Header Ads
Showing 3001 words to 6000 words out of 132567 words

Chapter 2 - BARRISTER IBRAHIM KHALIL Complete Document by Nafisa Isma'il Lawal.txt

Ads the beginning of article before Image

05 Jul 2024

1130

Ads at the middle of Article

yake hakan yasaka tajuya jiki a sanyaye tasoma gyaran cikin bedroom ɗin, bayan ta gama tawanke toilet sannan tafito palow, nan ma sai da tagyara ko ina kafin tanufi ɗakin ta.






.... .... ..... .... .... ....
Nocking ƙofan da akayi ne yasaka shi ɗan tsakaitawa daga aikin da yake cikin Computer


"Yas come in". Yabada umarni yana ci gaba da aikin sa


Ahankali taturo ƙofan tashigo, sai da tajingina da ƙofan tana ƙare mishi kallo na 30soconds kafin daga bisani tasoma takowa cikin office ɗin tanemi kujera tazauna inda aka tanada don baƙi, shiru tayi taci gaba da kallon sa batare da tayi magana ba, sam bata gajiya da kallon shi sabida sosai take mutuwar ƙaunar shi, komi nashi me kyau ne ba inda yake da makusa, ya haɗu ne tako ina duk da kasancewar shi baya da farar fata but skin ɗin sa irin golden colour ɗin nan ne me shaining, yana da kyawun fuska wanda yake zagaye da ɗan siririn saje baƙi siɗik gunun sha'awa, idanuwansa farare ne ƙal kamar zaiba, yana da dogon hanci har zuwa ɗan madaidaicin bakin sa me ban sha'awa da ƙananun lips, shi ma'abocin barin suma ne me tarin yawa, don haka koda yaushe sai dai kaganshi yayi gyaran fuska ba dai yayi aski ba, yana da tsayi sosai da faɗin chest kuma yana da ɗan jiki don baza'a kira sa siriri ba.


"Wai lafiya kika tasani gaba kike kallona?" Muryan shi takatse mata tunanin ta da take yi a kansa


Ɗan firgigit tayi tana sauke ajiyan zuciya kafin tasaki yalwataccen murmushin da yaƙara ma face ɗin ta kyau, cikin sanyin murya tace


"Koda yaushe bana gajiya da kallon ka ne My Ib, Burina ako yaushe kakasance mallakina ni Ni kaɗai, ina Son ka da yawa My Ib, har yaushe ne zan ta jiranka kayarda dani a matsayin wacce zata zama abokiyar rayuwanka? Yaushe ne nima zaka nuna min ƙauna kamar yanda nake tsananin ƙaunarka da begen ka? Yaushe zaka tausaya min kaji ƙaina kagane babu wacce tafini ƙaunarka a faɗin duniyar nan?".


Duk maganar da take yin nan idanuwanta na kansa batare da ko kaɗan ta ƙifta su ba, hakan yasaka har ƙwalla suka taru cikin idanun suna shirin zubowa


Sai lokacin yaɗago kanshi yasauke idanunshi cikin nata, dai-dai da lokacin da wasu siraran hawaye suka ɗigo saman kuncin ta, tsira mata idanun sa masu matuƙar kaifi da kyawu yayi na ɗan wani lokaci kafin yaɗauke kai yaci gaba da aikin sa, cikin sweet voice ɗin sa yace


"Bilkisu wai yaushe ne zaki fahimce ni nima? Kigane nifa bazan iya ɓata time ɗina kan wani soyayya ba".


Ɗan tsakaitawa da maganan yayi kafin yace


"Please ki dena ɓata lokacin ki akan wanann batun, yanzu ki koma kije kiyi aikin ki, ina Son yau ki kamalla komi ki kawo min".


Lumshe idanuwanta tayi tabuɗe su akan shi, duk maganganun da yafaɗa bakin sa kawai take kallo, sosai take jin daɗi idan yakira sunan ta don ji take yi kamar yafi kowa iya faɗan sunan


Nocking door ɗin akayi yabada umarnin shigowa, abokin sa Brr. Tahir ne yashigo, ita kuma Bilkisu tatashi tafice batare da tasake cewa komi ba, inda tatashi yazauna yana sakin murmushi yace


"Guy ya naga ta fita kuma? Kar dai ace laifina ne na katse muku jindaɗin ku?"


Brr. Khalil ɗago kan sa yayi yasauke mishi wani kallo kafin yace


"Wai meyasa kai in bakayi tsegumi kamar mace bane baka jindaɗi?"


Barr. Tahir dariya yayi yace


"To menene na tsegumi kuma? Akan kai da Billy ne zan yi tsegumi? Uhmm gaskiya ce fa kai na kula baka son ta ko kaɗan, Ni wlh na rasa meyasaka yarinyan nan tanace akan dole sai tasame ka, meye amfanin tsayawa wajen da ake wulaƙanta ta, ga waɗanda suka dace da ita suke son ta tsakani da Allah but taƙi su tana tusa kanta inda bazata taɓa karɓuwa ba".


"Ok na gane, kafito fili kawai kace min kai kana ciki ba wai katsaya kana faɗamin baƙa ba".


Brr. Khalil yafaɗi hakan yana yatsina fuska


"Ohh sorry abokina wasa fa nake maka, Ni dama nasan kana son yarinyan nan, kawai halinka ne yasaka bazaka iya nuna mata ba, but ni dai shawaran da zan baka Please and please Ib kadena wahal da yarinyan nan katausaya mata,


Tsaki Brr. Khalil yayi yana kau da kansa yaci gaba da aikin sa, shi kuma Brr. Tahir murmusawa yayi yace


"Uhmm kai dai gaskiya ne baka so abokina amma ni banga makusa kan Billy da har zaka ƙi ta ba, yakamata kadawo tunanin ka kasan masoyin ka Ib".


"Please kafita kabani waje kana damuwana da banzan surutunka".


Brr. Khalil yafaɗi hakan yana ɗago kan sa fuskarshi a ɗaure


Dariya Brr. Tahir yayi yace


"Babu inda zan fita wlh, idan har kaga na fita to lokacin tashin ka ne yayi".


Harara yabanka mishi yaja ɗan siririn tsaki still yaci gaba da aikin sa


"Wai ya maganar Alhaji Mubarak ne? Me ake ciki yanzu? Yakamata fa musan abin yi tun kafin lokaci yaƙure mana". Cewar Brr. Tahir kenan yana ɗan gyara zaman sa


Kamar bazai ce komi ba, sai can kuma yabuɗi baki ahankali yace


"Muna da enough time ai insha Allahu komi zai zo da sauƙi, zuwa nan da nest week ma zan je Eygpt ɗin".


Jinjina kai Brr. Tahir yayi yace




"Gaskiya Shari'a da irin su Alhaji Mubarak hatsari ne dashi, yakamata kakula Ib kasaka idanu da kyau, kafin lokacin zasu iya yin komi don kawai su hanaka samun nasara, but naga alaman kana ɗaukan abun kamar da wasa ne".


"Hmm babu abunda zasu iya yi, kai dai kazuba idanu kagani duk wani take-taken su ina sane dashi, kuma bazasu taɓa samun nasara ba, da yardan Allah sai nayi nasara sai na ƙwato mata haƙƙin ta, insha Allahu ta sanadiyar Nazeefa sai na kawo ƙarshen Alhaji Mubarak da duk kan mabiya bayan sa".


Brr. Khalil yafaɗi hakan yana kallon Brr. Tahir ɗin


"Gaskiya ne, Allah dai yabaka sa'a, yanzu ya take? Ina fatan tana samun lafiya?"


Ɗan jingina kan sa yayi saman kujeran da yake yana lumshe idanun sa kafin yagyaɗa masa kai sai kuma yace


"Ina son namaida ita asibiti ne domin ina son aƙara duba ta da kyau, zamanta gida babu amfani".


"Hakan yafi dacewa ai, amma baka ganin kakaita asibitin da Sameer yake? Inaga shima zai fi kula da ita".


"Nima nayi tunanin haka, sai dai kasan Dr. Hashim yace "abarta agidan hakan zai fi sirri, sannan kasan Big bro ba aikin sa bane, tun farko shi yace dani in nemi Dr. Hashim zai fi bata kulawa, kuma sosai take samun lafiya ba kamar da ba".


Gyaɗa kan sa Brr. Tahir yayi cike da gamsuwa, daga nan hira suka ɗan taɓa zuwa lokacin tashi aikin nasu kafin suka fito ko wanne yahau motan sa yatafi.


Kamar ko yaushe ahankali yake jan motan sa, yanzun ma hakan yake yi kamar baya son tafiya, ta cikin mirror ɗinsa yahango wata baƙar mota tana binshi, da farko be wani damu ba don a tunanin sa ko bashi take bi ba, sai yatsaya yana kallonta ta cikin mirror itama motan packing tayi can nesa dashi, tsawon minti 5 be tada motan ba itama haka motan tana nan yanda take, ahankali yataka yaci gaba da tafiya batare da yaƙara speed ɗin motan ba, yana yi yana kallon motan da taci gaba da bin sa, sai da yayi nisa sai kuma yasake tsayawa itama motan taja tasaya.
[8/31/2020, 8:20 AM] نفيسة أم طاهرة: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️




*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_




*بسم الله الرحمن الرحيم*






*FEENAH WRITER'S ASSO📚*
```{{Ɗaya tamkar da Dubu💪}}```


*JIKAR LAWALI CE*✍️


*Wattpad: UmmuƊahirah*👈




*⚜{{F.W.A📚}}*


```ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH```
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._


*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._


*MARUBUCIYAR*
```NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.```




.


*CHAPTER 4*




Gani yayi kuma Motan tayi revers tajuya da gudu ta tafi, ahankali yasauke ajiyan zuciya yatada nashi motan yaci gaba da tafiya, agaban wani ɗan madaidaicin gida yatsaya, har ya buɗe ƙofan zai fita wayan sa tafara Ringing, dakatawa yayi yakalli wayan dake ajiye a gefe, ganin sunan BILKISU ya fito asaman screan ɗin yasanya shi jan gajeren tsaki yafice tare da rufo ƙofan, direct gidan yanufa yashiga da sallama a bakin sa, matar dake zaune bakin ƙofanta ta'amsa mishi cike da fara'a tana faɗin


"Maraba lale Ibrahima sannu da zuwa".


Tana maganan ne tana janyo tabarma dake kusa da ita


"Zauna mana anan".


Cire black Combat ɗin dake ƙafan sa yayi yasamu waje yazauna yana faɗin


"Ina yini Baaba?"


"Lafiya lau Ibarahima, yagida ya aiki? Da fatan kowa dai yana lafiya ko?"


"Alhamdulillah Baaba".


"Ai jiya naji ka shiru bakazo ba, ince dai lafiya?"


Ɗan gajeren murmushi yasaki yace


"Lafiya lau Baaba, ban samu daman zuwa bane shiyasa, da fatan babu wata matsala baku nemi wani abu ba?"


"A'a wlh Alhamdulillah, Nazeefa ce dai ma tafarka ajiyan take neman ka, kuma daga baya sai barci yaɗauke ta, koda tafarka kuma yau bata tambaye ka ba ko magana ma batayi ba".


Ajiyan zuciya yaɗan saki kana yace


"Ina ga yau zan tafi da ita, Nagode sosai da taimakon ki Allah yasaka, ga wanna babu yawa".


"Ikon Allah bawan Allah baka gajiya? To Nagode Allah yasaka, ai babu komi yiwa kai ne, ita kuma Allah yabata lafiya".


"Ameen". Ya'amsa ataƙaice yana miƙewa


Itama tashi tayi tana faɗin


"Shiga tana ciki ai".


Be ce komi ba yashiga, yarinya ce da bazata gaza 16yrs ba a kwance akan katifa, fara ce sol sai dai shatin kwarmin idanunta yaɗan yi baƙi-baƙi kaɗan, barci take yi hankalinta kwance, ahankali yamatsa kusa da ita yasanya hannayen sa yaɗauke ta cak ajikinsa yafito, har waje Baaba Talatu tarako shi tana ta saka mishi albarka tare da godiya ga ɗawainiyan da yayi mata


A back sit yakwantar da ita kana yashiga yaja motan ahankali kamar yanda yasaba, shiru yayi yana nazarin abinda yakamata yayi, ta cikin mirror yake kallon ta duk da baya hango ta sosai, but jefi-jefi yakan kai idanun sa kanta.


A bakin Gate yadakata yayi hon, ba daɗewa aka wangale mishi gate ɗin yatura hancin motan ciki, a packing space yatsai da motan, sai da yaɗan yi minti 3 kafin yabuɗe motan yafito da ƙafan sa, wayoyin sa yaɗauka yashigar dashi cikin aljihu kana yafito yabuɗe bayan mota yana ƙoƙarin fito da ita, ahankali tabuɗe idanuwanta tasauke kan kyakkyawan face ɗin sa, hakan yasaka taɗan saki murmushi ahankali tace


"Yayana".


Shima murmushin yasakar mata yaɗan ja jikin sa daga ɗaukan ta da yayi ninya yace


"Nazeefa.. kin tashi?".


Gyaɗa masa kai tayi still tana murmushi


"Ok fito ahankali muje ciki, yau na dawo dake gida na, anan zamu ci gaba da zama kinji?"


Nan ma gyaɗa masa kai tayi kafin tayunƙuro tatashi tafito daga cikin motan, ahankali take kallon cikin gidan kafin tamai da idanuwanta kan sa, murmushi yasakar mata kana yariƙo hannun ta suka taka ahankali suka nufi cikin gidan, a main palow suka tsaya yanuna mata kujera yace


"Zauna anan".


Ba musu tasami waje tazauna tana ci gaba da kallon Palon don ba ƙaramin burge ta yayi ba, sosai yatafi da imanin ta, tsarin Palon da kayan cikin kan shi abun burgewa ne da sha'awa, fridge yanufa yaɗauko faro water yadawo yazauna gefen ta, miƙa mata yayi ta'amsa tana sakar masa murmushi, shi kuma wayan sa yazaro cikin aljihu yaɗan latsa yakara a kunne


"Ina kike?"


"Ok kizo palow Ina jiran ki".


3minute tafito cikin ɗakin ta, har gaban sa taƙarisa taduƙa tace


"gani Sir".


"Kikai ta ɗakin ki daga yau zakici gaba da kula da ita, zuwa anjima kiyi ma drever magana yakai ki super makert duk wani abun da take buƙata kisiyo mata".


Ita sai lokacin ne ma takalli wajen da Nazeefa take zaune, a ranta tana tunanin "to wacece ita awajen shi?"


Batakai ga ƙarisa zancen zucin nata ba taji muryan sa yana ma Nazeefa magana


"Tashi kibi ta ciki".


Babu musu tatashi, itama Lubna miƙewa tayi takama hanyan ɗakin ta Nazeefa na biye da ita abaya, da ido yabi su da kallo har suka shige kafin yasauke ajiyan zuciya, tashi yayi yanufi cikin ɗakin sa, wanka yayi yasauya kaya cikin ƙaraman t.shirt fara da yellow ɗin Three qweater, yafito palow yanufi saman dainnig yasami waje yazauna, tea cup yahaɗa yafara sipping yana latsa wayan sa, tsawon mintuna ashirin yaɗauka awajen kafin yamiƙe yanufi cikin ɗakinsa, be fito ba sai da aka kira sallan magriba kafin yaɗauro alwala yasanya jallabiya fara sol yafito yanufi masjid, sai da aka yi isha'i kafin yadawo, yana shigowa yatarda Nazeefa zaune saman kujera ta ƙudundune jikinta tana kallo, shigowan sa yasaka taɗago kai tana kallon shi, kujeran dake gefen ta yasamu yazauna yana kallon ta


"Sannu da zuwa yaya".


Tace dashi tana gyara zaman ta dakyau


"Yauwa.. kinci abinci?"


"Eh Yaya".


"Ok."


Shiru yagibta a tsakanin su na ɗan wani lokaci kafin yaɗago da kansa daga duba wayan sa yana kallon ta yace


"Kije kikwanta dare yayi, ki kira min Lubna".


tace "to".


Tamiƙe tawuce ciki, Lubna ce tafito taƙariso kusa dashi


"Kihaɗa min Coffee".


Amsa mishi tayi kawai tawuce cikin kichen, shima tashi yayi yanufi ɗakin sa, ko 2mint be yi ba yafito riƙe da briafcase ɗin sa, yana zama itama tafito tamiƙa mishi takoma ciki, ahankali yasoma aikin sa cikin Computer yana yi yana sipping ɗin Coffee ɗin, har wajen ƙarfe 11:00pm yana nan zaune cikin Palon be gama abinda yake ba, can yaji ihu cikin ɗakin su Lubna, ɗan tsakaitawa yayi daga latsa Computern da yake yi yana kasa kunne.
[8/31/2020, 8:26 AM] نفيسة أم طاهرة: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️




*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_




*بسم الله الرحمن الرحيم*






*FEENAH WRITER'S ASSO📚*
```{{Ɗaya tamkar da Dubu💪}}```


*JIKAR LAWALI CE*✍️


*Wattpad: UmmuƊahirah*👈




*⚜{{F.W.A📚}}*


```ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH```
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._


*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._


*MARUBUCIYAR*
```NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.```


_wannan shafin naku ne masoya Littafina, ina jin daɗin yanda kuke nuna ma Book ɗina ƙauna, thank you._ ❤️




.


*CHAPTER 5*




Tashi yayi yanufi ɗakin yabuɗe yashiga, duhu ne ako ina hakan yasaka yalaluba makunnin wutan ɗakin yakunna ko ina yagame da haske, akan ta yasauke idanun sa tana zaune saman gadon babu inda jikinta baya rawa, gefen ta yakalla yaga Nazeefa na kwance sai sharan barcin ta take yi ko motsi batayi ba, maida kyawawan idanun sa yayi akanta da itama tazuba nata cikin nashi sai ɓari take yi, ahankali kamar baya son magana yace


"Menene kike ihu cikin dare? Lafiyan ki ƙalau kuwa?"


Cikin rawan murya tace


"Mafarki nayi".


Tsare ta da idanu yayi yana nazarin ta, gaba ɗaya tsoro da firgici ne yabayyana a fuskarta, ɗan numfashi yaja sannan yace


"Wani irin mafarki ne haka da yabaki tsoro?".


Sharto gumin fuskanta tayi still cikin rawan baki tace


"Am uhm Mafarki nayi ak..akan Mamana".


"Kina son kije gida kenan?"


Yaje ho mata tambayan tare da ci gaba da faɗin


"Sai in saka drever yakai ki yanzu in kinaso".


Dasauri tagirgiza mishi kai tana faɗin


"A'a".


"Ok koma kikwanta, kitabbatar kinyi addu'a tukun".


Daga haka yajuya yafita bayan yakashe wutan ɗakin, ahankali tasulale takoma takwanta tana jin hawaye na sulalo mata a fuska, cikin raunin murya tace


"Dan Allah karku kashe min su, zan yi duk abinda kukeso".


Sai kuma tasaka hannu tashare hawayen fuskanta tana tuno fuskar sa a yanzu da yashigo, take wasu hawayen suka shiga sintiri saman fuskanta ahankali tafurta


"Ina matuƙar ƙaunar ka".




....... ....... ......... ......
Shi kuwa koda yakoma cikin Palon aikin sa yaci gaba da yi, be fi 20minutes ba yatashi yashige ɗakin sa, sai da yayi wanka yashirya cikin kayan barci farare sol yafeshe jikinsa da turare sai zuba ƙamshi yake yi kamar wanda yayi wanka dashi, kwanciya yayi yayinda fuskar sa ke kallon cilling ɗin ɗakin, yaɗaura kan sa saman dantsen hannun sa yayi matashi tare da lumshe idanun sa, ahankali yabuɗe idanunsa yana ƙure cilling ɗin ɗakin da ido, tunani yake yi cikin ransa, ya daɗe ahaka batare da yaji barci yazo mishi ba, ganin haka yasaka shi tashi yanufi Toilet yaɗauro alwala yazo yatada sallah yafara jero nafiloli, sai da yadaɗe yana Sallah kafin yasoma jin barci yatashi yahau gado yayi addu'a yarufe idanunsa, ba jimawa kuwa barci yasure sa.




.




****** ****** ******


Tsaye take a bakin titi tana jiran keke napep, tana sanye da uniform ɗin makaranta, riga da wando farare, sai ɗan ƙaramin Hijab kalan ruwan goro, sosai kayan suka yi mata kyau kuma suka ƙara fito da zallan yarintan ta da kyawun surar ta, school bag ɗin ta dake rataye a kafaɗan ta tazamo shi cike da gajiyawa, sosai ranan wajen yake dukan ta, tun ɗazu tana tsaye amma har yanzu bata sami abin hawa ba, gashi har abokan tafiyanta sun watse ita tana nan tsaye ba yau ba gobe, yatsina fuskarta tayi taɗan ɗaga face ɗin ta tana kallon ƙwallelen ranan da yasake fantsamo wa, bata kai ga sauke kanta ba taji hon ɗin mota a gefen ta, dasauri tasauke kanta taɗaura idanunta saman motan dake tsaye ɗan nesa da ita, cikin socond ɗin da be wuce 3 ba takalli motan taɗauke kanta, wanda ke cikin motan ne yafito ɗan kyakkyawan sauri ne yatunkaro inda take


"Assalamu alaikum". Yayi mata sallama yana kallon fuskarta da yake a yatsine


Bata kalle sa ba taɗan yamutsa fuska tana motsa ƙaramin bakin ta, hakan yasaka yaɗan saki murmushi yace


"Baiwar Allah da fatan dai ba laifi nayi ba da ban samu an amsa min sallama ba? Duk da nasan be dace natare ki anan ba, amma kuma babu yanda na iya ne tunda bazan iya bari kisuɓuce min ba".


Kallon sa tayi fuskanta a yatsine ga duk kan alamu hakan ya zame mata jiki ne, batace komi ba sai gyara zaman jakan ta da tayi tana kallon hanya


"Baiwar Allah ko dai ke kurma ce?" Yasake tambayan ta still yana kallon ta


Ahankali tagyaɗa masa kai tana ɗan kwaɓe fuska kamar zata yi kuka


"Ayya sorry rashin sani akace yafi dare duhu, kiyi haƙuri but ina son insan sunan ki gashi kuma ina son narage miki hanya, to ya za'ayi yanzu?"


Cikin sanyi da muryanta me daɗi tace


"Ce maka

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads