Header Ads
Showing 75001 words to 78000 words out of 132567 words

Chapter 26 - BARRISTER IBRAHIM KHALIL Complete Document by Nafisa Isma'il Lawal.txt

Ads the beginning of article before Image

05 Jul 2024

1155

Ads at the middle of Article

jikin nata yake yi sabida tsaban yau komi ya kai mata maƙura




Haneefa na zaune gefen ta tana bin ta da idanu cike da tsananin mamakin ta, bata hana ta yin kukan ba har sanda tayi ma'ishi tafitar da duk ƙuncin dake cikin ranta, sannan ne tadafa kafaɗan ta da hannu ɗaya tace




"Ban taɓa tunanin akan ɗa namiji bane kika shiga duk wannan damuwar Nazeefa, sabida ɗa namiji kika dena shiga aji kika dena mayar da hankalin ki kan karatun ki duk a sabida ɗa namiji? nayi mamaki wlh ƙawata duk kyawun ki kizauna kina ma ɗa namiji kuka".




Shiru Haneefa tayi tana jan numfashi tare da tsare Nazeefan da idanu




Ita kuma Nazeefa alokacin ne taɗago kanta tana kallon ta da rinannun idanuwan ta tace "baza ki gane a halin da nake ciki bane Haneefa, zuciyata tariga da ta mutu a ƙaunar sa, nayi duk iya abinda zanyi don in cire sa araina amma na kasa, wlh ji nake yi kamar in mutu saboda yanda nake ji a kansa, bana jin zan iya auren wanin sa idan bashi ba, bazan taɓa zama da kowa ba sai shi, tun bansan meye so ba zuciya ta takamu da mahaukacin ƙaunar sa har sanda nagane, gashi yanzu yayi min ratan da samun sa babban wani aiki ne agare Ni".






Dariya ma abun yaba ma Haneefa, sai tasaki baki tana yi




Hararan ta kawai Nazeefa tayi tana ɗauke kai cike da haushi




Tsai da dariyan Haneefa tayi tace "ƙawata kenan kin faɗa da yawa, Ni kuwa zan so ganin wannan Jarumin me babban matsayi a wurin ki, amma fa idan har kina son samun sa to ba wani babban aiki bane a wurin ki ƙawata sai dai idan kece baza ki bi hanyan da yadace ba, Allah na tuba don yana da mata sai kice yayi miki nisa?"




Kallon ta kawai Nazeefa take yi kamar idanun ta zasu faɗo ƙasa har sanda tadire aya kafin taɗaura da nata




"Wace hanya ce tadace da zanbi don samun sa? Kina ganin har akwai sauran hanyan da zanbi Ya Khalil yakalle Ni a matsayin Masoyiya?"




"Ƙwarai kuwa, me zai hana ki faɗa ma Mahaifiyarsa tunda ita tabuƙaci haka, na tabbata wlh zata share miki hawayen ki tunda tana ƙaunar ki".




Shiru kawai Nazeefa tayi don tasan baza ta taɓa iya faɗa mata ba, to taya shi Khalil ɗin zai kalli maganar? Abinda take tunawa kenan, ba wai faɗan bane.. matsalan ta na ga Uban gayyar".




Maganar Haneefan ne takatse mata tunanin ta, taɗago tana kallon ta cike da wani irin kallo me wuyan fassara, bakin ta har rawa yake yi wajen cewa




"Baki da hankali ne wannan wani irin shawaran banza ce? No bazan taɓa iya aikata hakan ba, idan kuwa nayi masa haka tabbas na zama butulu, tabbas idan na aikata hakan mutane zasu zage Ni sannan zasu la'ance ni tunda ban riƙe maraicina ba.."




Sai kuma tagirgiza kanta cikin kuka tace "bazan taɓa iya aikata masa haka ba, wlh gwara in mutu da in je wajen boka in cutar da wanda yataimaka min".




Haneefa cikin son nuna mata abunda take nufi tace "ƙawata ki gane mana hakan shine kaɗai mafita kuma hanyan da zaki samu zuciyar sa..."




Ɗaga mata hannu Nazeefa tayi tace "ya isa bana son ji, Kar ki sake min irin wannan maganan".




Tana faɗan haka tamiƙe tawuce tabar Haneefa nan zaune baki sake tana bin bayan ta da kallo.






Tun daga ranan kuma sai Nazeefa tadena sake ma Haneefa fuska, ko tazo school ɗin babu ruwan ta da ita, ita a ganin ta Haneefa ba ƙawar kirki bace da har zata bata wannan shawaran, duka-duka ma nawa suke da har zata bata shawaran zuwa wajen Boka?




Ita ma dai Haneefan tasha jinin jikin ta, tun daga ranan itama taja baya da ita, idan ba gaisuwa ba babu abinda ke haɗa su, a ganin ta taimakon Nazeefa zata yi, amma tunda ta nuna bata so to itama ta bar maganan, duk ranan da komi yarincaɓe mata tazo taneme ta ita kuma anan ne zata taimaka mata.






.












*Facebook: Muh'd Lawal Nafisat*


*Wattpad: UmmuDahirah*


*WhatsApp number:07065334256*




_plz karku manta da share, Vote, Comments. Nagode._
[11/22/2020, 1:20 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎓
🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️




*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_




*بسم الله الرحمن الرحيم*






*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```


*JIKAR LAWALI CE*✍️


*Wattpad: UmmuDahirah*👈




*\F.W.A📚/*


```ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH```
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._


*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._




*BOOK TWO*




.


_______________________________


*CHAPTER Five*


________🎓Rayuwan Khalil da Saleema rayuwa ce da suke yin ta cikin jindaɗin juna da nuna ƙauna da kulawa, zuwa yanzu komi yana tafiyan musu dai-dai




Gefe ɗaya kuma ciwon Saleema na zuwa mata jefi-jefi, duk da tana shan magani amma wataran haka zata tashi da tsananin ciwo har asibiti Khalil yake kai ta, sai kuma daga baya ciwon nata yalafa




Yanzun ma kwana biyu kenan bata jindaɗi sai dai ba sosai ba tana yin duk aiyukan ta tare da taimakon Khalil, idan yana gida shi yake taimaka mata da rainon Husna, girki kuma hanata yayi sai dai yayi musu Take-away, idan tatashi kuma da ƙwarin jiki sai tayi musu girkin






........ ........ ....... ........


Yau tun safe da Khalil yatafi aiki bayan ta gama gyaran gidan tayi ma Husna wanka itama tayi, sun shirya cikin farar atamfa me zanen ja da ruwan goro, ɗinkin riga da skert akayi mata sai akayi ma Husna doguwar riga dai-dai ita, duk kwalliyan da akayi iri ɗaya akai musu a rigan




Fitowa Parlour tayi da Husna a hannun ta ta'ajiye ta saman carpet, ita kuma tahaye kan 3sitter takwanta, yau sosai jikin ta yamatsa mata ga sanyi da take ji sosai duk da kuwa ta kashe AC da Fan ɗin parlour'n




A hankali ciwon yaci gaba da cin ta, hakan yasa tamiƙe takoma ɗaki tahaye kan gado taƙudundune da bargo, nan da nan tasoma rawan ɗari.






Wajen awanni biyu da shigan ta Khalil yadawo gidan, da sallama yashigo cikin parlour'n, da Husna yasoma cin karo tayi wasan ta har ta gaji tasoma ƙananun kukan ta daga ƙarshe barci yaɗauke ta a dungure a wajen ta kofa kanta kamar wacce take sujjada




Dasauri yaƙariso yana ajiye briafcase ɗin sa yasaka zara-zaran hannayen sa yaɗauke ta, sannan ne yaga ashe barci take yi, murmushi yayi yana kallon fuskarta da tataɓe baki duk hawaye ya gama bushe mata a fuskar




Gaban sa ne yafaɗi sakamakon ganin yanda kamannin ta da Halwa yasake fitowa ainun, basu da maraba a yanzu ɗin




Shiru yayi yana ƙure ta da kyawawan idanun sa, ya ɗau tsawon mintuna 3 kafin yamiƙe yanufi ɗakin Saleema da ita a hannun sa, yana shiga yahangi Saleeman kan gado nannaɗe cikin bargo




Dasauri yanufi bakin gadon dan yasan babu lafiya, ajiye Husna yayi can ƙarshen gadon kafin yamatso kusa da Saleeman yana zama ya yaye bargon yana kiran sunan ta




Zafin da yabuge sa ne yayi saurin sake yaye bargon yana tallabo kanta, nan yaga fuskarta sharkaf da hawaye idanun ta kuma sun kaɗa sunyi jawur gunun tausayi, gaba ɗaya jikin ta rawa yake yi ga shegen zafi kamar tafashashshen ruwa, shi kanshi dauriya yayi wajen riƙe ta




Cikin tsananin firgici yace "subhanallah.. Saleema meke damun ki? Tun yaushe kika fara ciwon?"




Bakin ta rawa yake yi ta ma kasa magana in banda hawaye da ke zuba kan kuncin ta yana gangara ta gefe yasauka hannun sa




Dasauri yakwantar da ita yana miƙe wa cikin sauri, wayan sa yaɗauka yakira doctorn ta, sai dai baya shiga hakan yasaka ya'ajiye wayan yafita da sauri




Sai kuma yasake dawowa yaɗauki Husna yakaima drever akan yakaita gida sannan yadawo yatallabi Saleema yasaka mata Hijab suka fito




A back seat yakwantar da ita yashiga yaja motan yafice cikin gidan da mugun gudu.








*___________________________*


Drever na zuwa gidan su Saleema Gateman yamiƙa ma Husna sannan yatafi




Nocking gate man yayi a bakin Parlour




Halwa na tsaye gaban Fridge tana shan ruwa, dawowar ta kenan dama daga makaranta tasoma nufan Fridge ɗin, ajiye ruwan tayi tanufi ƙofan tabuɗe, kallon Gate man tayi tare da Husna dake hannun sa




"Dama drever ne yakawo ta inji Mijin Hajiya Saleema". Cewar Gate man ɗin yana kallon Halwa




Mamaki ne Yakamata amma sai batace komi ba ta'amshe ta tarufe ƙofan takoma cikin parlour'n, ajiye ta anan ƙasan carpet tayi tanufi kan kujera inda jakar ta yake tazaro wayan ta tasoma kiran numban Saleema, sosai hankalin ta yaba ta babu lafiya ne don tasan babu ta yanda za'a yi Saleema tayarda adawo da Husna, ƙirjin ta sai fat fat fat yake yi gashi Ummi tana Hospital kuma tace mata zata biya anguwa, so dawowarta ma ba yanzu ba




Ringing wayan take yi but not answer, zuwa lokacin Halwa ta kasa zama sai Safa da marwa take yi tana sake danƙara mata kira, tsaki taja tana ɗaukan jakan ta tanufi ɗakin Saleema wanda yazama nata a yanzu




Ta dawo makarantan yau agajiye Allah-Allah take yi tadawo tayi wanka ko zata rage gajiyan, ga mugun yunwa dake addabar ta, amma a yanzu bata jin zata iya cin wani abu idan har batasan halin da take ciki ba, kayanta tacire tashiga wanka.






Larai ce tafito daga ɗakin ta tahangi Husna tana kuka, dasauri taƙarisa wajen ta taɗauke ta tasoma jijjiga ta tana tambayan ta "ina Mamarta? Wa yakawo ta?" Sai kace tana jin ta




Ɗakin Halwan tanufa tunda a tunanin ta Saleeman ce tazo gidan, amma koda tashiga babu kowa sai ƙarar ruwa da taji, hakan yasa tafita takoma ɗakin ta da Husnan.










*________________________________*




Lokacin da Khalil yakai Saleema asibiti Ummi tabar asibitin




Emargancy ward aka nufa da ita, hankalin Khalil duk ya tashi haka yake ta Safa da marwa, gashi be zo da wayan sa ba bare yakira gidan su yasanar musu




Wajen 1hour aka ɗauka ana duba ta kafin likitan yafito yabuƙaci ganin Khalil, kan dai matsalan ciwon ta ne sai kuma shigan ciki na sati Uku, gashi kuma sun gano da matsala sosai a mahaifar ta zai yi wuya ta'iya ɗaukan ciki har yagirma a jikin ta, sai dai sun ɗaura ta akan magani don aga yanda hali zai yi




Hankalin Khalil sosai yasake tashi da jin bayanin doctor, sai dai komi ya fawwala ma Allah hakan shine cikan imani




Motar sa yashiga yanufo gida tunda dama a kulawan likitoci take, yanke shawara yayi yasoma wucewa gidan su Saleeman yafaɗa ma iyayen ta don haka yakarya kan mota yanufi gidan.








_...... ........ ....... ....... ......_


Fitowar Halwa a wanka doguwar riga kawai tazira taɗaura ɗankwalin rigan tafito parlour




Tana zama Larai tafito cikin ɗakin ta goye da Husna abaya zataje kichen




"Au Ashe kin fito? Na shigo ɗakin ai duba ko Saleema ce tazo amma bangan ta ba".




Halwa kallon ta tayi da yanayin damuwa a face ɗin ta tace "eh na fito amma ba Saleeman bace tazo drever ne yakawo ta".




"Allah yasa dai lafiya ko?" Larai tafaɗa itama a yanayin wasi-wasi




Domin sun san babu yanda za'a yi akawo ta gidan idan har ba Saleeman bace tazo




"Wlh nima bansani ba, na kira dai wayan ta amma shiru ba'a ɗaga ba hankalina duk ya tashi, nayi tunanin kiran Ummi kuma kar yazo fahimtar mu ce hakan".




Larai tace "eh gwara kam kar ki kirata saboda bamu da tabbacin ko matsala ne, amma dai kici gaba da gwada kiran wataƙil adace".




Gyaɗa kanta kawai Halwa tayi taci gaba da kiran wayan kamar yanda Larai ɗin tace




Ita kuma Larai kichen tanufa don ɗaura girkin dare




Tashi Halwa tayi tanufi kan dainning tazauna, sosai take jin yunwa kamar hanjin ta zai tsinke, yau bata ci komi a school ba haka taje tadawo




Zama tayi tazuba abincin da yakasance Macoroni ne me manja, tana cin abincin tana sake kiran layin Saleema, ko kaɗan ta gaza haƙura, zuwa yanzu hankalin ta yayi ƙololuwar tashi, tabbas tasan akwai matsala




Abincin ma sai yakoma baya mata daɗi, turewa tayi dai-dai da lokacin da taji ana buɗe Gate ɗin gidan




Dasauri tamiƙe tanufi hanyan fita don tasan bazai wuce Ummi bane ko Abba, hankalin ta ne ya gaza kwanciya shiyasa tanufi wajen don tarban su duk da kuwa bata san me zatace musu ba




Tana fita tahangi motan da bana gidan ba, bata san cewa Khalil bane aciki tunda bata ganin shi, kuma ba wai tasan motan gidan shi bane bata tsayawa kallo bare ta tantance, tasan dai yana da motoci aƙalla sun kai biyar agidan




Shi kuwa tun sanda tafito idanun sa yasauka akan ta, har yayi parcking yafito yarufe motan




Zuciyar ta ne tabuga sakamakon ganin sa, duk da dama idan har zata ganshi hakan ke faruwa da ita amma kuma da fargaban ko wani abu ne yasamu Saleema, tana nan tsaye tana kallon sa yayinda zuciyarta ke ci gaba da dukan uku-uku, gaba ɗaya ta dunƙule hannun ta waje ɗaya saboda rawan da suke yi, daƙyar ta'aro jarumta da ya'iso wajen tagaishe sa




Amsa mata yayi yana ci gaba da kallon ta kamar zai cinye ta, tsananin ƙaunar ta ne ke ɗawainiya dashi, ya jima rabon da yaganta sai yaji wani sanyi aransa tare da wucewar wani abu da yatsaya masa a maƙoshi kwana da kwanaki




Matsa masa a hanya tayi batace komi ba




Shi kuma sai yashiga kafin tabiyo bayan sa




A kan ɗaya daga cikin kujerun yasamu wuri yazauna




Ita kuma taje taɗauko masa ruwa duk da kuwa batasan ko yana buƙata ba




Ajiyewa tayi a gaban sa saman Centre table tajuya da ninyan wuce wa duk da kuwa tana son tambayar sa Saleema, gashi kuma yanda idanun sa yake faman yawo ajikin ta yayi bala'in takura ta




Har ta soma tafiya taji sassanyan muryan sa yayi mata magana




"Ina Ummi?"




Juyowa tayi sai dai wannan karon baza ta iya kallon sa ba tasad da kanta ƙasa tace "bata dawo ba".




Shiru yayi kamar bazai yi magana ba




Ita kuma hankalin ta yagaza kwanciya, bata san sanda tajeho masa tambayan




"Meke damun ƴar uwata?" Tayi maganar idanun ta na kansa




Kai tsaye Khalil yasanar mata inda take




Hankalin Halwa atashe kamar zatayi kuka tace "don Allah zan bika mu tafi".




Gyaɗa mata kai kawai yayi yamiƙe yanufi hanyan fita




Dasauri taɗau wayan ta tacire ɗankwalin ta tayafa tabi bayan sa, lokacin har ya shige motan ya tayar yana jiran ta




Cikin sassarfa taƙarisa tabuɗe gaban tashiga yaja motan yafice bayan da me gadi yabuɗe masa Gate ɗin




Duk da Khalil yana son zuwa gida amma bazai ƙi biya mata buƙatar ta ba, wannan dalilin ne yasaka yayi tunanin kai ta kafin yakoma gidan




Koda yakaita be daɗe ba yace mata zai tafi




Bata tanka shi ba har yafice, sannan ne tasoma kiran layin Ummi, bugu biyu taɗauka anan Halwa tasoma sanar mata Saleema ce babu lafiya tana Hospital




Hankalin Ummi ya tashi nan da nan takaryo motan ta don har takusa isa gida, tana zuwa tatarar da Saleeman barci take yi Halwa ta tasa ta gaba sai kallon ta take yi




Fita tayi tanufi Office ɗin Doctor ɗin ta, anan take jin bayanin matsalan Saleeman, idan hankalin Ummi yayi dubu to ya gama tashi, sosai taruɗe da jin abinda ke faruwa




Koda tafito lungu tasamu tafashe da kuka na tsananin tausayin ƴar nata, babu abinda bakin ta ke furtawa sai salati, tabbas Saleema tana cikin jarabawa




Da fari ciwon zuciya sannan kuma ciwon hanta, yanzu kuma ga ciwo a mahaifar ta wanda ke barazanar da zata rasa haihuwa har abada




Tasha kuka sosai kafin tashare hawaye tagyara fuskarta, sannan taciro wayan ta a jaka takira Abba tasanar masa




Shima babu jimawa yataho




Gaba ɗaya sun yi zugun a ɗakin sun saka ta gaba sai kallon ta suke yi




Sai gab da magriba tafarka lokacin shima Khalil ya dawo, sosai take jin jiki don ko magana bata yi




A lokacin ne Abba ya lallaɓa Ummi suka tafi gida da Halwa tunda an sake mata alluran barci ta koma




Babu jimawa itama Mom tazo tare da Nazeefa, sun jima har wajen ƙarfe 11:00pm kafin suka tafi




Khalil shi yace zai kwana da ita don haka babu musu Abba yataho yabarta.
[11/24/2020, 2:36 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎓
🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️




*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_




*بسم الله الرحمن الرحيم*






*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```


*JIKAR LAWALI CE*✍️


*Wattpad: UmmuDahirah*👈




*\F.W.A📚/*


```ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH```
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._


*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._




*BOOK TWO*




.


_______________________________


*CHAPTER Six*


________🎓 Wasa-wasa sai da Saleema tayi kwana biyar cur kafin tasoma samun sauƙi, sai kuma daga baya ciwo yazo mata rigigim, blending take tayi nan likitoci suka rufu akan ta




Halwa kuka Ummi kuka sun rigada sun cire rai ma Saleema zata iya rayuwa




Khalil shi kansa ya rasa inda zai saka kansa, tsananin tausayin matar sa gaba ɗaya ya cika sa, sosai yadamu da halin da take ciki




A ranan duk wani me tausayi dole yatausaya mata, ashe wai duk ɓari zatayi shine yaja mata hakan, sai da aka ƙara mata jini leda biyu sabida yanda tazubar da jinin ta wajen ɓari




Kwanan ta biyu kafin tafarfaɗo, sosai Saleema tayi jinya gaba ɗaya ta rame tayi baƙi sabida jinin da ake ƙara mata, kullum zuwa gaishe ta ake yi




Ita Halwa ma gaba ɗaya dena zuwa school tayi sai da tasoma samun sauƙi sannan ne Ummi tatakura mata tafara zuwa




Idan kuma tadawo nan take fara wuto wa sai dare takoma gida




Haka shima Khalil yake yi, duk da aiki yayi masa yawa amma kullum yana kan zuwa




Satin ta ɗaya aka sallame ta duk da ba wani warkewa tayi ba amma haka takoma gida tana jinya, Khalil shi ke kula da ita ko kaɗan baya gajiya, tausayin ta tsantsa ne a ransa




Haka rayuwa taci gaba da shuɗewa gashi yanzu har an shafe watanni uku da ciwon da Saleema tayi, yanzu komi ya koma normal sai dai ciwon da ba'a rasa ba wanda take fama dashi koda yaushe.








*________________________________*




Ƙarfe 03:20pm. Su Zainab da friends ɗin ta suka

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads