Showing 117001 words to 120000 words out of 132567 words
Chapter 40 - BARRISTER IBRAHIM KHALIL Complete Document by Nafisa Isma'il Lawal.txt
wlh nasha aiki, kin jini ne tamkar zan rabe gida biyu".
Babu shiri Halwa tasaka dariya tana sake juyowa yanda zata ganta
"To dama wa yasaki? Aikin da babu lada kawai kin saka kanki".
Hararan ta Saleema tayi tana tashi zaune tace "ai in ke baki gode min ba Mijin ki zai gode min, kuma ai taimakon ku nayi ko?"
Dariyan dai Halwa tayi bata ce komi ba, murza hannun ta tayi tana tunanin yanda za'a yi tafurta abinda ke bakin ta, sai kuma tasake kallon Saleeman da a yanzu take ta faman jan hannayen ta tana naushin iska tamkar zata yi kuka, hakan sai yasake ba ma Halwa dariya, ai kuwa tasaka mata dariya
Yayinda ita kuma Saleema tasake kwaɓe fuska tana cewa "wlh sister ki dena min dariya dagaske nake yi baki ji yanda jikina ke min ciwo ba".
Rage dariyan nata tayi tana kallon ta tace "to Sister ai gaskiya nafaɗa miki dama, meyasa zaki yi wannan aikin baki jira Ni na tashi in taya ki ba? Kin san Baki da lafiya amma don Allah kin ɗaura wa kanki abinda yafi ƙarfin ki".
Saleema tace "to ai ke Amarya ce taya zan bar ki kiyi aiki? Bari ma kiji sai kinyi sati ɗaya curr Sannan zaki soma aiki agidan nan don na rigada na amshe komi". Taƙarishe maganar cike da fara'a wanda kana kallon ta zaka san maganar da tayin ya saka ta nishaɗi ne sosai
Halwa har ta buɗe baki da ninyan yin magana Saleeman takatse ta da cewa
"Yauwa yanzu kinga saura abinci zan je in dafa mana shi kaɗai yarage min".
Dasauri Halwa tamiƙe tana faɗin "ki barshi Ni zan yi".
Hararan ta Saleema tayi tana yin gaba tafice batare da ta tanka mata ba
Itama bin bayan ta tayi har zuwa kichen ɗin, duk magiyan da Halwa tayi ma Saleema akan tabar shi ita zata yi but samm taƙi sauraron ta, dole ta haƙura tahau taya ta tana mita
Abinci me rai da lafiya suka shirya cikin awannin da basu gaza biyu ba, sai da suka gama suka kai dainnig suka jera sannan suka zube saman kujera suna taɓa hira, har sannan Khalil be dawo gidan ba.
Sai gab da magriba yashigo, alwala kawai yaɗaura yasake ficewa zuwa masjid, be dawo ba sai da akayi sallan isha'i kamar yanda yasaba akoda yaushe
Suna zaune a parlour'n yashigo da sallama, atare suka amsa masa tare da mishi sannu
Amsawa yayi idanun sa na kan waya, zama yayi yana ci gaba da latsa wayan sa kamar yanda yashigo yana yi
Saleema ce tatashi takawo masa ruwa ta'ajiye masa, ganin hankalin sa baya kansu sai suka ci gaba da hiran su, yayinda shi kuma yake ta latse-latsen wayan sa, ga duk kan alamu abu me muhimmanci yake yi, daga ƙarshe ma tashi yayi yashige ɗakin sa, be fi mintuna goma ba yafito
Saleema da tayi masa maganar abinci sai be amsa mata ba kasancewar a yanzu ɗin ya saka waya a kunne yana amsa Call, da hannu yayi musu nuni su je su ci, sai suka miƙe suka nufi dainning ɗin suka zauna
Kamar mintuna biyar da zaman nasu shima yaƙariso yana jan kujera gefen Saleema yazauna, yayinda suka saka ta tsakiya kasancewar Halwa na zaune ɗaya side ɗin nata
Khalil ɗin be wani ci abincin sosai ba saboda hankalin sa kacokan yana kan waya, Call yake ta amsa wa, daga ƙarshe sai yamiƙe yana jan kujeran baya yawuce abin sa yakoma ɗaki
Ajiyan zuciya Halwa tayi aranta tana mamakin yau kuma lafiyan sa ƙalau? To waya babu ƙaƙƙautawa sai kace wani ɗan Film
Miƙewa itama Saleema tayi tawuce ɗaki bayan tayi mata bayanin zata je tayi wanka tayi shirin barci sabida yau da wuri zata kwanta, duk gaba ɗaya ta gama tara gajiya a jikin ta, kasancewar bata jin ƙarfin jiki hakan yasa aikin yayi tasiri duk yasaukar mata da gajiya
Gyara zama Halwa tayi kan kujeran dainning ɗin, aranta itama tana son taje tayi wankan tayi shirin kwanciya amma tunawa da cewa kayan ta na ɗakin Khalil sai bata yi gigin zuwa ba, Allah yaso ta da wayan ta a hannu sai tayi zaman ta abunta tasaka Game tana yi.
Shi kuwa Khalil tunda yashige zama yayi bakin gado, ya daɗe yana wayan kafin yasauke idanun sa kan agogo, lokacin ƙarfe 10:30pm. Sai yamiƙe yashige toilet yayi wanka yafito, Direct sip ɗin kayan sa yanufa, yana buɗe wa idanun sa suka sauka kan kayan Halwa, mamaki ne yakamasa
Shiru yayi yana tsirawa kayan idanu, ya jima ahaka kafin yarufe yana buɗe ɗaya side ɗin yaciro jallabiya fara da gajeren wando, sai da yafeshe da turaren sa me ƙamshi kafin yasaka yafito zuwa ɗakin Saleema, ko kaɗan be lura da Halwa dake zaune kan dainning ba, tunda yakalli cikin parlour'n yatabbatar babu su sai yashige ɗakin Saleeman a tunanin sa ko suna ciki.
Halwa dake zaune tana kallon fitowar sa da shigewar sa ɗakin Saleeman, hakan yasa tasauke ɓoyayyen ajiyan zuciya don tasan maybe bazai fito ba ya shiga kenan,
Bata san meyasa ba tunda Saleema tayi mata maganar ɗazu sai jikin ta yayi sanyi, komi tana yin sa ne tare da fargaban me zai biyo baya tunda har yanzu bata san makomar ta wajen Khalil ba, "shin zai amshe ta a matsayin matar nasa ne ko kuwa zasu ci gaba da zaman da suka yi ne na baya?" Wannan amsar ne bata sani ba don haka tatashi tanufi ɗakin nashi.
*****
Ƙariso wa Saleema tayi tazauna kusa dashi tana faɗin "Mijina yau fa ƴar uwata ke da kai bani ba?"
Murmushi Khalil yayi, duk da abinda ke ransa kenan amma be san yanda zai ce mata ba Cuz baya son tayi tunanin ko ya ƙosa ne, that's why yabari ko zuwa gobe sai yazauna yaraba musu kwana, sai ma gashi kamar ta fahimce sa take faɗan hakan
Girgiza hannun sa tayi ganin yayi shiru ya tsira mata idanu
"Ko baka ji me nace bane?" Tayi maganar tana faɗaɗa fara'an ta
Basarwa yayi yana taɓe baki yace "naji ki mana Matata, But Ni ba yau nayi ninyan zuwa ba, sai ki bari zuwa jibi inyaso sai in koma ɗakin ta tunda kece babba ai". Yaƙarishe maganar yana kashe mata idanu tare da janyo ta jikin sa
Bata san meyasa ba sai taji farin ciki aranta da maganar nasa, lumshe idanu kawai tayi tana ƙara lafewa a jikin sa, sai dai kuma bata jin zata iya barin hakan domin yau ta tanadar musu ranan nasa ne da Halwa, a ganin ta yau ɗin ɗakin ta yakamata yaje ba nata ba, don haka taɗago tana gyara zaman ta da kyau tace
"A'a Ni dai na yafe wlh, Ni fa na rigada na bar muku ka soma cin angoncin ka kamar yadda ko wani Ango yake yi na tsawon sati ɗaya, haka Shari'a ta yarje mana sannan sai mu raba kwana, bari ma kagani don Ni nayi muku tanadi".
Taƙarishe maganar tana miƙe wa tanufi lungun gadon ta ta ɗaya side ɗin taɗauko ledojin da ta'aiki Sale yasiyo mata kaji da kayan maƙulashe
Khalil dake kallon ta yana ganin ikon Allah har ta'iso ta'ajiye masa a gaban sa tana sake zama sannan takalle sa da murmushi tace "gashi nan na tarban Amarya ne".
Kallon ledan yayi, sai kuma yasaka hannu yaɗago yana duba wa, ɗago ido yayi yana kallon ta
Sai taware masa idanu still tana murmusawa
Be san me zai ce mata ba don haka sai yarungumo ta jikin sa yaɗago ta zuwa cinyan sa tare da haɗe bakin su waje ɗaya
Tabbas yau ya sake tabbatar wa Saleema na daban ce, da ita da Halwa bai san wacce tafi kyakykyawar zuciya ba, duk da Saleema tafi Halwa komi don bazai ce kyawu ne yaruɗe sa ba amma kuma zuciyarsa Halwa take tsananin ƙauna, be san meyasaka hakan ba, a ranan farko da yaganta be san komi nata ba but a kallon da sukai ma juna kaɗai zuciyar sa taharbu da tsananin ƙaunar ta, baya ga haka baya tunanin akwai abinda yaja ra'ayin sa ajikin ta da har yaji yana son ta tunda be san komi nata ba a lokacin, abun dai da zai iya cewa ƙaunar ta kawai daga Allah ne, shine yadasa masa ƙaunar ta a zuciya wanda yake jin sa yana gudana da jinin jikin sa tare da bugun numfashin sa, kullum ƙara jinta aransa yake yi memakon raguwa..
Tunda yahaɗe bakin su Saleema lumshe idanun ta tayi tana sauraron saƙon da yake aika mata dashi, ko kaɗan bata yi tunanin taya sa ba sabida bata son hakan yaɗau lokaci
Ganin dai yana wuce gona da iri sai tajanye jikin ta tana ƙara marairaice fuska ganin yana shirin sake haɗe bakin su, roƙon sa tasoma yi tana faɗa masa lokaci yaja be kamata yazauna anan ba
Daƙyar dai tasamu yabar mata ɗakin don sai da yaƙara ɓata lokaci wajen ta
Yana fita tagyara rigan ta tana faɗawa kan gadon tare da lumshe idanun ta hawaye masu ɗumi suka soma sulmiyo mata, wani irin tsananin ƙaunar mijin ta da kishin sa ne yake nuƙurƙusan ta, amma kuma tasan cewa yanzu ya tashi a nata kaɗai dole sai tayi sharing ɗin sa da wata, ko kaɗan bata jin haushin Halwa a yanzu, idan ma taƙi Halwan da mijinta ai dole sai ya auro wata tunda bazai zauna babu haihuwa ba
Danne zuciyarta kawai tayi taci gaba da rarrashin kanta, sai dai ta daɗe ahaka barci be ɗauke ta ba, sai kawai tatashi taɗauro alwala tasoma raya daren tare da roƙon Allah yaba su zaman lafiya kuma yakaɗe musu sheɗan a zamantakewar su, tare da roƙon Allah ya ƙara mata juriya da haƙuri, domin tabbas ba kaɗan ba zuciyarta tsananin zugi take mata kasancewar ta me fama da ciwo a zuciyan, shiyasa ta kasa jure zafin da take mata har tasaka kuka cikin sallan nata don dai kawai tasamu salama a zuciyar
[1/5, 3:37 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎓
🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuDahirah*👈
*\F.W.A📚/*
```ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH```
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
*BOOK TWO*
.
_______________________________
*CHAPTER Twenty Eight*
________🎓Yana tura ƙofan Halwa tabuɗe idanun ta, dama tun ɗazu bata yi barci ba tunani ya cika mata zuciya
Jin ya nufo wajen gadon sai tasake Rufe idanun ta tana sauraron bugun zuciyar ta dake sake hauhawa
Ajiyan zuciya yasauke lokacin da ya'iso bakin gadon yasami waje yazauna, fuskarta yake kallo kasancewar Facing ɗin sa take yi kuma da hasken lantarki da yakunna shigowar sa, yasan ba barci take yi ba don haka yace
"Tashi zaune muyi magana".
Runtse idanuwan ta tasake yi, sai kuma ahankali taware su kan bayan sa da yajuya mata, tashi tayi tazauna tana sake jawo bargon jikin ta duk da ba wai ta saka kayan barcin me nuna tsiraici bane, sai dai kasancewar yanda yalafe a jikin ta ana ganin komi, gashi kuma rigan iyakan ƙasan gwiwan ta yatsaya
Shima gyara zaman sa yayi sosai yana fuskantan ta
Kanta a ƙasa tana jiran abinda zai biyo baya, sai dai shiru yaƙi yin magana, ita kuma ta kasa ɗago kai bare ta kalle sa sabida tasan idanun sa na kanta
Zuba mata idanu kawai yayi yana kallon ta, jujjuya maganar da yake son furta mata yake yi a zuciyar sa, sai da ya ɗan ja lokaci kafin yafesar da numfashi yabuɗe baki yasoma magana
"Halwa". Yakira sunan ta a hankali
"Na'am". Ta'amsa masa batare da ta ɗago kanta ba
Hannayen sa yahaɗe waje ɗaya kafin yace "Da farko dai ina so in baki haƙuri agame da zamantakewar da mukayi abaya, sabida yanda na nuna miki halin ko in kula a matsayin ki na Matata, duk da ba wai nayi hakan a son Raina bane, har a cikin zuciyata ina jin zafin abubuwan da nayi miki, don Allah idan na ɓata miki ki yafe min yanzu ina so mu gyara zaman auren mu ne shiyasa nake so mu soma fahimtar juna a yanzu ɗin".
Lumshe idanuwan ta tayi hawayen da suka soma sintiri a fuskarta tun soma maganar sa suka ci gaba da tsiyaya, wani irin sanyi ne yake ratsa ta har cikin zuciyarta, har a yanzu ɗin ma bata ɗago kanta ba tace dashi
"Yaya Khalil wlh baka yi min komi ba, idan ma har kayi min to na yafe maka domin ban taɓa kallon ka matsayin me cuta min ba".
Tattausan hannayen ta yariƙo cikin nasa wanda sai da yasaka suka ji tsigan jikin su ya tashi, domin hakan ba wai ya taɓa faruwa bane dasu, fatar jikin junan su be taɓa haɗuwa waje ɗaya ba
Sauke ajiyan zuciya yayi yana ƙara damƙe hannayen nata, idanun sa kafe akanta duk da ba wai kallon sa take yi ba, sannan yasoma magana
"Duk da bansan cewa kina sona ko baki sona ba but ina me neman alfarma ki bani dama a cikin zuciyar ki, Ni kuma zan koya miki ƙaunata sannan nayi miki alƙwari zan faranta miki da iyawa ta, sannan duk abinda ke faruwa naji komi wajen Dad".
Shiru yayi yana jan numfashi sabida jin wani kishi ya turniƙe shi tunawa da wani banza shi yasoma ɓata wa Halwan sa rayuwa, ɗan daidaita muryan sa yayi yace
"Ina so in ƙwato miki haƙƙin ki wajen tsinannen mutumin da yaruguza miki rayuwa".
Yanda yayi maganar cikin wani irin murya da dole ne kagane tsananin kishin sa, duk da kuwa ya daure sosai wajen dai-dai ta muryan nasa, hakan yasa taɗago kai akaro na farko tazuba masa idanu, bata yi tunanin wai ko wannan maganar yake son faɗa ba koda yace mata yaji komi wajen Dad, cikin sanyin murya tace
"A'a Yaya Khalil abinda yawuce ya rigada ya wuce, duk da ada Ina da burin ɗaukan fansa amma yanzu tuni na cire hakan a raina, Husna yanzu ta zama mallakin Saleema na bata ita har abada.."
Katse ta yayi da faɗin "duk da haka dole ne na ƙwato miki haƙƙin ki, Ni lauya ne ke kuma Matata ce, taya kike tunanin zan iya barin wanda yataɓa yin ma Matata Fyaɗe batare da na ɗau mataki ba? Ba wai mayar masa da Husna za'a yi ba but dole ne Kotu ta yanke masa hukuncin abinda yayi, na rigada na gama bincike a kansa zuwa kwana biyu da yardan Allah zan miƙa Case ɗin kotu".
Wani irin farin ciki me haɗe da kuka ne suka taho mata, ko kaɗan ta kasa ɗauke idanun ta akansa, sai dai ta matse bakin ta gamm ta hana kukan nata fitowa illa hawayen dake ƙara sintiri saman fuskarta tare da murmushin farin ciki dake gudana
Kazalika shima kallon nata yake yi, yayinda yasauya riƙon da yayi wa hannayen ta yana murza mata su a hankali yana jin ƙaunarta na ƙara shiga zuciyar sa tare da ƙara girma sosai, yana son yafaɗa mata sirrin dake ransa sai dai kuma baya son yasanar da ita da baki illa a aikace, don haka yabata umarnin tamiƙe tasauko su gabatar da Sallah kamar yanda ko wanne ma'aurata suke yi
Hakan kuwa yafaru, ita tasoma yin alwalan tafito tasanya Hijab tazauna zaman jiran sa
Shi kuma sai da yayi wanka sannan yafito da alwalan sa, doguwar riga kawai yazira suka ta da Sallah, har suka idar yayi musu dogon addu'a inda daga nan kuma yafice zuwa kichen yaɗauko Plates da Spoon yasake kazan da Saleema taba shi, sai da yagama dai-dai ta komi sannan yayi wa Halwa magana akan tasauko su ci, don ita tuni ta haye kan gado tana lissafi cikin zuciyarta, tayi mamaki da ganin abinda ke gaban sa wanda hakan yatabbatar mata ya shirya ma daren, duk da ko kaɗan bata ji ƙamshin ba sa'ilin da yake sake wa illa motsin leda da take ta faman ji kuma bata yi tunanin dashi yazo ba
Babu musu tasauko duk da bata jin yunwa, amma kuma zuciyarta bata ba ta shawaran musa masa ba ko dan faranta masa da take son Yi, domin kuwa ta ɗau alƙawari faranta masa sosai a daren nan ta yanda zata nuna masa godiyar ta a duk kan komi da yayi mata kuma yana shirin sake mata wajen ƙwato mata haƙkin ta
Bata wani ci ba, shima haka ɗin, ita ta tattare komi zata kai kichen yadakatar da ita yakwasa yamayar
Kafin yadawo har ta shiga ta wanke bakin ta, yana shigowa tana fitowa sai tanufi kan gado tahaye
Shima ɗin Toilet ɗin yashiga, babu jimawa yafito yanufi gaban mirror, anan yagama shafe-shafen sa tamkar wani mace, sai da yabi ko ina nasa da turaruka kafin yakashe wutan yanufi kan gado ya haye...
A wannan dare Khalil da Halwa sun raya sa ne cike da farin ciki da annashuwa, tare da soyayya me tsayawa a rai ga duk kanin su, wanda tuni ko wannen su ya sanar da ɗan uwansa sirrin dake cikin ransa batare da sun an kare ba, har gabanin asuba kafin suka yi barci manne da juna tamkar zasu maida junan su ciki. 🤦🏻♀️🙄
*****
Washe gari a makare suka tashi dukan su, don lokacin ƙarfe 07:38am. Ne, Sallah suka gabatar a gurguje, suna idarwa Halwa tasake nannaɗe wa akan gadon don barci ne sosai a idanun ta tunda basu samu sun yi ishashshe jiya ba
Khalil kuwa shirin Office yayi a gaugauce Cuz lokaci ya ƙure masa, gashi babu daman zama agida tunda yana tsaka da soma wani Shari'a ne aiki yayi masa yawa sosai
Koda yagama shiryawa wajen gadon yanufa yasakar wa Halwa kiss a kumatu sannan yaƙara mata a goshin ta, yashafa kanta yana murmushi ganin yanda take yamutsa fuska tana gyara kwanciyarta,
Sosai idan tana yamutsa fuska take masa kyau ainun, ya kula hakan ya zame mata ɗabi'a ko da yaushe sai tayi
Gyara mata Bargon yayi yasake rufe ta yafice dasauri riƙe da briafcase ɗin sa, ɗakin Saleema yashiga sai dai babu ita ciki, har Toilet