Header Ads
Showing 114001 words to 117000 words out of 132567 words

Chapter 39 - BARRISTER IBRAHIM KHALIL Complete Document by Nafisa Isma'il Lawal.txt

Ads the beginning of article before Image

05 Jul 2024

1163

Ads at the middle of Article

tajira Mami ɗin takullo ƙofa tazo tasame ta kafin su ƙarisa wajen motan




A lokacin har me gadi ya ƙariso wajen yana kai gaisuwa wajen Mami






Amsa masa kawai tayi tana buɗe Boot






Dasauri yanufi wajen Halwa yana ƙoƙarin amsar jakan nata don yasaka mata a Boot ɗin, but Mami tatsai dashi da faɗin






"Ƙyale ta tasaka da kanta Ali, je kabuɗe min Gate".




"To Hajiya". Yafaɗa dasauri yana nufan Gate ɗin




Ita kuma Halwa saka Trollyn tayi sannan Mami tarufe suka shiga motan, sai da taja motan zuwa bakin Gate ɗin kafin tatsaya tazuge glass ɗin tana kallon me gadin tace






"Ali idan su Nafisa sun dawo kace musu su duba keey ɗin a inda nasaba ajiye musu, sannan kafaɗa musu su tabbatar sun tafi islamiyya yau bazan dawo ba sai zuwa dare".






"To Hajiya insha Allahu zan faɗa musu, Allah yadawo dake lafiya".






"Ameen ya Allah". Tayi maganar tana maida Glasses ɗin tarufe sannan taja motan taƙarisa fice wa.






.
























_To ga fa Halwa za'a koma gida Fans, ko me zai faru?_
[1/5, 2:40 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎓
🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️




*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_




*بسم الله الرحمن الرحيم*






*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```


*JIKAR LAWALI CE*✍️


*Wattpad: UmmuDahirah*👈




*\F.W.A📚/*


```ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH```
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._


*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._




*BOOK TWO*




.


_______________________________


*CHAPTER Twenty Six*


________🎓Kamar yanda Halwa tafaɗa mata address ɗin gidan su Saleema can tanufa, a cikin motan babu me magana, ita dai Halwa kallon hanya kawai take yi tana kitsa abubuwa aranta da tunanin abinda zai faru idan takoma..






Ƙaran horn ɗin da Mami ta danna ne yadawo da ita hayyacin ta, takai duban ta ga Gate ɗin lokacin har me gadi ya leƙo don ganin wanene, be buɗe musu ba sai da yazo har wajen motan yayinda Mami tasauke Glasses Motan




Har ya buɗe baki da ninyan yin magana sai yahangi Halwa, cike da tsagwaron murna da al'ajabin ganin ta don zuwa yanzu har ma'aikatan gidan sun san abunda yafaru duba da yanda iyayen gidan nasu hankalin su yake a matuƙar tashe da halin da Saleeman ke ciki






Washe baki yayi yace "Hajiya Halwa ke ce?"






Murmushi tayi masa cikin sanyin murya tace "eh Yusha'u".




"Masha Allah bari in buɗe muku ƙofan to". Yayi maganar yana nufan Gate ɗin dasauri har da haɗa wa da gudu




Yana shiga yabuɗe musu Mami taja motan zuwa ciki




Har wajen motan me gadin yabi su bayan da yamayar da Gate ɗin yarufe, anan ne suka gaisa da Mami itama Halwa tagaishe sa sannan sukai ciki




Halwa ce agaba don haka ita tabuɗe ƙofan tashiga da sallama a bakin ta




Ummi dake zaune saman kujera ta riƙe waya a hannu tana latsawa, kallo ɗaya kayi mata zaka hango tsantsan damuwar da take ciki




Sallaman Halwan shine yasa taɗago kai sabida jin muryan da bata taɓa zaton ji ɗin ba a halin yanzu, dasauri tamiƙe ganin dai itan ce zuciyarta cike da zallan mamaki tare da wani irin murna




"Halwa.." takira sunan ta idanun ta akanta don tama kasa motsawa




Murmushi Halwa tayi takalli Mami dake bayan ta, sai kuma tasad da kanta ƙasa




Mami gaba tayi zuwa cikin parlour'n hakan yasa itama Halwa tabi bayan ta, sai da suka zauna kafin Ummi tasake samun bakin magana




"Halwa ina kika shiga ne? Ina kika shiga kika bar mu cikin neman ki?" Tayi maganar tana dawo wa kusa da Halwan tare da riƙe mata hannu






Hawaye Halwa tasoma yi, cikin rawan baki tace "don Allah ku gafarce Ni Ummi nabi son Raina na tafi na barku amma bazan sake ba".




Washe baki Ummi tayi tana rungume ta cike da tsantsan murna, bakin ta sai faɗin "baki yi mana komi ba Halwa, baki yi mana komi ba wlh.."




Mami dai tana kallon su batare da ta furta komi ba




Tsawon mintuna biyu kafin suka nutsu har Halwan dake yin kuka




"Ummi tace tunda kika tafi Saleema taƙi lafiya, kullum cikin neman ki muke yi, yanzu ma haka tana nan ɗakina ta kwanta tana barci".




Zumbur Halwan tamiƙe tana shirin nufan ɗakin Ummi sai taji saukar muryan Mami tana faɗin






"Oh baza ki gabatar dani bane zaki tafi ki bar ni? Tunda anga uwa dole ki manta dani". Ta yi maganar ne fuskarta yalwace da murmushi






Juyowa Halwa tayi sai dai bata kai ga magana ba Ummi tariga ta da cewa






"Don Allah kiyi haƙuri wlh murnan ganin ta ne yaɗauke min hankali sam gashi ko gaisawa bamu yi ba".






Murmushi Mami tayi tace "babu komi ai".




Sannan suka gaisa kafin Mami ɗin tace "ina son ganin mahaifin ta idan babu damuwa sabida maganar da nazo dashi".




"To babu komi bari in Kira sa". Cewar Ummi tana ɗaukan wayan ta.






Halwa ita tuni ta shige ɗakin Ummi ganin sun manta da ita, koda tashiga Saleeman na barci kamar yanda Ummi ɗin tafaɗa, tunda tasauke idanun ta akan Saleeman hawayen ta suka sake gudu wajen fitowa, toshe bakin ta tayi ahankali tasoma takawa zuwa gadon, sai da tazauna sannan tasaka hannun ta tana shafa mata saman goshin ta cike da tsananin tausayin ta, wuni biyu kacal yasa ta wani irin mugun ramewa kai da ganin ta kasan tana jin jiki






Kasa riƙe kukan ta tayi tasoma shashsheƙan kuka duk da kuwa tana dannewa kar yafito fili






Sai dai hakan be tasiri ba don tuni kukan nata ne yatashi Saleema, ahankali tabuɗe idanun ta akayi Sa'a sai tasauke su kan Halwa da hawaye suka cika idanun ta har bata iya gani sosai sai ta rage su da hannu






Kallon ta kawai Saleema take yi batare da ta motsa ba




Sai Halwan tasakar mata murmushi cikin rawan baki tace "ƴar uwa.."




Lumshe idanuwan ta tayi tasake buɗe su akanta amma kuma bata da alaman motsawa, tsira mata idanu kawai tayi tana tunanin ko dai mafarkin da take yi ne a yanzu bata farka ba?




Sake kiran sunan ta tayi cikin sanyin murya tana cewa "Ya jikin naki?"




Sai da tasake ɗan ƙif-ƙifta idanun nata ta yanda zata tabbatar ba mafarki take yi ba, ganin dai har yanzu tana ganin Halwan sai tayi saurin tashi zaune idanun ta akanta takai hannun ta tana taɓa ta




Hakan sai yaba ma Halwa dariya don ta gane me take nufi tana kokwanton ita ce ko ba ita ba




Murmushi tayi taruƙo hannun nata da take shafa mata jiki tace "ƴar uwa Ni ce fa, na dawo gare ki ne".






Sai kawai Saleeman tafashe da kuka tana rungume ta, cikin kukan take faɗin




"Don meyasa zaki tafi ki bar ni? Kina tunanin zan iya ci gaba da rayuwan farin ciki ne bayan kin tafi? Ƙaunar da nake miki shine zai hana Ni samun farin ciki a rayuwata, wlh da baki dawo ba bazan taɓa yafe miki ba".




Itama Halwan kuka take yi sosai zuciyarta cike da tsananin rauni, tabbas tayi nadaman tafiya, da yanzu Mami Bata dawo da ita ba shikenan haka zata tafi tabar ƴar uwan ta cikin damuwa na rashin ta, abun da taguda ashe shine zai faru, tayi nesa dasu don farin cikin Saleeman amma kuma tafiyan nata yazama barazana ga rayuwan ta, ko kaɗan bata taɓa tunanin hakan ba, tabbas ƙaunar da Saleema take mata ya wuce tunanin ta




Sun jima ahaka kowa yaƙi sakin ɗan uwan sa, kuma basu fasa yin kukan ba sannan babu wani kalma da tasake shiga tsakanin su






Ummi ce tashigo ɗakin, ganin su ahaka sai tasaki murmushi tare da saka hannu tana share ƙwallan da yacika mata idanu, ahankali tataka wajen su cikin farin ciki tace




"To ya isa kukan haka kunji? Tunda komi ya wuce Allah yasa kin dawo sai mu gode waa Allah".




Sakin junan su suka yi yayinda Saleema takasa dena kukan




"Please sis ki dena kukan mana kar ki saka inji na tsani kaina mana, domin idan wani abu yafaru dake bazan taɓa yafe wa kaina ba".




Murmushi Saleeman tayi duk da hawayen basu dena zuba a idanun nata ba




Ummi tashafa kanta cikin jindaɗi da ganin ƴartan ahalin lafiya, sai takalli Halwa tace "muje kiyi sallama da Baƙuwar tamu zata tafi".




"To Ummi". Halwa ta'amsa mata tana tashi tsaye




Dasauri itama Saleeman tamiƙe tana jeho ma Halwan tambaya akan wacece? Don tuni Ummi tayi gaba ta fice




Ataƙaice Halwa taba ta amsa da faɗin "wacce tadawo dani ne".








Abba da Dad ne zaune a parlour'n suna sake sallama da Mami, kafin kuma su ɗunguma gaba ɗaya da Ummi dasu Saleeman suka je raka ta zuwa wajen motan ta, anan suka sake sallama yayinda Ummi take sake mata godiya tare da faɗa mata insha Allahu zasu har gida su sake mata godiya




Itama Halwa godiyar tasake mata tare da bata saƙon gaisuwa zuwa wajen su Safina




Har sai da tabar gidan sannan suka yo cikin gidan, Ummi tasoma yin gaba tabar su nan




Har zasu shige su ma suka jiyo ƙaran buɗe Gate, a tunanin su ko Mami ɗin ne sai duk suka waiga, saɓanin haka sai suka ga motan Khalil na shigowa ciki




Ahankali Halwa tajanye idanun ta daga kallon motan tabuɗe ƙofan tashige




Saleema da bata san da shigewar ta ba tajuyo da murna zata yi mata magana sai kuma taga wayan babu ita, murmushi tayi tagyara tsayuwar ta tana jiran isowar sa.






A ciki kuwa Halwa na shiga tanemi ƙasa tazauna tana gaishe dasu Abba duk kunya ya cika ta, su kuwa kamar babu wani matsala suka amsa mata cike da fara'a




Har ta tashi zata tafi Ummi tace mata takoma tazauna




Babu musu tabi umarnin ta




A lokacin ne su ma su Khalil suka shigo




Kusa da ita Saleema tazauna tana riƙo hannun ta gam, duk yanda ka kalli fuskarta zaka san tana cikin tsantsan farin ciki wanda hakan ba ƙaramin faranta ran iyayen nata suka yi ba, dawowar Halwa ɗin ya yaye mata duk wani ciwo da take fama dashi, tamkar ba ita ce take a mawuyacin hali ba ɗazu, har sai da aka yi mata alluran barci hankalin su yakwanta




Shima Khalil a ƙasa yazauna sabida girmama iyayen nasu, idanun sa ƙyam akan Halwa wacce kanta ke ƙasa ta kasa ɗagowa, sosai zuciyarsa tayi masa sanyi da jin labarin dawowarta wajen Dad..






Maganar Abba shi yadawo dashi hankalin sa har yaɗauke kansa daga kallon ta yana sauke ajiyan zuciya, a kwana biyun nan da babu ita har ya faɗa sosai sabida zullumi da tunanin rasa ta har abada, sai gashi kuma ta dawo wanda be taɓa tunanin hakan ba..






Faɗa sosai Abba yayi mata akan abinda tayi, daga ƙarshe kuma yayi mata nasiha me ratsa zuciya inda shima Dad yaɗaura da nasa, sannan yaƙare da faɗin




"Ina ga kamar yanda Hajiya tabamu shawara hakan yakamata muyi, Ibrahim ya sauwaƙe mata kar a sake samun matsala irin hakan, in yaso sai mu haɗa su ita da Sameer".






A razane Khalil yaɗago kansa yana ware idanun sa kan Dad zuciyarsa na matsanancin bugawa..
[1/5, 3:14 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎓
🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️




*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_




*بسم الله الرحمن الرحيم*






*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```


*JIKAR LAWALI CE*✍️


*Wattpad: UmmuDahirah*👈




*\F.W.A📚/*


```ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH```
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._


*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._




*BOOK TWO*




.


_______________________________


*CHAPTER twenty Seven*


________🎓Kuka Saleema tasaka tana roƙon Dad akan kar araba auren




Murmushi Dad yayi yana girgiza kai cike da mamakin irin wannan soyayyar nasu




"Don girman Allah kar araba auren nan Dady, wlh idan aka raba nima bazan zauna dashi ba dole sai ya sake Ni".




Babu wanda maganar Saleema be basa dariya ba har Khalil kuwa dake a cikin matsanancin ruɗu, a yanda tayi maganar cikin taɓara da sangarta wanda kuma ita iya gaskiyar ta take faɗa tana ci gaba da kukan ta




"Ya isa to ƴata baza'a raba ba, nima wasa nake yi wlh". Cewar Dad yana zuba murmushi




Cak kuwa taɗauke kukan nata jin abinda Dad ɗin yace






Yayinda Khalil yasauke ɓoyayyen ajiyan zuciya yana sauke kansa ƙasa zuciyarsa cike da tsananin ƙaunar Saleema, lumshe idanun sa yayi batare da ya sake jiyo zantukan da ake yi ba, domin tuni ya faɗa duniyar tunani, sai da Dad yaɗan zungure sa da ƙafa kafin yadawo hayyacin sa yana ɗago idanun sa masu tsananin haske da kyawu yazuba masa




"Tunanin me kake yi ana ta magana kana jin mutane?"




Ɗan wur-wurga idanu yayi ganin Dad ɗin ne da Abba kaɗai a cikin parlour'n, sauke kansa ƙasa yayi yana sosa ƙeya be ce komi ba




Murmushi Abba yayi yace "To Khalil sai kayi haƙuri da duk abinda zaka gani na zamantakewar ku, dama zaman tare zo mu zauna ne zo mu saɓa ne, bare in an haɗa da sha'anin mata, duk abinda zaka ganin kayi ta haƙuri kamar yanda kasaba, Allah yayi muku albarka gaba ɗaya".




"Amin Abba". Khalil yafaɗa idanun sa a ƙasa




Tashi Dad yayi yana faɗin "to Ni dai bari in soma gaba ko?"




"ai jira Ni sai mu koma tare nima ba zama zanyi ba". Cewar Abba shima yana miƙewa






Lokacin su ma su Saleema suka fito sai sukai waje gaba ɗayan su, inda Ummi tayi musu rakiya har waje






Dad da Abba sun hau motar su daban-daban suka bar gidan, kafin shima Khalil yahau nasa yana jiran ƙarisowar su Saleema dake gefe suna magana da Ummi, Saleeman ce tatsaya tana ma Ummi magiya akan gobe a haɗo mata kan ƴaƴan ta adawo mata dasu, yayinda Halwa ke tsaye tana sauraron su tana murmushi






Abun da yasa ma yanzu batace zata tafi dasu ba saboda ita Husna tana school tunda ta fara zuwa, shi kuma Ahmad yana wajen Larai ta tafi dashi gidan su






Sai da Ummi tayarda zata kawo su gobe kafin tasamu sukuni wajen Saleeman, motan suka ƙarisa suka shiga yaja yay bakin Gate yafice bayan an buɗe masa Gate ɗin






Yana dai-dai ta motan nasa akan titi yasauke idanun sa kan mirror yana kallon Halwa dake baya zaune




Itama dai-dai lokacin ta ɗago kai tana amsa wa Saleema maganar da tayi mata suka haɗa ido




Yanda yakafe ta da ido ne yasa tajanye nata tana lumshe su tare da kau da kai gefe, bata sake gigin ɗago kai ba har suka kai gida.








*****


Kusan ƙarfe 05:30pm. Saleema tafito haraban gidan, Sale takira taba shi aike sannan takoma ciki, dayake lokacin Khalil ya fita sabida wani waje da zai je yau ɗin, dama yaso yawuce ne lokacin da yatashi Office sai kuma Dad yakira sa akan dawowar Halwa, hakan ne yasa be je ba sai yanzu da yamma




Ita kuwa Halwa tunda suka dawo sallah kaɗai tayi ko abinci bata nema ba takwanta barci, har yanzu kuwa barcin take yi batare da ta tashi ba




Saleema tayi mitan tashin ta don taci Indomien da ta girka musu amma ina tamkar wacce mayen ƙarfe ke ja sabida barci ko motsi taƙi yi




Yanzu ma da tashigo ɗakin nata kai tsaye gaban Sip ɗin kayan ta tanufa tabuɗe tasoma ciro mata kayan ta, sai da taciro su tsab sannnan tazuba cikin Trolly taja zuwa ɗakin Khalil, buɗe sip tayi tasoma jera mata har tagama sannan tasake fice wa




Nocking door ɗin da akayi yasaka tazarce kai tsaye bakin ƙofan, tana buɗe wa Sale ne tsaye da Ledoji guda biyu da ta'aike sa saƙo




Amsa tayi tayi masa godiya tare da rufe ƙofan tajuya ciki, ɗakin ta takai ta'ajiye inda baza'a gani ba sannan tafito takoma ɗakin Halwa




Halwan na zaune abakin gado tashin ta kenan tana maida ɗankwali kanta da yakwance time ɗin tana barci




"Kasa kin ta shi?" Cewar Saleema tana murmushi




Fuskarta taya mutsa tamkar dai yanda tasaba sai kuma tasaki murmushi tana gyaɗa mata kai kasancewar hamma ya taho mata, hannu tasaka takare bakin ta tana sake waro idanu kan Saleeman dake gaban mirror tana kwashe kayan kwalliyan ta tana zuba wa cikin wani farin kwando




"Sis me zaki yi dasu ne?" Halwan tatambaye ta da mamaki




Bata ɗago kai ba illa amsa da taba ta




"Zan mayar miki ɗakin ki ne, daga yanzu komi naki zai koma ɗakin Barrister ne tunda can ne ɗakin ki ba nan ba, yanzu ke matar gida ce bare ki zauna a ƙaramin ɗaki".






Shiru Halwa tayi bata sake cewa komi ba amma zuciyarta na jujjuya maganar nata, sai kuma tamiƙe ahankali tashige Toilet, wanka tasoma yi duk da lokaci ya ƙure mata sannan sai taɗauro alwala tafito




Gaban Sip tatsaya tana ɗan murza idanun ta da sabulu yashiga wajen wanka, guntun tsaki taja kafin tabuɗe Sip ɗin tana kallon ciki da mamaki ganin babu komi, sai kuma tajuyo tana kallon Saleema wanda a yanzu har ta gama kwashe kayan gaban mirror ɗin tana tattara takalman Halwa a cikin wani kwandon




"Sister yanzu har kaya na kika kwashe?"




"Eh mana baki ji me nace miki bane? Ai daga yau kema zaki fara amsa matar *BARRISTER IBRAHIM KHALIL* na haƙiƙa, domin yau Amarya ce ke". Duk maganar nan da Saleema tayi tana ci gaba da aikin ta ne batare da ta ɗago ta kalli inda Halwan ke tsaye ta saki baki tana kallon ta ba




Shiru tayi tatsira mata idanu na tsawon lokaci batare da tayi abinda zai fishshe ta ba, sai da tagaji don kanta kafin tanufi ƙofa tafice tayi ɗakin Khalil, tana shiga tasauke ajiyan zuciya ganin babu shi ciki, da sauri ta'isa bakin sip ɗin tabuɗe tazaro doguwar rigan atamfa da tagani asama tare da ɗankwalin shi, Hijab tasake ciro wa tare da under wear tarufe, memakon tasaka a ɗakin sai takuma koma wa can ɗakin inda tabar Saleema har yanzu tana faman aiki, saka kayan tayi tahau kan sallaya tasoma gabatar da sallan Asar da bata yi ba




Lokacin da ta idar tuni Saleema ta gama kwashe mata komi, shigowar ta ɗakin ne Halwa dake zaune kan dadduma har yanzu tabi ta da idanu




Murmushi Saleema tayi tana dafe ƙugun ta da hannu biyu, taƙariso bakin gado tazube tana faɗin "washhh Allahna

Ads At the End of Article

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads