Header Ads
Showing 153001 words to 156000 words out of 188939 words

Chapter 52 - SAKAYYA Book 1 complete BY GARKUWA.txt

Ads the beginning of article before Image
Ads at the middle of Article

ƴan sandan jahan Taraba masu bincike akan abinda ya shafi ɓatan mutane da kuma kisan kai kana da fashi da makami ina fatan zaku bamu haɗin kai.
Mun samu kirane daga nan ƙaramin Headquarter din mu”,'.
Sai kuma ya sauƙe numfashi tare da kallon Moddibo da yayi ƙasa da kansa kana yana motsa laɓɓansa alamar tasbihi yake.
Kana ya cigaba da cewa.
“Mun samu masaniya Kan cewa Jameel ɗan Alhj Bashiru Maidala ya ɓata shiyasa nazo da kaina inji ba'asin maganar sannan muga ta inda ya kamata mu fara da taimakon Allah da kuma baya nan da zaku bamu zamuyi nasara wajen gano inda yake”.
Jinjina kai Abba yayi tare da rintse idanunsa kana ya fesar da numfashi tare da sunkuyar da kansa ƙasa hawaye masu zafi suka zubo masa.
Cike da tausayawa Asp Mahmud Adam Shani yace.
“Alhj ka kwantar da hankalin ka kayi min duk kan bayanin da zan gane saboda yanda zamu kula da aikin da kuma abinda ya kamata ayi akai”.
Jinjina kai Abba yayi tare da ƙoƙarin hana hawayensa zuba kana ya daure yace.
“Jameelu nine mutum na ƙarshe da yayi sallama dani ya fita ina tsaye ajikin window har ya fita bayan fitarsa na kai kimanin awa ɗaya da rabi ina tsaye ajikin window, Bayan nan kuma duk cikin mu babu wanda yayi magana da Jameelu domin ya fita akan zaije wajen Abokinsa amma bai isa ba”.
A hankali ya fesar da zazzafan iska tare da taune lip ɗin sa na ƙasa tare da kallon Asp Mahmud Adam Shani kana yace.
“Adaren Abokinsa yazo domin rashin samun layinsa da bai yiba”.
Jinjina kai Asp Yayi kana yace.
“Eh anyi min wannan bayanin daga Headquarter din mu na Nan Inspector Ayuba Garba kumo ya sanar dani komai to amma daga ɓatansa zuwa yanzu babu wanda ya kira ka!?”.
Cikin sauri Abba ya Girgiza masa kai kana yace.
“A'a babu".
Ido Asp ya zuba masa kana yace.
“A'a Alhj Bashir dan Allah kada kuce zaku bi sharuddan ire-iren mutane masu garkuwa da mutane, idan har akwai wanda ya kira ka ya maka barazana ko kuma ya nemi wani abu ka faɗa mana ko kuma ka bami number da suka kira Insha Allahu Jameelu zai kuɓuta sannan zai rayu da izinin Ubangiji zamu tsera tar dashi”.
Moddibo kuwa cikin sauri ya kalli Asp zuciyarsa na bugawa da masifar ƙarfi ya Girgiza kai tare da cewa.
“Babu wanda ya kira ai da akwai wanda ya kira zamu sanar daku sannan mu ma da hankalin mu zaifi kwanciya ma, mun san cewa yana raye”.
Ido Asp ya tsira musu kana yace.
“Anya kuwa anya babu wanda ya kira ku!?”.
Cikin sauri Moddibo ya gyaɗa kai kana cikin ƙoƙarin dai-dai-ta nutsuwarsa yace.
“Babu wanda ya kira tashin hankalin mu kenan”.
Abba ya karɓi maganar da cewa.
“Da har ankira Asp Mahmud da ace ankira kamar yanda kake zaton ƴan Kidnapping ne kuma sun buƙaci kuɗin ai da tuntuni nayi muku bayani sannan idan yakama da in basu kuɗi zasu dawo min da Jameelu na da tuni na bayar an dawo min da Jameelu na!”.


