Showing 45001 words to 48000 words out of 132567 words
Chapter 16 - BARRISTER IBRAHIM KHALIL Complete Document by Nafisa Isma'il Lawal.txt
yaƙure sa da idanu yace "to kaga dawowan su kamar yanda Alh. Mubarak yafaɗa shine yadawo da ita?"
Hannu Malam Umaru yasanya yagoge zufan da yake tsatstsafo mishi kana yace
"Eh na gani".
"Kana nufin sun dawo tare ɗin?"
"Eh tare suka dawo a motar sa bayan mituna ƙadan da fitan ta".
Murmushi Khalil yayi yana sake tsare sa da idanu yace
"Ok to idan har kaga dawowar ta cikin gidan, to da yaushe kenan takuma fita?"
Malam Umaru yace "gaskiya ban sani ba".
"A matsayin ka na me gadi ya akayi har mutum yafita cikin gidan baka sani ba?".
"Eh.. uhm naje zagayawa ne ai, don haka bansan ta fita ba".
"To a yaushe kafara jin ana cigiyar ta?".
"Bayan sa'o'i uku da dawowar ta, sai Hajiya tazo tasame Ni take tambayana "har yanzu Nazeefa bata shigo bane?" Shine nace mata ai tun ɗazu Tawuce".
Daga nan Brr. Kahlil zama yayi, sai Brr. Mahmoud yatashi shima yayi masa tambayoyi, Kana Brr. Kahlil yasake tashi yace
"Ina son inyi wa Hajiya Asiya Tambayoyi".
"Idan akwai Hajiya Asiya tafito".
"Zan so insan alaƙan ki da Alh. Mubarak".
"Mijina ne".
"Kun kai shekaru nawa dashi?"
"Mun kai shekaru 32yrs dashi".
"Ok kin taɓa fuskantar wata matsala dashi? Kamar kina zargin sa da yana aikata wani abu a ɓoye batare da sanin ki ba?"
Kallon inda Alh. Mubarak yake tayi, sai tayuyo da kanta tare da sad da kan ƙasa tace
"Ni ban taɓa zargin sa ba, kuma Mijina baya ɓoye min komi".
"Ok lokacin da kika ji shiru Nazeefa bata dawo miki aike ba, me kikayi akai?".
"Nazo na tambayi me gadi sai yace min "tariga da tawuce ai".
"Sannan kuma da kika koma nemanta kika yi ko me?" Khalil yafaɗa yana tsare ta da idanu
Yawu tahaɗiye kana tace "eh naje na neme ta ciki amma ban ganta ba".
Murmushi Khalil yayi yajuya yana kallon Alƙali yace
"Ya me girma me Shari'a ko da wannan jawaban da Malam Umaru da Hajiya Asiya sukayi zai tabbatar da ƙarya suke yi, coz inda Nazeefa ta dawo gida kamar yanda sukace ya akayi aka rasa ta lokaci guda? Taya har zata fice gidan batare da wani ya ganta ba idan akayi duba da gidan na mutane ne, sannan idan akayi la'akari da Labarin da Nazeefa ta bayar za'a gane gaskiya take faɗa, sannan kuma ansha neman masu aikin gidan Alh. Mubarak ana rasa su lokaci ɗaya batare da wasu dalili na laifi da suka aikata ba, sai dai aga an kawo sabbi, ko anan ya me Shari'a yakamata asan cewa Alh. Mubarak yana amfani da wannan daman ne wajen ɗaukan yaran mutane yana safaran su zuwa wani ƙasa, Nagode ya me Shari'a".
Komawa yayi yazauna, sai da Alƙali yayi rubutu kana yace
"Brr. Mahmoud ko kana da tambayan da zakayi?"
"A'a ya me Shari'a".
Rubutu yasake yi sannan yaɗago yana kallon Brr. Khalil yace
"Zaka iya ci gaba da bada shaidun ka".
Miƙewa Khalil yayi yana sakin wani kyakykyawar murmushi kana yace
"Ya me Shari'a abani dama Brr. Tahir zai je yazo da shedata ta gaba".
"An baka dama".
Miƙewa Brr. Tahir yayi yafita, bayan kamar mituna 3 sai gasu sun shigo da wani mutum, dasauri Alh. Mubarak dake tsaye tsakankanin ƴan sanda yaɗago idanun sa kamar wanda zasu fito waje yana kallon mutumin.
_To fa wanene wannan mutumin?_
[9/29/2020, 1:10 PM] نفيسة أم طاهرة: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuƊahirah*👈
*\F.W.A📚/*
```ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH```
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
*MARUBUCIYAR*
```NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.```
.
*CHAPTER 32*
Alh. Mubarak murmushi yasaki, coz yasan da cewa babu abinda Brr. Khalil zai samu a wajen mutumin, sabida sun riga da sun biya sa zunzurutun kuɗi kuma yayi musu alƙawarin bazai taɓa tona musu asiri ba
Ƙarisawa gaban sa Brr. Khalil yayi yace "kotu zata so tasan ainihin sunan ka da sana'ar ka?"
"Sunana Aliyu Gusau, amma amfi sanina da Gadanga, kuma sana'a ta shine gadi".
"Madalla.. to zan so kafaɗa min wa kake ma gadi?"
"Ina yiwa Alh. Mubarak da Dr. Sabit gadi ne".
"Ma'ana kana nufin kana aiki a gidan Alh. Mubarak sannan kuma kana aiki gidan Dr. Sabit?"
Girgiza kan sa yayi kana yace "ina musu gadi ne a wani gidan su dake Sabon layi G.R.A".
Brr. Khalil yace "to zan so kasanar da kotu abinda kasani a waɗannan mutanen biyu da ka lissafo".
"Da farko dai Ni me gadin gidan ne, kuma shekaruna 20 ina tare da waɗannan mutanen, abinda nasani shine suna kawo mata gidan suna ajiye su, kuma Ni ne jagoran da nake taimaka musu wajen tsare musu Matan da suke kawo wa, sannan Ni ke basu abinci a ko yaushe".
Murmushi Brr. Khalil yayi yace "ina jin ka, daga nan kuma ya ake yi dasu?"
"Dr. Sabit shi ke musu allura sannan yasaka musu Coken acikin su, bayan kamar mintuna 20-30 za'a zo da motoci a tafi dasu, suna safaran su zuwa wasu ƙasashe ne, Ni iyakan abinda nasani kenan".
Still Murmushi Brr. Khalil yayi kana yace "ita kuma Nazeefa ya akayi tabar gidan batare da sanin ku ba?"
"A lokacin Dr. Sabit ya aike Ni zuwa gidan sa don naɗauko wasu yara, to ina tunanin a lokacin ne tafita don basuyi zaton zata iya farkawa a time ɗin ba".
Gaba ɗaya kotun ne yahargitse da surutu sai hayaniya ake yi, shi kuwa Alh. Mubarak tun sanda yaji Gadanga yana zayyano bayani yarufe idanun sa yana jin wani baƙin ciki a ransa, saɓanin Dr. Sabit dake zaune cikin mutane, be taɓa tunanin asirin sa zai tonu ba da be zo wajen ba, sosai yashiga firgici don yasan yau kashin su ya bushe tasu ta ƙare
Brr. Khalil yace "ina son kotu tabani dama zan kira Dr sabit don amsa tambayoyi".
"Dr. Sabit zaka iya fitowa gaban kotu".
Jiki a sanyaye yafito yana gyara glass ɗin idanun sa duk zufa ya jiƙa masa fuska, matsowa kusa dashi Khalil yayi yace
"Dr. Sabit shin me zaka iya cewa game da bayanin Gadanga?"
Shiru yayi yana sad da kai ƙasa, gaba ɗaya hannayen sa rawa suke yi don be san kuma abinda zai iya cewa ba, "shin yaƙaryata abinda aka faɗa akansa ne ko ya?"
"Dr. Sabit kai muke sauraro, kana da abin cewa ko kuwa ka yarda da zargin da ake muku?"
"Eh.. eh na amince mun aikata duk abinda ake zargin mu dashi.."
"Ƙarya ne wlh ƙarya yake min ni dai, Ni ban amince da abinda yafaɗa ba". Cewar Alh. Mubarak gaba ɗaya yazama tamkar zararre, sai ƙara maimaita abinda yafaɗa yake yi
Buga guduma Alƙali yayi yace "ya isa Alh. Mubarak, nan kotu ne Yakamata kanutsu kasan me kake yi".
Sai alokacin yayi shiru yana share zufan dake keto masa, mutane kuwa sai faɗin albarkacin bakin su suke yi, sai da Alƙali yasake buga guduma sannan suka nutsu, takowa Brr. Khalil yayi zuwa tsakiyan kotun yana cewa
"Ya me girma me Shari'a sai kuma Shaidata ta ƙarshe, abani dama in gabatar da Fadila Muhammad".
"Idan da Fadila Muhammad tafito".
Baby Dil dake zaune can baya tamiƙe tataho, sai da idanun kowa yakoma kanta coz yanda take tafiya cike da yanga, wanda kallo ɗaya zakayi mata kagane ita ɗin ba ƙaramar gogaggiyar ƴar duniya bace, duk a yanzu ɗin tayi shigan mutunci, but hakan be hana bayyanuwan Tatue ɗin dake zane a jikin ta ba, ƙarisawa tayi tasaya kamar yanda kowa ke yi, sannan shi kuma yatako kusa da ita yana faɗin
"Fadila zan so kisanar da Kotu sunan ki da inda kike?"
Murmushi tasakar masa kana takalli dandazon mutanen wajen tace
"Sunana Fadila kuma Ni ɗin ƴar garin Kano ce, but ina zaune a EGYPT yanzu, kuma daga can nadawo nan".
"Ok shin ko kinsan Alh. Mubarak me kuɗi?"
"Ƙwarai kuwa nasan shi tun shekaru 7 da suka wuce, yana yawan zuwa EGYPT wajen uban gidan mu".
"Shin menene alaƙan shi da uban gidan naku? Kuma kinsan me yake zuwa yi?"
"Eh na sani, yana siyar wa da Mr. Jay pitter ƴan mata, shi kuma sai yazamar dasu karuwai".
Murmushi Brr. Khalil yayi yace "mun gode Fadila, zaki iya komawa kizauna".
Sannan yajuya ga wajen zaman sa, kallon Brr. Bilkisu yayi yai mata alama da ido, sai tamiƙo masa wasu Files, amsa yayi yadawo tsakiyar kotun yana cewa
"Waɗannan Files ɗi su ne duk wani shaidu da ke kan Alh. Mubarak me kuɗi na zuwan sa EGYPT da safaran ƴan mata da yake yi duk suna cikin nan".
Sannan yamiƙa ma Maga-takarda yaci gaba da faɗin
"Da wannan nake roƙon kotu da tayanke wa Alh. Mubarak da Dr. Sabit da duk wasu waɗanda suke da hannu aciki hukunci dai-dai da abinda suke aikatawa, Nagode ya Me Shari'a".
Zama yayi, Alƙali yakalli Brr. Mahmoud yace
"Kana da abin cewa Brr. Mahmoud?"
Miƙe wa yayi yace "a'a ya me Shari'a, sannan yakoma yazauna
Rubutu yasoma yi Alƙalin kafin yaɗago kansa yana kallon mutanen wajen yace
"Abisa zargin da ake ma Alh. Mubarak me kuɗi tare da abokan aikin sa bisa ga tarin hujjoji da aka gabatar, kotu ta gamsu kuma ta yanke hukuncin ɗaurin rai da rai ga Alh. Mubarak me kuɗi tare da Dr. Sabit, sakamon kama su da yin babban laifi na safaran mata tare da raba su da iyayen su amaishe su karuwai, sannan tare da laifin siyar da Coken, zasu ƙare rayuwan su cikin Jail tare da horo me tsanani, sannan kuma zasu biya taran Miliyan biyar ko wannen su, sannan kotu ta yanke ma Aliyu Gadanga ɗaurin gidan kaso na shekara 10 sakamakon da hannun sa cikin aikata laifin, wannan shine sakamakon hukuncin da suka aikata".
Daga nan Alƙali yabuga guduman sa yamiƙe tsaye, gaba ɗaya mutanen wajen suka miƙe suna me faɗin "Kooooooootuuuuuuu".
Hayaniya wajen yakaure dashi yayinda mutane ke ta turuwan ficewa, alokacin ne kuma ƴan sanda suka taso ƙeyan su Alh. Mubarak zasu tafi dasu, iyalan su in banda kuka babu abinda suke yi
Brr. Khalil kuwa tun aciki yasoma gaisawa da mutane ana masa murna sai zuba murmushi yake yi, koda suka fito waje nan ƴan jarida sukayi masa caaa, dasauri Kausar tature mutane tamatso kusa dashi tana cewa
"Brr. Zamu so kasanar mana wani irin farin ciki kake ji yayinda kayi nasara a wannan gagarumar shari'ar?"
Murmushi yasakar mata kana yace "Farin ciki mara misaltuwa, ko ba komi yau na kawo ƙarshen wasu daga cikin mugayen ƙasar mu, kuma ina roƙon Allah yatona asirin duk waɗanda suke da hannu a ɗaukan ƴaƴan mutane suna fita dasu wasu ƙasan don karuwanci".
"To wani jan hankali kake dashi a gare su?"
"Su tuna cewa su ma suna da ƴaƴa, idan hakan tafaru dasu bazasu ji daɗi ba, idan har basu tuba sun dena wannan banzan harƙallan ba to da sannu zasu girbe abinda suka yi sannan ƙarshen su bazai taɓa kyau ba".
Wasu tambayoyin suka soma mishi amma yayi gaba abin sa batare da ya amsa musu ba
"BARRISTER".
Yaji an kira sunan sa daga bayan sa, juyowa yayi yana kallon ta sai yasakar mata murmushi, ƙarisowa tayi wajen itama tana murmusawa tace
"Congratulations, na gode sosai da taimakon ka gare Ni, haƙiƙa bazan taɓa mantawa da kai ba, thank you so much BARRISTER".
Still yana murmusawa yace "Babu komi Fadila, yanzu yaushe zaki koma gida?"
Ɗan fari tayi da idanu tace "yanzu".
"Ok sai kin kawo mana ziyara kenan?".
Murmushi tayi tace "insha Allahu".
Daga nan sallama sukayi kafin yanufi wajen motan sa inda su Sameer da su Mom tare da su Brr. Tahir suke jiran sa, yana isowa Sameer yaja kumatun sa yace
"Ɗan ƙanina na tayaka murna".
Dariya gaba ɗayan su sukayi kafin sukayi sallama duk suka shiga motocin su ganin Ƴan Jarida na damun su, suka bar wajen.
[9/30/2020, 10:43 AM] نفيسة أم طاهرة: 🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
```®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓```
*JIKAR LAWALI CE*✍️ ~Wattspp Number 07065334256~
*Wattpad: UmmuƊahirah*👈
*\F.W.A📚/*
```ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH```
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
*MARUBUCIYAR*
```NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.```
.
*CHAPTER 33*
Halwa ce zaune saman gado kusa da na Saleema dake barci har yanzu bata farka ba, but yanzu babu Oxgyen da aka saka mata sabida Numfashin ta ya dai-daita
itama Halwan an sanya mata drip a hannun ta, Ummi dake zaune saman kujera tana yanka Lemo cikin plate, bayan ta gama sai taɓare ayaba shima duk tajera akan plate ɗin tamiƙa ma Halwa tace
"Riƙe kisha wannan nasan zai fi miki, bazaki zauna haka tun safe baki ci komi ba".
Babu musu Halwa ta'amsa tasoma ɗauka tana sha, Nurse ce tashigo da sallaman ta taƙariso wajen su tana cewa
"Ya jikin naki? Da fatan yanzu kina jin ƙarfi sosai ajikin ko?"
Gyaɗa kai Halwa tayi tana kallon ta
"Ok gashi wannan maganin ki ne zaki riƙa sha a rana sau biyu, Allah yasauwaƙe".
Ummi ne ta'amshi maganin tana cewa "Ameen mungode".
Matsowa tayi tagyara mata ruwan kafin tafito da allura cikin aljihun ta tasoma haɗawa tana faɗin
"Har yanzu ita bata farka bane?".
"Eh". Ummi ta'amsa mata tana kallon Saleema".
"Ok idan ta farka Sister Asma'u sai ki sanar da Doctor ɗin".
Ummi tace "ok ba matsala".
Alluran tatsira cikin Drip ɗin Halwa kana tayi musu sallama tafice, ruwa Ummi tamiƙo mata tare da ɓallo maganin shima tamiƙa mata tace
"Gashi kisha, amma kiyi sauri kishanye Fruits ɗin kinsan babu komi acikin ki".
Gyaɗa kanta tayi ta'amsa maganin tazuba a baki tana runtse idanu kafin takora da ruwa, daƙyar ta iya haɗiyewa tana sakin nishi, murmushi Ummi tayi tace
"Da alamu bakison magani ko?"
Itama Halwa murmushin tayi tana sauke kanta ƙasa
"To yi sauri kishanye mana".
Ci gaba tayi da shan Fuirts ɗin har tashanye, Ummi ta'amsa plate ɗin ta'ajiye, gyara zaman ta tayi tana kwanciya tare da rufe idanun ta, barci take ji sosai kasancewar Alluran da akayi mata cikin Drip ɗin na barci ne coz ana son tasamu hutu sosai, babu jimawa kuwa barci yayi awon gaba da ita, koda Ummi tayi magana taji shiru hakan yatabbatar mata da barci ya ɗauke ta, tashi tayi takoma saman kujerun dake ɗakin taɗau remote tana sauya tasha, a *ƳAN CI T.V* tabari tasoma kallon Labaran da ake nunawa na hukuncin da aka yanke akan su Alh. Mubarak, in banda girgiza kai babu abinda Ummi take yi.
Tsawon awa ɗaya kafin ruwan da aka saka ma Halwa yaƙare, har wannan lokacin kuma acikin su babu wacce tafarka, tashi Ummi tayi tacire mata Drip ɗin kana tashiga Toilet tayi alwala tafito, fita tayi babu jimawa tadawo riƙe da dadduma, sallan la'asar tayi, bayan ta idar tana zaune tana lazimi Abba yashigo, ƙarisowa yayi yazauna yana kallon ta, itama ɗago kanta tayi tai masa sannu da zuwa, amsawa yayi yace
"Yakamata ki koma gida sai in zauna dasu, tunda yau ba aiki zakiyi ba".
Ummi tace "a'a Abban Saleema babu abinda zan yi ko na koma gida, nasan tunda akwai Larai zata kula da komi, kuma zata kawo mana abinci nan tunda tasan muna nan ɗin".
Gyaɗa kansa yayi yace "ok shikenan, bari ni inje yanzu zan dawo insha Allah, idan ƴar Baba tatashi ki kira ni awaya idan ban dawo ba".
"Toh".
Daga nan tashi yayi yafice ita kuma taci gaba da lazimin ta.
***** ******* ***********
Shigowan sa kenan cikin gidan nasa, tun gama shari'an gaba ɗaya suka wuce gidan su sai yanzu yadawo, ahankali yabuɗe ɗakin nasa yashiga, aje komi yayi tare da cire kayan jikin sa yawuce cikin Toilet wanka yayi sannan yafito, ko mai be shafa ba yaɗauko kayan sa ƙaramar riga fara da dogon wando robber shima fari yasaka, fitowa Parlour yayi yazauna saman 3sitter, wayoyin sa da suke kashe duk ka biyun yaɗauka yakunna, saƙonni ne suka soma shigowa, sai da suka gama gaba ɗaya sannan yasoma buɗe wa yana gani, duk yawanci Abokan sa ne da waɗanda yasani suke tayasa murna, be fi guda goma yabuɗe ba yamayar da wayan ya'ajiye tare da kwanciya yana ɗaura hannun sa ɗaya saman fuskar sa yalumshe idanun sa, ya ɗau tsawon awanni yana ahaka, babu abinda yake yi sai tunani, sai da yaji kiraye-kirayen sallan Magriba kafin yamiƙe a kasalance yashiga Toilet ɗin dake parlour'n yaɗaura alwala yatafi masjid.
*** ***** **** ****
*BAYAN KWANA BIYU*
A kwana biyun nan sosai jikin Saleema yayi sauƙi, don haka aka sallame su suka koma gida, gaba ɗaya Ummi tahaɗa su tana basu kulawa kasancewar har alokacin itama Halwa sosai take fama da jikin ta, laulayi ya sako ta gaba ko abinci sai anyi dagaske take ci, gaba ɗaya ta rame sai haske da tayi, komawar su gida ma sai da Ummi tasake saka mata Drip sabida yawan aman da take yi.
Yanzun ma kwance take saman gado, duk ta ƙudundune jikinta cikin bargo tana ta rawan ɗari, Saleema kuma na zaune gefen ta tabuga uwar tagumi tana kallon ta, fuskarta ya nuna damuwa sosai kamar tayi mata kuka, cikin tsananin tausayawa tace
"Wai meyasaka baza'a cire cikin bane? Kina shan wahala da yawa.."
Ummi da shigowar ta ɗakin kenan taji maganar da Saleeman take yi tayi saurin katse ta
"Kull.. kar in sake jin kin bata wannan shawaran, bakisan haramun bane zub da ciki? Bana son in sake jin kin faɗa mata hakan kinji ni?"
Gyaɗa kanta Saleema tayi tace "Toh Ummi".
Zama Ummin tayi tana ajiye Coolarn da tashigo dashi tare da plate tace
"Tashi kici abinci Halwa, Faten wake ne nasanya akayi miki nasan zakiji daɗin sa kinji? Tashi maza kici".
Saleema tace "to Ummi kawo in zuba mata".
"Ai har dake zakici, in kun gama sai kusha maganin ku ni zan tafi asibiti, sannan nasaka Larai tayi muku Farfesun kayan ciki, shima sai kuhaɗa dashi kuci, ni natafi ku kula da kanku sosai kunji?".
Gyaɗa mata kai sukayi, daga nan ficewa tayi bayan Saleema tayi mata "adawo lafiya". Tana fita Saleema tabuɗe Coolar'n tazuba musu Faten waken da yaji nama sai tashin ƙamshi yake yi, kallon Halwa da har yanzu take kwance tayi tace
"Tashi muci".
Sai kuma ta'ajiye abincin a ƙasa