Header Ads
Showing 126001 words to 129000 words out of 132567 words

Chapter 43 - BARRISTER IBRAHIM KHALIL Complete Document by Nafisa Isma'il Lawal.txt

Ads the beginning of article before Image

05 Jul 2024

1145

Ads at the middle of Article

sa a hukunta Alh. Sheƙau komin girman sa a ƙasan kuwa, tunda yana da gwamnati a hannu, but be yi hakan ba ya ƙyale su tunda dama zargi yake yi, amma yau da ya gansu sai ya tabbatar da zargin sa




Be damu kansa ba kawai Shari'an ya gabatar, kuma cikin ikon Allah ya ƙwato wa yarinyan haƙƙin ta, inda aka yanke wa Yaron Alh. Sheƙau hukuncin zaman gidan yari na shekara 8 sakamakon kama sa da yin wa yarinya fyaɗe, kuma babu Beli, sannan kuma dole zai bada kuɗi dubu ɗari cif don nema mata magani.






Hakan ya faranta ran mutane matuƙa, ya saka wasu kuka da hawayen su sabida tsaban farin ciki, da yawan su kuma hakan ya taɓa faruwa da yaran su, sai dai rashin samun wanda zai taimake su ba sa iya ƙwato wa ƴar su haƙƙin ta, amma kuma wannan hukuncin da aka yanke wa mutum ɗaya ya sa zuciyoyin su fari da wanke duk wani tabo da ƙuncin dake cin su






Kowa sai sanya wa Khalil albarka yake yi, tare da addu'ar gamawa da duniya lafiya, gaskiya yayi na mijin ƙoƙari, kuma samun irin su a duniyar mu masu jajircewa wajen tsayawa tsayin daka don hukunta masu laifin fyaɗe, hakan zai saka a rage yawaitan su a duniyar mu, idan suka ga ana musu hukunci to dole zasu dena abinda suke yi




Sai dai kuma matsalan al'umman mu suna jin tsoron su fito da irin wannan maganar su bayyana wa mutane don ƙwato wa ƴar su haƙƙin ta, suna ganin tamkar sun tona wa kansu asiri ne, kuma hakan zai ja musu tsangwama a wajen mutane, wannan dalilin yasaka suke ɓoye wa har a kasa hukunta masu laifin fyaɗe, su kuma hakan ke saka wa suna ci gaba da aikata laifin tunda babu abinda ake iya musu.






Don Allah mata duk wanda hakan ya faru da ita, ya jajirce wajen ƙwato wa kansa haƙƙi, iyaye su ma su dage su tabbatar an hukunta wanda ya aikata ɗin, hakan na taimaka wa sosai wajen rage yawaitan laifukan, Allah ya ƙara tsare mu da zuri'armu baki ɗaya Ameen.






Daga wanann Shari'an ne aka shiga na su Halwa, alokacin ne Halwa da su Mama suka ga juna, sai dai babu halin magana tunda Alƙali na ciki




Shima Nura ya ganta, sai dai ita bata ganshi ba, mamaki sosai ya cika sa ganin yanda ta sauya gaba ɗaya tamkar ba ita ba, tsananin kyan da tayi masa ma ya kasa ɗauke idanu akanta, yanayin canjin rayuwan da ta samu duk da su ma suna da rufin asiri sosai, amma kuma yanzu tana cikin daula ne dole kaga sauyawan Halwa, ga ta dama tun farko tana da kyan ta da dirin jiki, but yanzu komi nata ya sake canja wa tayi kyau matuƙa, skin ɗin ta tuni ya sake haske tare da wani irin fresh, Kai da gani kasan babu wahala a rayuwan ta, jin daɗi da kwanciyar hankali ya zauna mata, bare uwa uba tana tsaka da cin amarcin ta ne, ƙyallin amarci da Albarkan aure ya sake fito da ita.🥶😫



Koda Khalil ya tashi ya gabatar da kansa a matsayin Lauyan dake kare wacce ta kawo ƙara, komawa yayi ya zauna




Sai dai su Haris basu da lauya, domin tuni Haris yace "be buƙatar lauya a halin yanzu, ya yarda zai amsa laifin sa sannan a bashi ƴar sa". Don haka ya ga babu amfanin ya samu Lauyan ma




Dadyn sa da Mamy basu ji daɗi ba, amma babu yanda zasu iya tunda yace "zai amsa laifin sa".