Anutse Asp ya gyara zamansa kana cikin sauri yace.
“Alhj na roƙe ka dan Allah koda ankira ance kuɗi ake buƙata kada ka basu, kawai ka bamu Number sannan kayi mana bayani shine abinda muke bukata amma ana temakamu sune sannan ana ƙara basu ƙarfin gwiwa dayi musu abinda suke so shiyasa suke ƙara yin abinda suke su ɗin”.
Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe tare da jingina bayansa da jikin kujeran kana yace.
“Insha Allahu zanyi ƙoƙari duk abinda ake ciki zan sanar muku Nagode sosai musamman tattakin da kayi daga Taraba zuwa nan”.
Dai-dai lokacin Hajiya Karima tazo Idanunta akan Asp Mahmud Adam Shani da sauran Folisawan Kallonta ta mayar kan Abba kana tace.
“A baƙi mukayi ne sannun ku da zuwa”.
Asp dake rubutu awata ƙaramar takarda yace.
“Yawwa”.
Kana ya cigaba da rubuce-rubucen sa.


Kallon Abba Hajiya Karima tayi tare da kallon Moddibo da idanunsa ke lumshe haƙoransa uku na sama na kan laɓɓansa na ƙasa numfashi ta fesar kana ta ƙara sa kusa da Abba da har zuwa lokacin bayansa ke jingine ajikin kujera tace.
“Alh ga Hajiya Fatima mahaifiyar Jameel ta iso”.
Ahankali Abba ya ɗago kansa kana cikin sanyin murya yace.
“Kice ta iso”.
Kai ta gyaɗa tare da juyawa ta fita ba jimawa ta shigo Ummi na biye da ita Ahankali Ummi ta ƙara sa kusa da Moddibo ta zauna Hajiya Karima ta juya ta fice cike da tausayawa Moddibo da Abba ke kallonta ganin yanda Idanunta suka kumbura sukayi jawur sun ƙanƙance.


Anutse Asp ya ɗago kansa tare da kallon Ummi kana yace.
“Wannan ce mahaifiyarsa?”.
Kai Abba ya gyaɗa tare da faɗin.
“Eh itace”.
Atausashe Asp ya gyara zamansa tare da cewa.
“Sannu Mmn Jameel Ubangiji Allah ya bayyana sa ya kuma tsaresa aduk inda yake, ki kwantar da hankalinki in sha Allah zamuyi iyakar iyawarmu zamu samoshi a duk inda yake”.
Kai ta gyaɗa cikin muryanta daya dishe da kuka tace.
“Ameen ya Allah”.
Miƙewa Asp Yayi kana yace.
“Alhj to bari mu tafi amma dan Allah duk abinda ake ciki a faɗa mana”.
Kai Abba ya jinjina tare da cewa.
“Toh Insha Allah”.
Bayan tafiyarsu Ummi ta juya tare da kallon Abba cikin raunin murya tace.
“Alhj har yanzu basu sake kira ba!?”.
Kai Abba ya gyaɗa kana yace.
“Fatima har yanzu basu kira ba”.
A raunace ta sanya gefen hijabinta tare da share hawayen da suka zubo mata kana tace.
“To idan sun sake kira duk abinda suke so dan girman Allah kataima keni kaceci rayuwar Jameel kayi musu”.


Girgiza kai Abba yayi idanunsa na tara ƙwalla yace.
“Fatima ba sai kin roƙeni kin haɗa Ni da Allah ba, idan har banyi musu abinda suke so andawo min da Jameel ba menene amfanin dukiyata?”.
Sai kuma ya runtse Idanunsa kana ya cigaba da cewa.
“Jameel yafi min komai aduniyar nan zan iya sadaukar da duk dukiyata domin ceton rayuwar Jameel insha Allah zanyi iya bakin ƙoƙarina wajen ganin ya dawo”.
Ajiyar zuciya ta sauƙe kana tace.
“Toh shikenan Nagode Ubangiji Allah ya kuɓutar dashi Allah yasa su faɗi abu mai sauƙi kada su faɗi abinda yafi ƙarfin mu Allah ya tsaresa Allah yasa yana cikin ƙoshin lafiya”.
Atare Moddibo da Abba ke Amsawa da Ameen cike da tausayawa.
Kallon Abba tayi kana tace.
“Bari na tafi gida”.
Kai Abba ya gyaɗa kana yace.
“Toh shikenan”.
Cikin sanyin murya Moddibo yace.
“Ummi muje in kaiki gida”.
Kai ta gyaɗa kana ta miƙe.
Suka fita da kallo Abba ya bisu cike da tausayawa.


Moddibo kuwa yana ajiye Ummi agida kai tsaye makarantar Malam Arɗo ya nufa yana isa yayi Parking tare da fita ya nufi harabar makarantar iska na kaɗa shi kai tsaye Office din malam Arɗo ya Murɗa handle din ya shiga bakinsa ɗauke da Sallama.


Anutse Malam Arɗo dake duba wani littafi ya ɗago kansa tare da sauƙe Idanunsa akan Moddibo ganinsa cikin wani irin yanayi yasa yayi saurin miƙewa tare da riƙe hannun sa kana yace.
“Moddibo ya dai?”.
Kai Moddibo ya Girgiza cikin sanyin murya yace.
“Bakomai”.
Kujera Malam Arɗo yaja masa ya zauna kana shima ya koma mazauninsa.


Cike da kulawa Malam Arɗo yace.
“To ina ƴan biyun naka?”.
ƙasa yayi da kansa tare da runtse Idanunsa kasancewar sa ba mai saurin kuka ba ya tabbata da ace yana da saurin kuka da zaran an ambaci sunan J ɗin sa zaiyi kuka ko hakan zaisa ya samu sassaucin abinda yake ji Aransa ya sake damƙe lip ɗin sa da ƙarfi wanda zuwa lokacin ya sake kumbura kana yayi ja sai sheƙi yake.


Ido Malam Arɗo ya tsira masa kana yace.
“Ya dai Aliyu mai yake faruwa da Jameelu tun jiya da yamma naji ana raɗe-raɗin wai ba agansa ba nayi ta kiran wayarka baka ɗauka sannan shi kuma idan na kirasa akashe ina Jameelu da gaske ne babu shi!??”.
Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da ɗago kansa still yana taune da lip ɗinsa kana cikin raunin murya yace.
“Babu J”.
Kai Malam Arɗo ya gyaɗa kana yace.
“Na sani Aliyu ka nutsu ka dawo hayyacinka Aliyu na sani babu Jameelu sannan na gaskata tunda har naga kai kaɗai kazo nan na tabbata do min idan anganka tamkar anga wata ne dole za'aga zara”.
Ya faɗa tare da miƙewa ya dafa kafaɗar sa.
Runtse Idanu Moddibo yayi


“Yanzu ya ake ciki?”.
Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da shafa ƙirjinsa dake bugawa da ƙarfi kana yace.
“Nima kaina ya kulle a duniya bansan me zanyi ba bansan ya zanyi na ganni da J ba?”.
Dafa kafaɗar sa Malam Arɗo yayi cike da tausayawa yace.
“Toh yanzu wani mataki aka ɗauka akan lamarin!?”.


Cikin raunin murya yace.
“Babban matakin da aka ɗauka shine addu'a da faɗawa Ubangiji abinda yake faruwa”.
Jinjina kai Malam Arɗo yayi tare da faɗin.
“An ɗauki mataki mai kyau, da girma wanda ya dace da dukkan Musulmi yanzu mu shiga cikin makaranta mu faɗawa yara su tayamu da addu'a Ubangiji Allah ya tsare malam Jameelu ya kuma bayyana sa aduk inda yake”.
Kai Moddibo ya gyaɗa tare da miƙewa kana yace.
“Toh Nagode Allah ya saka da alkhairi”.


