Header Ads
Showing 123001 words to 126000 words out of 132567 words

Chapter 42 - BARRISTER IBRAHIM KHALIL Complete Document by Nafisa Isma'il Lawal.txt

Ads the beginning of article before Image

05 Jul 2024

1170

Ads at the middle of Article

kyau Umma tayi sai kuma tace, "oh ikon Allah Halwa kece? Wlh ban gane ki ba ko kaɗan gaba ɗaya kin sauya min, Allah Sarki ashe da rabon zamu ganki?".




Still Murmushi Halwa take yi, tasake gaishe da Umman




Ta'amsa mata cike da fara'a tana bin ta da idanu




"ALLAH Sarki tamkar ba ke ba abin ki, waɗannan yaran naki ne?" Umma tayi maganar tana kallon Husna da talafe a jikin Halwan, yayinda Ahmad ke kan cinyan ta shima kwance




"A'a Umma ga mahaifiyar su nan". Halwa tayi maganar tana nuna Saleema




Jinjina kanta Umma tayi tace "Masha Allah to Allah ya raya su ta farkin Gaskiya".




"Ameen Umma, Ina Zainab ko bata nan ne?"






"Ai Zainab tayi aure kusan watanni bakwai kenan".






Halwa cikin tsantsan farin ciki tace, "Umma yanzu Zainab tayi aure ashe? Allah Sarki ashe bazan ga auren ƙawata ba?"






Umma na murmusawa tace, "ai kam Zainab tayi aure, ai dayake babu nisa da nan ɗin da gidan ta, sai in saka yara ma sukai ki idan zaki je".




"To umma amma naje gida ban ga su Mama ba, ko wani abun ya faru ne?"




Umma tace, "ai su Mama sun tashi tuni, ai ba anan anguwan ma suke zaune ba, Nura ya sai musu sabon gida, ashe baki sani ba?"




Murmushi Halwa tayi tana gyaɗa mata kai, kafin kuma tace, "eh umma ban sani ba wlh".




"To kin tafi can Gombe kin ɓoye ba dole ba, ina ga kema har auren kinyi bamu da labari ko?" Umma tafaɗa cike da fara'a




Still Murmushi Halwa tayi bata ba ta amsa ba






Sai Saleema ce taba ta amsa da "Eh umma itama tayi aure ai".






"Allah Sarki to Allah ya sanya alkhairi, bari inje maƙota in Kira yaro sai yakai ku gidan Zainab ɗin". Umma taƙarishe maganar tana tashi tafice.
[1/20, 4:52 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎓
🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️




*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_




*بسم الله الرحمن الرحيم*






*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```


*JIKAR LAWALI CE*✍️


*Wattpad: UmmuDahirah*👈




*\F.W.A📚/*


```ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH```
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._


*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._




*BOOK TWO*




.


_______________________________


*CHAPTER Thirty*


________🎓 A ƙofar gidan da Zainab take aure Saleema tafaka motar ta ta kamar yanda yaron da Umma tahaɗo su dashi yace musu, fitowa suka yi tare da sallaman yaron suka shiga cikin gidan, sallama suka yi duk kan su wanda yajawo fitowar Mahaifiyar Aliyu daga ɗaki




Amsa musu tayi cikin fara'a tare da musu maraba




Halwa ce tayi mata bayanin wajen Zainab suka zo




"Allah Sarki, to ku shiga tana nan ai, ku bi tanan ne ga hanyan sasan ta nan, sannun ku da zuwa". Still tayi maganar cike da fara'a tana sake musu sannu




Inda tanuna musu nan suka shiga, a bakin ƙofar ɗakin suka yi sallama




Zainab dake zaune a tsakar ɗakin ta, ta baje ƙafafuwa da ɗan ƙaramin cikin ta da be wuce watanni huɗu ba, yanzu ne ma yake shirin shiga na biyar ɗin, dayake ta taɓa yin ɓari, yanzun ma salat take yanka wa tana so tayi kwaɗon shi taci




Jin sallaman su yasanya tatsai da yankan tana ɗago kai ta'amsa musu tare da basu iznin shigowa




Shigowar kuwa suka yi Halwa ce a gaba




Hakan yasa Zainab tasauke idanun ta kan Halwa ɗin duk da bata gama gane ta ba, sai tawaro idanu tana son gasgata gizau ɗin da idanun ta ke mata




Lokacin tuni sun gama shigowa, yayinda Halwa kuwa kallon ta kawai take yi tana zuba murmushi, a take anan wani irin farin ciki yamamaye ta sakamakon ganin Aminiyarta wacce suka fi kowa shaƙuwa tun ƙuruciya, babu abinda ke raba su akoda yaushe har tasowar su, sai gashi rana tsaka sun rabu wanda basu sake ganin juna ba tsawon shekaru kusan biyar






"Halwa". Zainab tafaɗa da rawan baki still itama tana bin ta da idanu batare da ta motsa daga inda take zaune ba






"Zainab ɗina". Halwa itama tafaɗa ahankali idanun ta na kawo ruwan hawaye




Ai tuni Zainab ta yunƙura tamiƙe cikin tsananin murna ta nufo ta tarungume tana sake kiran sunan ta batare da ta furta wani kalman ba, kuka suka fashe dashi na tsananin kewar juna da farin ciki.




Saleema da tuni ta nemi waje ta zauna, Ahmad na hannun ta dayake tun shigowar su ta'amshe shi, kallon su kawai take yi cike da tsantsan tausayin su, kasancewar ta me rauni itama tuni ta soma hawaye batare da ta san tana yi ba






Sun daɗe rungume da juna suna ta sambatu da nuna kewar da sukai wa junan su, kafin kuma suka saki juna suka sami waje suka zauna, bakin su gaba ɗaya yaƙi rufuwa Cuz farin cikin da suke ji a yau ɗin




"Wlh bansan da bakin da zan iya nuna murnan da nake ciki ba da ganin ki Halwa, nayi kewar ki nayi kewar ki fiye da yanda kike tunani, tun ina saka ran dawowar ki har sai da kika saka nacire rai da ganin ki, nayi kewar ki wlh". Zainab taƙarike maganar nata tana me share ƙwallan da yacika mata idanu




Murmushi Halwa tayi tace "kiyi haƙuri Ƙawata, kina raina bazan taɓa manta wa dake ba, naso zuwa a lokuta da dama sai dai Allah be nufa haɗuwar mu ba sai yanzu".




Hannu Zainab tasake saka wa tashare hawayen ta, sai kuma takalli Saleema dake kallon su har yanzu ta kasa cewa uffan




Hakan yasa Halwa tace "Sunan ta Saleema, ƴar uwata da tamaye mini gurbin ki, da ba don ita ba ban san ya rayuwata zata koma ba, ita ce tamaye min farin cikina dana rasa abaya.."




"Haba ke kuwa kiyi shiru mana mu gaisa". Cewar Saleema tana katse mata maganar ta




Baki a washe Zainab tagaishe ta duk da kuwa Saleeman ba wai ta basu tserayan shekaru bane, da shekara ɗaya ta girme musu




Cikin fara'a Saleeman ta'amsa cike da ƙaunar Zainab ɗin aranta




Sai da suka gama gaishe-gaishen nasu har Zainab ɗin tatashi takawo musu drinks, Ahmed ta'amsa daga hannun Saleema takoma tazauna tana faɗin




"Kema ƴar lukuta zo nan wajena".




Husna dake maƙale jikin kujera tana jan igiyoyin kwalliyan da akayi, tataho dasauri ganin Saleema ita take kallo, dayake yarinya ce me shegen wayau ga son mutane




