Showing 84001 words to 87000 words out of 132567 words
Chapter 29 - BARRISTER IBRAHIM KHALIL Complete Document by Nafisa Isma'il Lawal.txt
yanda zata ji daɗi sannan takoma tazauna tana kallon ta, cikin tausayin ta tace "Daughter don Allah ki dena kukan haka nan, kinsan bazan ji daɗi ba idan naga hankalin ki ba'a kwance ba".
Share hawayen ta Saleema tayi wasu na sake fitowa, cikin muryan mara lafiya sosai tace "Ummi shikenan idan nasami ciki zai dinga zube wa bazan haihu ba? Kullum haka zan riƙa shan wahala idan na samu ciki?"
Hannun ta Ummi taruƙo cikin lallami tace "kar ki damu komi ya wuce zaki haifi yaron ki kema?.."
"Taya Ummi bayan ina da matsala?" Takatse Ummin da faɗin hakan idanun ta na zirarar da hawaye
Ummi har ta buɗe baki zata yi magana Halwa taturo ƙofan tashigo, daga school tabiyo ta nan tunda dama haka take yi
Ganin Saleema zaune ya matuƙar faranta ranta, nan da nan tawashe bakin ta tanufo bakin gadon tana faɗin
"Sister kin tashi?"
Sai kuma tasauya fuska tana kallon Ummi tace "Ummi me yafaru ne meyasaka take yin kuka?"
Numfashi Ummi taja kafin tace "tunda tatashi take yin kuka sabida cikin ta ya zube".
Kallon ta Halwa tayi kafin tariƙe ɗaya hannun ta da Ummi bata riƙe ba tace "Sister meyasa zaki riƙa saka ma kanki damuwa bayan kinsan kina fama da ciwo? Don Allah ki dena in ba so kike mu ma mushiga wani hali ba".
Cikin rawan baki Saleeman tabuɗe baki zata yi magana sai kuma takasa sabida kukan da yataho mata, saurin duƙar da kanta tayi tana sakin kukan ahankali
Itama Halwa sai tasoma kuka tana sake riƙe hannun ta sosai
Ummi tace "kiyi shiru don Allah Saleema Allah ne yabaki cikin nan kuma shine ya'amsa ko baki yarda da ƙaddara bane?"
Shiru Saleeman tayi sai dai bata yi magana ba tana sauraron Ummi ɗin da taci gaba da maganar ta, cakk tahaɗiye sauran kukan nata tana ɗago kanta tana kallon Ummin, sai kuma takalli Halwa da tasakar mata murmushi tana gyaɗa mata kai alaman tabbaci da abinda Ummi ke faɗi
Shafa fuskar ta Ummi tayi tana murmushi tace "Halwa ta amince zata rainan miki cikin ki har tahaifa miki, sai dai ban sanar ma Abban ki ba don kar yahana, amma kuma da yardan Khalil muka yanke hukunci, yanzu kar ki bari Abban ki yaji ko kuma wani kinji? Mun yanke hukunci Halwa zata yi rainon cikin a sirri ne".
Saleema kallon Halwa kawai take yi cike da farin ciki, tabbas bata san da bakin da zata yi ma Halwa godiya ba, kawai sai tafashe da kukan farin ciki tana faɗin
"Wlh bansan da bakin da zan miki godiya ba ƴar uwata, amma na san cewa..."
"Shiiiiiiii... Yi shiru my Sister".
Halwa tafaɗa tana rufe mata baki, sannan taci gaba da faɗin
"Duk abinda zan miki Sister babu godiya a tsakanin mu, ke ce kika taimaki rayuwata a lokacin da narasa tudun dafawa, inda baki shigo rayuwata ba a yanzu bansan wani hali zan shiga ba, duk abinda zan yi wlh sister bazan taɓa biyan ki ba don haka kar ki soma kiyi min godiya kinji?"
Taƙarike maganar tana cire hannun ta kan bakin Saleeman, idanun ta cike da hawaye
Murmushi Saleema tasaki hawaye na zirara a kuncin ta
Hannu tasaka tashare mata lokacin itama nata sun zubo
Ummi kuwa kallon su take yi cike da farin ciki, ta gode Allah da yahaɗa su da Halwa, idan ba ita ba babu wanda zai iya taimaka ma ƴar su, tabbas ta cancanci Godiya me yawa
Murmushi tayi tace "yanzu to bari in haɗa miki tea ɗin kisha kar doctor yadawo tunda hankalin ki ya kwanta".
Kallon Ummin suka yi gaba ɗaya suna murmushi
Vowel tasoma ɗauko wa tare da ruwa tace "ki wanke bakin ki don kiji daɗin bakin, bari in taimaka miki".
Amsar Vowel ɗin Halwa tayi tace "kawo Ummi bari in taimaka mata".
Da taimakon Halwa Saleema tawanke bakin ta don ko kaɗan bata da ƙarfi ajikin ta, bayan ta gama tasha tea ɗin kaɗan
Doctor da yadawo yaɗaura mata Drip sannan yabata magani, babu jimawa tasoma barci tunda har da maganin barci aka bata don samun hutun ta
Sanda su Abba suka zo suka ji ta farka jikin kuma alhmadulillah sun ji daɗi sosai, tunda basu yi zaton hakan ba, amma Alhmadulillah kowa yake faɗi.
[11/26/2020, 6:00 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎓
🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuDahirah*👈
*\F.W.A📚/*
```ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH```
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
*BOOK TWO*
.
_______________________________
*CHAPTER Ten*
________🎓 Satin Saleema biyu acikin asibitin kafin abata sallama tunda ta samu sauƙi sosai
A ranan da aka sallame ta Ummi tasamu Abba da maganar komawar Halwa gidan Saleema ɗin a matsayin zata zauna da ita
Abba be kawo komi akai ba ya'amince tunda shi da kansa Khalil ɗin yabuƙaci hakan kamar yanda Ummi tafaɗa masa
A ranan Halwa tahaɗa kayan ta da komi drever yakai ta gidan, ɗakin da Lubna tazauna ada nan aka gyara mata komi sai da Khalil yasauya mata na ciki
Wannan ranan kuma tazo ma Khalil cikin wani irin farin ciki, sosai yatsinci kansa a matuƙar murna kasancewar sa gida ɗaya da abar kaunar sa.
Tun daga ranan Halwa take musu komi girki, gyaran gida da duk abinda yadace, har alokacin kuma gaisuwa kaɗai ke haɗa su
Ahaka har kwanaki suka shuɗe inda Saleema tasake samun sauƙi sosai, a lokacin ne kuma suka shirya gaba ɗaya suka tafi asibiti inda za'a yi aikin saka ma Halwa ƙwayoyin haihuwar su don tahaifa musu ɗa, Ma'ana Invibrosfertilization a turance
A can suka haɗu da Ummi tana jiran su, babu ɓata lokaci Likita yahaɗa duk abinda Yakamata sannan aka shigar dasu ɗakin Theater aka yi, a lokacin ne kuma aka juyar ma Saleema da mahaifa batare da ta sani ba, tunda ita a tunanin ta duk aikin da za'a yi ne wajen saka ma Halwa ƙwan haihuwar ta
Har yanzu basu faɗa mata za'a juyar mata da mahaifa ba sai zuwa nan gaba idan hankalin ta ya kwanta sanda Halwa tahaifa mata yaron ta, hakan zai sa baza ta wani tada hankalin ta ba.
****** ****** ******* ***** *******
*TWO MONTHS AGO*
A cikin wannan watannin sai ga Halwa ta soma Laulayin ciki, koda suka je asibiti an tabbatar musu tana ɗauke da cikin dagaske har na tsawon watanni biyu
Zo kuga murna wajen Saleema da Khalil, sosai suke tsananin murna, ita dai Halwa sai dai tataya su da murmushi
Tun daga ranan kuma sai yazamana babu abinda Halwa take yi sai zaman hutu idan taje makaranta ta dawo, Khalil da kanshi wani lokacin yake kai ta school idan tana da lectures ɗin safe, sai drever kuma yaɗauko ta
Sun saba sosai dashi tunda yanzu suna zaune gida ɗaya, har hira suna yi tare
Saleema bata barin ta tayi komi duk ita take yi yanzu duk da Halwan tana taimaka mata tunda cikin ba me laulayi sosai bane kamar yanda tayi na Husna me wahala
Ummi ita da kanta tasanar da Abba Saleema na da ciki, sosai yayi farin ciki musamman jin cikin ya wuce wata ɗaya hakan na nufin an samu nasara kenan.
*****
Yau ma tana da lectures ƙarfe 11:00am.
Bayan ta shirya cikin blue and white colour ɗin atamfa ɗinkin riga da skert, tayi Rolling Farin gyale akanta, sai tasaka flet shoes shima fari da kalan baƙi a ƙasan, ta ɗau jakar ta kenan tana ƙoƙarin ratayawa
Saleema tashigo ɗakin riƙe da Plate a hannun ta, tana sanye cikin atamfa ja da kalan ruwan Powder ajiki, ɗinkin riga da zani sai taɗaura zanin ta gefe, ɗankwalin kuma taɗaura sa normal
Zuwa tayi kusa da ita tajanye jakan tana faɗin "ina zaki je baki ci abinci ba?"
Murmushi Halwa tayi tana kallon ta tace "wlh sister bana jin yunwa ne".
Hannun ta tajanyo suka zauna gefen gado tace "ai baki isa ba babu inda zaki je sai kinci wannan, shiyasa ma nashiga na dafa miki taliyan nan me ɗan romo-romo sabida yayi miki daɗi, kin gani ma har da yaji nazuba miki da yawa zai miki daɗi ai".
Sai kawai Halwa tasoma dariya
Itama kuma Saleeman dariyan tasoma duk da batasan me take ma dariyan ba, kafin taɗibo taliyan a cokali takai bakin ta tana faɗin
"Haaa bakin ki".
Hakan yaƙara saka Halwa tsananin dariya har tana tuntsura wa kan gadon
Wannan karon baki Saleema tasaki tana kallon ta
Kusan shuɗewar one minute kafin tace "wai menene kike ma dariya haka?"
Tashi zaune Halwa tayi tana ci gaba da dariyan nata kafin tace "Allah dariya kike bani Sister kin maishe Ni tamkar yarinya".
Murmusawa Saleema tayi tace "to ba dole ba kina ɗauke da cikin babynmu, nifa wlh ma kewar Husna nake yi dole zan saka Yaya Barrister yaje yaroƙi Ummi tabani ita".
"Me kike ci na baka na zuba tunda ga sabon baby zai fito? kibar wancan me ƙwallon kan".
Hararan ta Saleema tayi tace "Ummina ce me ƙwallon kai ko?"
Sai Halwa tayi saurin girgiza kanta tana fiddo ido waje tace "wlh suɓutar baki ne".
Sai da Saleema ta dara sabida yanda tayi maganar a tsorace
"To shikenan naji amma kar ki sake, yanzu kici abincin kar kiyi latti".
Amsan Plate ɗin tayi tana faɗin "wlh bana jin yunwa my sister don ke kawai zan ci".
"To na gode yi maza kici sai kisha ruwa". Saleeman tafaɗa tana tsare ta da idanu
Murmushi Halwa tayi lokacin da takai spoon ɗin bakin ta, ahankali tay taci ba don ranta na so ba don dai kawai ta faranta ran Saleeman, suna yi suna hira har tagama sannan Saleema taɗauko mata ruwa taba ta tasha suka fito
Har wajen mota sai da taraka ta taga fitan su kafin tadawo cikin gidan.
****** ****** ****** *****
Ƙarfe 01:45pm. Khalil yabar office yanufi gidan su, yau a waje yayi parcking ɗin motan nasa tunda baya son yadaɗe, kwana biyu rabon sa da zuwa gidan shiyasa yau yayanke shawaran zuwa daga nan kuma yasanar ma Mom ƙaruwar da suka samu Saleema na da juna biyu
Koda yayi sallama cikin parlour'n Mom ɗin ce kaɗai zaune, ta ɗan kishingiɗa kanta saman kujera tana ta faman kallo
Sallaman sa shi yatada ita tana amsa mishi kafin tace "my son idanun ka kenan ko?"
Shafa kansa yayi yana nufo ta
Shi kansa yasan be kyauta ba, musamman yanzu da ba samun lokaci yake yi ba ko waya ba suyi a kwanakin
Zama yayi yana kallon ta da tsadadden murmushin sa yace "I'm very sorry Mom kinsan aiki yayi min yawa shiyasa bana samun zuwa wlh, ina yini?"
"Lafiya lau my son ya matar taka?" Mom ɗin ta'amsa masa cikin fara'a
"Lafiya lau Mom tana gaishe ki ma".
"Ina amsa wa, yanzu Sameer yafita baku haɗu ba?"
Girgiza kansa yayi yana kallon ta, kafin yace "Mom babu lafiya ne?"
"To lafiyan dai za'a ce, Aamir ne yake fama da zazzaɓi, duk da dai Baban nasa ma yace min ya samu sauƙi".
Cike da damuwa Khalil yace "ayya bansani ba insha Allahu zan je gaishe shi yau ɗin nan".
"To Allah yabaka iko".
Sallaman Nazeefa yasaka suka kalli ƙofan suna amsa mata
"Nazeefa an dawo?" Cewar Mom tana kallon ta da murmushi
Itama Nazeefan murmushin take yi cike da farin cikin ganin Khalil tana tahowa ta'amsa mata da "Eh Mom Barka da gida".
Sannan takalli Khalil ɗin da a yanzu yafito da waya cikin aljihu tace "Yaya ina wuni".
Sai da yaɗago yakalle ta kafin yace "lafiya ya school?"
"Alhmadulillah Yaya".
Je ki cire kayan makarantan sai ki zo ki zuba ma Yayan naki abinci, yau babu Atine agidan".
Kafin takai ga amsawa Khalil yayi saurin faɗin "a'a Mom bana jin zan iya cin komi yanzu".
Mom ɗin bata tsawaita bincike ba tace "to shikenan".
Ita kuma Nazeefa sai tayi hanyan ɗakin ta Mom tabi ta da kallo, kafin tajuyo ga Khalil dake latsa waya tace
"Wai ni kam Auta dama akwai maganar da nake so muyi da kai".
Be amsa mata ba illa ɗago kai da yayi yana bata attention ɗin sa
Nazeefa da har ta shiga ɗaki tana ƙoƙarin rufe ƙofa tajiyo muryan Mom tana faɗin sunan ta, hakan yasa tadakata don jin me zata ce
"Ni kuwa ina maka sha'awar Nazeefa".
Kallon rashin fahimta Khalil ɗin yayi mata, kafin kuma yace "Mom sha'awa kuma? Kamar ya?"
Murmusawa tayi tace "Ni naga tunda matar ka bata da lafiya kuma kaima kana buƙatan ƴaƴa, ba'a son ranan dacewa ba bare ta haifa maka, me zai hana kaƙara aure? Ga ƙanwar ka Nazeefa tunda ba wani matsala ce da ita ba sai ka aure ta, in yaso sai wani hidindimun dake kan Saleeman su ragu, kaima zaka fi samun nutsuwa ko?"
Tunda tafara maganar yake yamutsa fuska, maganar tazo masa a bazata sosai, cikin rashin jindadin abinda tafaɗa yace
"Momyyy why zaki yi irin wannan tunanin? Ni fa na ɗauki Nazeefa tamkar ƙanwata ce wacce muka fito ciki ɗaya da ita, ban taɓa kallon ta a matsayin da kike magana ba, don Allah ki dena wannan maganar ma kar wani yaji".
Mom dariya tayi tace "sai kace wani abun kunya? Tunda baka so shikenan, dama sai da nayi ma Daddyn ku magana yace "shima babu ruwan sa idan ka amince to" tunda yanzu ka nuna baka so ai shikenan babu dole a zancen".
"Kuma Mom komi yanzu ya zama normal tunda yanzu tana ɗauke da ciki har na tsawon Two month". Yayi maganar yana turo baki
Da fara'an ta tace "haba dai? An dace kenan?"
"Insha Allahu Mom haka muke saka rai tun da gashi ya wuce wata ɗaya".
"Masha Allah, Allah Sarki wlh yarinyan nan tana bani tausayi matuƙa Allah yaraba lafiya, yanzu tana gidan su ne ko kuwa don kasan dai baza ta zauna ita kaɗai ba?"
Khalil yace "A'a bata koma gida ba, sai dai Halwa tana zaune da ita".
"To masha Allah haka ake so, har yanzu ita babu labarin komawar ta gidan mijinta ne?"
Khalil ɗan waro ido yayi don be fahimci maganar da take yi ba
Hakan yasa Mom ɗin tasake cewa "ina nufin ita Halwan tunda naji ance sun rabu da mijin ne".
Ɓata fuska Khalil yayi yana shafa sajen sa yace "Ni bansani ba".
Yanda yayi maganar ne sai da Mom tasake duban sa, sosai taga ɓacin rai a fuskarsa har a maganan da yayi sai da yanuna
"Mom zan tafi". Yafaɗa yana miƙewa tsaye
Itama miƙewar tayi tana faɗin "yauwa bari in baka saƙo sai kabata, ina zuwa".
Wuce wa ɗaki tayi taɗauko tabashi sannan suka sake sallama yafice.
****
Kuka Nazeefa tafashe dashi tana zame wa ƙasa, da rarrafe tanufi cikin ɗakin har zuwa bakin gado tahaɗa kai da gwiwa tasoma rera kuka ahankali, kukan rashin madafa a wannan halin da take ciki, shikenan tasan babu ita babu auren KHALIL tunda be taɓa mata kallon yanda take masa ba, infact ma ya ɗauke ta tamkar wacce suka fito ciki ɗaya ne, hakan yasa tasake fashe wa da kuka tuna abinda yace, sai dai yanzu tasan dole tararrashi zuciyarta tunda baza ta taɓa samun sa ba.
[12/2/2020, 3:00 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎓
🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuDahirah*👈
*\F.W.A📚/*
```ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH```
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
*BOOK TWO*
.
_______________________________
*CHAPTER Eleven*
________🎓 A parking lot yayi parking ɗin motan sa sannan yafito saƙale da briafcase ɗin sa a kafaɗa yanufi cikin gidan
Yana shiga parlour'n da sallama a bakin sa
Saleema tafito cikin ɗakin ta riƙe da waya, amsa masa tayi tana kallon sa cike da fara'a a face ɗinta sannan tanufe sa, jakan hannun sa ta'amsa tana mishi sannu da zuwa
Amsa mata yayi yana ɗan guntun murmushi
Har ta juya yariƙo hannun ta suka jera tare cikin ɗakin
A gaban gadon suka tsaya ta'ajiye masa jakan tana shirin janye hannun ta yasake riƙe wa yana kallon ta, don haka bata yi yunƙurin sake janye wa ba tatsaya tana kallon sa cike da so
Murmushi yasakar mata yana zama kan gadon kafin yajanyo ta ya'aza ta kan jinyan sa yana faɗin "yau Halwa taje school kenan tabar min matata ita kaɗai da kewa ko?"
Murmushi Saleema tayi tana ɗan gyaɗa masa kai cike da kunyan sa
Numfashi yaja yana lumshe idanun sa kafin yabuɗe akan ta, yanda yake mata wani irin kallon ƙurilla hakan yasa tayi saurin cewa
"Uhmm abincin ka.. in kawo maka nan?".
Shiru yayi kamar bazai ce komi ba har alokacin idanun sa na yawo ajikin ta, ahankali yaɗan matso da kansa kusa da fuskarta yaraɗa mata
"Saiiiii nayiii wanka zan ciiiiii..."
Yanda yayi maganar cikin jan kalmomin hakan yasa tsigan jikin ta miƙe wa, tayi saurin ɗaga kanta hakan yasa kansu yahaɗe waje ɗaya
Dasauri yaɗan ja baya da nasa yana yarfe hannu cikin shagwaɓe fuska tare da runtse idanu yace "zaki fasa min kai ne?"
Yanda yayi maganar yasa ta yin dariya itama tana sosa goshin ta tace "ya haƙuri ban kula ba".
Taɓe baki yayi kafin yace "sai na rama".
Kafin ma tayi magana ya ɗaura hannun sa akanta yazame ɗankwalin dake kan ta, sannan yamayar da hannayen nasa bayan ta yasoma jan zip ɗin rigan yana faɗin "bari muyi wanka tare ko?"
Murmushi Saleema tayi tana Sad da kanta ƙasa
Sai da yagama zage mata zip ɗin kafin yasake faɗin "zamu je gidan Bro.. Aamir yana fama da zazzaɓi, zuwa yaushe Halwa zata dawo?"
"Zuwa 04:00pm. Tafaɗa min zasu gama lectures". Tayi maganar ahankali
Shiru yayi kawai yaci gaba da zame mata hannun rigan, sai da yagama yaja sa ƙasa zuwa cikin ta, sannan yaɗaga ta shima yamiƙe, cakk yaɗauke ta suka nufi cikin Toilet ɗin batare da ya cire kayan ba.
*30minutes*
Khalil zaune kan dainning yana cin abinci, yana shirye cikin