Hannunsa Malam Arɗo ya riƙe bayan ya mike suka fita kai tsaye bangaren ƴan primary suka fara shiga Ajinsu Ramadan da Raudat yaran na ganinsa suka miƙe cike da farin ciki suna cewa Moddibo Moddibo Kusan a tare Raudat Ramadan da wasu ɗalibai uku suka ce Moddibo ina Malam Jameel munyi kewar ku bakwa zuwa.
Lumshe Idanunsa da yaji suna masa zafi da zaran an ambaci sunan J ɗin sa zuciyarsa zata buga da masifar ƙarfi tsayuwar sa ya gyara agaban ajin tare da cewa.
“Ina ɗaliban Malam Jameel?”.
Baki ɗaya yaran suka ɗaga hannu suna tsalle tare da cewa gamu nan Moddibo ina yake munyi kewarsa bakwa zuwa yanzu, dan Allah kace yazo muna san ganinsa.
Kasa furta komai Moddibo yayi hakan yasa ya jingina bayansa da jikin bango yayi ƙasa da kansa yasan yanda J ɗin sa ke son Yara da kuma wasa da su wanda a ra'ayinsa baison koyar da yara amma saboda yanda J ɗin sa ke son Yara Yasa yake shiga koyar musu ganin haka yasa Malam Arɗo yayi gyaran murya Atake duk yaran suka nutsu tare da tsirawa Malam Arɗo ido.
A hankali Malam Arɗo ya sauƙe tare da faɗin.
“Kuna jina?”.
Kai suka gyaɗa masa.
Ya sauƙe numfashi tare da cewa.
“To zaku yiwa Malam Jameel din ku addu'a Allah ya bayyana shi?”.
Aruɗe yaran suka ce Malam Jameel ya ɓata ne?."
Kai Modibbo ya gyaɗa musu cike da damuwa.
Cikin zare ido Raudat tace.
“Malam Jameel din mu ya ɓata kuma to ina yaje?”.
Ramadan kuwa miƙewa yayi tare da zuwa gaban blackboard ɗin cikin yanayin damuwa sosai ya riƙe hannun Moddibo da har zuwa lokacin Idanunsa ke lumshe yace.
“Moddibo ina Malam Jameel ɗin mu yaje dan Allah ka kira wayansa kace ya dawo Muna so sa”.
Kasa cewa komai Moddibo yayi sabida zulumi.
Gyaran murya Malam Arɗo yayi tare da cewa.
“Kuyi masa addu'a Allah ya bayyana shi idan kunyi sallah kuyi addu'a Allah ya bayyana Malam Jameel sannan ku faɗawa iyayenku suma suyi masa addu'a Allah ya karesa ya kuma dawo dashi cikin aminci da salama”.
Hawaye Ramadan ya fara zubdawa tare da cewa.
“Toh Malam zamuyi masa addu'a zan faɗawa Mommy da Addah Khausina suma zasuyi masa addu'a Allah zai dawo dashi”.
Ahankali Moddibo ya shafa kansa tare da cewa.
“Yawwa Ramadan kuyi masa addu'a ayanzu babu abinda Malam Jameel yake buƙata awajen mu face addu'a”
Cikin rauni sosai yaran suka ce zamu yi masa.
Cikin sanyin jiki Malam Arɗo da Moddibo suka fita zuwa bangaren Secondary bayan sun fita anan suka shiga ɓangaren na naziri saida suka gama zagaye ko wani aji suna sanarwa Ayiwa Malam Jameel addu'a Ubangiji Allah ya bayyana shi cikin tashin hankali ɗalibai suka shiga masa addu'a.


Bayan sun fito Moddibo ya nufi hanyar gate
Cikin kula malam Arɗo yace.
“Moddibo baza ka shiga office din ku ba?”.
Kai ya girgiza tare da cewa.
“Um-um bazan shiga ba zan tafi bazan iya zama babu J ba”.
Ya faɗa tare da ficewa yashiga motarsa kai tsaye gidan Abban M Jameel ya nufa bayan yayi Parking ya fito tare da shiga falon bakinsa ɗauke da Sallama A inda ya fita yabar Abba anan ya dawo ya sameshi zaune still wayarsa na gabansa ya zubanusu Ido da alama tun bayan fitarsa ko motsawa baiyi ba.


Ahankali Abba ya ɗago kai tare da zuba masa ido cike da tausayinsa baki ɗaya ya rame ya canza idanunsa sun sake girma da ja kana idanunsa sun faɗa, Ahankali Moddibo ya ƙaraso ya zauna agefensa aƙasan Capet Cike da tausayawa Abba yace.
“Aliyu ba kayi wanka ka sauya kaya ba”.
Siririn tsaki Moddibo yaja tare da yin ƙasa da kansa kana yace.
“Abba har yanzu basu sake kira ba!?”.
Kai Abba ya Girgiza tare da cewa.
“Har yanzu basu sake kira ba gani nan ina zaune tamkar gadin waya nake sai tsumayin kiransu nake amma basu kira ba, amma yanzu ka samu kaje kayi wanka ka samu kaci abinci”.


“Abba banajin yuwa”.


“Ya zamuyi Aliyu idan kaima baka ci abinci ba ai faduwa zakayi. Insha Allah addu'ar mu bazai bar Jameelu ya ta gayyara ba”.
Sai ya kuma maida kallonsa kan Hajiya Karima data shigo wacce ita ma baki ɗaya tayi sanyi ahankali yace.
“Ki zubawa Aliyu sbinci”.
Kai ta gyaɗa tare da nufar dining ta ɗauki Plate ta zuba masa jollof fice da yaji bushesh-shen kifi da namar kaza ta kawo masa.
Moddibo kuwa hannu ya daga mata alamar kada ta ajiye masa ganin ta ajiye yasa ya maida kansa jikin kushin ɗin ya jingina tare da lumshe idanunsa yace.
“Ina ma ace tare suka ɗauke Ni da J da yafi min farin ciki ina rayu dashi aduk inda yake duk halin da yake ciki ace muna tare wallahi da yafi min farin ciki akan rabani da Jameel da sukayi”.
Kallonsa Abba yayi cike da tausayawa wannan shine karo na farko arayuwar sa da yaji Moddibo ya kira Complete sunan M Jameel cikin raunin murya yace.
“Toh ya zamuyi Aliyu ka daure kaci abinci”.


“Abba ba zan iya cin abinci ba”.
Cikin rarrashi Abba yace.
“Haba Aliyu ka naso kasake sa kamu cikin damuwa ne rashin cin abinka dai dai yake da yiwa kan ka illah, wanda bazan so hakan ba dan Allah ka daure kasa wani abu acikin ka”.
Kai Moddibo ya gyaɗa kana yace.
“Toh Abba abani tea”.
Miƙewa Hajiya Karima tayi ta nufi dining kana ta haɗa masa tea cup ɗaya ta kawo masa ahankali ya karba tare da kaiwa bakinsa da ƙyar ya iya shan rabi ya ajiye Cup ɗin.
Abba bai tilasta shiba dan shima akaran kansa yasan ba zai iya saka komai acikin sa ba baya ga tea ɗin da yake sha dan raya kai, cikin sanyin murya yace.
“Aliyu kaje ɗakin Jameelu kayi wanka ka sauya kaya”.
Girgiza kai yayi cikin rawan murya yace.
“Abba bari in je gida saboda nabar Innayi ita kaɗai tun safe sannan na barta cikin damuwa”.
Kai Abba ya gyaɗa tare da cewa.
“Toh Aliyu ka gaisheta”.


Yana isa gida yayi Parking tare da wucewa Bedroom ɗin sa, kai tsaye toilet ya shiga tare da sakarwa kansa ruwan sanyi sai alokacin ya lura da Dick ɗin sa daya kwanta luƙui tamkar bai taɓa tashi ba tsanananin fargaba da tashin hankali da yake ciki yasa ya kasa tantance shin shi ɗin wani irin halitta ko kuma wanne irin jinsi ne shin shi ɗin namiji ne ko mace baisan matsayin da yake ba bare kuma ace sha'awa baki daya Dick ɗin sa ya kwanta tamkar babu wani abu mai suna sha'awa daya taɓa ji cikin sanyi Jiki ya gama wankan tare da fitowa ya shirya cikin Jallabiya kana ya fesa turare kai tsaye sashen Innayi ya nufa.


Misalin ƙarfe 5:00pm da wasu Mintuna bayan antaso Amakaranta motarsu Ramadan na shiga harabar gidan tayi Parking Ramadan ya ɓude tare da ficewa da gudu.
Acan falo kuwa Mommy da Khausar ce zaune suna kallon TV cikin tashar Nat geo well Suna kallon namomin daji Ramadan ya shigo tare da zama gefen Khausar kana ya langwaɓar da kansa tare da cewa.
“Addah Khausi”.
Hankalinta na kan wasu irin halittun ruwa tace.
“Na'am Ramadan”.
Cikin muryan rauni yace.
“Addah Khausi wai Malam Jameel ya ɓata”.
Cikin sauri ta kallesa tare da riƙe hannunsa kana cike da mamaki tace.
“Malam Jameel ya ɓata kuma!?”.
Kai ya gyaɗa mata kana yace.
“Eh Addah Khausi Moddibo da Malam Arɗo su suka shiga ajinmu suka faɗa mana Malam Jameel ya ɓata ba asan inda yake ba”.
Cike da mamaki da kuma al'ajabi Khausar tace.
“Ha'a wace iriyar magana ce wannan Malam Jameel ya ɓata ba'a san inda yake ba!?”.


Mommy kuwa cike da mamaki take kallon Ramadan kana tace.
“Ramadan ka tabbatar kuwa?”.
Kafin yace wani abu Raudat ta shigo da kuka fuskarta jage-jage da hawaye kana ta zauna kusa da Mommy tare da cewa.
“Wallahi Mommy wai ya ɓata!”.
Da sauri Mommy ta ɗauki wayarta dake hannun kujera kana tace.
“Gashi kiramin Umminsa”.
Amsar wayar Khausar tayi still da mamaki atare da ita tace.
“Eyyy aikuwa Jiya naga miss call ɗin Asma'u bana wajen daga baya kuma da nazo ina ta kiranta bata ɗaga ba”.
Dai-dai lokacin Hajiya Bunayya ta shigo sanye da hijabi har ƙasa kana ta zauna kusa da Khausar dake laluɓo number Ummi ya zama na sun sa Ramadan Atsakiya kasancewar kujeran 2sitter ne.


Bayan Mommy ta amsa Sallamar ta tace.
“Hajiya wai kinji abinda yaran nan suke faɗa wai Malam Jameel ya ɓata!”.
Kai Hajiya Bunayya ta gyaɗa tare da cewa.
“Eh dama baki ji bane aini tun jiya da yamma Aminu ke faɗa min wai yaji Amasallaci ana cewa ayi addu'a Allah ya bayyana ya kuma tsaresa ashe dama ba kiji ba?”.
Kai Mommy ta.
Girgiza fuska cike da damuwa tace.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Wallahi ban jiba Subhanallah ya Salam Ubangiji Allah ya tsaresa”.


Hajiya Bunayya kuwa ahankali ta saci kallon Mommy sai taga idanunta nakan Khausar data maƙala waya akunnenta cike da dabara ta sake murza turaren dake hannunta kana ta fito dashi ta ɗaura akan Ramadan tana shafa masa aranta kuwa fari fess tana cewa Alhamdulillah wannan turaren dai na samu na shafa masa saura kuma gobe in faɗawa Boka Kar'uzu na shafa masa turaren.


Khausar kuwa jin Asma'u tayi Picking call ɗin yasa cikin sauri tace.
“Asma'u”.
Cikin wata dashash-shiyar murya mai cike da rauni Asma'u tace.
“Na'am Khausar”.
Cikin alamun damuwa Khausar tace.
“Asma'u wai me nake ji?”.
Cikin muryan kuka Asma'u tace.
“Khausar an sace Yah Jameel yau kwana biyu kenan kusan na uku ba Yaya Jameel ba labarinsa”.
Atsorace Khausar ta dafe hannunta aƙirji kana tace.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n ansace Yah Jameel Kuma?”.
Kai Asma'u ta gyaɗa hawaye na bin kuncinta tace.
“Eh”,
Cikin sanyin murya tace.
“Ubangiji Allah ya bayyana shi aduk inda yake Allah ya fito mana dashi”.
Ameen Asma'u ta amsa tare da katse kiran.


Kallon Mommy Khausar cikin tashin hankali tace.
“Mommy wallahi da gaske an sace sa”.
Girgiza kai Mommy tayi tare da cewa.
“Ya Salam

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads