BY GARKUWA.txt

Ads the beginning of article before Image
Ads at the middle of Article

tsokana Jalaludeen yace.
“Katakon dake gefenka”.
Murmushi M Jameel yayi tare da kallon Moddibo yace.
“A.J ɗin nawa ne katako?”.


“Eh inba katako ba shi menene? ka faɗa masa cewa akwai furen dake ƙoƙarin tsiro a jikinsa tun daga ƙasa har ya isa zuciya ya gab da kanshi tuni ma ya ratsa zuciyarsa amma bai sani ba”.
Murmushi M Jameel yayi tare da kallon Moddibo da still Idanunsa ke lumshe kamar mai bacci kana yace.
“Wai yace in faɗa maka akwai furen da zai fito tsakiyar kanka yama ratsa zuciyarka”.
Sai asannan Moddibo ya buɗe idanunsa ya kalli M Jameel tare da faɗin.
“Ka ganni karabu dani da kalaman Jalaludeen, shiya sani can yaje yata faman maganganunsa da baza ka gane kansu ba bare gindinsu ya riƙa yi mana maganar damu mutane zamu gane ba sai wanda sai sune masu ganewa ba”.


Dariya Jalaludeen yayi yace.
“Zaka gane ne ai lokaci ne yana zuwa”.
Dariya M Jameel yayi tare da hong aƙofar gidan Ummi ganin shiru ba'a buɗe masu bane yasa, M Jameel fitowa ya buɗe, kana ya dawo yaja motar still kafaɗarsa saƙale da wayar
Jalaludeen ne yace.
“Ku gaishe da Ummi idan kun shiga”.
Sannan ya katse wayar kana shi kuma ya kutsa kai cikin gidan.


Dai-dai lokacin da a dai-dai-ta ya ajiye Khausar kudinsa ta basa tare da buɗe ƙaramin ƙofar dake maƙale da gate ɗin tashiga,
Batama lura da babban gete ɗin dake ɗan buɗe ba,
ganin mota a fake a harabar gidan yasa ta isa wajen kasancewar glass ɗin tink-tenk ne yasa bata fahimci da mutane aciki ba rawar kanta kuma ya hanata fahimtar alamun yanzu motar ta tsaya.


Jikin gefen mai zaman banza ta nufi tare da kallon fuskarta ajikin mirrow sai kuma ta juya manyan Idanunta kalaman Aunty Ruƙayya suka dawo mata kunne tana kama da Preety matsa pinch lips ɗin ta tayi tare da lasa kadan sai kuma ta juya manyan Idanunta.
M Jameel kuwa dake mazaunin Driver murmushi ya saki domin ya tabbata bata san da mutane aciki ba.


Acan ɓangaren su Hajiya Bunayya kuwa zaune suke gaban boka Kar'uzu cikin tsananin ɓacin rai da fushi Boka Kar'uzu ya buga musu wata razananniyar tsawa cikin sautin muryarsa mara daɗin sauti
bayan ya gama sauraron Hajiya Bunayya yace.
“Ai seda na faɗa muku aduk lokacin data fara aiki da maganin kada tayi alwala da sallah na tsawon wata ɗaya amma saboda taurin kai kuka bari tayi alwala tayi sallah shiyasa yake kallon fuskar ta kamar na ƙonennen Biri”.
Atsorace Hajiya Bunayya ta juya ta kalli Hajiya Lami da itama ɗin Iran take kallo.
Sun kasa hafimtar sharrin boka na wasa da hankali da ƙarya sun kasa tuna sam bai faɗa musu hakanba a lokacin, su kasa aminta mgnar boka dubune babu gsky ko ɗaya sai yaudara da taɓewa.


Acan ɓangaren su Moddibo kuwa sake kallon madubi Khausar tayi tare dasa hannu ta gyara man lips ɗin ta sai kuma danna MP ɗin cikin Sa'a kuwa sautin waƙar BUGA ya fara tashi.
A hankali ta gyara tsayuwar ta, tare da fara jujjuya ƙugunta a hankali tana mai rausaya jikinta.
Zuwa tsakiyar waƙar kam fa da abu ya jiƙa, sai ga mayafinta bisa kafaɗarta gefe ɗaya, sosai take jujjuya mazaunenta tare da motsa dukkan jikinta, tana mai kallon kanta a madubi.
Sai kuma ta kalli Glass ɗin tare da ɗaura bakinta akai ta saki zazzafan kiss muahhhh.
Shi kuwa Moddibo dake zaune idanu ya zuba mata tare da manna kumatunsa adai-dai glass ɗin sai kuma hakan yasa lips ɗinta sauƙa kan....!




FREE page sun kusa ƙarewa 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA ki biya 1k dinki ya isheki






By
*GARKUWAR MARUBUTA*
📝✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️🍇


*SAKAYYAH*
_Page 12_


_NA_
*AYSHA ALIYU GARKUWA*


🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


*Littafin SAKAYYAH na kuɗine wannan Free page ne ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276 saura shafi huɗune kacal ana biyar na gama Free page*






Da sauri Modibbo ya rintse idanunsa, tare da shafa sajensa domin, badan glass dake tsakani ba da akan tattausan sajensa sumbatar zata sauƙa.
Shi kuwa M Jameel cikin sauri ya lumshe idanunsa tare da gyara zamansa yana fuskantar ta da kyau.
Ita kuwa Khausar hannu tasa tare da gyara zaman ɗaurin ɗan kwalinta, sai kuma ta canza Baitin da take ji zuwa.
Waƙar Lamba tana marming tamkar zabia kai kace itace ta raira waƙar, bin baitukan takeyi tana jujjuya manyan idanunta, tana mai girgiza jikinta zuwa ƙugunta.
lumshe manyan Idanunta kumayi tare da fitar da sautin zazzaƙar muryanta a fili ta tace.
“Kai zan yiwa kalamaina.
Kai zan baiwa muƙamai na. Ungo makullaina ka riƙe.
Ta ida bautin tare da nuna saitin fuskar Moddibo da yar yatsarta ma nuniya.
Wani irin shu'umin murmushi M Jameel ya sake tare da sa hannunsa ya riƙon hannun Moddibo da ya yunƙura zai ɓalle karfin motar.


Ita kuwa Khausar, cikin azama taci gaba da bin waƙar cike da zazzafan shauƙi tace.
“Ni ban furta da wasa ba, samari dukka basu kai ba, kana nan banganin kowa da ido, dan basu isheni kalloba”.
Tayi mgnar bisa alamu daga ainihin cikin ranta take bin waƙar, M Jameel kam murmushi yakeyi cike da shauƙi.
Modibbo kuwa ya cika yayi fam dan har ransa yakeji yarinyar ta tarainashi gani yake kai tsaye ma dashi takeyi, gashi kuwa M Jameel ya riƙe masa hannunsa ƙam-ƙam.


Ita kuwa Khausar mazari uwar rawa, ƙugunta da ƙirjinta take motsawa a slowly tana mai ci gaba da cewa.
“Kai zaka zauna adamana, kuma ka bani gurin kwana, wannan shine fassarar mafarkin da nake kullum cikin baccina”.
Wani irin yar-yar Moddibo yaji tsikar jikinsa na tashi domin suna jinta ras kasan cewar Glass ɗin bayan motar a suna ƙasa kaɗan.
Ita kuwa Khausar
ida baitin tayi tana mai nuna Moddibo dake kwance jikin kujeran Idanunsa alumshe da yatsan hannunta tana murmushin dake ƙarawa fuskarta kyau.


Shi kuwa Moddibo Cikin fushi ya fuzge hannunsa daga riƙon da M Jameel yayi masa tare da sanya tattauaan tafin hannunsa da niyyan buɗe motar.
Shi kuwa M Jameel cikin sauri ya riƙe tafukan hannunsa da ƙarfi tare da girgiza masa kai alamar ya bari suga iya gudun ruwanta.


Ƙwafa Moddibo yayi tare da jingina bayansa da jikin kujeran ya cigaba da kallonta.
Ita kuwa rawanta ta cigaba dayi tana Girgiza jikinta ganin abin nata ba mai ƙare wa bane yasa Moddibo buɗe motar cike da tsananin fusata.


Kamar walƙiya ko wanda ya diro daga sama haka taga Moddibo a gabanta,
Cikin tsoro, mamaki, da kiɗima kalli fuskarsa cikin zare ido ta tayi ƙasa da kanta,
domin bata tsammaci da mutum aciki ba.


Shikuwa Moddibo cikin nutsuwarsa da kuma kamala ya fito daga motar tare da tsaida idanunsa akanta yana mai ƙara tsananta suƙe fuskarta da ya ƙara razanata.


Ita kuwa cikin tsananin ruɗu da tashin hankali mara misaltuwa ta ɗaura hannunta akai.
tare da zubewa akan gwiwoyinta tana mai girgiza kanta gaba ɗaya ta gaza cewa komai.


M Jameel kuwa gefen Driver ya buɗe tare da fitowa yana dariya mai sassayan sauti,
dai-dai lokacin da Ummi da Asma'u suka fito daga cikin gidan zuwa harabar gidan.
Idanu Ummi ne suka sauƙa akan Moddibo da M Jameel kafin kuma ta maida ganinta kan Khausar dake durƙushe ta kama kai da hannunta duka biyu,
cike da mamaki asaman fuskarta Ummu tace.
“A'a ikon Allah Khausar lafiya ya dai haka!?”.
Kasa cewa komai Khausar tayi, still hannunta na kanta haka zalika ta kasa ɗago kanta banda bugawa da ƙarfi babu abinda zuciyarta keyi da ƙarfi.


Ganin Ummi da tambayar da take yiwa Khausar yasa Moddibo basarwa kamar baisan da ruwan ɗigon Khausar dake tsugunne gabansa ba,
cike da nutsuwa da kuma takun ƙasaita ya janye ƙafarsa da ya ɗaga da niyar zaiyi wasan ƙollo da Khausar ɗin yana mai maida fushinsa ya haɗiye ya juya ya nufi gaban Ummi.


Murmushi Ummi tayi Idanunta akan Moddibo tace.
“Sannun ku da zuwa Babana, dama yanzu nake shirin zuwa unguwa zanje duba jikin Maman Khausar”.
Ta ida mgnar ta maida kallonta kan Khausar da har zuwa yanzu take durƙushe sai dib dab dib dab da sautin zuciyarta ke badawa, cikin kula tace.
“A'a Khausar yaushe kika zo? ya jikin Mommyn ki?”
Ita dai Khausar bata ɗago ba bare kuma ta motsa, gani take aduk lokacin da tayi kuskuren ɗaga kanta Moddibo zai iya kifeta da azabebben marinsan nan mai sa mutum ganin taurari masu wutsiya.
Cikin kula Ummi ta juya ta kalli Moddibo dake tsaye hannunsa na acikin aljihu murmushi tayi kana tace.
“Allah yayi zaku zo ku sameni, kuzo mushiga daga ciki”.
Kai suka jinjina tare da wuceta, ita kuwa Ummi juyawa tayi zuwa gaban Khausar ɗan tsugunna tayi tare da riƙo hannun Khausar tace.
“Duk cikin gaishe da Malama ne har haka Khausar? to taso mu tafi”.
Sai asannan Khausar ta ɗago kanta tare da sakin wani nan-nauyan ajiyar zuciya, ganin Moddibo bai nan cikin mutuwar jiki tabi Ummi falon.
Suna shiga Khausar tayi saurin janye hannunta daga cikin na Ummi, kana ta kama na Asma'u suka nufi Bedroom ɗinta”.


Suna shiga Bedroom ɗin Khausar ta janye hannunta daga na Asma'u ta zauna agefen gadon Idanunta cike da ruwan hawaye ta dafe ƙirjinta tare da cewa.
“Asma'u nashiga ukuna!nikam yau naga ta kaina, Allah yana jarabtana ta hanyar haɗani da Moddibo a bauɗaɗɗen yanayi,
zuwa na kenan naji wata waƙa tamin daɗi na tsaya ina bi uwa zabiya.
Kuma kin sanima fa ni ban fiye jin waƙa ba, sannan bai dameni ba amma kawai ɗazu naji wata waƙa MP din Haiydar Wai ita Buga da Lamba kuma wallahi nasan Haiydar ne ya haxa min da bai bani aron MP ɗinsa ba ai da banjita ba bare inji yamin daɗi, kawai na kama rawa tamkar yar gala,
ashe Moddibo na kallona nikam bansan irin hukuncin da zai minba gobe amakaranta, ƙilan ma ya sake sakani kaɗe ɗan kwali nikam nashiga Ukuna! Laifi kan laifi gashi gyale na yafa ga uban turaren dana zumbuɗa ga rawa dajin waƙa Wayyo ni Batula Faɗimatuzzahara naga ta kaina!”.


Ta gumi Asma'u tayi tare da kallon, Khausar da tayi narai-narai da ido kana tace.
“Ke kam dai Khausar kamar saɓani Allah yake haɗaki dashi”.
Narai-narai tayi da ido tare da dafe kuncinta da hannun biyu kana tace.
“Mummunan saɓani ma kuwa, na sharri ma ya Allah kashiga tsakanin na gari da mugu, Allah kara bani dashi ya Allah kada ka bashi ikon zalunta na, tun da dai arashin sani nayi kuma babu wanda yafi ƙarfin kuskure ai seya min uzuri ko?”.


Janye mata tagumin Asma'u tayi tana dariya tace.
“Kece Khausar wani zubin sai ahankali, kawai daga zuwa saiki hau rawa kamar mazari da anyi magana ki wani ce Allah yashiga tsakanin na gari da mugu sannan da kike maganar uzuri a'a ba'asi za amiki ba uzuri ba kuma waye mugun waye na garin”.


Sheƙeƙe Khausar ta ɗago kai tare da tsirawa Asma'u Idanu kana tace.
“Nifa na lura dake tun ba yanzu ba, kinfi ƙaunar Moddibo dani wato har kina goyon bayan sa akan ni kin zaɓe sa kin barni? Yoh shine mugu mana ni ta gari”.
Ware idanu Asma'u tayi tare da langwaɓar da kai tana dariya tace.
“Haba ƙawar arziƙi matsayinki yafi haka, dan Allah kada ki sake faɗan hakan aise kisa ayimina dariya”.


Taɓe baki Khausar tayi tare da faɗin.
“Kinsan gwara in gane matsayina ai tun wurima,
idan kinfi ƙaunar Moddibo insan matsayina”.
Dariya mai sauti Asma'u tayi da faɗin.
“Maida wuƙar ranki shi daɗe Fattanah”.
Murmushi Khausar tayi tare da kishingiɗa akan gadon.


Acan falo kuwa bayan Moddibo da M Jameel sun sake gaisawa da Ummi ta miƙe tashiga kichen ba daɗewa ta fito hannunta riƙe da babban tray dake ɗauke da Warmers ta ajiye musu.
Murmushi Moddibo yayi yace.
“Sannu da gajiya Ummi”.
Murmushi tayi tace.
“Yawwa Babana”.
M Jameel kuwa miƙewa yayi yashiga kichen ya dauko musu Plate da cups guda biyu kana ya dawo ya zauna.
Kulan ya buɗe, da sauri ya gyara zamansa jin wani ƙamshi mai daɗin ya ratsa hancinsu.
M Jameel ya lumshe ido tare da zuba musu akan Plate.
Moddibo ya matso tare da tsirawa Pride rice ɗin da yaji vegetables da naman kaza amsar spoon ɗin da M Jameel ke miƙa masa yayi, cikin fesar da numfashi Moddibo ya ɗibi abincin ya kai bakinsa, lokaci ɗaya yaji daɗi ya mamaye masa baki, kallon Ummi yayi tare da faɗin.
“Ummi wannan girkin yayi daɗi”.
murmushi tayi tare da tsiyaya musu tea mai ɗumi.


Bayan sun gama ci.
M Jameel ya goge bakinsa da tissue kana yace.
“Ummi ɗazun ina zakije dama?”.
Tana matsar da Flaks ɗin tea tace.
“Wallahi Maman Khausar zanje dubawa, bata da lafiya shekaran jiya a asibiti suka kwana jiya ne aka sallame su da safe”.


Girgiza kai yayu kana yace.
“Ayyah Subhanallah Allah yabata lafiya Allah yasa zakkan jikine”.
Amin Ummu tace.
Yayinda shi kuwa Moddibo Aransa yace. “Uhhhm yarinyar kamar aljana ita da mahaifiyar ta babu lafiya har ankwantar da ita a asibiti jiya-jiya aka sallame su, amma yau har ta gararo yawo, har tana rawa agidan mutane kamar wacce aka yiwa bushara da Aljanna, ita kuwa wannan daɗin me takeji”. sai kuma ya taɓe baki takaicin halayyar yarinya yasa bece musu komai amaganar ba.
Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da faɗin.
“Toh Ummi mu zamu tafi”.
Ummi ta juya ta kallesa da murmushi afuskarta tace.
“Da wuri haka Babana?”.
M Jameel ne yace.
“Ai dama a gaggauce muka zo Ummi, dan kwana biyun nan naga ya maida hankalinsa akan rubutun da yake inagama ya kusan gamawa”.


Ummi kuwa kallonta ta mayar kan Moddibo kana tace.
“Masha Allah Ubangiji Allah ya taimaka, ya kuma baku sa'a ka kusa gama wa kenan?”.
Cike da nitsuwa Moddibo ya amsa da.
“Ameen”,Kana yace.
“Eh Ummi na kusa gamawa, amma waɗan da na tura ƙasar Ɓadamaya ma tukunna wanda na turawa, Sheykh Jabeer ya duba min su har yau basu dawo ba, to inaso kawai na haɗa wa'annan ma dake wancan bugun Hafs ne wannan kuma Warash ne”.
Yai da mgnar tare sauƙe numfashi kana ya cigaba da cewa.
Warash ne nake rubuta wa to inaso idan nagama rubuta wannan ɗin na tura masa, wala Allah ya tuna mishi da duba wancan ɗin.
Nasani abubuwa ne suka masa yawa da yake ya wanci yakin arewacin nan duk wanda ya rubuta Kur'ani shi ya ake turawa sai ya duba yagani toh zanyi ƙoƙari na gama rubuta wannan ɗin sai ahaɗa akai gaba ɗaya ko zan samu ya haɗa min su lokaci ɗaya idan ya duba ingancin su”.


Jinjina kai Ummu tayi cike da yabawa jajurcewarsa da kuma ƙoƙarin sa tace.
“Masha Allah Allah yatemaka Allah ya bada sa'a abu yayi kyau Allah yabar mana irinku Moddibo Allah yayi jagora”.


Moddibo kuwa cikin jin daɗin addu'ar ta yace.
“Ameen Ummi Allah ya amsa Nagode”.
Miƙewa M Jameel yayi idanunsa akan Ummin sa yace.
“Ummi zamu tafi”.
Tana ƙoƙarin kwashe Plate da sukayi amfani dashi tace.
“Toh Nagode Allah ya muku albarka”.
Suka haɗa baki wajen faɗin.
“Ameen”.
kana suka fice.


Bayan sun ɗauki hanya M Jameel ya dubi Moddibo wanda shike Driving ɗin yanzu yace.
“Ni ka sauƙe ni agida”.
Moddibo da still hankalin sa ke kan Driving yace.
“Ba zamu tafi tare ba?”.
Girgiza kai M Jameel yayi kana yace.
“A'a nasan rubuta zaka je kayi sannan Abba ya kirani akan batun yana so naje Ɓadamaye batun Company sa akwai sabbin Injina da aka kawo, za'a saka kaga na daɗe ban jeba, amma wannan karon ko naje baze wuce kwana biyu zanyi in dawo ba”.


Moddibo kuwa jinjina kai yayi kana yace.
“Toh yaushene tafiyar?”.
Kai M Jameel ya Girgiza tare da faɗin.
“Toh dai ban sani ba tukun”.
Moddibo dake ƙoƙarin shan kwana yace.
“Yawwa zanyi ƙoƙari inga na gama rubutunan idan zaka tafi sai ka tafi min dashi”.


Shi kuwa M Jameel Kai ya gyaɗa cike da gamsuwa da maganarsa yace.
“Toh shikenan hakan ma yayi Allah yatemaka”.
Moddibo ya amsa da.
“Ameen”,tare da parking motar bayan ya isa ƙofar gidan su M Jameel.
Sauƙa M Jameel yayi tare da yi masa sai anjima, kai Moddibo ya gyaɗa kana yaja motar ya tafi.


Yana isa gida bayan yayi Parking motarsa ya wuce Bedroom ɗinsa kasancewar yana da alwala yasa ya ɗauko abubuwan buƙatar sa na rubun Alkur'ani da yakeyu kana yaciigaba da rubutu, saida aka kira sallar La'asar sannan ya tashi yaje masallaci ya gabatar da sallan la'asar, bayan ya dawo kuma, yazo ya cigaba da rubutun, yana yi yana karantar Suratul Kahfi kasancewar yammacin jumma'a ne, sai misalin ƙarfe biyar kafin ya ajiye Kur'ani.


Acan ɓangaren Innayi kuwa zaune take akan kujera ’yar tsugunno acikin kichen tana juya miyar zogala wanda yaji namar Rago da kuma wadataccen man Shanu da wake yana tashin ƙamshi bayan ta sauƙe miyar ta ɗaura Ruwan shayi daya ji na'ana, kaninfari da kuma ɗanyan citta yana tafasowa yana ƙamashi mai daɗin shaka.
Flaks guda biyu ta ɗauka ta juye sannan ta ɗauki ɗaya ta nufi sashen Moddibo dashi.


Acan gidansu Asma'u kuwa bayan tafiyar Moddibo da M Jameel Khausar ta miƙe tare da fitowa falon Idanunta akan Ummi tace.
“Toh Ummi mu tafi ba dama kince gidan mu zaki jeba”.
Jinjina kai Ummi tayi tace.
“Eh Khausar inaso naje na duba jikin Mommyn ki”.
Ba tare data zauna ba tace.
“Toh Ummi mu tafi”.
Kai Ummi ta jinjina kana ta miƙe suka fita su ukun Bashir ƙanin Asma'u ne kaɗai suka bari agida Ummi da kanta take Driving Khausar da Asma'u na baya suna hira.


Acan ɓangaren su Hajiya Bunayya kuwa Kallonsu Boka Kar'uzu yayi cikin wata razananniyar tsawa yace.
“Wannan maganin ya riga daya ɓaci, ta lalata komai yanzu sai anyi aikin dai-dai-ta fuskarta ma tukunna kafin azo ayi aikin jawo hankalinsa, yaran nan biyu da kuka gani kuke magana akansu yarane dasu na tsaye da sunan Allah da riƙo da Ibada, musamman ma Moddibo da kuke magana akansa kwata-kwata baya rabuwa da alwala ajikinsa ka masa zaiyi wuya”.
Cikin tashin hankali Hajiya Bunayya ta juya ta kalli Hajiya Lami da duk tagama shiga ruɗu.


Boka Kar'uzu kuwa cigaba yayi da cewa.
“Yanzu sai munyi aikin wata uku kafin fuskarta ya dawo dai-dai sannan sai tabar Sallah na tsawon watanni shida kafin mu samu

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads