Showing 30001 words to 33000 words out of 132567 words
Chapter 11 - BARRISTER IBRAHIM KHALIL Complete Document by Nafisa Isma'il Lawal.txt
nan, sun bala'in yin masa kyau sosai, kan sa babu hula sai gashin sa da iska ke ta kaɗawa, gaban sa kuma ɗan ƙaramin table ne ya ɗaura Lapton ɗin sa akai, gefe ɗaya kuma glass cup ne da Fruits a cikin plate, aiki yake yi time to time kuma yana ɗan kurɓan Black tea ɗin, wayan sa dake ajiye ne tasoma ringing yaɗan tsayar da aikin yakalli wayan, ganin sunan Dad ya fito raɗo-raɗo a screan ɗin yasanya shi saurin ɗauka yana peacking call ɗin tare da karawa a kunne
"Hello Dad.. au assalamu alaikum".
Murmushin Dad ɗin ne yabayyana cikin wayan kafin yace
"Kai dai baza ka dena halin nan naka ba ko?"
"Sorry Dad na manta ne, but ai na gyara ko?" Yayi maganar a shagwaɓe
Still Dad murmusawa yayi yace
"Auta kenan, Mom ɗin ka tariga ta gama ɓata ka, kana yin abu sai kace ƙaramin yaro".
Murmushi Khalil yayi yana shafa kan sa yace
"Dad ai ku kaɗai nake ma wa, coz a wajen ku ni har yanzu yaro ne".
Dad yace "to gobe da safe kafin kawuce office kabiyo gida ina neman ka".
"Dad lafiya kuwa?"
"Lafiya lau My Son, sai dai in ka zo zaka ji, kar kuma kace min ka manta kashanya ni jiran ka".
"Tom Dad, insha Allahu zan zo". Khalil ɗin yafaɗa cike da girmama wa
Daga nan sallama suka yi Khalil ya'ajiye wayan sa yaci gaba da aikin sa.
[9/17/2020, 7:20 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuƊahirah*👈
*\F.W.A📚/*
```ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH```
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
*MARUBUCIYAR*
```NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.```
.
*CHAPTER 23*
*TOMORROW MORNING*
Khalil ne zaune a parlour'n mahaifin nashi yana sauraron abinda yake faɗa mishi
"Ibrahim har yanzu dai bakasan zurun ba ko? Tun yaushe nayi maka maganar aure but har yanzu shiru babu wani motsi da kake yi".
Ɗago kan sa yayi yana kallon Mahaifin nashi, be yi tunanin wannan maganar ce tasaka yakira shi ba, kuma ko kaɗan be shirya ma hakan ba
"Ina jin ka tunda ka bari sai na tambaye ka, yanzu kasanar dani wacce yarinya ce kake so don mugaggauta nema maka auren ta?"
Shiru Khalil yayi yana sad da kai ƙasa
"Kayi shiru kuma?" Dad yatambaye sa yana kallon sa
"Uhm Dad ni har yanzu ban sami wacce nake ƙauna ba".
"Ohho nagane me kake nufi Ibrahim".
Cewar Dad yana kaɗa kan sa, sannan yaci gaba da cewa
"But nasan maganin ka tunda naga kamar har yanzu baka yi hankali ba, tun yaushe muke wannan maganar da kai amma dayake baka ɗau maganar ta wa da wata muhimmanci ba shine ka shashantar dashi, yanzu gashi har Sameer yana da yaro kai kazauna kana son kazama tuzuru, to na baka nan da lokacin da zaku gama wannan shari'an, katabbatar ka sami matar aure idan ba haka ba ni da kai ne, kana ji na?"
Dad ɗin yaƙarike maganar yana riƙe kunnen sa tare da kallon sa
Ɗan turo baki gaba yayi kana yagyaɗa masa kai
"To tashi katafi, Allah yamaka albarka".
Ciki-ciki ya'amsa yamiƙe yafita daga parlour'n, girgiza kan sa Dad yayi yana ɗaukan Jaridan da yake karantawa yace
"Wannan yaron in ba haka nayi maka ba, to naga alaman ba auren ne a gaban ka ba, in ba ma rashin wayau ba ya zauna har War haka be yi aure ba".