Brr. Khalil ne ya miƙe yafito gaban kotun bayan ya nemi iznin magana da Halwa




Fitowa tayi tatsaya a inda aka tanada don tsayawar masu amsa tambayoyi




Khalil ya tambaye ta sunan ta da sunan mahaifin ta, sannan kuma ya buƙaci ta ba ma kotu Labarin asalin abinda yafaru a ranan da mummunan ƙaddaran yafaru da ita






Tiryan-tiryan tasoma faɗa wa kotu abinda yafaru






Tsit kotun tayi ana sauraron ta, tuni masu saurin kuka da tausayi sun soma zub da hawaye, sabida sosai abinda yafaru da Halwan ya matuƙar basu tausayi




Ita kanta tana ba da labarin ne tana kuka, sabida yanda take jin ƙunci da baƙin ciki a zuciyar ta tamkar lokacin da ake keta mata haddi ne






Zina tabo ne babba ga duk wanda ya tsinci kansa a halin; dole ne ya koka, musamman waɗanda akayi musu ta ƙarfi, su kansu masu aikata wa da za su gane illa da girman laifin da suke yi, wlh wlh da har su mutu baza su dena kuka ba saboda tsoron haɗuwar su da ALLAH😭, ya Allah ka kare mu da kariyan ka, bamu da wayau ko dabara ya Allah ka kare mana zuri'armu daga faɗa wa mummunan makoma. 🙏🏼




Har sanda ta dasa Aya tana shashsheƙan kuka






Khalil kallon ta kawai yake yi cike da tsantsan tausayi tare da tarin ƙaunar ta a ransa, ji yake yi tamkar yajawo kayan sa yarungume ta ya rarrashi abin sa, amma kuma babu hali 🤠, don haka yaja numfashi yana lashe bushashshen laɓɓan sa, cike da sanyin murya yace mata "taje ta zauna". Sannan ya juya ya fuskanci Alƙali ya nemi iznin ganin Haris






Fitowa yayi ya tsaya inda Halwa ta tashi




Khalil kallon sa yake yi tamkar ya kama sa ya maƙure shege😃, sai dai babu hali, don haka ya murtuke fuska yasoma masa tambayoyi




Babu abinda Haris ya musa a tuhuman da ake masa, sai ma ƙara wa da yayi da abinda basu sani ba, ya faɗa musu komi da yanda ya nemi taimako wajen Nura.



Tirƙashi! nan ake yin ta fa, ai nan da nan kotu ta hargitse saboda jin bayanan Haris, waɗanda suka san Nura kuwa kamar su: Mama, Baba Zainab Halwa, da su Saleema, daskare wa suka yi sabida tsantsan mamaki da Al'ajabi




Halwa bata iya ko motsi ba, don ba ta tunanin kunnen ta ya jiye mata dai-dai, shiyasa tabi Nuran da kallo wanda tuni Khalil ya buƙaci ganin sa, zuba masa ido kawai tayi tana sauraron abinda zai fito daga bakin sa






Lumshe idanuwan ta tayi da suka cika da hawaye, ko kaɗan baza ta iya juran abinda yake faɗa ɗin ba, don haka tasaka hannun ta biyu ta toshe kunnuwan ta tana fashe wa da kuka me tsananin sauti




Duk mutanen wajen sai da suka kallo ta, sosai ta basu tausayi wasu har da zubar mata da hawaye




Ita kanta Saleema dake kusa da ita hawayen take zubar wa, tasaka hannu tariƙo mata nata hannayen, cikin rawan murya tasoma rarrashin ta




Halwa bata dena kukan ba, sai ma ɗaura kanta da tayi saman cinyoyin ta tasoma rerawa kamar zata shiɗe, babu abinda zuciyarta ke maimaita mata sai sunan Nura, taya hakan ma zai faru? Taya ɗan uwanta masoyin ta, wanda tafi yarda da shi a baya fiye da kowa, shine zai yi sanadin shigar ta wannan halin, meyasa? Me tayi masa?






Guduma Alƙali yabuga don hayaniyar kotun tayi yawa, tsit kake ji an yi duk da kuwa har yanzu Halwa bata dena kukan ba, amma kuma ba'a ji acikin kotun sai can wajen su






Khalil bayani ya sake yiwa kotu kafin yakoma wajen zaman sa ya zauna




Sai da Alƙali yayi rubuce-rubucen sa kafin ya ɗago yasoma yanke hukunci, hukuncin ɗaya ne aka yanke musu daga shi Nuran har Haris, domin dai basu da maraba tunda duk laifi ɗaya suka aikata, don haka an yanke musu hukuncin zaman gidan kaso na shekara 8 batare da beli ba, sannan kuma dole Haris zai biya kuɗin rainon masa ɗiya da akayi, kuma bashi da damar amsar ɗiyar sa sai idan mahaifiyar sa ta amince.






Sosai iyayen Nura suke kuka sabida abinda suka ji, tabbas yau suna nadaman abunda suka yiwa Halwa, shin da wani ido zasu kalle ta? Sun kore ta sabida gudun zubewar mutuncin su, ashe ɗan su shine SILAR KOMAI, Mama tafi kowa shiga tashin hankali, tana ganin tafi Nura ma laifi, domin abinda ta aikata wa ɗiyar ƴar uwanta yafi na Nura muni, shin ina hankalin ta yaje ne a lokacin da har ta manta wacece Halwa a wajen ta?






Suna ji suna gani aka tasa su Nura, amma ko kallon inda yake ba suyi ba, suna ji da ƙuncin dake ransu.






Halwa kuwa sabida shiga ruɗu da kukan da take yi, tuni numfashin ta ya rabu da gangan jikin ta, ta kasa jure abinda taji, ta rasa taya ma zata ɗaura abun akan mizani, shin dama akwai ɗan uwa irin haka da zai iya cutar da ƙanwar sa sabida kuɗi?






Hankalin Khalil da su Ummi ya tashi sosai, musamman ma Saleema, ai nan da nan Khalil ya ɗauke ta ya fice da ita suka take masa baya, mutane sai kallon su suke yi kowa da tunanin da yake yi aransa






Asibiti Direct aka wuce da ita, domin a cikin su babu wanda yayi tunanin zuba mata ruwa ko zata iya farfaɗowa.










𝗕𝗔𝗬𝗔𝗡 𝗦𝗛𝗨𝗗𝗘𝗪𝗔𝗥 𝗔𝗪𝗔𝗡𝗡𝗜 *2*




Tuni su Halwa sun koma gida, sai dai har alokacin sun kasa gane kanta, abinda Nura yayi mata ya matuƙar saka ta a Shock, kuka kawai take yi ta kasa yin shiru




Khalil da Saleema in banda zaman rarrashi babu abinda suka zauna yi




Sukuku ta koma, gaba ɗaya ta dena walwala, to idan ɗan uwanka yayi maka haka, wanene ma bazai maka ba? Nura ya cuce ta, duk tsanar da take yi wa Haris, sai taji gaba ɗaya ma ya gushe ya koma kan Nura, tsantsan tsanar sa ne ya ɗarsu a ranta, ji take yi ta tsane sa fiye da mutuwar ta, kuma ba ta tunanin zata iya yafe masa har ta koma ga mahaliccin ta.






Bayan kwana biyu sai ga su Mama da Baba sun zo har gida neman gafarar Halwa, kuka suke yi suna roƙon ta, yayinda itama take nata kukan tare da rungume Mama, tabbas tayi kewar iyayen nata fiye da zaton me karatu, taya zata ƙi yafe musu bayan su ne iyayen da tabuɗe idanu tagan ta tare da su? Bata taɓa kallon wasu a iyayen ta ba sai su, su ne tatashi tasani; su ne kuma suka raine ta, ko waɗanda suka haife ta bata jin su kamar su






Shiyasa tanuna farin cikin ta da ganin su, ko babu komi iyayen ta sun dawo gare ta, shekaru kusan biyar basa tare, gaskiya tayi kewar su matuƙa, kuma ko kaɗan bata kalle su da abinda ɗan su yayi mata ba.






Mama kuwa kunya da dana-sanin abinda suka aikata mata yasa ta kasa kallon Halwan, gashi sabida son zuciyar su sun aikata babban kuskure, sai dai Allah ya yafe musu.


























.




𝑇𝑜 𝐴𝑙𝑙𝑎ℎ 𝑦𝑎 𝑟𝑎𝑏𝑎 𝑚𝑢 𝑑𝑎 𝑚𝑎𝑠𝑢 ℎ𝑎𝑙𝑖 𝑖𝑟𝑖𝑛 𝑛𝑎 𝑠𝑢 𝑀𝑎𝑚𝑎, 𝑠𝑎𝑏𝑖𝑑𝑎 𝑘𝑎𝑑𝑑𝑎𝑟𝑎 𝑦𝑎 𝑓𝑎𝑑𝑎 𝑤𝑎 '𝑦𝑎𝑟 𝑠𝑢 𝑠𝑎𝑖 𝑠𝑢ka 𝑚𝑎𝑛𝑡𝑎 𝑑𝑎 ℎ𝑎𝑘𝑎𝑛 𝑠ℎ𝑖𝑛𝑒 𝑘𝑎𝑑𝑑𝑎𝑟𝑎𝑛 𝑡𝑎, 𝑠𝑎𝑖 𝑠𝑢ka 𝑘𝑜𝑟𝑒 𝑡𝑎, 𝑘𝑜𝑑𝑎 𝑚𝑎 𝑑𝑎 𝑔𝑎𝑛𝑔𝑎𝑟 𝑡𝑎 𝑎𝑖𝑘𝑎𝑡𝑎 ℎ𝑎𝑘𝑎𝑛 𝑏𝑒 𝑘𝑎𝑚𝑎𝑡𝑎 𝑠𝑢 𝑘𝑜𝑟𝑎 𝑡𝑎 𝑏𝑎, 𝑑𝑜𝑚𝑖𝑛 ℎ𝑎𝑘𝑎𝑛 𝑏𝑎𝑏𝑏𝑎𝑛 𝑘𝑢𝑠𝑘𝑢𝑟𝑒 𝑛𝑒, 𝐴𝑙𝑙𝑎ℎ 𝑦𝑎 𝑘𝑦𝑎𝑢𝑡𝑎.
[1/20, 5:29 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎓
🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
𝐁𝐀𝐑𝐑𝐈𝐒𝐓𝐄𝐑 𝐈𝐁𝐑𝐀𝐇𝐈𝐌 𝐊𝐇𝐀𝐋𝐈𝐋
♠️




𝑊𝑟𝑖𝑡𝑖𝑛𝑔:✍️ 𝐵𝑦
𝐍𝐚𝐟𝐢𝐬𝐚𝐭 𝐈𝐬𝐦𝐚'𝐢𝐥
(𝐹𝑒𝑒𝑛𝑎ℎ 𝐽𝑖𝑘𝑎𝑟 𝐿𝑎𝑤𝑎𝑙 𝐺𝑜𝑚𝑎)




*بسم الله الرحمن الرحيم*






𝐅𝐄𝐄𝐍𝐀𝐇 𝐖𝐑𝐈𝐓𝐄𝐑'𝐒 𝐀𝐒𝐒𝐎📖
®Ɗ𝚊𝚢𝚊 𝚝𝚊𝚖𝚔𝚊𝚛 𝚍𝚊 𝙳𝚞𝚋𝚞💪✓


𝗝𝗜𝗞𝗔𝗥 𝗟𝗔𝗪𝗔𝗟𝗜 𝗖𝗘✍️


𝗪𝗮𝘁𝘁𝗽𝗮𝗱: 𝗨𝗺𝗺𝘂𝗗𝗮𝗵𝗶𝗿𝗮𝗵👈




\𝗙.𝗪.𝗔📚/


𝙰𝙻𝙷𝙰𝙼𝙳𝚄𝙻𝙸𝙻𝙻𝙰𝙷! 𝙰𝙻𝙷𝙰𝙼𝙳𝚄𝙻𝙸𝙻𝙻𝙰𝙷!! 𝙰𝙻𝙷𝙰𝙼𝙳𝚄𝙻𝙸𝙻𝙻𝙰𝙷!!!
𝐴𝑙𝑙𝑎ℎ 𝑛𝑎 𝑔𝑜𝑑𝑒 𝑚𝑎𝑘𝑎 𝑑𝑎 𝑘𝑎 𝑏𝑎𝑛𝑖 𝑑𝑎𝑚𝑎𝑟 𝑟𝑢𝑏𝑢𝑡𝑎 𝑤𝑎𝑛𝑛𝑎𝑛 𝑙𝑖𝑡𝑡𝑎𝑓𝑖𝑛 𝐵𝑟𝑟. 𝐼𝑏𝑟𝑎ℎ𝑖𝑚 𝐾ℎ𝑎𝑙𝑖𝑙, 𝐴𝑙𝑙𝑎ℎ 𝑘𝑎 𝑏𝑎𝑛𝑖 𝑖𝑘𝑜𝑛 𝑟𝑢𝑏𝑢𝑡𝑎 𝑎𝑏𝑖𝑛 𝑑𝑎 𝑧𝑎𝑖 𝑎𝑚𝑓𝑎𝑛𝑖 𝐴𝑙'𝑢𝑚𝑚𝑎𝑛 𝑚𝑢, 𝑘𝑢𝑠𝑘𝑢𝑟𝑒𝑛 𝑑𝑎 𝑧𝑎𝑛 𝑦𝑖 𝑎𝑐𝑖𝑘𝑖 𝑘𝑢𝑚𝑎 𝐴𝑙𝑙𝑎ℎ 𝑘𝑎 𝑦𝑎𝑓𝑒 𝑚𝑖𝑛 𝐴𝑚𝑖𝑛 🤲 𝑦𝑎 𝐴𝑙𝑙𝑎ℎ.


𝗦𝗔𝗗𝗔𝗨𝗞𝗔𝗥𝗪𝗔
𝑁𝑎 𝑠𝑎𝑑𝑎𝑢𝑘𝑎𝑟 𝑔𝑎 ƴ𝑎𝑛 𝑢𝑤𝑎𝑛𝑎 𝑚𝑢𝑠𝑢𝑙𝑚𝑎𝑖 𝑏𝑎𝑘𝑖 ɗ𝑎𝑦𝑎.




𝗕𝗢𝗢𝗞 𝗧𝗪𝗢




.


_______________________________


𝗖𝗛𝗔𝗣𝗧𝗘𝗥 𝗧𝗵𝗶𝗿𝘁𝘆 𝗧𝘄𝗼


________🎓 Bayan sati Uku da faruwan abun Hutun su Halwa ya ƙare, ta koma school yanzu bata cika zaman gida ba, tunda yanzu sauran su ɗan watanni ne su ƙarashe, karatu suke yi sosai.




Sai ga Zainab wani ranan asabar ta kawo musu ziyara, ai kuwa sun yi farin ciki matuƙa, ranan wuni suka yi hira har yamma kafin Aliyu yazo ya ɗauke ta, sun rabu cike da kewar juna




Washe gari kuma sai ga iyayen Haris sun zo wai ganin Husna, tare da matan Haris ɗin da wasu makusanta cikin Familyn su, duk da kuwa da yawan su ganin ƙwaƙwaf suka zo yi




Tarba me kyau Halwa da Saleema suka yi musu




Tunda suka zo Mamy da Daddy suka naniƙe Husna ko sakin ta sun ƙi yi, dayake har ciki Daddy yashiga, ƙaunar yarinyan sosai yashige su, yanzu basu da abunda suke tunawa sai ita, tunda yanzu ɗan su yana magarƙama, har hawaye Mamy take share wa idan ta kalli Husnan, tana jin soyayyar yarinyan sosai aranta duk da kasancewar ta shegiya, amma su suna son ta a matsayin jikar su






Sun roƙi Halwa taba su ita su tafi da ita, amma firr Halwan taƙi, sai ma faɗa musu tayi ta kyautar da ita yanzu, don haka su yi haƙuri




Babu yanda zasu yi haka suka haƙura, sai dai sun sake neman alfarman zasu riƙa ɗaukan ta tana musu hutu.






Da zasu tafi Daddy ya ajiye masu kuɗi me yawan gaske, duk da Halwa taƙi amsa, sai Khalil ne yace "ta'amsa" tukun ta amsa.






Bayan kwana biyu kuma sai ga Mamy ta sake dawowa da kaya niƙi-niƙi, wai ta kawo ma Husna ne, har da Ahmad sai da takawo mishi nashi




Ranan ma Halwa tana school daga ita har Husnan, sai Saleema da Khalil ne da shima dawowan sa kenan, sun amshi kayan tare da yin mata Godiya




Ƙin tafiya tayi, har sanda aka dawo da Husna ta ganta kafin tatafi.






Rayuwa taci gaba da tafiya da daɗi babu daɗi, gashi har su Halwa sun rubuta Exams ɗin su ta ƙarshe, yanzu kuma sai jiran result.