Ɗaukan ta Zainab tayi taɗaura saman kujeran tana cewa "Yauwa ƴan mata na, ya sunan ki?"




"Husna". Tafaɗa tana jujjuya jikin ta cikin wasa




Kallon Husnan tayi da kyau, sai taɗago tana duban Halwa tana murmusawa tace "wlh sak irin ku ɗaya, daga gani yarinyan nan taki ce, ashe kema kinyi aure?"




Dariya kawai Halwa tayi batare da tace komi ba




Saleema ce taba ta amsa da "Eh".




"Allah Sarki rayuwa kenan, ashe babu rabon muga auren juna, amma mun gode Allah tunda Allah ya haɗa mu da ran mu da lafiya".




Sai kuma takalli Ahmad tace "kai kuma ya sunan ka ɗan kyakykyawa?"




Husna ce taba ta amsa da faɗin "cunan sa Ahmad, amma kincan mene Aunty Mamy take ce mici?" ( Tana nufin Halwa)




"A'a sai kin faɗa?" Zainab tafaɗa tana shafa mata kai




"Tana ce mici Amadidi".




Dariya suka yi ban da Halwa da tayi murmushi kaɗai kana tace




"To Sarkin surutu faɗi ba'a tambaye ki ba".




"A'a ki ƙyale ta tayi surutun ta, ai duk surutun ta baza ta kai ki ba na sani". Cewar Zainab tana dariya




Yayinda Saleema ke taya ta, ɗan barkwanci suka taɓa na tuna baya kafin Zainab ɗin tace




"Wlh na shiga damuwa lokacin da su Mama suka faɗa min kin bi Dangin mahaifin ki Gombe, ban san meyasa naka sa yarda cewa wani abun ne yafaru dake ba, domin Ni dai har ga Allah nasan baza ki taɓa tafiya batare da kin sanar min ba".






Murmushin takaici Halwa tasaki tuno da abinda yafaru da ita a shekarun baya, sai dai ko kaɗan baza ta taɓa iya ɓoyewa Zainab sirrin ta ba, ita ɗin Aminiyarta ta ce wacce suka shaƙu matuƙa, kuma ta san ko babu komi zata taya ta jimamin abinda yafaru da ita, don haka tagyara zaman ta tasoma bata labarin komi da komi tun tafiyan ta har zuwa yanzu, abinda ta ɓoye mata kaɗai shine haihuwar Ahmad, don ko kaɗan bata kawo shi a zancen ta ba




Sai da Zainab ta dinga share hawaye sabida tausayin ƙawarta




"Ashe abun da yafaru dake kenan? Meyasaka su Mama suka aikata miki hakan? Dama akwai ranan da zata zo su guje ki? Waɗannan wasu irin mutane ne masu baƙin hali marasa yarda da ƙaddaran Allah, tirrrr da su wlh, tun farko shiyasaka zuciyata takasa amince wa da abinda suka faɗa mana".






Numfashi Halwa taja kana tace "Ni har yanzu ban ga laifin su ba Zainab, abinda nasani kawai shine Yaya Nura da yaƙi faɗa musu gaskiya, na tabbata wlh da ya sanar musu dole zasu yarda, har yanzu na kasa manta kalaman da Yaya Nura ya faɗa min aranan, bayan komi a gaban sa yafaru, shin meyasa ya aikata min hakan? shine abinda nake so in sani".






"Ya kuwa zaki sani tunda maci amana ne shi, idan be faɗa musu gaskiya ba su basu san ƙaddara bane? Ko kuwa basu fi kowa sanin halin ki bane? Dama sun yi ne da gayya don su kore ki sai gashi Allah yasa baza ki taɓa muzanta ba, wlh sun bani mamaki ko a mafarki bazan taɓa yarda zasu iya juya miki baya ba".




Haka Zainab ta dinga faɗa kamar zata ari baki, sai zagin su take yi musamman ma Nura da tafi tsanar sa a yanzu, bata dena ba sai da tayi ta gaji don kanta




Anan ne Halwa take faɗa mata tana son zuwa inda suka koma tagan su, gashi sun fito Umma bata faɗa musu ba bare su san gidan




Zainab ce mata tayi "ai Ni wlh ko na sani bazan faɗa miki ba balle ma ban sani ba, me zaki je kiyi musu tunda su suka kore ki? Wlh kar ki soma ki je tunda sun kore ki; ki bar su har abada".






Sai anan Saleema tasaka musu baki




"A'a hakan be kamata ba, su ɗin dolen ta ne kuma makusantan ta, kar ki manta Ƙanwar mahaifiyar ta ce, ko babu komi taci darajan ta, insha Allahu zamu je ko ba yau ba, kuma duk abinda suka yi su da Allah ne ba mu da hurumin ɗaukan mataki".






Ita dai Zainab taɓe baki tayi bata sake tanka zancen ba, sai ma sauya wa da tayi nan da nan suka ɓarke da hira, daga ƙarshe Zainab ɗin tatashi don yin musu girki, amma basu bar ta ba don tare suka shiga kichen ɗin gaba ɗayan su suka yi girkin, koda zasu ci ma a Plate ɗaya suka ci cike da nishaɗi.




Sai yamma sakaliya sannan suka baro gidan Zainab, yayinda itama tayi musu alƙawarin zuwa nan ba da jima wa ba, duk da dama Halwa ta faɗa mata zasu shiga Kotu jibi, kuma tayi mata alƙawarin zata saka Aliyu ya kawo ta Court ɗin, domin baza ayi babu ita ba.








***** ***** ****** ******
*MONDAY*


Tun ƙarfe 07:00am. Brr. Khalil yafice a gidan.








Su kuma su Halwa sai wajen ƙarfe 09:00am. Suka gama shiryawa, dayake sai ƙarfe Goma ne za'a shiga court ɗin




Husna tuni an shirya ta drever ya tafi da ita school, shi kuma Ahmad tare dashi zasu tafi yana hannun Saleema, sai da suka shiga mota ne sannan Halwa ta'amshe shi tunda Saleema ce zata tuƙa su








Direct gidan su Khalil suka wuce, saboda zasu taho tare da su Mom ne






Lokacin da suka je ba wani zama suka yi ba Mom tafito suka tafi, tunda dama ita kaɗai zata bi su, yau Monday Nazeefa na school, shima Dad yana da aiki don haka bazai samu zuwa ba






Kafin goma sun isa court ɗin, acan suka haɗu da Ummi har da Zainab da tayi musu alƙawarin zuwa






Abun mamaki kuma har da Mama da Baba da Nura a wajen, duk da Halwa bata gan su ba, su ma ɗin basu gan ta ba, amma su sun zo ne kasancewar Nura yace musu za shi ana Shari'a da uban gidan shi, shi ne Baba yace "be kamata su zauna agida ba dole su je, ko don martaba uban gidan sa tunda yayi musu halarci, a sanadiyar sa ɗan su ya sami kuɗi sosai, sannan basu da masaniyar komi akan Halwa ce wacce za'a yi Shari'an da ita






Nan kuwa basu sani ba, Haris ne yasaka shi tilas yazo, kuma yace "idan be zo ba zai iya tona masa asiri, don haka gwara yazo yaga me zai faru, be san cewa Haris wayau yayi masa ba don ya rigada ya shirya amsa duk wani tuhuma da ake musu sabida samun ƴarsa, sannan kuma ko hakan zai sa Halwa ta yafe masa har ta aure sa.








Lokacin da suka isa Halwa aka bari a baya, tana rungume da Ahmad tana shirin fitowa sai ganin Haris tayi a gaban ta






"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un". Tafaɗa a fili sa'ilin da tayi tozali dashi






Gaban ta ne yayi matsanancin faɗuwa, sai dai bata nuna firgitan ta a fili ba, ta kai duban ta gare shi fuskarta a ɗaure tamkar bata taɓa sanin sa ba, tana shirin sake yunƙura wa tafito taji muryan sa ya daki dodon kunnen ta




"Halwa ashe zamu sake haɗuwa? Nasan bani da bakin da zan roƙe ki; ki yafe min, but duk da haka ina neman afuwar ki, wlh nayi nadaman abunda..."






"Kai da Allah dakata min". Takatse sa da faɗin hakan tana me banka masa harara tamkar zata maƙure sa dan baƙin cikin ganin sa da jin muryan sa






"Ka ɓace min agaba ko in maka wulaƙacin da sai kayi nadaman zuwan ka duniya".






Shi kansa Haris yayi mamakin furucin nata da yanda tafaɗa cikin tsananin fushi tamkar ba Halwan da ya sani ba abaya, duk da dama ta sauya masa sosai amma hakan be sa ya kasa gane ta ba, kuma yasan irin hakan take masa magana domin dai bata sauya ba a yanda ya santa






Yana shirin sake magana






taja ƙofar da ƙarfi ta rufe kanta aciki, domin dai babu yanda za'a yi tabar wajen dole sai ya matsa, ita kuma baza ta iya juran sake jin maganar sa ba, ta matuƙar tsanar sa fiye da kowa a duniya






Hannun sa ya kai zai ƙwanƙwasa Glasses Motan, sai jin murya daga bayan sa yayi, wanda ya dakatar dashi daga abinda yayi ninya






"Malam don Allah kayi haƙuri ka bar nan wajen, Halwa yanzu matar wani ne baka da hurumin da zaka iya mata magana kaji ko?". Cewar Saleema dake tsaye gefe tana kallon duk abinda suke yi tun ɗazu






Shima dai kallon ta yayi tamkar sakarai, babu abinda ke kai kawo a zuciyar sa sai ce masa da tayi "Halwa matar wani ne". "Kenan tayi aure?" Ya tambayi kansa batare da zai iya samun amsar ba






Be sake motsawa ba, tamkar gunki ya zama sabida ba ƙaramin taɓa sa maganar yayi ba, har be san ma a wani yanayi yake ciki ba






"Excuse me zan wuce". Tayi maganar tana kallon sa ganin be da ninyan jirga wa






Ɗan ja baya yayi kaɗan ya matsa mata kamar wanda be da jini a jiki






Buɗe ƙofan tayi ta'amshi Ahmad daga hannun Halwa, sannan tayi mata maganar tafito




Ko kallo be ishe ta ba sanda tafito, gaba kawai tayi tabar Saleema na rufe ƙofan kafin tabiyo bayan ta






Idanu kawai ya kafa ma bayan ta hawaye na sintiri a face ɗin sa.
[1/20, 5:15 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎓
🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️




*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_




*بسم الله الرحمن الرحيم*






*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```


*JIKAR LAWALI CE*✍️


*Wattpad: UmmuDahirah*👈




*\F.W.A📚/*


```ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH```
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._


*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._




*BOOK TWO*




.


_______________________________


*CHAPTER Thirty One*


________🎓 Kafin Shari'an su Halwa akwai Shari'an da Khalil ya soma yi




Na wani yaro ne da yayi wa ƴar aikin gidan su fyaɗe, tun wajen watanni uku da soma Shari'ar sai yau ne ake shirin ƙarƙare shi




Kasancewar uban yaron me kuɗin gaske ne, tun a zaman farko da yaga Khalil na shirin yin nasara akan su, shi ne sanadin da ya samo ƴan daba suka je suka harbe shi, sun so su kashe sa ne gaba ɗaya sai Allah be basu Sa'a ba




Lokacin da Alh. Sheƙau (kar ku ce da Sheƙau ɗin sambisa nake yi fa lolx 🤪) ya basu aikin; to ya bar ƙasan ma gaba ɗaya shi da ɗan sa tunda ya samu beli, ƴan daban kuma da suka yi aikin sun tabbatar masa Khalil ya mutu duk da kuwa su ma daga baya suke jin yana da rai, sun so su sake komawa asibitin su kashe sa but a time ɗin akwai jami'an tsaro, to sai suka yi wa Alh. Sheƙau bayanin cewa sun wulla Khalil barzahu, don haka ya biya su kuɗin su sukai gaba a bin su






Sai kwanaki biyun nan suka dawo ƙasan sabida a yau ɗin za'a koma kotu a yanke hukuncin ƙarshe, sun saki jiki babu abinda zai faru tunda an kashe musu Khalil, duk da a time ɗin har da Brr. Tahir ya taya shi shari'ar, amma sun fi so su ga bayan Khalil tunda shine yadage sai ya amsar wa yarinyan haƙkin ta.






Yau kuma da aka shiga kotu sai hankalin su yayi mummunan tashi ganin Khalil a raye be mutu ba






Shi kuwa Khalil murmushi kawai yayi yana bin su da kallo, don shi tuni ya gane Alh. Sheƙau ne ya saka a kashe shi, be faɗa ma kowa bane don baya son maganar tayi tsawo, duk da kuwa yana da hanyan da zai

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads