Showing 21001 words to 24000 words out of 132567 words
Chapter 8 - BARRISTER IBRAHIM KHALIL Complete Document by Nafisa Isma'il Lawal.txt
awani gida, dama abinda muke nema kenan musami aikin da zamu dogara dashi ni da iyayena, kwana biyu da soma zuwana, uban gidan mu yakai ni wani gida, ni dai ban fahimci ko ina ne ba amma akawai ƴan mata irina da yawa don mun kai mu sha biyu, muna ji muna gani akai mana allura wanda bamu fahimci na menene ba, tun daga lokacin hankalin mu yagushe, ashe makocin mu ne yasiyar dani ga mutumin da yasamar min aiki gidan sa, shima kuma yasiyar dani ga wani uban gidan sa".
Shiru tayi tatsira ma waje ɗaya idanu taci gaba da faɗin
"Wannan alluran da akai mana yagusar mana da hankali, anyi haka ne don su cin ma manifan su akan mu, suna harƙallan sai da coken that's why suke samun ƴan mata sufarka cikin su azuba musu coken ɗin nan aciki, alluran da ake yi yana da ƙa'ida, yana ɗaukan iya awannin da zai kai mu ƙasan da za'a kai mu ne, don haka lokacin da akai mana hankalin mu gushewa yayi bamu sake sanin inda muke ba sai a wannan ƙasar, sun kawo mu nan an kuma mana aiki an cire mana coken ɗin, sai dai basu bar mu haka ba suka sai damu ga Mr. Jay pitter, mutum ne shi da yake safaran ƴan mata ƙasa-ƙasa wasu kuma yamai dasu karuwan sa don samun kuɗi dasu, acikin waɗanda muka taho tare gaba ɗaya yasiyar dasu a wasu ƙasashe sai ni da wata yabar mu a matsayin karuwan sa, tun sanda natsinci kaina a wannan ƙasa nake kuka ina roƙon su da sumai dani ƙasata, sai dai aikin gama yariga da yagama su mutane ne da basu tsoron Allah, daga farko da sukaga ina musu taurin kai har nayi yunƙurin guduwa haka sukai ta gana min azaba, but duk da haka ban sa ran wataran zan ƙi guduwa ba, sai dai duk wani hanya da yakasance zan bar ƙasar nan sun toshe ta, ataƙaice dai zan faɗa maka babu yanda za'a yi nabar ƙasan nan batare da sanin su ba, haka nahaƙura naci gaba da zama dasu nima har lokacin da nasaba, nima nadawo nagoge azahiri namanta da komawa ta gida, sai dai abaɗini abin na nan araina, aduk sanda natuna da iyayena sai nayi kukan baƙin ciki, ina tunanin awani hali suke na rashina, shiyasaka har yanzu ban fid da raina zan koma ba".
Muryan ta da yasoma rawa ne yasaka ta yin shiru, sai da tashare hawayen fuskarta kafin taci gaba
"Shi kuma Alhaji Mubarak tare suke harƙalla da Mr. Jay Pitter, yana kawo masa ƴan mata sosai, duk wani aikin da Mr. Jay yake yi tare suke yi dashi, nasan shi sosai domin yana yawan zuwa nan ɗin, kuma insha Allahu duk wani sirrin su zan iya nemo maka inhar kayi alƙawarin zaka mayar dani ƙasata, ina son nakoma gun iyayena, kataimake ni don Allah, sosai naji zuciyata ta aminta da kai". Taƙarike maganar tana fashewa da kuka
Brr. Khalil kallon ta kawai yake yi cike da tausayin ta, sosai tabashi tausayi kuma yana ji aran sa insha Allahu sai ya taimaka mata, dama wannan daman yake nema wanda zai kawo ƙarshen masu safaran mata, koda iyakan Alhaji Mubarak da mutanen sa yakawar tabbas yasan ba ƙaramin Jihadi yayi ba, ko ba komi za'a rage yawaitan mugaye irin su, ajiyan zuciya yasauke yana tuno Nazeefa
"Yanzu shikenan da itama nan za'a kawo ta? Yarinya ƙarama, kai amma waɗannan mutanen basu da imani, Allah kaɗai yasan iya adadin yaran da suka kawo waɗanda ma basu kai ta ba".
Numfashi yaɗan ja yana kallon ta yace
"Kiyi shiru Fadila, insha Allahu zan taimaka miki kibar wannan ƙasan, zaki koma ga iyayen ki in Allah ya yarda nayi miki alƙawari".
Kallon shi tayi da idanuwanta da sukai jazur tayi masa murmushi tace
"Nagode sosai".
"Babu godiya tsakani na dake, ke dai ki aiwatar da duk abinda zan saka ki".
Daga nan yasoma bata bayanai akan abinda yakamata tayi masa, sun daɗe suna tattaunawa kafin tatafi, shi kuma tashi yayi yashige toilet yayo wanka tare da ɗauro alwala yafito, shirya wa yayi cikin farar jallabiya da dogon wandon jeans yashimfiɗa sallaya yayi sallah, sannan yamiƙe yaɗau tellphone ɗin dake ɗakin yakira Receptionist yayi odan abinci, yana zama babu jimawa akayi nocking door ɗin yaje yabuɗe ya'amso yadawo yazauna yasoma ci, abincin yake ci sai dai hankalin sa baya wajen yana nazari, wayan sa dake saman gado tasoma ringing hakan yasaka yaɗan kalli wajen kafin yasauke ajiyan zuciya, yamiƙe yanufi inda wayan take yaɗauka, ganin Bro ɗin sa ne babu ɓata lokaci yayi peacking call ɗin yana zama
"Hello My Bro".
"Hi ɗan ƙanina ya kake?"
Ɓata fuska Khalil yayi yana shafa goshin sa yace
"Bro bana so".
Dariya Sameer yayi yace
"Sabida me um ɗan ƙanina?"
Shiru yayi yaƙi magana
Still dariya Sameer yasake yi yace
"I'm sorry dama tsokanan ka nake, ai yanzu kai big boy ne tunda kafara aje yara, kasan fa Hakima ta haihu".
"Dagaske Bro? Yaushe? Me tahaifa?" Yayi masa tambayoyin ajere yana miƙewa yakoma wajen abincin sa
"Yanzu babu daɗewa, ai nayi tunanin Mom tariga ni sanar maka, namiji tahaifa".
"A'a tun safe da mukai waya bamu sake ba, Allah yaraya shi Yaya, ina fata ni za'a yi wa takwara ko?"
Sameer yace "tabb kai awa?"
"Ni a Dadyn sa, Please Bro kasan munyi alƙawari dani da kai, duk wanda yahaihu cikin mu zamuyi ma junan mu takwara".
"A'a to ai bance maka na fari ba, ni Dad zan ma takwara sai dai kabari tasake haihuwa lokacin ma kayi naka auren, kaga sai su tashi tare ko?"
Ajiyan zuciya Khalil yayi yace
"Dama haka zakace ai, kafison Dad dani, shikenan sai kayi ta sakawa".
Dariya Sameer yasaki jin yanda Khalil ɗin yayi maganan cike da shagwaɓa, cikin dariyan yace
"Haba autan Mom Kar kayi fushi tunda nace zan saka, kuma kasan da cewa ni dama na wurin Dad ne, dole na fifita shi akan ka, amma fa ina son ka sosai fa, daga shi sai kai a zuciyata".
Murmushi Khalil yayi yace
"Uhmm naƙi daɗin bakin, ai dama Mom ta sanar dani kuma yanzu na yarda, yanzu ni dai kagaishe min da me jegon da kyau da kyau tare da My Son".
"Ok zasu ji, ya aikin naka? Dafatan komi yana tafiya normal?"
"Alhamdulillah Yaya, Ina samun duk abinda naje nema".
"To Allah yataimaka yabaka Sa'a".
"Ameen Bro, katura min photon Baby ta WhatsApp in ganshi".
Sameer yace "ok yanzu kuwa".
Daga nan sallama suka yi, yaci gaba da cin abincin sa yana latsa wayan sa.
[9/12/2020, 1:32 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuƊahirah*👈
*\F.W.A📚/*
```ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH```
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
*MARUBUCIYAR*
```NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.```
.
*CHAPTER 17*
*WASHE GARI*
*NIGERIA*
Da sallaman ta tashigo gidan, Mama dake zaune tana gyaran lagwani ta'amsa mata tare da faɗin
"A'a maraba da Zainaba"
"Mama ina wuni?"
"Lafiya lau, ya Umman taki?"
"Tana lafiya, tace in gaishe ki".
"Ina amsawa, ya wajen su Zaituna, ina fata kina leƙata?".
Murmushi Zainab tayi tace
"Eh Mama ina zuwa sosai".
"To madallah haka akeso, kishiga ƙawar taki na ciki ai, bata jindaɗi ne".
"Eyya Allah yasawaƙe, ai bani da labari".
Mama tace "ameen, ai zazzaɓi ne kuma jiya da dare ne ma jikin yamatsanta mata".
Cike da tausayin ƙawartan tasake cewa
"Mama Allah yasawaƙe bari in shiga wajen ta".
"Ameen Zainab".
Zainab na shiga taga Halwa saman gado ta kwanta tajuya ma ƙofa baya, ƙarisawa tayi kusa da ita tazauna a gefen katifan tana faɗin
"Halwa ya jikin naki?"
Halwa da tarufe idanunta batare da tamotsa ba tace
"Dasauƙi".
"Allah yabaki lafiya, shine kuma baki kiran awaya kin sanar dani ba? Yanzu da ba don naji Umma tana maganan saka ranan ki jiya ba shikenan bazaki faɗa min ba? Abin yaban mamaki ai ince kina cikin wannan farin ciki nasan da tuni kin garzayo kin fesa min".
Duk wannan surutun da Zainab take yi Halwa taƙi cewa komi illa jinta da take yi, hannu Zainab ɗin tasaka tataɓa wuyan Halwan tana cewa
"Wai jikin yayi tsanani ne haka da bazaki tashi muyi magana ba?"
Ahankali Halwa tabuɗe idanunta tatashi zaune tana kallon Zainab ɗin, cikin kasala tace
"Wani magana zamuyi?"
Zainab kallon yanda duk tayi wani yaushi idanuwanta sukayi luhu-luhu suka yi ja tayi tace
"Ƙawata me ke damunki ne? Kinga yanda kika koma? Ke da ciwo baya hana ki walwalan ki amma yanzu duk kin wani iri kamar kin daɗe kina ciwo?"
Ɗan dafa kan ta Halwa tayi tace
"Zazzaɓi ne kawai".
"To Allah yasawaƙe".
"Amin" Halwa tafaɗa tana komawa takwanta
"Banji daɗi ba ƙawata da baki da lafiya, sai da lokacin farin cikin ki yazo sai kuma gashi ciwo na son hanaki walwalan ki".
"Inji wa yace miki bana farin ciki?" Cewar Halwan tana ƙirkiro murmushi
"Hmm kowa yagan ki yasan da cewa sosai kina jin jiki Halwa, ciwon kwana ɗaya ya maidake haka, nasan da cewa da bakya jin jiki tabbas bazaki kwanta haka ba, ƙafan ki babu inda bazai zagaya wajen sanar da cewa an sanya miki ranan aure ba".
Halwa hararanta tayi tace
"Tunda an ce miki bani da kunya ko?"
Dariya Zainab tayi tace
"Anan kam ai nasan baki da kunya, zakiyi abinda yafi hakan ma".
"Ke dai kika sani". Halwa tace hakan tana ɗaura hannu asaman goshinta
"Yauwa ya maganar Assignment ɗin nan na Malam Isma'il? Kinsan yace "shine Test ɗin mu, kuma wlh na duba nawa bangani ba, ara min naki in kwafe Questions ɗin"
"Kiduba jaka na kiɗauka nima banyi ba, kije dashi kiyimin don Allah".
Miƙewa Zainab tayi tana faɗin
"Ok ba damuwa".
Inda take rataye School bag ɗin tanufa taciro, taduba littafin taɗauko tadawo tazauna tace
"Ni zan tafi gida Umma na can tana jirana zataje anguwa, amma goben zakije school ɗin? Don naga jikinki ya matsanta miki"
"Zani".
"Tom sai muhaɗe acan kenan, ina Yaya Nura? gashi zan tafi ban mishi Allah yasanya alkhairi ba".
Halwa tace "ki neme sa a waya mana, ko kin ban ajiyar sa?".
"To ai naga kece Gimbiyar tasa wataƙil kinsan inda yake, kinga ni ba jan magana zan yi ba na tafi".
Fita Zainab tayi tayima Mama sallama tatafi.
***** ***** ******
Kwance take saman gadonta ta ɗaura hannayen ta saman fuskarta, babu abinda take tunani sai Khalil, tun sanda yakawo ta gidan nan har tafiyan shi takasa samun sukuni, kullum dashi take kwana kuma dashi take tashi, tarasa meyasaka tunanin sa yake damunta kullum, kuma ta kasa gane takamaiman abinda take ji acikin ranta game dashi, tsananin kewar sa ne yake damunta ako da yaushe, burin ta kawai yanzu tasanya shi a idanunta ko ta sami sauƙin zuciyarta, ahankali tamiƙe zaune tana ƙura ma waje ɗaya idanu, can tasaki ajiyan zuciya tatashi tsaye tasanya room slippers tanufi ƙofa, tafiya take yi ahankali tana saukowa daga upstairs, tun sanda takusa saukowa tahango Mom zaune a parlour tana waya, har takusa isa kuma sai tajuya da ninyan komawa Mom takira ta
"Ina zakije kuma Nazeefa? Zo ga yayan ki kugaisa".
Jiki a sanyaye tajuyo tazo wajen Mom tana jin zuciyarta cike da farin ciki, amsan wayan tayi bayan da tazauna takara a kunne tana faɗin
"Hello Yaya".
"Nazeefa". Yakira sunan ahankali cike da salo
Hakan yasaka Nazeefa lumshe idanuwanta cikin jindaɗin muryan sa da yaratsa mata har cikin kwanya tace
"Ina wuni Yaya".
"Lafiya lau, ya jikin ki? Dafatan kina shan maganin ki akan ƙa'ida?".
Gyaɗa masa kai tayi kamar yana kallon ta, sai kuma tace
"Eh ina sha".
"Ok kici gaba da kulawa".
Shiru ne yagibta, hakan yasaka Nazeefa taɗan saci kallon Mom taga hankalinta na kan t.v, sai tace
"Yaya yaushe zaka dawo?"
Shi da har yai tunanin ko ta ba Mom ne still yaji muryan ta tana tambayan shi
"Kina so in dawo ne? Yatambaye ta cike da kulawa
"Eh Yaya nayi kewarka ne sosai".
Tafaɗi maganar ahankali, don ita kanta batasan sanda tafaɗa ba, umarnin zuciyarta kawai tabi
Shi kam Khalil jin maganar yayi wani iri a zuciyar sa, sai kuma yashare tunanin da yakawo mishi rai yace
"Very soon zaki ganni, miƙa ma Mom wayan".
Ba musu tacire wayan a kunni tamiƙa ma Mom, waya suka ci gaba da yi ita kuma Nazeefa tana zaune tana sauraron su, duk da bata jin muryan Khalil ɗin but sai sakin murmushi take yi kamar an mata bushara, tunanin ta kawai yatafi wajen tuno kyakykyawar fuskar sa ne, tana jin wani iri sosai a game dashi musamman ma duk sanda zasu haɗa idanu sai taji gaban ta ya faɗi, ko kuma da zaran ta gan shi hakan ke faruwa da ita, sai dai ita batasan menene ba bare tace ga matsayin abinda take ji, sai dai tasan shi ɗin wani haske ne a rayuwanta, me haskaka mata duk wani baƙin duhun dake cikin rayuwanta, kuma Mai Taimakon rayuwanta.
_Shin zaku iya faɗamata abinda ke damunta Fan's? Don nasan kun sani ai._
~Khalil-Billy~
~Khalil-Lubna~
~Khalil-Nazeefa~
_Muje zuwa Fan's_
_karku manta ku suburɓuro comments fa._
[9/15/2020, 11:32 AM] نفيسة أم طاهرة: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuƊahirah*👈
*\F.W.A📚/*
```ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH```
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
*MARUBUCIYAR*
```NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.```
~Khalil-Billy~
~Khalil-Lubna~
~Khalil-Nazeefa~
.
*CHAPTER 18*
*TOMORROW*
*MONDAY MORNING*
Halwa ce tsaye cikin ɗakin ta tana riƙe da Hijab ahannu, kayan makaranta ne ajikin ta da tagama sakawa, tanufi wajen jakan ta dake rataye taciro tasaƙala shi a kafaɗa sannan tasanya Hijab ɗin tafito waje, leƙa ɗakin Mama tayi dake zaune tana cin tuwo tace
"Mama ni na tafi sai na dawo".
"To uban wa kika bar ma abin karyawan naki?"
Yamutsa fuska tayi da yazame mata jiki tace
"Mama ni nayi latti banda lokacin cin abinci".
Harara Mama tawurgo mata tace
"Tunda an faɗi maƙiyin ki ai dole kice kinyi latti, kizo kizauna kici tun kafin in saɓa miki, ayi mutum sam baya son cin abinci? Rayuwan zata yiwun miki ahaka ne? Nura dai zai yi aiki wlh".
Buga ƙafa Halwa tayi cike da shagwaɓa tace
"Ni wlh Mama bazan iya cin tuwon nan ba, ki ƙyale ni kawai natafi".
"Wlh kuwa in bakizo kinci ba sai dai kifasa zuwa makarantan nan, shegiyar yarinya me taurin kai".
Fuska a kumbure Halwa tashiga cikin ɗakin tawafci kwanon tuwon dake ajiye agefe zata fita
"Dan ubanki dawo nan, zauna kici anan don nasan in dai kika fita sai dai kizubar".
Babu musu takoma tazauna, sai dai gaba ɗaya in kakalli fuskarta zaka gane ranta aɓace yake, haka tatsulma hannu tasoma kai abincin baki tana yamutsa fuska kamar tana cin kashi, Mama kam bata ƙara bi takanta ba taci gaba da cin tuwon ta duk tana ankare da ita, ganin tana yunƙurin yin mata amai a ɗaki ne tace
"Wlh Halwa idan har kikai min amai a ɗaki sai na mugun saɓa miki".
Gyaran murya Baba dake bakin ƙofa yayi yace
"Wai menene haka kika tasa yarinya gaba kina ta mata faɗa?"
"Kaima kasan halinta tunda an haɗa ta da abokin gaban ta, makaranta zata tafi bataci komi ba".
Murmushi Baba yayi yace
"Kiriƙa lallaɓa ta mana Hauwa, kinji tashi kije ɗakina akwai raguwan ƙosai da narage kiɗauka kitafi dashi".
Miƙewa tayi kamar zatayi kuka ta cika bakinta da tuwo amma takasa haɗiye wa
"Ungo nan riƙe wannan kiƙara ki sayi wani abun kici".
Amsan kuɗin tayi tafice dasauri, ɗakin Baban tashiga taɗauko ƙosan tafito, sai da tazubar da tuwon dake bakin ta tukunna takuskure bakin tafice dasauri, akan hanya suka haɗu da Zainab
"Ai da naji shiru baki biyo min ba nace bari in zo in duba Madam ɗin nan lafiya?" Cewar Zainab kenan
Yamutsa fuska Halwa tayi tace
"Ƙalau, Mama tatare ni dole sai na karya sannan zan fita".
Dariya Zainab tayi tace
"Ke dai har yanzu bazaki dena wannan halin naki ba sai kace ƙaramar yarinya, kullum sai kin saka Mama ta ɗaga murya akan cin abinci, Allah yakyauta miki, Yaya Nura dai zai yi aiki wlh".
"Uhm itama haka tagama cewa, ko wani aiki zai yi oho?"
Zainab tace "ai da gaskiyar Mama, kullum wajen cin abinci zai yi fama dake".
Taɓe baki kawai Halwa tayi bata sake cewa komi ba, ita kuma Zainab sai mata hira take har suka kai bakin titi suka tari abin hawa
Bayan sun kai suka sauka Halwa taciro Hamsin tamiƙa, ita kuma Zainab tajuya da ninyan tafiya Halwa tariƙo ta tana faɗin
"To uwar son banza ai ban bada da naki ba, sai ki biya sa".
Kuɗin taciro cikin jaka tamiƙa mishi suka juya suka tafi
Zainab tace "wlh ke ƴar wulaƙanci ne Halwa, nima zan rama".
Dariya Halwa tayi tana waro idanu tace
"me nayi miki kuma? Don kawai nace kibada kuɗi?".
"Oho ke kika sani". Cewar Zainab
Still dariya Halwa tayi tace
"Kiyi haƙuri to, wlh banda kuɗi ne yau, nasan kuɗin da nake dashi bazai ishe ni har nabiya miki ba, coz akwai abinda nake so nasiya dashi".
Zainab tace "uhmm naji, but kinsan da muka zo nan sai natuna da Haris? Wlh sai naji gabana na faɗi sabida abinda kikai mishi ranan Wednesday kullum mukazo nan sai na tuna, I know zai zo yarama".
Jin sunan Haris da Halwa tayi ba ƙaramin bugawa zuciyar ta tayi ba, tsoro da fargaba suka zo suka dirar mata alokaci ɗaya, nan da nan annurin fuskarta yaɓace ɓat, ɗan sauran kuzarin da take ji shima yaɓace ɓat, take tasoma jin kamar wani sabon zazzaɓi ne zai rufe ta, Zainab sai magana take mata but ko kaɗan takasa furta komi har suka shige makarantan, koda suka shiga cikin class ɗin su tunda Halwa tazauna bata sake magana ba, Zainab da tatambaye ta ce mata tayi "kanta ke mata ciwo, da alamu zazzaɓin ne ke son dawo mata", don haka Zainab ɗin bata wani matsa mata ba taƙyale ta, a ranan haka ta wuni duk