**** ***** ***** ****




Itama Nazeefa a wannan shekaran ne tagama Secondary School ɗin ta, koda result ɗin ta yafito sai Dad yatambaye ta Aure ko karatu? Ita kuma tace masa karatu take so taci gaba, tunda har yanzu soyayyar Khalil ne aranta bata taɓa tsayawa da kowa ba, ko da tace auren take so ba ta da wanda zata iya fitar wa, kuma ba ta jin ma zata iya aure yanzu idan har ba ta cire soyayyan Khalil bane aranta, duk da tayi iyakan ƙoƙarin ta amma ta kasa manta sa, don haka ta samu Dad tafaɗa masa tana son tayi school ɗin nata ne ba'a state ɗin nan ba, ko ba komi tasan idan tayi nesa dashi zata manta shi




Dad be yi musu ba kuwa, yace mata ta zaɓa inda take so




A.B.U Zaria ta zaɓa don nan ne yafi mata, duk da kuwa bata san school ɗin ba, amma yanda take jin labarin sa tasan ba ƙaramin makaranta bane tunda yayi fice a ƙasar Nigeria.






Dad sai da yatara Sameer da Khalil ya faɗa musu komi don jin shawaran su, nan Khalil yaba da shawaran akai ta Abroad tayi acan, cikin su babu wanda yanemi ja da maganar nasa tunda suna ganin shine yakawo ta gidan, don haka shi yafi iko da ita fiye da kowa, Mom CE ma tanemi ta hana, amma kuma ganin Nazeefan tana murna sai tasaka albarka kawai ta ɓame bakin ta






Ƙasan Sudan Nazeefa ta zaɓa, domin tafi son fannin Islamic shi za ta karanta, su ma su Dad sai hakan yayi musu daɗi.






Cikin ikon Allah aka fara mata shirye-shiryen tafiyan ta, Sameer ne akan komi har sai da komi ɗin ya kammala, sai kuma tafiyan ta nan da ɗan watanni kaɗan.










*** **** **** ******* ****






Yau su Halwa sun tashi da farin cikin haihuwar Hakima ne, wajen ƙarfe 10:00am. Suka shirya suka tafi gidan Sameer ɗin






A lokacin ma tuni ƴan uwan Hakiman sun soma zuwa, kasancewar agida ta haihu, kuma lafiyan ta lau da ita da Babyn ta, wannan karon ma namiji ta haifa






"Masha Allah". Abin da su Saleema suke ta faɗa kenan da suka ga yaron, sak Sameer basu da maraba, dayake shima Aamir ɗin Dadyn nasa yabiyo, sai yaron ya koma tamkar Aamir sanda yake ƙarami ( na kula jinin su shi da Khalil ƙarfi ne dashi lolx🥴)






A can suka wuni suna ta hira, Abida ma ta shige cikin su ana tayi da ita, dayake yanzu ta ajiye batun soyyayyar Khalil agefe bare tayi kishi dasu, yanzu ma haka har ta fitar da mijin aure acikin waɗanda suke zuwa wajen ta, tunda tasan wanda take so ɗin ba samun sa zata yi ba, shiyasa tayi wa kanta faɗa, wata biyu masu zuwa zasu sha biki






Har yanzu tana zaune agidan Hakiman ne, tunda iyayen su sun rasu, shine Hakima ta ɗauke ta, kuma Sameer cewa yayi shine zai mata auren.






Sai dare Khalil yazo ya wuce dasu.








To rayuwa dai haka taci gaba da tafiya, zaman su Halwa sai son BARKA, babu ruwan su da faɗa ko kishin juna, sun zama tamkar ƴan uwan juna ba kishi ne ya haɗa su ba, komi tare suke yi, shi kansa Khalil yana alfahari da samun su matsayin matan sa, babu abinda zai ce wa Allah sai godiya, farin ciki kullum sake wanzuwa yake yi agidan sa, ko wacce cikin su yana matuƙar ƙaunar ta kuma yana jin ta arai da magudanan jinin sa, babu ma wanda zai iya tantance wacce yafi so, sai dai shi Khalil ɗin yana ji aran sa yafi ƙaunar Halwa, a ganin sa fa. 🤣






An yi suna lafiya an gama lafiya, yaron yaci sunan mahaifin Hakima, Abdulrahman, zasu ringa ce masa Haneef.












𝐀𝐅𝐓𝐄𝐑 𝐎𝐍𝐄 𝐘𝐄𝐀𝐑 𝐀𝐆𝐎.






A wannan shekaran abubuwa da dama sun faru, ciki kuwa har da zamowar Halwa cikakkiyar Lauya, yau ta amshi certificate ɗin ta






Ko wani masoyin ta yau yana taya ta farin ciki






Don haka Khalil shi da kansa ya shirya mata gagaruman walima

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads