Header Ads
Showing 132001 words to 132567 words out of 132567 words

Chapter 45 - BARRISTER IBRAHIM KHALIL Complete Document by Nafisa Isma'il Lawal.txt

Ads the beginning of article before Image

05 Jul 2024

1157

Ads at the middle of Article

hankalin su a tashe, kowa yayi jugun ana jiran abinda hali zai yi.




Alhmadulillah an samu nasaran ciro wa Halwa yara biyu duk ka maza, kuma duk ka yaran suna a cikin ƙoshin lafiya, sai dai Mahaifiyar su ne da akayi zaton ta mutu ma, sai da likitocin suka yi iya yin su kafin suka gane tana da rai, Oxgyen suka saka mata sannan suka fito da yaran suka yi musu albishir da samun ƙaruwar twins


Sun yi murna sosai duk da suna cikin damuwa da halin da aka sanar musu Halwa na ciki, Khalil kawai aka bari ma yashiga wajen ta


Tunda ya shiga idanun sa na kanta, hawaye ne kawai suke kwaranya a saman kuncin sa, yana saka hannu yana share wa cike da raunin zuciya, ganin yanda Halwan nasa ta koma tamkar ba ita ba, har wani baƙi tayi sabida tsaban rame wa, tamkar ba ita ce wacce ta kumbura tayi himm ba, amma yanzu lokaci ɗaya ta zabge tamkar ba ita ba


A hankali ya taka ya isa gaban gadon, a ƙasa ya ajiye gwiwowin sa yana tura hannun sa cikin tafin hannun ta da aka saka mata Drip, damƙe hannun yayi sosai kafin ya ɗaura kansa saman cikin ta yana ci gaba da hawaye, hawayen tausayin ta, gaba ɗaya zuciyar sa ta gama rauni, bazai iya juran itama ya rasa ta ba, taya zai iya rayuwa idan ta tafi?






Ɗago kansa yayi yana kallon fuskarta, cikin sanyin murya yace, "Ina ƙaunar ki Halwa, don Allah.. kar ki tafi kema ki bar Ni, wlh idan na rasa ku duka zuciyata bugawa zata yi, don Allah kiyi haƙuri ki tashi, ki tashi mu raini ƴaƴan mu da Allah yayi mana kyautan su, kinji ki tashi don ALLAH.."




Dole yayi shiru sabida kukan da yataho masa, sai ya sake ɗaura kansa saman jikin ta yana ci gaba da tsiyayar da hawaye, sosai yake ji a jikin sa itama zata tafi ne






Yanda hawayen sa ke zuba ajikin ta hakan yasa take jin sanyin har cikin fatar ta, wannan dalilin ne yasa tafarka a time ɗin, idanuwan ta kaɗai ta buɗe tana bin ɗakin da kallo, tsawon sokonni kafin tagane akwai mutum kusa da ita, sai kuma daga baya ta fahimci Khalil ne, hakan yasa taɗago ɗayan hannun ta ahankali ta aza a kansa




Cakk ya tsai da kukan nasa yana ɗago kai dasaurin sa, nan idanun sa suka faɗa cikin nata da suka ƙanƙance suke a lumshe, daƙyar ma take iya buɗe su sabida halin ciwo




Be san sanda ya washe baki ba yana ta faɗin Alhamadulillah...


𝗧𝗢 𝗯𝗲 𝗰𝗼𝗻𝘁𝗶𝗻𝘂𝗲..✍️




_Nima ALHMADULILLAH anan na kawo karshen book ɗin 𝐁𝐑𝐑. 𝐈𝐁𝐑𝐀𝐇𝐈𝐌 𝐊𝐇𝐀𝐋𝐈𝐋, abun da na rubuta daidai Allah ya amfanar damu, kuskuren da nayi kuma Allah ya yafe min._ 𝑎𝑚𝑖𝑛










𝐼𝑛𝑎 𝑚𝑎 𝑚𝑎𝑠𝑜𝑦𝑎𝑛𝑎 𝑓𝑎𝑡𝑎𝑛 𝑎𝑙𝑘ℎ𝑎𝑖𝑟𝑖, 𝑠𝑎𝑘𝑜𝑛 𝑘𝑢 𝑚𝑎𝑠𝑜𝑦𝑎 𝑦𝑎 𝑖𝑠𝑜 𝑔𝑎𝑟𝑒 𝑛𝑖 𝐴𝑙𝑙𝑎ℎ 𝑦𝑎 𝑏𝑎𝑟 𝑧𝑢𝑚𝑢𝑛𝑐𝑖 𝑛𝑎 𝑔𝑜𝑑𝑒 𝑘𝑤𝑎𝑟𝑎𝑖






𝐽𝑖𝑛𝑗𝑖𝑛𝑎 𝑎𝑔𝑎𝑟𝑒 𝑘𝑖 𝐒𝐇𝐔𝐆𝐀𝐁𝐀 𝐒𝐀𝐅𝐍𝐀 𝐀𝐋𝐈𝐘𝐔 𝐉𝐀𝐖𝐀𝐁𝐈, 𝐴𝑙𝑙𝑎ℎ 𝑦𝑎 𝑘𝑎𝑟𝑎 𝑑𝑎𝑢𝑘𝑎𝑘𝑎 𝑘𝑖, 𝑦𝑎 𝑘𝑎𝑟𝑒 𝑘𝑖 𝑎 𝑑𝑢𝑘 𝑖𝑛𝑑𝑎 𝑘𝑖𝑘𝑒, 𝐴𝑙𝑙𝑎ℎ 𝑦𝑎𝑠𝑎 𝑘𝑖 𝑓𝑖 ℎ𝑎𝑘𝑎, 𝑓𝑎𝑡𝑎𝑛 𝑎𝑙𝑘ℎ𝑎𝑖𝑟𝑖 𝑘𝑎𝑤𝑎𝑖 𝑧𝑎𝑚𝑢 𝑟𝑖𝑘𝑎 𝑚𝑖𝑘𝑖 ℎ𝑎𝑟 𝑚𝑢 𝑘𝑜𝑚𝑎 𝑔𝑎 𝐴𝑙𝑙𝑎ℎ, 𝐴𝑙𝑙𝑎ℎ 𝑦𝑎 𝑏𝑎 𝑘𝑢𝐧𝑔𝑖𝑦𝑎𝑟 𝑘𝑖 𝑛𝑎 𝐏𝐞𝐫𝐟𝐞𝐜𝐭 𝐖𝐫𝐢𝐭𝐞𝐫'𝐬 𝑛𝑎𝑠𝑎𝑟𝑎, 𝐴𝑙𝑙𝑎ℎ 𝑦𝑎 𝑠𝑎𝑘𝑒 𝑑𝑎𝑢𝑘𝑎𝑘𝑎 𝑠𝑎 𝑓𝑖𝑦𝑒 𝑑𝑎 𝑛𝑎 𝑦𝑎𝑛𝑧𝑢 𝑎𝑚𝑖𝑛.








𝑩𝒊𝒔𝒔𝒂𝒍𝒂𝒎 𝒎𝒂𝒔𝒐𝒚𝒂🤝, 𝒌𝒖 𝒕𝒔𝒖𝒎𝒂𝒚𝒆 𝒏𝒊 𝒂 𝒔𝒂𝒃𝒐𝒏 𝒃𝒐𝒐𝒌 𝒅𝒊𝒏𝒂 𝐑𝐀𝐔𝐃𝐇𝐀 𝒏𝒂𝒏 𝒃𝒂 𝒅𝒂 𝒋𝒊𝒎𝒂 𝒘𝒂 𝒃𝒂. 🥰😍👌




𝐉𝐢𝐤𝐚𝐫 𝐋𝐚𝐰𝐚𝐥𝐢 𝐜𝐞 𝐭𝐚𝐤𝐮 𝐦𝐞 𝐤𝐚𝐮𝐧𝐚𝐫 𝐤𝐮...❤️ 𝕃𝕠𝕧𝕖 𝕪𝕠𝕦 𝕗𝕒𝕟𝕤.

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads