Showing 81001 words to 84000 words out of 132567 words
Chapter 28 - BARRISTER IBRAHIM KHALIL Complete Document by Nafisa Isma'il Lawal.txt
alwashin sai yayi mata abinda baza ta taɓa mantawa dashi ba, domin kuwa tunda yake babu wanda yataɓa taɓa masa lafiyan jiki
A lokacin babu abinda be sani akanta ba, har soyayyar da suke yi da Nura ya san komi sabida yana da yaran da suke bibiyan masa ita
Abu na farko da yasoma yi shine neman Nura, har gida aka kawo masa Nura kuma yafaɗa masa buƙatarsa, a lokacin Nura be amince ba sai da yaji kuɗi Miliyan uku da yayi masa alkawarin zai basa in dai zai sadaukar masa da budurcin Halwa, shi a ganin sa idan har yakawar da sha'awar Halwa aransa to tabbas duk wani soyayya da yake mata zai gushe, wannan dalilin ne yasaka yanemi aikata mata fyaɗe bayan ya nemi taimako wajen Nura
Shi kuma Nura babu musu ya amince, a ganin sa idan har yasadaukar da budurcin Halwa akan wannan zunzurutun kuɗin be faɗi ba, kuma hakan yana ganin dama ce tazo mishi da zai yi kuɗi batare da yasha wahala ba, sannan yarigada ya saka ma ransa shi zai auri Halwa ɗin yarufa mata asiri tunda SHINE SILA, kuma shine zai ɗau alhakin duk abinda zai same ta don yarage girman laifin sa
Take nan ya amince sannan suka shirya yanda za'a yi har Halwa tazo hannun Haris, kamar yanda kuka gani abaya
Duk wannan abinda yafaru da Halwa da haɗin bakin Nura, sannan kuma lokacin da yaji maganar ciki hankalin sa yayi mugun tashi duk da alokacin yana tunanin bazai iya auren macen da yasan ba ta tare da mutuncin ta ba, anan ne dabara yazo masa har yanuna shi be san da maganar Fyaɗen da akayi mata ba don kawai ya yakice ta ajikin sa
Haris kuma tun sanda yayi mummunan aika-aikan nan yakoma Abuja kasancewar acan yake aiki, yana kula ma mahaifin sa da ƙaramar Companin sa da yabuɗe na Shinkafa, amma me tunda yakoma sai yazamana bashi da sukunin zuciya, ƙaunar Halwa tayi masa bakeke a rai ta hana sa saƙat, be taɓa tunanin sonta ya kai haka ba sai da yayi nisa da ita, ya so yadanne yajure ko zai manta da ita amma hakan ba me yiwuwa bane
Dole yadawo gida don ganin ta ko yaji sanyi a ransa, lokacin watan sa biyu acan kuma a lokacin tuni Halwa tayi wajen two weeks da barin gida
Dawowar sa da jin abinda yafaru wajen Nura hankalin sa yayi ƙololuwar tashi, yayi baƙin cikin koran ta da sukayi da cikin sa ajikin ta, ya sake shiga damuwa matuƙa, haka ya bazama neman ta ko Allah zai sa adace, domin ya rigada ya ɗau alwashin muddin yaganta zai aure ta kuma su raine abunda zata haifa, yana matuƙar son ta bazai iya rabuwa da ita ba, har Gombe can dangin mahaifin ta sai da yaje amma akace bata zo ba, su ma alokacin suka ji abinda yafaru, sai dai basu wani damu ba tunda Mama ta faɗa musu cikin Shege tayi suka koro ta nan ashe bata zo ba, su aganin su hakan ma da tayi yadace tunda ko tazo su ma ɗin korata zasu yi don baza su iya riƙe ta da abun kunya ba
Rayuwa ta sauya ma Haris matuƙa ya shiga damuwa sosai akan rasa Halwa wanda har sai da yakwanta ciwo, kullum bashi da buri idan ba yahaɗu da ita ba, a haka iyayen sa suka tilasta masa auren ɗaya daga cikin dangin su, domin su a ganin su idan har yasamu mata hakan zai dawo masa da nutsuwar sa, duk da dai basu san musabbabin abinda yafaru ba amma sun san cewa akan mace yashiga wannan halin, tunda be da abin faɗa sai sunan ta
Be musa musu da auren ba tunda shima hankalin sa baya jikin sa, ahaka akayi auren Amarya Zubaida tatare a gidan auren ta, da daɗi babu daɗi haka tazauna dashi tunda dama ita tana matuƙar ƙaunar sa, haka rayuwa taci gaba da tafiya har komi yalafa ma Haris duk da har yanzu ƙaunar Halwa na ransa sai dai yanzu ya cire duk wani damuwa aran sa ya dawo daidai yaci gaba da aikin sa, sai dai yaƙi komawa Abuja acewar sa anan Katsina Yakamata yazauna yayi aikin sa koda Allah zai haɗa sa da Halwa, baya son ko kaɗan yayi nisa da garin duk da be san cewa tana nan ko bata nan ba
Haka shekara ɗaya da watanni yashuɗe Zubaida bata taɓa koda ɓari ba, gashi burin iyayen sa su samu jikoki masu yawa tunda shi kaɗai Allah yabasu, hakan sosai yaɗaga musu hankali har shi Haris ɗin don shima yana son ganin yaran sa, don haka suka soma ziyartan asibiti amma sakamako ya nuna lafiyan su ƙalau lokaci ne be yi ba
Ana cikin haka Mahaifiyar Haris tasake ce masa yayi aure domin ita bata yarda matsalan ba daga wajen Zubaida yake ba, shi kuma Haris ko kaɗan baya ƙaunar tara mata da yawa don haka yabijire mata duk da kuwa ba wai yana son Zubaida bane amma suna zaune lafiya sosai sabida kyautata masa da take yi
An kai ruwa rana kafin Haris yayarda aka yi masa aure, don iyayen nasa duk sun goyi bayan ƙara auren nasa tunda suna son suga jikokin su nan kusa, duk da kuwa shekara biyu kenan da auren
Haris ya rigada ya sa aransa duk sanda yahaɗu da Halwa idan har zata aure sa to tabbas sai ya rabu da duk matan nasa tunda shi a tsarin sa mace daya yake so, sosai yaji daɗin cikin da tatafi dashi, kuma hakan yasa ya gane cewa shi ɗin yana haihuwa Allah ne be kawo ba, bashi da buri a yanzu illa yaga abinda tahaifa masa, ƙaunar ɗan nasa da be taɓa gani ba tuni ya shiga ransa sosai
Da maganar ƙara auren nasa da auren be fi wata biyu ba akayi komi aka gama, Amaryan sa Fahima ta tare a sabon gidan da mahaifin shi yagina masa tare da Uwar gida Zubaida
Itama dai tunda tazo ɗin bata taɓa koda ɓatan wata bane, har sanda itama tashafe shekara ɗaya curr kafin Allah yabata Ciki, zo kuga murna wajen Familyn baki ɗaya don kowa ya ƙosa yaga yaran Haris, iyayen sa babu wanda yakai su murna, haka akai ta tattalin Fahima da ɗan tayin cikin ta
Sai dai tunda tasamu cikin babu lafiya, yau suna asibiti gobe suna gida, yana watanni uku tayi ɓarin sa wanda har sai da aka dangana ga asibiti saboda yanda take zuban jini ta fita hayyacin ta gaba ɗaya, haka aka ɗauke ta ranga-ranga aka nufa Hospital da ita duk hankalin su a tashe.
______________________
A wannan lokacin itama Saleema ashe ciki ya shiga jikin ta, duk yanda kaso da dabara Allah idan yariga yaƙaddara abunsa to babu yanda zakayi, duk maganin hana ɗaukan cikin da Khalil yay ta bata amma a banza gashi ta samu shigan ciki har na wata ɗaya kamar yanda idan yakai hakan take ɓarin sa wannan ma karon hakan tayi, sai dai na wannan karon yafi na kowanne baƙin wahala
Tunda aka kai ta asibiti suke sintiri su ji me zai biyo baya amma babu likitoci babu alamun su, sai da akayi kamar mintuna 30 kafin suka fito suka nemi jini, tana buƙatar jini leda huɗu saboda ta bala'in zub da jinin ta
Haka aka ɗibi na Khalil dana Abba, sai aka siya ɗaya duk aka saka mata, su kansu Likitocin basa tunanin ma ko zata iya rayuwa a yanda take, ko numfashi bata yi sai da taimakon Oxgyen
Likitan ta yarigada yayi ma su Abba bayani dole sai an juya mata mahaifa sabida idan taci gaba da samun ciki to ƙarshe rasa ta zasu yi har abada, yanzu ma basu da tabbacin ko zata iya rayuwa.
Can ɗakin da aka kwantar da Saleema, su Ummi ne suka shiga tare da Halwa, gaba ɗayan su hawaye suke yi, yanda suka ganta tamkar matacciya hankalin su ya daɗa tashi ainun, Halwa kasa jurewa tayi tarufe bakin ta tafita dasauri cikin ɗakin, wani lungu tasamu tasoma gurzan kuka kamar zata shiɗe, kuka sosai take yi na tausayin Saleema
Haris lokacin yashigo asibitin kawo ma Matar sa abubuwan buƙata tare da abinda zasu ci, tunda a ranan kwanan ta biyu a asibitin kuma har tasamu sauƙi ana saka ran sallaman su yau ko gobe
Tunda yashigo idanun sa yasauka kan Halwa da tahaɗa kai da gwiwa tana ta sharɓan kuka, sosai yaji babu daɗi aran sa, haka kawai kuma yaji yana son ganin ko wacece yasan damuwar ta, sai kallon ta yake yi kamar yaje sai kuma yashige cikin asibitin yanufi ɗakin da aka kwantar da matar sa
Ƙanwar Maman Fahiman ce take jinyan ta, su biyu ne a ɗakin
Yana shiga suka gaisa ya'ajiye kayan da yazo dashi, tunda yazauna yarinyan da yawuce tana kuka ita ce tahana zuciyarsa sukuni, daga ƙarshe sai yamiƙe yafito don zuwa wajen ta yatambayi abinda ke damunta.
[11/24/2020, 9:03 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎓
🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuDahirah*👈
*\F.W.A📚/*
```ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH```
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
_Wannan shafin naku ne masoyana na cikin group ɗin Khaleesat Haydar, na gode da nuna soyayyar ku gare Ni, Allah yabiya._❤️
*BOOK TWO*
.
_______________________________
*CHAPTER Nine*
________🎓Yana zuwa wajen sai dai babu ita, ya dudduba amma be ganta ba don haka yakoma cikin ɗakin da aka kwantar da Fahima, dama kawai don ta tsaya masa a rai ne but tunda yaduba be ganta ba sai be sake tuna ta ba har yabar asibitin.
____________________
Halwa tana tashi a wajen komawa ɗakin tayi, sai dai tana zuwa bakin ƙofa kunnuwan ta suka jiye mata maganganun Abba dake faɗa ma Ummi matsalan Saleema ɗin, sai kawai tazame nan ƙasa tasaki kuka me sauti, daga inda take zaune tana jin kukan Ummi itama don takasa jurewa, sai da Abba yayi ta rarrashin ta yanuna mata zata iya damun Saleema idan bata dena kukan ba tunda an ce kar suyi hayaniya da zai dame ta, hakan yasa Ummi tarage kukan ta takoma kukan zuci da hawaye
Abba ne yafito yatarda Halwan anan ƙasa tana nata sharɓan kukan, gaba ɗaya idanunta sun rine sun kumbura suntum wanda kallo ɗaya zaka yi mata katabbatar ta jima tana kuka yanda har fuskarta sai da yakumbura
"Subhanallah.. Daughter me kike yi anan? Kukan me kike yi?" Yatambaye ta yana saka hannu yaɗago ta
Halwa bata iya bashi amsa ba sai ƙara sautin kukan ta da take yi, duk da kuwa ta toshe bakin ta da Hijabin ta hakan be hana an ji fitan sautin kukan ta ba
Dafa kanta Abba yayi cike da ƙarfin halin sa yace "kiyi shiru kinji? insha Allahu ƴar uwanki zata samu sauƙi ki dena kuka haka nan".
Ya daɗe yana rarrashinta kafin yabuɗe mata ƙofar ɗakin yabata umarnin tashiga, shi kuma yajuya yatafi.
Tana shiga taƙarisa gaban gadon inda Ummi ke zaune ta tasa Saleema agaba tana zirarar da hawaye
Gefen gadon taɗan ɗofana mazaunan ta tana kallon Saleeman itama, wasu sabbin hawayen ne suka soma sintiri a face ɗin ta sabida tausayin ta, lumshe idanuwan ta tayi tabuɗe su akan Ummi da har yanzu ko ƙifta idanu bata yi, cikin rawan murya tace
"Yanzu shikenan Ummi.. baza ta haihu ba? Meyasa za'a juya mata mahaifa? Meyasa baza'a nema mata magani ba? Don Allah.. kar ayi.. gaggawan wannan..aikin". Taƙarike maganar nata cikin tsananin rawan baki da jan numfashi
Itama Ummi numfashin taja cike da sanyin murya da idan kaji zaka san tana cikin matuƙar damuwa tace "Ni kaina bansan wani irin ciwo ne wannan dake damun ta ba, sai dai sun tabbatar mana akwai wasu tsirrai a cikin mahaifan ta da baza su taɓa bari ta raini ciki ba, sannan kuma mahaifan ta babu ƙarfi ko anyi mata aiki ba lallai ne asamu nasara ba".
Halwa tace "Ummi idan har za'a iya dashen cikin ajikina Ni zan iya rainon mata, zan haifa mata idan har zata ga ɗan ta a duniya, a shirye nake in sadaukar da komi nawa don samun farin cikin ta".
Ummi kallon Halwa take yi kamar bata gane me take nufi ba
Sai Halwan tasake cewa "Ummi ki duba magana ta, idan har Saleema tasan da cewa an juya mata mahaifa hakan na nufin baza ta ƙara haihuwa ba to zata shiga matsanancin damuwa, kuma kinsan tana da ciwon zuciya idan hakan yayi tasiri zamu iya rasa ta, tunda ina da hanyan taimakon ta zan rainan mata cikin in haifa mata sai in bata yaron ta".
"Halwa idan har na amince za'a yi hakan Mahaifin ta da Mijin ta ba lallai su yarda ba, bansan me zan faɗa musu ba".
Daga maganar Ummin sai suka yi shiru gaba ɗayan su suna tunani
A lokacin ne Mom suka zo ita dasu Dad har da Khalil dasu Sameer, gaigaisa wa akayi tare da tambayan me jiki?
itama Halwa tagaishe su suka amsa cikin farin ciki, daga haka bata ƙara cewa komi ba tana jin su suna maganan su, daga baya su Dad suka fita ɗakin yarage daga Mom sai Ummi sai ita Halwan, har sai da likita yazo kafin suka fito waje
Sai dare ita Mom tatafi gida lokacin Khalil ya dawo sai yatafi da ita
Ita kuma Halwa sai da Larai takawo musu abinci sannan suka koma tare
A ranan Ummi ta kwana ne da maganganun Halwa a ranta, sosai tahau tunanin neman mafita, daga ƙarshe kuma tayanke shawaran zata soma tuntuɓan mijin Saleema da maganar idan ya amince tasan sauran babu matsala
Da sassafe Khalil ɗin shi yasoma zuwa, Ummi batayi ƙauron baki ba tafaɗa masa komi da kuma taimakon da Halwa tace zata yi ma ƴar su
Khalil shiru yayi kawai yana sauraron Ummi har sanda tagama maganar ta, lokacin hawaye kawai take yi
Sai tausayin ta duk yakama sa, shi kansa zai so hakan sabida tsananin tausayin Saleema dake ransa, yasan da cewa idan har taji komi zata shiga wani hali sosai, ba abu ne me sauƙi ba ace baza ka taɓa haihuwa ba bare kuma fa waɗanda suke son ƴaƴan, yana matuƙar tausayinta ta yanda Allah yajarabce ta da cututtuka kala-kala, gwara shi namiji ne yana da damar da zai iya ƙara aure yahaihu da wata matar, idan har hakan shine maslaha to ya yarda zai taimaka mata, idan tasamu ɗanta ko guda ɗaya ne hakan zai sanyaya mata ranta, sannan ma ba wai wata daban ce zata rainan masa cikin ba Masoyiyarsa wacce yake matuƙar ƙauna aransa ne zata raini cikin, ko babu komi zai yi farin ciki da hakan
Don haka koda yanuna ma Ummi ya amince tayi farin ciki sosai, su biyun suka nufi office ɗin Doctor sai suka bar Halwa don alokacin tarigada tazo
Sun jima suna tattaunawa, duk da shi doctor ɗin ya nuna musu kuskuren yin hakan tunda musulunci Bata yarda da hakan ba, amma kuma duk kansu sun rigada da sun san hakan mafita kawai suke nema, ba don komi ba sai dan taimakon Saleema, sun manta da cewa haka ƙaddaran ta yake, sai dai sun san idan da lafiyan ta lau ba ta ɗauke da ciwon zuciya tabbas haka nan zata ɗau ƙaddaran ta
Kasancewar akwai kayan aikin a asibitin don haka anan suka shirya yin aikin
Doctor shi da kansa yayi ma Abba bayani kamar yanda suka shirya, kuma Ummi bata son Abba yasan da zancen, don haka Doctor yayi masa bayani akan baza su juyar mata da mahaifa ba zasu soma ɗaura ta a magani da suke sa ran za'a iya dacewa
A zahiri kuma sun shirya za'a juya ma Saleeman mahaifa batare da kowa ya sani ba sai su kaɗai ɗin, ko da nan gaba Halwa ta haifa mata yaron kowa zai ɗauka Saleeman ce tahaifa tunda sun san dama ba'a juya mata mahaifa ba, ita kuma Halwa zata koma gidan Khalil da zama ta raini cikin a sirri har tahaifa.
___________________________
Kwanan Saleema biyar kafin tafarfaɗo, tunda tafarka take kuka Ummi tayi rarrashin duniya taƙi yin shiru, duk hankalin Ummi ɗin ya tashi kar yazo wani abun yafaru da ita
A lokacin Ummi ita kaɗai ce a ɗakin
Sai doctor da yashigo yanzu yaganta tana kuka, yasoma tambayan Ummi abinda yafaru
Cikin tsananin tashin hankali Ummu tace "wlh doctor bansan meke faruwa da ita ba, yanzu tatashi kuma tunda tatashi take kuka, nayi-nayi tayi shiru taƙi yi, yanzu nake shirin kiran ka sai ga ka ka iso".
Kallon Saleema dake kwance tana sharɓan kuka yayi, cikin tausayawa yace "Saleema meke faruwa ne me yasaka ki kuka? Ko wani wajen na miki ciwo ne?"
Girgiza kanta tayi tana kallon su da rinannun idanuwan ta wanda suka faɗa suka yi baƙi, ita kanta gaba ɗaya ta zurma ta faɗa sosai gunun tausayi
"To menene faɗa min?" Likitan yasake tambayar ta
Cikin kukan take cewa "Doctor.. cikinaa.."
Sai tasoma numfarfashi kamar ranta zai fita
"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un.." Ummi tafaɗa cikin ruɗewa tana ruƙo ta tare da fashewa da kuka
Shima Doctor ɗin ya ruɗe Nan da nan yamatso da zumman taimaka mata
Sai tasake cewa "doctor.. cikina.. ya zube ko?"
Duk kan su shiru suka yi don basu san amsar da zasu bata ba, ita Ummi kuka ya hana ta magana
Sai Doctor ne yayi ƙarfin halin kwantar mata da hankali
"Don Allah Saleema ki kwantar da hankalin ki, yanzu insha Allahu mun samo matsalar ki komi zai wuce kinji? Kiyi haƙuri kar ki saka ma ranki damuwa tunda yanzu lafiyan ki muke so, Ummin ki zata yi miki bayani kinji kiyi shiru".
Ummi ma cikin son ƙara kwantar mata da hankali tace "my Dear ki dena kukan yanzu komi yazo ƙarshe kinji?".
Sai tasaka hannu tana share mata hawayen
Doctor yace "Sister yanzu abata ko ruwan tea ne tunda jikin ta babu ƙarfi, idan nadawo zan yi mata allura sai in saka mata Drip, ki kula da ita sosai Please".
Gyaɗa kanta Ummi tayi sannan tace "to doctor".
Sai da yasake duba ta tare da yin mata tambayoyi kafin yafice.
Ummi taimaka mata tayi tatashi zaune, tagyara mata pilow abayan ta