Showing 6001 words to 9000 words out of 132567 words
Chapter 3 - BARRISTER IBRAHIM KHALIL Complete Document by Nafisa Isma'il Lawal.txt
akayi ina buƙata?"
Sai kuma tayi saurin kallon sa tana ɗaura hannu abaki tare da zaro idanu waje tace
"Na manta".
Don ko kaɗan tamanta da yanzu tayi masa ƙaryan ita kurma ce, shi kuwa da yasaki baki yana kallon ta be san sanda yatuntsire da dariya ba yace
"Kai Allah Nagode maka, kinga lokaci ɗaya Allah ya kamaki, sai yasaka ki kika manta kika yi magana, Uhm babu rabon ki wahalar dani kenan, kuma banda abinki ai ƙarya be kamace ki ba, ko kadan bakiyi zubi da masu faɗan magana wanda ba dai-dai ba shiyasa na'amince dake nan take".
Murmushi kawai tayi tana jin kunya na kama ta, ba haka taso ba, taso in yagane ita kurma ce yatafi yabata waje amma kuma sai gashi asirinta ya tonu
"To yanzu dan Allah kitaimaka kifaɗamin sunan ki, kuma dan Allah karki ƙi tayina muje nasauke ki gida kinga akwai rana kar yayi miki illa, kamar ki kyakkyawa be kamata kina tsaye rana na gasa ki ba, ko ba haka ba?"
Ɗan taɓe baki tayi tace
"Ni fa bansan meyasaka kake faɗamin waɗannan kalaman ba, kuma bansan meyasaka kakeson taimako na ba, meyasa zaka damu idan rana tagasa ni? Baka tunanin nafison hakan ne shiyasaka nazaɓi tsayuwa anan ɗin?"
Murmusawa yayi yace
"Ai banga aibu ba idan har nataimake ki, kuma kinsan da cewa duk namiji idan har yaga mace ahanya yanemi yataimake ta to akwai abinda yake so wajenta ne, kuma kema kinsan da haka sai dai in bazaki faɗa ba".
"Zai fi kyau dai kasanar dani da bakinka, tunda nasan da cewa Maza kala da iri ne kuma ko wannen su da abinda ke kawo su wajen yarinya, to kai kuma bansan menene yakawo ka ba".
Ɗan numfashi yaja yana kallon ta cike da burgewa yace
"Tunda kinfi son sai nafaɗa miki dalla-dalla to shikenan, Ni sunana Yazeed tunda Ni kinyi min ruwan sunan ki, kuma abinda yatsai dani wajen ki so da ƙauna ne, tun sanda naƙyalla idanu na naganki naji zuciyata ta kamu da matsananciyan ƙaunarki, kuma wlh ba da wasa nake miki ba, ina son kibani dama Dan Allah na nuna miki irin yanda kika shiga zuciyata kika mamaye min ita acikin mintuna ƙalilan kinji dan Allah".
Ɗan gajeren murmushi tayi kana tace
"Ayya Malam Yazeed Nagode da ƙaunarka gare ni, sai dai ina tunanin ka makaro domin Ni ɗin nan da kake gani tuni na zama mallakin wanin ka, ina faɗa maka wannan maganan ne don kar nawahal da kai".
Murmushi yasaki cike da rashin yarda yace
"To shikenan amma dai kizo muje nasauke ki mana, dan Allah karkice a'a plz ƴar kyakykyawa".
Batasan sanda tasaki murmushi ba takalle sa tace
"Uhm kana son kayi min daɗin baki ko?".
"Ai gaskiya nafaɗa ƴan mata, ko makaho yashafa yasan akwai kyau anan".
Taɓe bakinta tayi tace "to muje".
Gaba yayi yabuɗe mata gaban motan tashige, shima yazaga yashiga yaja motan, sai da yadaidaita motar tasa asaman kwalta ɗin kafin yace
"Har yanzu dai anƙi sanar dani sunan Gimbiyan, sai faman rowa ake min" .
Murmushi kawai tayi ataƙaice tace
"HALWA".
"Wow nice name, Gaskiya sunan yadace dake sosai, Masha Allah suna me daɗi".
"Ko?"
Yace "eh mana, ko bakisan da haka bane?"
Batayi magana ba sai murmushi da tasaki me sauti, daga haka yayi ta jan ta da surutu ita kuma tana amsa mishi wasu kuma iyakan tayi murmushi kawai, har bakin layin gidan su yakaita tace "ya aje ta nan".
Bayan yayi packing ɗin motan yajuyo yana kallonta yace
"To bakiso nakai ki har ƙofar gida ne?"
Ɗan kallon sa tayi tagyaɗa masa kai
"Meyasa to?"
"Babu komi". Ta'amsa mishi ataƙaice
"Uhmmm ko dai bakiso nahaɗu da saurayin ki ne?"
Turo bakin ta gaba tayi sai kuma tataɓe shi tace
"Ba laifi bane hakan ai tunda na sanar da kai dama".
Murmushi yayi yace
"Gaskiya ne, to yanzu bani Numbanki mana tunda kinga ban sauke ki har gida ba, kar kuma yanzu in kin tafi shikenan na rasa ki".
"Hmm tunda har kakawo ni nan ai kamar kakawo Ni gida ne, babu wanda zaka tambaya anan wajen be kai ka gidan mu ba idan har kafaɗa masa suna na, kuma gidan mu ai ba ɓoyayye bane, kana cewa gidan Malam Ayuba za'a kawo ka".
Yazeed yace "to NUMBAN kuma fa bazan samu ba kenan? Please". Yaƙarike maganar yana ɗan marairaice fuska
Cike da ƙosawa tace "bani da waya, sai anjima nagode sosai".
Tabuɗe motan tafito, shi kuma yana ɗaga mata hannu tare da faɗin
"Sai kin ganni kenan ko?"
Kawai gyaɗa masa kai tayi tawuce abin ta, shi kuma yaja motan sa yatafi fuskarsa cike da nishaɗi.
Da sallama tashiga gidan, matar dake zaune tana tatan koko ta'amsa mata tana faɗin
"ƴan makaranta an dawo?"
Cike da gajiyawa taƙarisa kusa da ita tazauna saman turmi tace
"Eh wlh Umma, kin ganni sai yanzu".
Umma tace "gaskiya ne kinsha hanya, ga uban rana da ake ƙwalla wa ai yau ko da gani kin gaji".
"Uhmmm Umma bari ke dai, wlh yau nasha wahala ga wuyan abun hawa da ban samu da wuri ba". Cewar Halwan tana tashi ta'aje jakan ta saman turmin tanufi wajen randan ruwa tabuɗe tana ninyan ɗiba
Umma tace "karki sha wannan ruwan, je ɗakina kiɗauko fure water yanzu na'aiki yara suka siyo min".
"To Umma".
Ɗakin tashige sai gata tafito riƙe da fure water'n ahannu tana faɗin
"Umma ya jikin Zainab ɗin?"
"Alhamdulillah dasauƙi sosai, zazzaɓin ya saukar mata ai, tana nan kwance cikin ɗaki inaga ko barci take yi ne?"
"Ok bari in shiga in ganta".
Ɗaukan jakan ta tayi tashige ɗakin Zainab ɗin, kamar yanda Umma tace kuwa tana kwance tana sharɓan barci duk tayi ɗai-ɗai saman katifan ta sai baza hanci take" bakin gadon tasamu waje tazauna tatsiyaya ruwan ahannun ta tazuba mata a fuska, jin sanyi ya ratsa mata fuska atake tabuɗe idanunta da suka ƙanƙance suka yi ja tana maida su tana rufewa
"To kasa tashi haka barcin ya isa, don nasan ba tun yanzu kike yi ba".
Ɗan yamutsa fuska Zainab tayi taƙara ware idanunta tana kallon HALWA kana tatashi zaune tana sakin hamma, cike da kasala tace
"Har kin dawo?"
Halwa tace "eh na dawo, ya jikin naki? Umma tace "kin samu sauƙi ko?"
"Eh dasauƙi sosai, dama wlh don kaina ya matsa min ne da babu abinda zai sa naƙi zuwa makaranta". Zainab ɗin tafaɗi hakan tana zamewa takoma takwanta
"Gaskiya gwara da kika zauna ɗin don yau babu abunda akayi, Monday ma za'a fara test, amma fa ina faɗamiki show ya wuce ki".
"Dan Allah fa? Ke da mutumin naki?"
Harara Halwa tasakar mata tana yatsina tace
"Banson iskanci fa Zainab, wlh yanzu sai mu ɓata idan kika sake kiran min ɗan iskan nan, mtwww".
Taja tsaki tana ɗaure fuska tare da huro hanci
Ita kam Zainab dariya tayi tace
"Sorry ƙawalliya roman jaɓa wasa nake miki fa, kinsan ni dake bamu haka, bani labari to me yafaru?"
"Ai kuma baki isa ba wlh tunda kika taɓo ni nafasa baki labarin, kinga Ni tafiya ma zanyi dama na biyo ne don naduba jikin naki, tunda yanzu na ganki garas to kinga tafiyata".
Tashi tayi tasaɓa jakan ta a kafaɗa tafice, Zainab na kiran ta amma ko waige batayi ba, tana fita taga Umma har yanzu bata gama tatan ba tace
"Umma na tafi".
"To har zaki tafi? Ina jiran in sauke Dambu nasawo muku kuma?" Umma tace hakan tana kallon Halwa
"A'a Umma kibar sa kawai yau banjin tsayawa ne".
"To shikenan kigaida gida, kigaishe min da Maman naku".
"To zataji".
Daga haka tafice
[8/31/2020, 8:29 AM] نفيسة أم طاهرة: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER'S ASSO📚*
```{{Ɗaya tamkar da Dubu💪}}```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuDahirah*👈
*⚜{{F.W.A📚}}*
```ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH```
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
*MARUBUCIYAR*
```NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.```
.
*CHAPTER 6*
Shiga tayi cikin gidan nasu da sallama a bakin ta, Mama da fitowar ta kenan daga ɗaki riƙe da kwano ahannu ta'amsa mata tana kallon ta, ƙarisowa Halwa tayi tana kallon Maman nata da tasami waje saman tabarma tazauna tace
"Mamana sannu da gida".
"Yauwa ƴata takaina, kin dawo?".
"Washh.. nagaji wlh Mama".
Halwa tafaɗa tana zama gefen Maman
"Ai daga ganin yanayin ki nasan da haka, da fatan dai ba wahalan mota ce tatsai dake ba?"
"Shine wlh Mama, kuma sai nabiya gidan su Zainab na je duba jikinta".
Mama kallonta tayi tace
"To ya ya jikin nata? Ta samu sauƙi dai ko?"
"Alhamdulillah Mama jikin nata ya warware ai sosai, Umma ma na gaishe ki".
"Tom Ina amsawa, naso ma in shiga in gaishe ta Allah be yiba, sai ki tashi kije kiɗau abincin ki yana ɗakin ki, don nasan tunda kika langaɓe anan sai kizauna kiyi ta zuba bazaki ci ba, kuma nasan da yunwa atattare dake".
Dariya Halwa tayi tace
"Wlh Mamana shiyasa nake ƙara son ki sabida ƙaunar da kike nuna min, uhm ai yau bazan iya wasa da abinci ba sabida yanda naji hanjin cikina suna kaɗawa, bari dai inje in ɗauko".
Tamiƙe tsaye tana kwaɓe hijabinta, Mama kuma taɓe baki tayi tace
"Da dai bansan halinki bane, yanzu sai ki jagula kibar shi nan".
Halwa shigewa ɗaki tayi tana ɗaga murya tace
"Mama banda yanzu dai, kibari kigani har ƙari ma sai kinyi min".
"To bansan surutu kimaza kiɗauko kizo nan kizauna kici".
Fitowa tayi riƙe da coolar ahannun ta da wayanta, zama tayi tana tanƙwashe ƙafafunta tasoma danna wayan tana faɗin
"Mama har yanzu Yaya be dawo ba?"
"Ni ban ganshi ba, sai ki neme sa ta waya kiji inda yatsaya". Cewar Mama tana ci gaba da ɓare maggi
Wayan takara akunni tasoma buɗe coolar'n, hannu tasaka tasoma kai loman abincin dai-dai lokacin da aka ɗaga wayan nata tace
"Wai yaya ina kaje ne har yanzu shiru baka dawo ba?"
"Sorry my Dear, Ina nan kusa naje wajen abokina ne, amma yanzu zaki ganni".
Ɗan shagwaɓe murya tayi tace
"To kayi sauri kaji?"
"Ok karki damu my dear, Yayanki yakusa dawowa".
Daga haka sukayi sallama ta'aje wayan gefe, taci gaba da cin abincin tana yi tana zuba ma Mama surutu, ita kam sai Umm take ce mata, Mama da tagama ɓare maggin miƙewa tayi tashige kichen, lokacin ne Nura yayi sallama yashigo, ɗago kanta tayi dai-dai lokacin da ta'afa shinkafan cikin baki tana kuma amsa mishi sallaman
"A'a yi ahankali mana karki ƙware, wannan loma haka sai kace abincin zai gudu".
Nura yafaɗa hakan yana dariya bayan da yaƙaraso kusa da ita yasami wuri yazauna, ɗan yatsina fuska tayi sai kuma tasakar masa harara tana faɗin
"To aina kaga na zuba loma yaya? Ko bakaga yanda naɗibo bane?"
Ɗan sakin murmushi yayi yana ƙare mata kallo yace
"Na gani mana, ba gashi kin ciko hannu ba kamar wanda take gudun shigowan wasu don halin rowa, nasan fa halin ki Sarkin rowa ce".
Ture abincin tayi tana ɓata fuska, cikin shagwaɓa tace
"Mama kin gansa ko?"
Daga kichen ɗin Mama ta'amsa mata da faɗin
"Ni kin ganni babu ruwana kunfi kusa, karki sako ni cikin zancen ku".
Nura dariya yasaki yana mata gwalo, ai ko kawai tasakar masa kuka
"Kai wai me tayi maka ne Nura daga zuwanka zaka sa ta kuka? Bansan haka fa tam". Cewar Mama kenan tana leƙo kai waje
"Wlh Mama Ni ban mata komai ba kinsan halinta ai bata raina abun kuka, to kiyi shiru mana beuaty daga wasa? kinga nakama kunni na ma".
Dena kukan tayi tana turo baki gaba tace
"Ai kuma mun ɓata tunda Ni kace ma me rowa".
Haba ƴar ƙanwata abar ƙauna ta, kiyi haƙuri kiyafe ma yayanki, ban sakewa wlh kinji? Matso da kunnin ki ma kiji wata magana?"
"Me zaka faɗamin?" Tafaɗa tana kallon sa
Murmushi yayi mata yana kashe mata ido ɗaya yace
"Kalaman da kikafi so mana" ko in aje kayana baƙya buƙata?"
"Ina so mana yaya". Tafaɗi hakan dasauri tana matso da kunnen ta kusa dashi
Magana yaraɗa mata tasaki dariya tana janye kunnen ta, ɗage mata giran sa yayi yace
"To muje mana".
"To bari in sauya kaya, kaje kajira ni a zaure sai ka'aiko yaro ko?".
"Eh haka zamuyi". Nura yafaɗi hakan yana miƙewa dasauri
Itama tashi tayi tashige ɗaki, Mama da tafito daga kichen tabi Halwa da tashige ɗaki da kallo, kana tamaida idanunta kan Nura da yasaka takalmin shi yana shirin ficewa waje tace
"To yanzu kuma me kuka shirya ne na ji kuna ƙus-ƙus?"
Dariya Nura yayi yace
"Zance zamuyi mana Mama, amma yau a zaure zamuyi, zan aiko yaro yakira min ƴar taki, dan Allah karki hanata fita".
Kama haɓa Mama tayi tabi shi da kallo don takasa cewa komai, shi kuma fita yayi yana faɗin
"Sweety kiyi sauri fa, karki shanya Ni kuma don nasan shegen nawan ki".
Babu jimawa kuwa Halwa tafito riƙe da ɗankwali da Hijab ahannu, tsayawa tayi tana ƙoƙarin ɗaura ɗankwalin
Mama tace "eh haƙiƙa yaran nan dagaske kuke yi, yau kuma gaba ɗayan ku kenan haukan taku tamotsa?"
Halwa dake shirin magana sai ganin yaro tayi ya shigo yana faɗin
"Wai Halwa tazo inji Nura".
Ƙarisa saka Hijabin ta tayi tana faɗin
"Kai kace gata nan zuwa".
Sai takalli Mama tace
"To Mama Ni nafita".
Bata jira jin ta bakin Maman ba tafice dasauri, girgiza kanta kawai Mama tayi tana murmushi tace
"Allah yashirya ku, yaran zamani baku da kunya wlh, ai bari Baban naku yadawo sai ya ji komi".
.
****** ****** *****
Shigowan ta kenan ɗakin taji wayan ta na ringing dasauri taƙarisa taɗauka tana karawa a kunni
"LUBNA kenan". Cewar Mutumin da yakira ta yana sakin dariya
Shiru tayi tana sauraron shi, sai dai babu inda jikinta baya rawa, har zuciyanta na wani irin tsalle kamar zai faso ƙirjinta
"Har yanzu dai kin ƙi aikata abinda muka sakaki ko? Da alamun kina son kirasa kowa naki ne".
Kallon inda Nazeefa take akwance tayi wanda sai sharɓan barcin ta take yi ta ƙudundine jikinta cikin bargo, cikin ƙasa da murya tace
"Dan Allah kuyi haƙuri har yanzu Ban samu nasara bane, wlh kullum sai nashiga nayi muku bincike amma baya barin komi".
"Kina dai wasa da rayuwan Mahaifiyarki da ta ƙannin ki, domin muddin bakiyi abinda mukasa ki ba zaki rasa su, tun yaushe muka baki aikin nan amma kullum magana ɗaya kike faɗa? To ki saurare ni da kyau, akwai wata yarinya da yakawo ta gidan nan kitabbatar da kin fito da ita cikin gidan nan, zan aiko yarana su ɗauke ta".
Cikin rawan murya Lubna tace
"Meee? Nazeefa?"
"Yess ita, ita nake so naɗauka, kijira umarni na".
Ƙitt yakashe wayan, yayinda ita kuma taciro wayan daga kunnen ta tana kallon Nazeefa
"Menene alaƙan su da wannan yarinyan? Me tayi musu? Me suke so da ita?"
Dasauri tamatsa bakin gadon tazauna tana ƙare mata kallo, sai kuma taji kawai hawaye na zubo mata, kifa kanta tayi saman gadon tasoma rera kuka mara sauti
"Meyasaka waɗannan mutanen suka shigo rayuwanta? Me tayi musu ne? Meyasaka sai ita ne zasu zaɓa? Meyasa basuyi tunanin bazata iya aikata duk wannan aikin ba musamman ma akan shi? Tabbas tana da rauni bazata taɓa iyawa ba".
"Waye zai fitar dani cikin wannan ƙangin?"
Tafaɗi hakan lokacin da taɗago kanta idanuwanta sharkab da hawaye
"Allah gani gare ka kataimake ni".
Kallon Nazeefa tasake yi kafin tamiƙe ahankali tashige toilet.
.
.
_shin su waye waɗannan mutanen ne?_
_Meyasaka suke takura ma Lubna?_
_meye alaƙan su da Nazeefa?_
🤷🏻♀️ 💃💃💃💃💃💃
[8/31/2020, 8:31 AM] نفيسة أم طاهرة: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖️ *FEENAH WRITER'S ASSO📚*
```{{Ɗaya tamkar da Dubu💪}}```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuDahirah*👈
*⚜{{F.W.A📚}}*
```ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH```
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
*MARUBUCIYAR*
```NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.```
.
*CHAPTER 7*
Ahankali yake taka motan kamar koda yaushe, wayan sa dake ajiye ne tasoma ringing, hannu ɗaya yamiƙa yaɗau wayan bayan da yaduba yaga me kira, picking call ɗin yayi tare da saka ta a speaker 🔊 yamaida ya'ajiye
"Hello Bro".
Daga can Sameer yace
"Kana ina da Allah?"
"Yanzu gani na taso wajen aiki zan koma gida".
Sameer yace "yauwa kazo kaɗauke ni Please, motata ce tasami matsala an tafi da ita, ina office Ina jiran ka".
"Ok ganinan".
Juya kambun motan yayi yasauya hanya, minti 15 yakawo shi babban asibitin da Sameer yake aiki, bayan yayi packing fitowa yayi yashiga cikin asibitin, direct office ɗin Sameer yazarce, yana shiga yaganshi zaune yana cike wasu takardu, hannu yabasa suka gaisa sannan yasami waje yazauna
Sameer yace "just give me 10 mint don Allah yanzu zan ƙarisa sai mutafi".
"Babu Matsala". Khalil ɗin yafaɗa yana gyara zaman shi kan kujeran yalumshe idanun sa
"Ka gaji ko?"
Ɗan yamutsa face ɗin sa yayi ba tare da ya buɗe idanun sa ba yace
"Sosai ma, barci kawai nake ji wlh yanzu".
Ɗan kallon sa Sameer yayi yace
"Wai ya maganar tafiyan ka ne? Har yanzu banji kace komi ba?"
Idanuwan sa yabuɗe yana kallon Sameer ɗin yace
"Zuwa Friday zan tafi".
Jinjina kai yayi yace
"But Yakamata kayi taka tsantsan kasan Alhaji Mubarak ba ƙaramin mutum bane, don bani da shakka duk abun da kake shirya wa ana sanar masa, Ni yanzu maganar ma da nake so nayi maka kan Nazeefa ce, Yakamata kaciro ta daga wannan gidan kakaita wajen Mom hakan zai fi".
Khalil yace "ai jiyan nan naɗauko ta namaida ita gida na, inaga can zata zauna".
"Kana ganin babu Matsala?" Cewar Sameer
Gyaɗa masa kai kawai yayi
"Ok amma dai Yakamata kaƙara masu gadi, don nafi tunanin in har tana gidan ka zasu fi sanin haka, sannan kuma kaga kai tafiya zakayi Yakamata kaduba shawarata".
Shiru Khalil yayi naɗan wasu sokonni kafin yace
"Ok Bro".
Daga haka hira suka soma duk dai akan case ɗin Alhaji Mubarak, kafin Sameer yagama suka tashi suka fice, har gidan sa yasauke sa Sameer ɗin yace
"Baza ka shiga ba?"
Girgiza kan sa kawai yayi yace
"No kagaishe min dai da auntyna, sai wani lokacin zan shigo".
Ɗan taɓe bakin sa kawai Sameer yayi yace
"Kunfi kusa ai".
Kafin yabuɗe motan yafice, shi kuma yaja ahankali yatafi, a bakin Gate yadakata yadanna hon aka buɗe masa yashige, bayan yayi parcking motan yabuɗe yafito riƙe da briefcase ɗin sa a hannu, yafara tafiya cikin ƙasaita yanufi cikin gidan, hannun sa yasaka yabuɗe ƙofan yana ɗan motsa bakin sa yashige, tana tsaye wajen dainning table tana jera abinci taɗago kanta takalle shi, saurin sauke kanta tayi ganin sun haɗa idanu, cike da