Showing 60001 words to 63000 words out of 132567 words
Chapter 21 - BARRISTER IBRAHIM KHALIL Complete Document by Nafisa Isma'il Lawal.txt
Fans ɗinsa ko ku zaku gane sa, don dagaske ya sauya sosai fiye da yanda nasan shi, gold skin ɗin sa yayi wani irin haske sosai sai ɗaukan ido yake yi, hutu da kwanciyar hankali kawai nake hangowa a tattare dashi da alamun dai ƙasar tayi mugun amsar sa don ba ƙarya ya sauya ɗin, sai zuba murmushi yake yi abinda ba kasafai kake gani a face ɗin sa ba
Har sanda ya'amso trolly ɗin sa yafito haraban airport ɗin sannan ne drever yahange shi yataho dasauri yazo wajen sa yana miƙo masa gaisuwa, amsa masa yayi cike da fara'a sannan suka shiga mota sukayo gida, bazan iya fasalta muku yanda Familyn suka nuna farin cikin su ba, bayan an gaigaisa ya huta sosai sannan aka wuce dainning, anan kowa yaci abinda yakeso tukun suka dawo parlour, hira aka dasa ana ta dariya, wlh idan kukaga Khalil baza kuce shine ba domin har dashi ake ta wasa da dariya, kai sai ince har da ɗabi'u aka sauyo masa acan ɗin, Nazeefa da Abida kuwa babu abinda suke yi sai kallon sa ko wacce zuciyarta na mafarkin yakasance nata na har abada, don har alokacin Abida taƙi tacire sa aran ta duk da kuwa Hakima sai da tagargaɗe ta tamanta dashi baza ta taɓa samun sa ba coz yanzu aure zai yi, kuma itama taso ƴar uwan nata ta aure shi har mitan maganar tarinƙa ma Sameer but basu samu nasara ba.
Su Brr. Tahir suka soma tafiya sannan Khalil shima yayi musu sallama drever yanufi gida dashi, lokacin da suka isa layin su motoci yai ta gani duk sun cika layin, sai da suka matso gab gidan sa sannan ne yafahimci agidan su Kausar ake taron, ga jama'a nan burjik awaje maza da mata kowa na sha'anin gaban sa da alamu dai biki ake yi, mamaki sosai ne a fuskarsa sai dai be iya furta komi ba har Drever yayi hon agidan sa aka buɗe musu Gate motan tashige, bayan drever yayi parcking Khalil yafito lokacin duk ma'aikatan gidan sa sunyo wajen suna miƙa masa gaisuwa, haka yai ta amsa musu cikin sakin fuska sannan ne yanufi cikin gida Sale na biye dashi da trolly ɗin sa
Cikin gidan an gyara masa ko ina kuma yasan duk aikin Sale ne hakan ya faranta masa rai sosai, anan parlour yaba ma Sale umarnin ya'ajiye Jakan sannan yafice, shi kuma yaja trolly ɗin yanufi ɗakin sa, yana shiga yasaki hannun trolly ɗin yazauna gefen gadon sa, ya ɗan yi wajen mintuna 5 kafin yatashi yacire kayan sa yashiga wanka, yayi kusan mintuna talatin kafin yafito yashirya cikin farar t.shit da gajeren wando fari da ɗige-ɗigen ja, zuwa yayi yazauna kan kujera yasoma latsa wayan sa, kusan mintuna goma yaɗauka sannan yasoma laluban numban Kausar yadanna mata kira
Lokacin Kausar na zaune a ɗakin ta tare da ƙawayen ta an gama mata kwalliya, kasancewar yamma tayi har motocin ɗaukan amarya sun zo, becouse acan garin Daura zasu zauna tunda anan ne Sharif ɗin yake aikin sa, duk da dama nan ne tushen sa amma iyayen sa anan Katsina suke zaune
Tsananin firgita Kausar tayi da ganin wanda yake kiran ta har batasan sanda takusa sulmiyar da wayan ƙasa ba, sai wata ƙawarta dake kusa da ita ne tayi saurin taro wayan tana cewa
"Kee Kausar Ina hankalin ki yaje zaki saki waya ƙasa?"
Kausar da tayi mutuwar zaune sabida mamaki, ƙyafta idanun ta tayi da suka cicciko da hawaye tana bin wayan da kallo, ƙawarta me suna Rumaisa tamiƙo mata wayan da aka sake kira akaro na biyu tace
"Riƙe gashi an sake kira".
Ahankali tasaka hannu ta'amsa wayan sai dai takasa anwer call ɗin, ko kaɗan bata taɓa tunanin ganin kiran sa a wannan lokacin ba duk da tasan cewa lokacin dawowan sa yayi, tun sanda yatafi basu taɓa waya dashi ba wannan dalilin ne yasaka tashiga ruɗu da bugawar zuciya
Shi kuma a fannin Khalil tunda yatafi ya nemi layin ta sama da biyar duk sanda zai kira ta wayanta sweech off, daga ƙarshe shine yadena kiran ta gaba ɗaya don a tunanin sa ko akwai matsala ne, ita kuma kullum da tunanin kiran nasa take kwana dashi kuma take tashi, koda yaushe tana jiran taga kiran sa amma har tsawon wannan lokacin babu shi babu labarin sa kuma gashi ita bata da numaban sa na can
Batasan tana zub da hawaye ba sai da Rumaisa tadafa ta tana cewa
"Wai lafiyan ki ƙalau kuwa? Kuka fa kike yi Kausar?"
Sai alokacin tadawo hankalin ta tana kallon Rumaisa da tabi ta da kallo cike da tsananin mamakin ta, lokacin gaba ɗaya hankalin ƴan matan har ya dawo kan su, dasauri Kausar tatashi batare da ta furta komi ba tashige Toilet tana rufo ƙofa, hakan yasaka duk suka bi ƙofan da kallo suna tunanin abinda ke faruwa da ita
Tana shiga kiran yasake katsewa, sai ga wani kiran don shi Khalil ya kasa haƙura da kiran nata, sai da tajingina da bango kafin ta'amsa kiran tana sakawa a kunne, cikin ƙasa da murya tace
"Hello".
Daga can ɓangaren Khalil kuwa shima jingina bayansa yayi da kujera cikin cool voice ɗin sa me daɗi yace
"Hello Friend".
Kausar danne duk abinda ke cikin ranta tayi cikin ƙarfin hali tace "dama ashe zaka iya mantawa dani?"
Ɗan shafo sajen sa yayi yace "Kausar kiyi haƙuri nasan ban kyauta miki ba, amma kuma nayi ta neman Phone Numban ki bana samun ki".
Hannun ta taɗago tana kallon fingers ɗin ta da suka sha jan lalli, cikin son maida kukan da yataho mata tare da ɗaura jarumta a muryan ta tace
"Na gane Barrister, ya hanya to?"
"Alhmadulillah.. da fatan kema kina lafiya?"
Murmushi taƙirƙiro dai-dai lokacin da hawaye suka sauka kan kuncin ta tace "sai alheri friend".
Khalil shima cikin murmushin yace da ita "Allah ko?"
"Ƙwarai". Tataɗa tana dariya ahankali
"To bani nasha".
Sai da taja numfashi kafin tace "Allah yayi an ɗaura aurena yau".
Cikin tsananin mamaki da al'ajabi Khalil yace "haba dai serious fa?"
Kausar tace "I'm serious.."
Sai kuma taɗan saki murmushi me sauti tace "kaga na rigaka ko?"
"Sosai don ban yi tunanin hakan ba, sau da dama kina bani labari kuma ban taɓa jin kinyi min maganar samarin ki ba, ashe ashe.."
Sai kuma yai dariya yana cewa "to Allah yatabbatar da alheri gaskiya naji daɗin wannan maganan".
Shiru kawai Kausar tayi bata amsa ba, hakan ya tabbatar mata da cewa tabbas bata cikin zuciyarsa, ita kaɗai take kiɗan ta kuma take rawan ta
Murmusawa shi kuma yayi yace "Amarya kenan bari in barki haka ko? don nasan yanzu kina busy".
Share hawayen ta tayi cikin rawan murya tace "to".
Daga haka bata iya furta komi ba don idan tasake faɗan kalma ɗaya zata iya fashewa da kuka
Nocking ƙofan da akayi yasaka tayi saurin juyowa tana kallon ƙofan, sai kuma tamaida idanunta kan wayan lokacin ne Khalil yadatse kiran, lumshe idanuwan ta tayi tana jin wani ƙunci da baƙin ciki na mamaye ilahirin zuciyarta
"Kausar wai me kike yi aciki? ki buɗe mana".
Maganar Rumaisa yadawo da ita cikin hayyacin ta, dasauri tasanya hannu tashare sauran hawayen ta tanufi ƙofan tabuɗe, duk bin ta suka yi da kallo har da ƙanwar Mamanta da tashigo yanzu, ita kuma sai tasad da kai ƙasa don bata son su fahimci wani abun
Ƙanwar Maman nata ne tace "wai me kuke jira ne, ku fito motoci sun rigada sun iso".
Juyawa tayi tafita tana cewa "su hanzarta".
Kausar sai da tasha nasiha wajen ƴan uwa kafin aka fito da ita, a lokacin sai kuka take yi, Ni dai bansan ko na menene ba ni dai naga an saka ta a mota sun fice, to sai muce Allah yasanya alkhairi *KAUSAR.*
....... ....... . .. ....
Khalil kuwa tunda suka gama wayan ya'ajiye yalumshe idanun sa yana tunani, yaji babu daɗi yanda suka rabu sabida shaƙuwan da sukayi, be taɓa tunanin baza su sake haɗuwa ba idan yadawo, ya so ba yau bane auren ta ko shima yahalacci auren nata, amma gashi har anyi an gama batare da yaje mata ba, hakan yaƙara saka shi rashin jindaɗi
Allah Sarki haka shaƙuwa yake dama, a ranan kuwa haka yawuni shiru duk bashi da walwala, har yayi sallan magriba da isha'i yadawo gida komi be ci ba yakwanta, ya daɗe yana tunani kafin barci ɓarawo yaɗauke shi.
.
**** **** ***** *****
A cikin kwana biyu da dawowar Khalil sai gashi ya samu kira agidan gwamnati, koda yaje meeting akayi dashi, sun tattauna na wajen awanni kafin su gama, daga ƙarshe dai an ɗauke shi aiki a matsayin Lauyan gidan
Gwamnati, ga albashi me tsoka da zai riƙa samu, duk da dama can sosai Khalil yake samun kuɗi don zan iya cewa ko mahaifin sa be fi sa kuɗi ba, sai dai shi Lauya ne me zaman kansa haƙƙin talakawa kaɗai yake ƙwatowa, Duk wani mara galihu idan har yaje gare sa shi kuma zai share masa kuka, asannu-asannu sunan sa yayi shura sosai talakawa sun soma sanin sa, gaba ɗaya gidajen talabijin da rediyo, jaridu duk maganar sa yanzu ake yi, acikin lokaci ƙalilan Allah ya ɗaukaka shi fiye da Da, kuma duk saboda ƙarin girman da yasamu ne yanzu da kuma ɗaukan sa aiki da akayi agidan gwamnati, sanin da talakawa sukai mishi yanzu har sun soma kawo masa Cases kala-kala, shi kuma don yashare musu kuka haka yake faɗi-tashi wajen taimaka musu da ƙarfinsa da kuɗin sa.
_dama akace dare ɗaya Allah kan ɗaukaki bawa fiye da tunanin me tunani, yanzu sunan Brr. Khalil ya zagaye duk faɗin garin Katsina da kewaye sabida ƙwazon sa, sosai ake ji dashi.
October 2020.
[11/7/2020, 2:40 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎓
🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuƊahirah*👈
*\F.W.A📚/*
```ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH```
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
*MARUBUCIYAR*
```NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.```
.
*CHAPTER 42*
An tsai da ranan auren Brr. Kahlil da Saleema nan da Four Month, zuwa lokacin tarigada ta rubuta Final Exams ɗin ta, asannu-asannu rayuwa taci gaba da tafiya cikin nasarori da akasin sa, wasu tazo musu da daɗi wasu kuma tazo musu a yanayin da babu daɗi, ga dai shi Saleema a wannan lokacin sosai ciwon ta yatashi kullum cikin nema mata magani ake yi, wani lokacin adace wani lokacin kuma rashin sa, ga kai ya ɗau zafi karatun su ya zo ƙarshe haka take lallaɓawa take zuwa School sai dai ba kullum ba, duk ta rame sosai take jin jiki.
A fannin Khalil kuwa yanzu yana da Numban ta kuma yana kiran ta akai-akai yatambayi jikin ta tunda yasan bata da lafiya, kusan sau biyu yana zuwa gidan, shima yanzu aiyuka sun yi masa yawa baya zama sosai kullum cikin aiki yake, ahaka Allah yasa biki yaƙarato ko wani fanni tuni sun soma shiri ana hidima kala da iri, amma ta fannin Amarya babu lafiya har yanzu sai dai ba kamar da ba don yanzu jikin da sauƙi
Ummi tare tahaɗa su da Halwa ake musu gyaran jiki, itama yanzu Halwa ta soma shirye-shiryen zana WAEC da zatayi.
Yau ta kasance saura sati ɗaya biki kuma a yau ne Halwa zata soma zana jarabawan ta, haka tatsallake tatafi bada son ranta ba don ko kaɗan bataji daɗin yanda za'ayi bikin Saleema ita kuma tana Exams ba, sai idan taje tadawo ne ake Hidiman biki da ita.
Fannin su Mom yanda suka ɗau bikin nan da girma zai baka mamaki, komi cikin wadata da nuna su ɗin masu kuɗi ne don tun ana saura sati biyu ake shagulgula agidan, idan kashiga cikin gidan ko matsuguni baza ka samu ba tun kafin ma bikin yazo kenan, ƴan uwa da abokan arziƙi duk sun cika gidan.
Nazeefa kuwa damuwan da tasaka aranta har bacci bata iya yi ishashshe hakan yahaifar mata da ciwon kai me tsanani tare da zazzaɓi, duk shagulgulan da ake yi tana ɗaki taƙule taƙi fita ayi da ita, sosai take jin jiki har sai da Sameer yakaita asibiti aka dubata, koda suka dawo Mom tayi ta kula da ita tana bata drugs duk ta tashi hankalin ta, gaba ɗaya ko lokacin kanta bata dashi ga jinyan Nazeefa ga hidiman mutane, wannan yasaka taba Nazeefa tausayi sosai hakan yasa tadaure taɓoye duk abinda ke damunta tayi kamar ta samu sauƙi tana fitowa ana biki da ita, hakan yasa Mom taji daɗi har hankalin ta yakwanta.
Fannin Ango kuwa baya zama yanzu sabida Case ɗin da yake gudanarwa a Court, shiyasa duk wani shagulgula bashi ciki, sai idan ya sami kansa ko zuwa dare ne yake zuwa gidan su.
..... ...... ...... ...... ....
Gidan su Amarya su ma ba laifi ana ta shagulgula duk da babu wani armashi Amarya tana kwance babu lafiya, wannan dalilin ne ma yasa basu shirya komi ba in banda taron bikin kawai da za'a gudanar
Duk abunda ake ma Amarya anyi wa Saleema, an mata lalli an mata gyaran jiki komi an mata, sosai tayi kyau tafito a Amaryan ta duk da kuwa zallan raman da tayi
Sai ana gobe biki ita Halwa akayi mata nata Lallin sabida ranan bata da Exams, kuma a ranan akayi musu gyaran kai ita da Saleema, komi har gida ake zuwa ayi musu basu zuwa ko ina.
*** **** **** **** ****
Washe gari ya kasance Saturday aka shaida ɗaurin auren *BARRISTER IBRAHIM KHALIL ABDURRA'UF* tare da Amaryan sa *SALEEMA MUSTAPHA*
Ana gama ɗaurin auren ango da abokanan sa suka tafi Hotel inda zasuyi ƙwarya-ƙwaryan liyafan da suka shirya.
*GIDAN SU AMARYA*
Amarya tasha kyau cikin shigan ta na Material Less me ruwan Hoda da ratsin ash colour, ɗinkin riga da sket da suka ɗauki jikinta sosai, ba'ayi mata kwalliya ba don taƙi yarda shiyasa ba'a matsa mata ba
tana zaune akan gado ta ɗaura Husna ajikin ta da take ta faman wasa da kayan Saleeman, sosai yarinyan tasake girma ga wayau sosai, idan kaganta baza kace watanni tara da haihuwar ta ba
Cikin ɗakin akwai friends ɗin ta na school su wajen biyar, sai hira suke yi suna shewa, wasu kuma suna mata tsiya "gwara tawarke don dole akaita yau ɗin"
Ita kuwa ɓata fuska tayi sai sake marairaice face ɗin ta take yi, kallo ɗaya idan kayi mata zakasan ta faɗa ainun hakan yasa tasake haske sosai, bata kula su ba sai dai bin su da ido da take yi
Ana haka Halwa taturo ƙofa tashigo, dawowarta kenan daga Exams da taje tarubuta, fuskarta yalwace da murmushi take kallon Saleema da itama tasanya mata idanu tana ƙara ƙwaɓe fuska kamar zatayi kuka, takowa tayi tashigo ciki tana gaisawa da ƙawayen Saleeman sannan tanemi wuri tazauna gefen Saleema tana sake yalwata fuskarta da murmushi, sosai take farin ciki a yau ɗin tana taya ƴar uwan nata murna
Hannu tasaka tadafa kafaɗun Saleema bakin ta yaƙi rufuwa, sai kuma tamaida hannun kan kumatun ta taja tana cewa
"Haba ƴar uwa ya haka kin ɓata fuska? Don Allah ki saki ranki kiyi farin ciki yau ranan ki ne, ko so kike Angon yayi tunanin bakya son sa ne? Kinga hakan zai jawo masa matsala akasa gane kansa".
Hakan yasa Saleema tasaki dariya babu shiri saboda maganar Halwa ɗin, ita kuwa Halwa kallon ta take yi tana murmusawa cike da jindaɗi, sai kuma tamaida kallon ta kan Husna tana haɗe rai tace
"Waye kuma yakawo wannan yarinyan nan?"
Itama Saleema kallon Husnan tayi da tatsare su da idanu ta saka hannu ɗaya cikin baki tana ɓashe bakin kamar tana jin su
"Kawo ta in kaita wajen Larai, yau fa ranan ki ne be kamata kizauna kina raino ba, banda abinki ma ke da baki da lafiya?"
Ture hannun ta Saleema tayi tana hararan ta tace "to Ni nace akawo ta ina ruwan ki?"
"Haba Sister don Allah yau rana ɗaya kibarta wajen Larai". Cewar Halwa tana sake kai hannu zata ɗauke ta
Sake ture hannun Halwan tayi tarungume ta da kyau tana cewa "Ni fa nace akawo min ita, wlh babu inda zata don tana nan wajena har mu tafi".
Waro idanu Halwa tayi tana cewa "wai da ita kike nufin zaki tafi?"
"Eh mana.. da dake zan tafi?"
Sai ƴan ɗakin dake kallon su suka kwashe dariya
Zaliha tace "kai wani lokacin Saleema bata da hankali al'ƙur'an tana jinta kamar sokuwa ne".
Sai suka sake ɓarke wa da dariya, ita kuma tabi su da harara tana cewa
"Ni ce bani da hankali ko?"
"Ai da gaskiyar Zaliha idan ba sokuwa bace ke taya ma zaki tafi da yarinyan nan? Ai mijin ma sai yakoro ki". Cewar Dija Babbar ƙawarta tana sake kecewa da dariya
Halwa murmushi tayi tace "Sister wlh kuwa maganar su gaskiya ne, kema kinsan Ummi baza ta barki ki tafi da ita ba gwara ki sauya shawara".
Shiru kawai Saleema tayi bata sake cewa komi ba
Cikin lallami Halwa tasake cewa "kinga koda nan da sati ɗaya ne sai in kawo miki ita idan ma wai tafiyar da ita zakiyi".
Saleema tace "sati ɗaya ai yayi yawa, sai dai idan zakiyi min alƙawari gobe".
Gyaɗa mata kai kawai Halwa tayi don ba wai ta yarda zata kai mata ɗin ba, daga nan hira sukaci gaba dayi, sai da Saleema tace ma Halwa taje tashirya sannan tamiƙe tashiga wanka.
*****
Da ƙarfe 08:00pm. Akazo ɗaukan Amarya, tasha kuka sosai haka taƙanƙame Ummi taƙi tafiya, daƙyar aka samu aka shiga da ita mota Halwa tazauna kusa da ita tana rarrashin ta
A gidan sa aka kaita, sosai gidan yaɗau hankalin duk wanda yashigo, kamar ba gidan da akayi amfani dashi ba komi an sauya sai ƙamshin sabunta yake yi
Ɗakin ta kusa dana Khalil aka shigar da ita, haka mutane sukai ta zagayawa suna ganin abun arziƙi har da Halwa a zuwa gani, anan sukayi sallan isha'i suna ta hayaniya kamar zasu tsaga gidan
Wajen ƙarfe 10:00pm. Abokan ango suka zo tafiya dasu, lokacin ne itama Halwa takira Drever'n gidan su A wayan da Abba yasiya mata don