Shi kam Khalil daga fitan shi ɗakin Mom yashige, tana zaune a gefen gado tana gyara drowan ta data hargitsa tana neman sarƙan da zata saka, yashigo fuska a turɓune hannun sa cikin aljihu, ɗago kai tayi tana kallon sa, sai da takaranci yanayin sa kafin tace
"Yah ya Me yafaru ne? Me Dad ɗin naka yafaɗamaka naga fuskar ka ta sauya?"
Ahankali yatako yazo kusa da ita yazauna kafin yasoma magana ciki-ciki
"Wai Dad ya bani nan da bayan gama Shari'a na da Alhaji Mubarak in fito da mata, sai kace neman matan sauƙi ne dashi".
Murmushi Mom tayi tana riƙo hannun sa ɗaya da yaciro su daga aljihu yaɗaura saman cinyoyin sa yadunƙule su
"Haba My Son ya zaka ga laifin Dad ɗin ku? Ai ni inaga ya baka lokaci sosai tunda ba yau yasaba maka maganar ba?"
Kallon ta yayi yace
"Mom kwanaki ne fa suka rage? Meyasa bazai ƙara min zuwa nest year ba?"
Hannu taɗaura a saman kan shi tana shafa baƙin gashin sa da yasha gyara yakwanta luf gunun sha'awa tace
"Wai to menene na tada hankalin ka ne Son? inace Kai ɗin me farin jinin ƴan mata ne, duk wacce kazaɓo acikin matan da suke son ka da gudu zata aure ka, ko acikin Family ne sai kazaɓa ɗaya kaga hakan ma sai yaƙara mana ƙarfin Zumunci, don ban faɗa maka bane kwanaki ma Hajja Mero tazo har nan, takawo min maganar ƴar ta Shukra, me zai hana a haɗa auren ku tare, kaga in ka amince kawai sai in Kira ta in sanar da ita, cikin lokaci ƙanƙani sai ayi komi a gama ko ba haka ba?"
Kwaɓe fuska Khalil yayi yace
"Wai menene haka Mom, ya na kawo miki magana don ki rarrashi Dad yaƙara min time kuma kike mayar da hannun agogo baya? Ni in rasa ma waɗanda zan aura sai yaran nan da basu da kunya, kullum idanun su a tsatstsaye kamar zasu cinye mutum, ina Allah yakyau wlh". Yaƙarike maganar kamar yaga abin ƙyama
Dariya Mom tayi tace
"Ban da abin Auta to menene laifin su? Kuma menene laifin wanda ke son ka, in ma kana tunanin sun yi maka yara ne ai naga hakan kuka fi so yaran zamani, kuma sun fi daɗin zama ai, zaka ji daɗin zama dasu wlh".
"To ni Mom bance miki Ina son yara ko manya ba, Ni kawai har yanzu ban ga wacce nake ƙauna bane, and Mom kuma ki dena maganar yaran nan ma kar suji su ce zasu raina ni".
Mom tace "to shikenan na daina Autana, yanzu dai katabbatar ka samo matar da zaka iya zama da ita tun kafin Dad yazaɓo maka".
Marairaice fuska yayi yana faɗin
"Yanzu Mom baza ki roƙe sa ba?"
"Kasan halin Dad ɗin ka, in yariga yaba ma mutum dama kasan bazai saurare shi ba, don haka kawai kayi abinda yace maka, but insha Allahu dai zan yi masa magana yaƙara maka lokacin yanda zaka samo min suruka me kyau da hankali kamar kai, wanda take ƙaunar ɗana kuma takula min dashi sosai".
Murmushi Khalil yayi yace
"Mom kenan, to amma dai bari ince ameen".
mom dariya tayi tana jan kumatun sa tace
"Ja'iri kawai, kana so kana kai wa kasuwa ko?".
Shima dariya yayi kawai yana sosa kan shi
"To tashi kaje kar kayi late da yawa, kaga har 08:00am. Ta kusa".
"Ok Mom".
Sai da yayi mata peck a cheeks ɗin ta kafin yamiƙe yayi mata sallama yafice, har yakusa isa ƙofar da zai fita daga Parlour Nazeefa tafito daga kichen riƙe da plate a hannun ta, tana hango shi takira sunan shi
"Yaya".
Har yariƙe handle ɗin ƙofan yajuyo yana kallon ta, saurin ɗauke kan ta tayi daga kan shi ganin kallon da yake mata, ita kan ta batasan me zatace mishi ba takira shi, sai dai kuma bataso yatafi batare da ya ganta ba, ko da magana ce yahaɗa su
"Ina kwana Yaya". Tace dashi tana ɗago kan ta takalle shi
"Lafiya, ya jiki?"
"Alhamdulillah Yaya".
Fita kawai yayi batare da yasake furta ko kalma ɗaya ba, ita kam murmushi tasaki tana jin daɗi a ranta, juyawa tayi tanufi ɗakin ta.
Lokacin da ya'isa yayi parcking yafito, ahankali yake tafiya har ya'isa office ɗin sa, har yakama handle ɗin ƙofan zai murɗa sai yakalli setting office ɗin Billy dake rufe, taɓe bakin shi yayi kawai yashige office ɗin sa yamayar da ƙofa yarufe, ahankali ya'isa jikin window yana saka hannu ya yaye cooten ɗin, gyara tsayuwan sa yayi yasanya hannayen sa cikin aljihu yana ƙure waje da idanu, a zahiri titi yake kallo but a baɗini tunanin mafita yake yi, tsawon mintuna yana wajen kafin yataka yanufi kujera yazauna, buɗe computer'n sa yayi, sai kuma yadunƙule hannun sa biyu yaɗaura a haɓar sa yaci gaba da tunanin sa
Nocking Brr. Tahir yayi yashigo, har yazauna Brr. Khalil be san ya zauna ba, sai da yakaɗa masa hannun sa a setting face ɗin sa tukun yaƙyafta idanu yana kallon shi
"Wai tunanin me kake yi ne har nashigo baka sani ba?"
Ajiyan zuciya Brr. Khalil yayi yana gyara zaman sa yace
"Wlh Dad ne yake son tada min da hankali".
"Me yafaru?" Brr. Tahir yatambaye sa
"Wai cewa yayi nan da lokacin da zamu ƙarƙare Shari'a nafito da matar da zan aura, ko wa yace mishi na damu da auren yanzu, kawai zai jagula min lissafi wlh".
Dariya Brr. Tahir yayi kana yace
"Wlh kana bani mamaki Ib, wani lokacin har tunani nake yi ko dai ba lafiyanka ƙalau ba, ni a ganina kai kakeso katakura kan ka but ban ga aibun Dad anan ba".
"To me kake nufi kenan?" Khalil ɗin yatambaye sa yana ɗaure fuska
"No babu komi, but ni dai shawaran da zan baka kafitar da wata cikin matan da suke ƙaunar ka, ko da kai ba ka ƙaunar ta".
Khalil yace "kana nufin kenan in yi auren rashin ƙauna?"
"Eh mana tunda har yanzu baka sami wacce tayi maka ba duk acikin matan da suke son ka, ba mamaki kai irin mazan nan ne da basu gane meye so sai lokacin da suka auri matar, sannan alokacin zasu gane sun faɗa tafkin ƙauna".
Shiru Khalil yayi yana tunani
Brr. Tahir yace "kar ka matsa ma kanka Ib, me zai hana ka amince wa Billy, tunda ita kaɗai naga alaman zatafi dacewa da kai, kuma kai kan ka sheda ne yanda take matuƙar ƙaunar ka, zata iya yin komi sabida kai, don haka kawai kaba ma zuciyar ka dama takoyi son ta kafin zuwan lokacin, idan har kaji zuciyar ka bata kwanta da ita ba zaka iya sauya wa".
Still dai shiru Khalil yayi yana nazarin maganganun Brr. Tahir ɗin, kuma daga baya sai yace
"Shikenan zan yi tunani akai".
"Ok".
Daga nan tattauna wa sukaci gaba da yi kafin Brr. Tahir yatafi yabar shi, shi kuma yaci gaba da aiki har zuwa lokacin tashin shi, ahankali yamiƙe cike da gajiya yatattara kayan sa yafice, a hanya suka haɗu da Brr. Tahir har suka ƙarisa wajen motan su
Brr. Tahir yace "yau baka tambayi mutumiyar ka ba? Kuma kana gani yau ɗin baka ganta ba".
Ɗan taɓe fuska kawai Khalil yayi yabuɗe motan sa yana shirin shiga, riƙo murfin motan Brr. Tahir yayi yace
"Kenan baza ka tambaya ba ko?"
"To tunda kayi ninyan faɗa min menene kuma sai na tambaya?" Khalil ɗin yafaɗa yana tsare shi da idanu
Murmushi Brr. Tahir ɗin yayi yace
"Gaskiya baka da dama Abokina, in ba ni ba babu wanda zai iya da halinka".
Harara Khalil yayi masa kamar wani mace yace
"Tunda gani me baƙin hali ko? Dole kace babu wanda zai iya dani".
Dariya yayi yana rufe bakin sa yace
"Rufa min asiri don Allah wasa nake maka, but seriously Billy ɗin ka bata da lafiya fa, yanzu nima nake ji wajen Brr. Kuma".
Wani irin kallo Khalil yayi masa, be ce komi ba yajanye murfin motan sa yarufe, leƙo da kai Brr. Tahir yayi yace
"Bakace komi ba zaka tafi?"
"Me kake so nace maka Umhm?" Khalil ɗin yafaɗa yana ma Motan keey
"Muje mu gaishe ta mana, kaga daga nan sai kashigar da kanka ka gane ai". Brr. Tahir yace hakan yana dariya ƙasa-ƙasa
Gajeran tsaki yayi tare da jan motan sa yayi gaba, shima dai Brr. Tahir ɗin motan sa yanufa yashiga yana ci gaba da dariya tare da girgiza kan sa.
[9/18/2020, 9:47 AM] نفيسة أم طاهرة: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuƊahirah*👈
*\F.W.A📚/*
```ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH```
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
*MARUBUCIYAR*
```NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.```
.
*CHAPTER 24*
Lokacin da ya'isa gida yayi parcking motan sa, sai da yayi kusan mintuna 5 kafin yabuɗe motan yafito, ahankali yake takawa har yashiga cikin gidan, akan sofa yazube yana kwantar da kan sa cike da gajiya, dafe goshin sa dake ɗan sara masa yayi yana lumshe kyawawan idanun sa, few minutes ago yacire hannun yana tashi tsaye yanufi ɗaki, koda yashiga wanka yasoma yi sabida yaji ƙarfin jikin sa, don sosai yake jin sa kamar an mishi dukan tsiya, bayan ya shirya cikin brown ɗin jallabiya da Three qweater sai yafito parlour yanufi kichen kai tsaye, shiru yayi yana tunanin abinda zai dafa, don sosai yagaji da cin indome, kuma so yake yaci abu me ɗan nauyi coz yunwan dake ƙwaƙulan sa, tea yafara haɗawa yazauna nan kichen ɗin yashanye cikin ƙanƙanin lokaci, kana yasoma girka makaroni, shi ba wani ma'abocin iya girki bane don be taɓa yi ba in banda indome da yake dafa wa, but haka dai yayi karanbanin sa yasoma ƙoƙarin girka wa, sai da yaɗaura tukunya a wuta sannan yakurma ruwa rabin tukunyan, yana soma zafi yaɗauko makoroni biyu yasake, don yana son yagirka ne har dare yahuta da ɗame-ɗame, bayan ya sake ne sai yaɗauko Maggi yazuba sannan yaɗauko kayan miya, blanda yaɗauko yasoma yunƙurin blanding ɗin sa, lokacin duk zufa ya ishe shi hakan yasaka yatashi yafice, rigan jikin sa yacire yajefa saman sofa, yadawo daga shi sai singlate ajikin sa yasoma blanding kayan miyan, bayan ya gama duk yasake cikin tukunyan, yazauna nan yana jiran yanuna, gaba ɗaya ya manta da cewa ko mai be zuba ba, sai da yabuɗe yaga yana ta zaɓarɓaka yatuna ai be zuba mai ba, ɗauko wa yayi yadiddila yamayar yaci gaba da zama, sai da yabashi good 30min kafin yabuɗe, lokacin tuni ya nuna sai dai ruwa da yayi yawa hakan yasaka yacaɓe, but be damu ba yaɗauko plate yaɗiba yarufe sauran, ɗauka yayi yafito yanufi saman dainnig ya'ajiye, sai yaje yaɗauko Faro water da kwalin Juice yadawo yazauna, spoon yaɗauka yana kallon abincin, kamar baya son ci sai kuma yasaka spoon ɗin yaɗiba yakai bakin sa, taunan farko yadakata yana taɓe baki, ahankali kuma yaci gaba da taunawa har yahaɗiye, kana yasoma tsakalan abincin kaɗan-kaɗan yana ci, ko kaɗan babu daɗi but yakasa dena ci sabida yunwan da yake ji, yayi dana sanin dafa wa, da tun farko yayi indome'n sa da tuni yacinye lafiya lau duk da ba wani iyawa yayi ba, but yafi wannan jagwalgwalon, sai da yaji cikin sa yasoma murɗa masa yana mishi ciwo kafin yamiƙe yaɗau plate ɗin yakai kichen tare da sake sauran cikin tukunya
Parlour yadawo yazauna yana ɗaukan wayan sa dake ajiye yasoma latsawa, ahankali yatsai da abinda yake yi yana nazarin abinda yake son aikata wa, tsawon minti 3 kafin yaci gaba da latsawa sannan yakara a kunne
"Assalamu alaikum".
Jin muryan ta a cikin kunnen sa yasaka shi lumshe idanun sa yana gyara zaman sa tare da ɗaura kan sa saman kujeran
"Wa'asalaikis Salam". Ya'amsa mata cikin cool voice ɗin sa me daɗin sauraro
Shiru ne yabiyo bayan amsa sallaman nasa, domin ita a fannin ta mamaki ne yakusa kashe ta, abinda bata taɓa gani ba ko da a mafarki ne wai Brr. Khalil zai kira ta.. katse mata tunanin ta yayi da faɗin
"Baki iya gaisuwa ba?"
Bilkisu da rawan baki tace
"Ina yini?"
"Lafiya, ke fa yakike?"
Tace "lafiya lau".
"Ke da akace min baki da lafiya kuma shine kike Son yin min ƙarya?"
Batasan sanda tasaki murmushi ba cike da tsananin farin cikin da yakusa kashe ta tace
"Ai naji sauƙi, dama zazzaɓi ne".
Taɓe baki yayi sai kuma yagyaɗa kan sa, still kuma yace
"Ai naga alama tunda gashi kina min dariya".
Kamar yana ganin ta tayi saurin rufe bakin ta tana faɗin
"Wlh ba da kai nake yi ba".
"To da wa kike?" Yatambaye ta yana wani rage murya
Bilkisu ta kasa magana fa, sai kace ba abinda take nema bane yasamu amma kun ji tayi gumm kamar munafuka
"Kin yi shiru kuma? Ko bazaki faɗa min ba?"
"Uhm babu kowa".
"Ok dama nakira naji jikin ki ne, tunda kin sami sauƙi naji daɗi, bye".
Be jira cewar ta ba yakatse wayan.
Ita kam Bilkisu tana jin yakashe kiran sai tawani kurma ihu tana burgima saman gadon ta, Allah yasa ita kaɗai ce a gidan da har waje sai an ji
"Wayyo Allana yau daɗi zai kashe Ni, wai Ib ne yakira ni? Wayyo ko dai mafarki nake yi?"
Sai tamiƙe daga kwancen da take tana rarumar wayar ta taduba, washe baki tayi ganin dai ba mafarki bane, kwanciya takuma yi tana rarumo pilow tamatse tana cewa
"Wayyo daɗi kashe ni, wayyo ni Billy yau duniyar ta kai min inda nake so, gaskiya yau na kasance me Sa'a, wayyo Allana Wayyo Allana wa zai taya ni farin ciki?"
_(Ni kam nace *NAFEESA GROUP FAN'S* su taya ki, ko kuma *BRR. IBRAHIM KHALIL FAN'S* don Ni dai ban da lokacin ki lol😅 💃💃)_
Shi kuma da gama wayan miƙe wa yayi yaɗau rigan sa yasaka kafin yashige ɗaki, alwala yaɗauro yafito yanufi masjid, bayan ya idar da sallah yafito yakamo hanya, gab da yakusa isa gidan sa yahango Kausar tafito daga gida, tana sanye ne cikin wata Farar riga me dogon hannu zuwa cinyan ta, sai wani burgujejen wando Three qweater me manyan aljihu kalan Orange 🍊, sai tasanya hula facing cap shima kalan wandon, kitson da tayi guda biyu jelan tazubo shi gefe da gefen kafaɗan ta, tunda itama tahango shi tanufo shi da murmushi a fuskar ta, tana iso wa wajen sa tace
"Yanzu nake tunanin ka a raina sai ga ka".
Yanda tayi maganar ne yasaka shi ɗan murmusawa yace
"Zaki bani wani abu ne?"
Sai ta langaɓar da kan ta tace
"Eh in dai kana so".
"Why not?" Yafaɗa yana waro idanun sa
Sai tayi murmushi kana tace
"Dama