Header Ads
Showing 9001 words to 12000 words out of 132567 words

Chapter 4 - BARRISTER IBRAHIM KHALIL Complete Document by Nafisa Isma'il Lawal.txt

Ads the beginning of article before Image

05 Jul 2024

1133

Ads at the middle of Article

sanyin murya tace


"Sannu da zuwa".


Gyaɗa mata kai kawai yayi yana ci gaba da kallon ta, ahankali yasoma takowa cikin Palon kafin yace


"Ina Nazeefa?"


"Tana ciki tana barci".


"Tasha maganin ta?" Yasake jeho mata tambayan still yana kallon ta


Lokacin itama taɗago kai taɗan saci kallon sa dasauri taɗauke kanta tace


"Tasha".


"Ok ki tashe ta taci abinci".


"To Sir".


Wucewa ɗakin sa yayi, ita kuma tabi sa da kallo tana jin tsananin ƙaunar sa na ƙara shigan ta, ɗauke kanta tayi bayan da yashige tana sauke ajiyan zuciya, tasan da cewa babu yanda za'ayi tasame shi, yafi ƙarfin ta tako ina koda a mafarki ne, haƙiƙa zuciyanta tayi ganganci da takamu da ƙaunar wanda be san ma tana yi ba, tasan da cewa zuciyarta ba ƙaramin yaudaranta take yi ba da har taso uban gidan ta a matsayinta na ƴar aiki. Ci gaba da jera dainning ɗin tayi kafin tagama tashige ɗaki


Shi kuwa yana shiga ɗakin sa kayan jikin sa yasoma ragewa kafin yashige toilet, be daɗe ba yafito yasaka farar singlate da Black Three qweater yafaɗa saman gado, sosai yake jin barci kuma gashi yana jin yunwa, sai dai bazai iya tashi yaje yaci abinci ba sabida tsananin barcin da yake ji cikin idanun sa, ai kuwa yana kwanciya babu daɗewa barci yaɗauke shi


Ba shi yatashi ba sai 05:04pm, yana buɗe kyawawan idanun sa yaɗaura kan agogon dake manne jikin bango, dasauri yamiƙe yana salati, direct toilet yawuce agurguje yayi wanka yaɗauro alwala yafito, jallabiya kaɗai yazira ajikin sa yashimfiɗa dadduma yagabatar da sallan asar, lokacin da ya'idar ne yaji wani yunwa na ƙwaƙwulan cikin sa, ɗan shafa cikin nasa yayi yana lumshe idanu kafin yabuɗe su yamiƙe tsaye, gaban sif ɗin sa yanufa yaciro kayan da zai sa, kafin yakoma gaban mirror yasoma shafa Lotions, sai da yagama sannan yasaka kayan sa, riga da wando ne, rigan kalan maroon ne me hoton kan sarki, daga saman ta an rubuta THE KING da black colour, haka ma wandon sa Black jeans ne, sai yazira room slippars yafeshe jikinsa da turare sai tashin ƙamshi yake yi, wayoyin sa yaɗauka yanufi palow, babu kowa ciki yanemi kujera a ɗaya daga cikin kujerun dainning yazauna, buɗe coolar'n gaban shi yayi yaga farar shinkafa ne zalla da yankakken hanta a sama, be da sha'awan buɗe sauran, plate kawai yaɗauka yaɗibi abincin yarufe, sannan yabuɗe coolar'n dake kusa da wancan ɗin yaga miya ce na jajjage wanda yaji kifi sai tashin ƙamshi yake yi, zubawa yayi yasoma ci ahankali yana yi yana latsa wayan sa


Nazeefa ce tafito daga cikin ɗaki sanye da doguwan riga ja me kwalliyan furanni, ta yafa gyalen kayan tana tafiya ahankali kamar wacce ƙwai yafashe mata a ciki, saman kujerun Palon tanemi wuri tazauna tana kallon shi, cikin sanyin murya tace


"Yaya ina wuni".


Sai lokacin yaɗan ɗago kai yakalle ta naɗan wani lokaci kafin yamaida idanun sa kan wayan sa yaci gaba da abin da yake yi, can kuma ya'amsa mata da


"Lafiya".


Shiru ne yabiyo baya, sai kuma tagyara zamanta tana kallon shi, gaba ɗaya hankalinta da tunanin ta yana gare shi, komi nasa yana matuƙar burgeta, to meyasa? Take tatuno sanda suka fara haɗuwa yataimake ta duk da bata cikin hayyacin ta, wani kyakykyawan murmushi tasaki tana jin zuciyarta na mata sanyi da daɗi, memakon tariƙa kukan maraici sai dai ko kaɗan yanzu ji take yi tamkar bata rasa komi nata ba, duk sanda tatuna fuskar sa tana ji ne kamar tafi kowa Sa'a a duniya


"Wannan wani irin yanayi nake ji haka? Meyasaka nake jin sa daban da sauran maza?"


Zuciyarta tayi mata wannan tambayan, batakai ga lalubo amsan ta ba taji muryan sa me tsananin daɗi a cikin kunnen ta yana faɗin


"Kidena yawo da yawa saboda aikin dake cikin ki, kiriƙa tambayan Lubna duk abinda kikeso bana son yawan fitowa nan in ba da ƙwaƙwƙwaran dalili ba".


Nazeefa gyaɗa masa kai tayi, sai kuma ta'amsa mishi ganin baya kallon ta yayi maganan


"To Yaya".


Tafaɗa cike da sanyin murya kafin tatashi tasoma tafiya don komawa ɗaki, ahankali take takawa har tashige, tana shiga Lubna takallo ta sai kuma taɗauke idanun ta taci gaba da tunanin ta, itama Nazeefa samun waje tayi gefen gadon tazauna tana tunanin Brr. Khalil, daga ƙarshe tazame takwanta tana rufe idanuwanta, tashi Lubna tayi tafice zuwa kichen don ɗaura abincin dare, koda tafito idanuwanta akan shi suka sauka, sosai yau yayi mata kyau duk da ko yaushe shi ɗin me kyau ne, amma yau sai takasa ɗauke idanunta akan sa har sai da tagama ƙare masa kallo kafin tashige kichen


Ahankali yamiƙe yanufi ƙofan fita, a Compound ɗin gidan yatsaya yajingina bayan sa da bango yana lumshe idanuwan sa tare da sanya hannun sa ɗaya cikin aljihun wandon sa, shiru yayi yana sauraron bugun zuciyan sa yana tunani, ya jima awajen har sai da yaji kiran sallah kafin yanufi inda me gadi yake yayi alwala anan, tare suka jera da me gadin da sauran ma'aikatan biyu suka nufi masallaci, shi dama ba ma'abocin girman kai bane ga masu aikin sa, wani lokacin ma in yasami time wajen su yake zuwa suyi ta mishi hira shi kuma yana kallon su, duk da baya magana amma sosai yake fahimtar su, wani lokacin har yaɗan dara in suna bashi labari me daɗi, acan suka baro shi sai da yayi sallan isha'i kafin yadawo gida, Direct saman dainnig yanufa yahaɗa tea yasha, ko minti 10 be yi ba yatashi yakoma ɗakin sa, acikin ɗakin da yake aikin sa yashige, kujera yasamu yazauna yajanyo lapton ɗin sa yasoma aiki ciki, minti 5 da soma aikin nasa yamiƙe yafita, briefcase ɗin sa yaɗauko yadawo yazauna, Computer yaciro da wasu ducuments yaci gaba da aikin sa, sai da ƙarfe 12:017pm yayi kafin yadakata yarufe lapton ɗin da Computer, tashi yayi yana miƙa cike da gajiyawa yafice yanufi Toilet, alwala kaɗai yayi yafito yasauya kaya zuwa kayan barci yakwanta tare da kashe fitila.












.








_to nima bari in dakata anan, karku manta da_


*Like*
*Comments*
*Vote*
*Share*




_ina yin ku masoyana_ 💃💃💃💃💃
[9/1/2020, 10:12 AM] نفيسة أم طاهرة: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️




*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_




*بسم الله الرحمن الرحيم*






*FEENAH WRITER'S ASSO📚*
```{{Ɗaya tamkar da Dubu💪}}```


*JIKAR LAWALI CE*✍️


*Wattpad: UmmuƊahirah*👈




*⚜{{F.W.A📚}}*


```ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH```
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._


*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._


*MARUBUCIYAR*
```NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.```




.


*CHAPTER 8*




Tafiya suke yi suna sanye da uniform, fitowan su kenan akan hanyan su tazuwa school, Halwa take bata labarin haɗuwan su da Yazeed jiya, ita kuma Zainab zai ɓaɓɓaka dariya take yi har da riƙe ciki


"Ke kiyi fa ahankali karki jawo mana mutane nan". Cewar Halwa kenan tana kallon Zainab


"Ƙyale ni in dara, wlh kin bani dariya, hhhhh wai ke adole ga kurma, kai wlh banji daɗi ba da bana nan akai wannan draman, kawai lokaci ɗaya Allah yatoni asirin ki".


Sai takuma kwashewa da dariya, Halwa bige mata kafaɗa tayi tana faɗin


"Ke fa tsiyata dake ba'a zancen arziƙi dake, yanzu sai kihau ma mutane wannan haukan naki, mtswww".


Taja gajeren tsaki tana ɗaure fuska, sai lokacin Zainab taɗan sassauta dariyan da take yi tace


"Wooo kurma ta Yazeed yi haƙuri ban sakewa".


Wani irin kallo tayi mata tace


"Gyara kalaman ki, kidena danganta ni dashi, kinsan dacewa ni ɗin mallakin Yaya Nura ne shi kaɗai, to dan Allah kidena bana so".


Taɓe baki Zainab tayi tace


"Nafi kowa sanin haka ai, amma babu yanda Allah baya lamarin sa, yanzu sai kiga an sauya d.."


Saurin bige mata baki Halwa tayi tana faɗin


"Kull.. karki soma, wlh in kika ƙarisa sai an ji mu dani dake, Allah ni nakula ma kamar baƙin ciki kike min, to ta Allah ba ta ki ba, insha Allahu sai na zama mallakin Yaya Nura na sai dai kimutu".


Zainab dariya tayi tace


"Hmmm yi haƙuri ƙawalli na dena, in kinso ma gobe aɗaura miki aure dake dashi, ni wlh bata shafen ba".


Halwa tace "to ai ko bakice ba, ni inda za'abi ta shawarata wlh kafin muƙarisa wannan makarantan kawai aɗaura mana aure, domin ni a tsarina bana son nagama secondary batare da nashiga daga ciki ba".


Baki Zainab tariƙe tana kallon ta


"Lallai Halwa kin ƙosa da yawa, amma bansan haka ba sai yanzu, to gaskiya Yakamata su Mama suyi saurin miƙa ki tun kafin aji sautin kiɗan ya sauya".


"Ni da ma zaki taimaka min da yafi, kije kisanar mata tunda su har yanzu sun kasa sanin haka, wlh Zainab ina faɗamiki auren wuri daɗi ne dashi, kema dai ki aje wannan aƙidan naki kawai mu jone ayi mana tare ko ma huta, ko ba haka ba?" Cewar Halwa tana kallon Zainab tare da ɗage mata gira


Girgiza kai Zainab tayi tace


"A'a ke dai da kikaga zaki iya sai kiyi tayi, wai ma duka-duka nawa muke da har zamuyi aure, just 18years fa kenan, kinga ke kin riga da kin lume a soyayyan Yayan ki bazaki gane ba, amma ni bar ni sai na zaɓa Wanda naga ya dace dani, kuma wanda yafi kwantawa da ra'ayina".


Halwa tace "ni fa nasan halin ki, be wuce kice me kyau kike nema ba, to me zai hana nahaɗa ki da Yazeed wlh zaku dace sosai, domin ya haɗu tako ina kamar dai yanda kikeso".


"Haba dan Allah?"


"Wlh kuwa sai ma kin ganshi, nima ba ƙaramin burge ni yayi ba, sai dai kinsan tuni zuciyata ta riga ta makance ga wanin shi, babu wanda nake gani da zaifi min Yaya Nura na".


Zainab taɓe baki tayi tace


"Na kula fa kamar ma kinfi son sa akan shi, ke dai baki da zance sai ta wani Yaya Nura, uhmmm Allah dai yanuna mana ranan, amma ni gaskiya ba yanzu zanyi aure ba, sai na yi nisa a karatuna".


Daidai lokacin da wata keke napep tazo wucewa Halwa tatare tana faɗin


"Ameen inda gaske kike, kuma ko me zakice sai dai kice".


Zainab batace komi ba in banda dariya da tayi, napep ɗin suka shige yaja suka tafi, a cikin motan ma hiran suke tayi har yakawo su, bayan sun sauka Halwa ce talaluba cikin jakan ta taciro gudan ɗari tamiƙa masa, har sun soma tafiya sai wata mota tasha gaban su, atare suka tsaya suna kallon motan, wani ingarman saurayi ne yafito, yana sanye da ɓakin singlate da farar wando Three qweater, jikin sa duk zanen tatue ne kai da gani kasan irin ƴan iskan nan ne waɗanda suke tsula tsiyan su cikin gari, wani shegen aski ne akan sa oho ni na manta sunan sa ma, wuyan sa duk sarƙoƙi ne har guda biyar, tun sanda yafito yazuba ma Halwa idanu yana wani irin murmushi tare da ɗage mata gira, ita kuma sai taɗauke kanta takama hannun Zainab zasu kewaya su wuce, wuf yashige gaban su yana ci gaba da bin ta da wani mayataccen kallo yace


"Babyna babu magana?"


Ko ɗago kai bata yi ba illa sake riƙo hannun Zainab da tayi tana son sauya hanya, yasake shan gaban ta yana cewa


"Wai Baby bakiyi missing ɗina bane? Meyasaka kike min haka ne? kinsan da cewa ina matuƙar ƙaunarki da sha'awanki why bazaki bani dama ba?" Yaƙarike maganar sa yana matso da fuskar sa kusa da nata still yana murmushi me ma'anoni da yawa


Ɗan ja da baya tayi tana yamutsa fuska kana tabi shi da banzan kallo, batace komai ba dai tajuya da ninyan barin wajen gaba ɗaya sai ji tayi ya janyo mata Hijab, kiiiii sai gata tadawo gaban sa, yasanya hannu yariƙo hannun ta yana faɗin


"Common Baby sai yaushe zaki waye ne.."


Marin da tasauke mishi a fuska ne yakatse mishi maganar shi, sakin ta yayi yadafe kuncin sa da hannayen sa biyu yana kallonta cike da tsantsan mamaki, ba shi ba har Zainab sai da tatsora ta da marin da Halwa tayi mishi


Muryan Halwan ne yakatse musu mamakinsu su duk ka biyun


"Wlh koda wasa kasake ɗaukan banzan hannunka me datti kaɗaura shi akaina sai nayi maka mafiyin wannan, banza ɗan iska".


Tajuya zata tafi yayi saurin sake tare ta, cikin tsananin ƙunan rai kamar wanda zai kai mata duka wanda har sai da taɗan tsorata da ganin yanayin sa yace


"Ni kika mara Halwa? Ni Ko?"


Ɗan girgiza kan shi yayi yana sakin murmushin gefen baki yaci gaba


"Zan nuna miki waye Haris, wlh sai kinyi nadaman zuwanki duniya, sai nayi miki abinda har kimutu bazaki taɓa manta ni a rayuwanki ba tunda har kika iya cire hannu kikayi min abinda ba'a taɓa min ba, kijira kika me zai biyo baya".


Yana faɗin haka yajuya dasauri yabuɗe motan sa yashige, har motan shi yayi nisa bata ɗauke idanunta kan shi ba, sosai tatsora ta da ganin yanayin sa, ita tasan waye Haris, ba ƙaramin tantirin ɗan iska bane batasan me zai biyo baya ba kamar yanda yace "tajira zata gani" amma kuma ko kaɗan batayi nadaman marin da tayi masa ba, inda tana da ƙarfin da zatayi mishi mafiyin haka to wlh sai tayi masa


Zainab ce takatse mata tunanin ta da faɗin


"Mun shiga uku Halwa me kikayi haka? Haris fa kika mara? kuma kinsan ko shi waye a garin nan, wlh sai yaɗaure kaf dangin mu babu wanda ya'isa yafiddo mu, meyasa dan Allah kikayi wannan ɗanyen aikin? Kinsan fa ba yau yasaba miki irin haka ba".


Kallon ta Halwa tayi cike da jin haushin maganan ta tace


"Kenan kinaso kice min in barshi ya taɓa min jiki a banza? Kinsan halin sa ɗan iska ne idan har ban taka mishi birki ba gobe ma sakewa zai yi, yaje yayi duk abinda zai yi ta Allah ba tashi ba, mtswww ke kike jin tsoron sa".


Tana faɗin hakan tawuce tabar ta nan, biyo bayan ta itama tayi tana kiran sunan ta, ita ko bata kula ta ba tabuɗe Gate ɗin tashige, babu wasu mutane cikin school ɗin sai ƴan tsiraru, Direct class ɗin su da yakasance s.s3 suka wuce.








.
















_To fa me zai faru?_🤔




*Comments & share plz*
[9/1/2020, 4:35 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️




*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_




*بسم الله الرحمن الرحيم*






*FEENAH WRITER'S ASSO📚*
```{{Ɗaya tamkar da Dubu💪}}```


*JIKAR LAWALI CE*✍️


*Wattpad: UmmuƊahirah*👈




*⚜{{F.W.A📚}}*


```ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH```
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._


*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._


*MARUBUCIYAR*
```NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.```




.


*CHAPTER 9*




"Mom wai yaushe Dad zai dawo?"


Shafo suman kanshi tayi tace


"Inaga sai gobe zai dawo, amma kaneme shi ta waya mana".


"Ok".


Mom tace "ɗazu Sameer yake sanar dani jibi tafiyan ka ko?"


Gyaɗa mata kai kawai yayi yana gyara zaman shi


"Ok Allah yakaika lafiya, kadai ta addu'a banaso kana wasa da addu'a, kasan aikin nan naka akwai maƙiya sosai dole sai kariƙa neman kariya wajen Allah, nima ina nan ina tayaka, Allah yamaka albarka yasa kafi haka Autana".


Murmushi Khalil yayi yace


"Ameen Mom, dama Ina so ince miki zan dawo da Nazeefa wurinki sai tazauna anan".


"Ok ai babu damuwa kadawo da ita, dama nan ɗin yafi dacewa kakawo ta, yanzu katashi muje kaci abinci tunda an gama".


Be musa mata ba yamiƙe yanufi wajen dainning ɗin, itama biyo shi tayi suka zauna a jere sannan tayi saving ɗin sa, yasoma cin abincin ita kuma tana masa hira, shi kuma sai dai yasaurare ta da kunni kawai wani lokacin kuma yana gyaɗa mata kai.






******
Shigowan ta sau biyu cikin ɗakin tana ganin ta kwance, sai dai ta kasa aiwatar da abinda tazo yi ɗin, yanzun ma har zata koma sai kuma tayanke shawaran kawai zuwa, ahankali tatako tazo bakin gadon tasami waje tazauna, shiru tayi don ta rasa ta ina zata fara, ba kasafai suke magana ba tun kwana biyu da zuwanta cikin gidan, daurewa tayi dai ahankali takira sunan ta


Nazeefa da idanuwanta ke kulle sai dai ba barci take yi ba, hakan yasaka tabuɗe idanunta tabi Lubnan da kallo, sai tasakar mata murmushi tace


"Na ganki shiru ne tun ɗazu, shiyasaka nace ko zakizo kiraka ni zanje gidan mu kar in fita in barki ke kaɗai".


Itama murmushi tayi mata sannan tatashi zaune tace


"Ai babu damuwa anty, muje in rakaki, dama zaman ya ishe ni haka".


Murmushin samun nasara Lubna tayi tatashi tana faɗin


"To muje ko".


Miƙewa Nazeefa tayi taɗau hijabinta dake ajiye saman gadon tasaka, tabi bayan Lubna da har tasoma tafiya zata fice a ɗakin, ahankali take takawa sai dai tafiyan ta ba normal take yin sa ba sabida aikin dake cikin, hakan yasaka take ɗan duƙawa kaɗan, fitowa sukayi daga cikin gidan suka tunkari bakin Gate, har suka ƙarisa babu kowa, shima me gadi ya zagaya baya, don haka kai tsaye suka tunkari ƙofan Lubna tabuɗe suka fice


Daga can nesa wata baƙar mota ce aka faka, ba'a ganin cikinta ko kaɗan, tunda suka fito Lubna tahango motan don haka Direct wajen suka nufa, ita dai Nazeefa sai bin bayanta take yi tana yi tana kalle-kallen tsarin wajen, gaba ɗaya layin gidajen masu kuɗi ne kamar g.r.a haka layin yake.






.














_shin me zai faru?🤔 Ina Lubna zatakai Nazeefa?_


_ku bini asannu don jin me zai faru._




*More comments more post* 💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️
[9/2/2020, 1:47 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️




*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_




*بسم الله الرحمن الرحيم*






*FEENAH WRITER'S ASSO📚*
```{{Ɗaya tamkar da Dubu💪}}```


*JIKAR LAWALI CE*✍️


*Wattpad: UmmuƊahirah*👈




*⚜{{F.W.A📚}}*


```ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH```
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._


*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._


*MARUBUCIYAR*
```NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.```




.


*CHAPTER 10*




Har sunyi rabin wajen motan sun kusa isowa sai ga motan Khalil ta shanyo kwana, ahankali ya'iso wajen su yatsai da

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads