Showing 33001 words to 36000 words out of 296907 words
Chapter 12 - A RUBUCE TAKE BOOK COMPLETE DOCUMENT
musu wayarsa ta dauki tsuwwa,sai ya fidda wayar yana dubawa,kawun sa ne,wanda shima gidansa ke jikin gidan kawu hassan,gida daya ne daa gaba daya,bayan rasuwar mahaifinsu aka raba gado aka fitarwa da kowa shiyyarsa ya gyara ya maidata gida me zaman kansa.
Hajiya dake faman tsokanar mimi ya kalla
"Hajiya bari naje,kawu imrana ke nemana,yace yaga motata a waje"
"To ba laifi saika dawo" sai ya juya ya fice.
A harabar gidan ya hangeta waje daya ta shimfida dankwalinta tana sallah,ya dauke kansa a hankali ya doshi gate din,ina hajiya ta samo wannan?,duka sauran yaran muhsin ne ya sani,amma wannan mai tsalle tsallen fa?. Dan tsaki yaja yana ture tunanin gefe guda ya doshi qofar gidan kawu imrana.
Koda ta gama sallarta tattarawa tayi ta shige ciki,don ita ko sau daya ba wanda ta gani,tun daga shigowar tasa har fitarsa ta yanzun,bata jima da shiga ba hajjaa ta iso ta hada kansu suka wuce gida tana sake yima hajiya godiya da ban gajiya.
Sai bayan magariba ya dawo,yaci abincinsa sukayi hira da hajiyan,sanda ya tasamma tafiya mimi tayi bacci,don haka ya barta a gidan
"Babu matsala abbas kuwa idan ka barta?" Hajiyan ta tambaya a fakaice,saboda tasan halin hafsat,tana da tsananin nuna son 'ya'ya,bata iya boyewa gaban kowa,idan ka gansu sun kwana wani guri to tare da ita ne.
Wani abu yaji ya tsaya mas a wuya,jikinsa yayi sanyi,mahaifiyarsa ke shakku da kokwanton kwanan diyar da shi ua haifeta a hannunta?,tabbas da saake,akwai kuma gyara
"Ba komai hajiya,idanma kina buqatar wasu qarin kwanakin sai na debo miki kayanta" murmushi ta saki tana shafa kan mimin
"A'ah,kwana dayan ma yayi alhmdlh" boyayyar ajiyar zuciya ya sauke,sukayi sallama ya fita.
Yana tuqi a hanya amma tunani ne fal kwanyarsa,qarar wayarsa ce ta taimaka masa ta katse masa tunanin,ya duba mai kiran,sai ya dan saki miskilin murmushin nan nasa,ya miqa hannu ya daga
"Allah ya taimakeka ranka ya dade,tuba nake,kwana biyu an zubda ni,naji tsoron kada hakan ya zama silar watsewar zumunci nace bari na kiraka"
"Wallahi ko yau naso shiga na gaida umma,kawu ma'aruf ne ya tsaidani,sai kuma na sha'afa,ta yaya zan manta da kai,ayyuka ne suka taru sukayimin yawa,that's why na ajjiyema governor ADC dinsa saboda na ragewa kaina wasun sabgogin,so kuma maimakon su barni na huta,wallahi kaga sun sake cillani KD"
"Naji labari,ina nan ina tunanin me yasa ka ajjiye appointment din?,bayan kana da sauran lokaci?" Kansa ya shafa da hannunsa
"Mu hadu kawai gobe idan kana gari"
"Ina nan,babu damuwa zan sameka gida"
"To sai na ganka" sukayi sallama ya ajjiye wayar yana furzar da iska me zafi daga bakinsa,hadi da sanya idanunsa kan hanya yana duba shagon dake masa aski,ya samu suna nan don haka ya gangara yayi parking ya kashe motar ya fito.
Babban kanti ne na matasa masu aji,masu j da jini a jika wadanda duniyar ke garawa,suna qaruwa ga jikinsa sosai,sun kuma san matsayinsa,don haka tarbar musamman sukayi masa,ya zauna yana duba jaridar da suke ajewa kafin a gamawa wanda ka samu.
Goma na dare ya baro wajen,ya tsaya ya siya fruit ya wuce gida,don yaga kaman nasun ya qare,to amma babu lallai ta gaya masa babu ya sanya a kawo kamar yadda aka saba,qila sai ya tashi amfani dashi sannan tace masa babun.
Kulle ko ina yayi sannan ya wuce sashenta don ya duba lafiyarsu kamar yadda ya saba,ko me sukayi da ita baya fasa wannan,ko bai shiga don ita ba zai shiga don yaransa.
Abun mamaki yau zaune ya sameta a falon,saidai fuskarta gana daya babu annuri,yau din ba laifi,wani lace ne a jikinta peach color dinkin riga da zani,fuskarta tas babu digon komai,sai daurin ture kaga tsiya da tayi.
Tana daga zaunen tayi masa sannu da zuwa,ya amsa mata yana wucewa dakinsu mimi,yaga nawwara sannan ya fito,sai ta miqe tana cewa
"Ina kaje wai?,sanda ka shigo gidan nan fa goma ta wuce" hannayensa zube a aljihun wandonsa ya waiwayo ya zube mata manyan idanunsa yana kallonta,a nutse ya buda baki
"Ina wajen hajiya,daga nan na wuce aski" ya bata amsa yana kafeta da kallo me alamta sai kuma me?,kasa jurar idanuwan nasa tayi,sai ta kauda kanta,cikin salo na mita tace
"Amma yanzu dai tsakani da Allah duk inda kaga dama kake zuwa,kama daina gayamin kana waje kaza" hannunsa ya fidda daga aljihunsa ya juya kawai yaci gaba da tafiya ba tare daya tanka mata ba
"Ina mimi?" Ta fada tans leqe leqe,don sai a sannan hankalinta ya bata ba tare suka shigo ba
"Tana wajen hajiya,zata kwana can" wani abune yayi mata tsaye a maqoshi,har ta bude baki zatayi magana sai kuma ta hadiye data tuna da maganganun anty ummee,ranta a bace amma tayi qoqarin rage kaifin bacin ran nata daga samsn fuskarta ta sake cewa dashi
"Ga abincinka" ya riga ya qoshi sosai,amma yana cewa bazaici din ba sabuwar magana zata balle da ita,abinda bai buqata
"Me kika dafa?"
"Tuwon shinkafa ne" kai ya jinjina,ba kasafai tuwon shinkafarta ke shiga ba,koda bata jima da gamashi ba kana gutsura yana wargajewa,ga uban gaari da zaka yita cin karo dashi a ciki wanda ta d'aure tuwon
"Babu wani abun sai shi?" Sai a sannan ta tuna ta yiwa anty ummee dafadukan taliya,wadda har shi ta dafa amma anty ummee din tace ta daure ta canza masa abincin da tasan yafi so,hakan zai sake sassauto dashi
"Sai jallop din taliya" kai ya jinjina,duka babu wanda zai iya ci,sai yace da ita
"Hadomin black tea kawai,ki saka kayan qamshi please sosai a ciki"
"Tom" ta amsa takaici na cikata,baisan tana yi ba ya sanya kai ya fice,saita daga kai tana kallon agogo,takaici goma da shirin,ta zauna ta wahala tayi masa tuwon amma ya watsa mata qasa a ido,ita anty ummee idan tana bata wasu shawarwarin rashun sanin halin abbas dinne yasa take gaya matan,sannan yanzun qarfe goma harda kusan rabi a sanya mutum wani shig kitchen,ko uwarta bata taba bata wannan aikin ba,tana qananun motoci haka ta shige kitchen din,rabi da rabin hankalinta yana kan mimi dake wajen hajiyar,taja tsaki yafi a qirga,wai duka duka nawa mimin take da tsohuwar zata nace sai ta kwana wajenta(ni kuwa nace uhmmm,sai kace ke din wata uwar kike iya musu).
Saman tray ta kammala komai ta wuce sassanshi dashi,sanda ta shiga bedroom din taji motsin ruwa a toilet,da alama wanka yakeyi kenan,sai ta dora masa saman madubi tana tabe baki,shi mutum Allahn da yayishi bashi da wani aiki saina wanka kamar kwado?,da wannan tunanin ta koma nata sassan don ta kashe wutar ta kuma dauko nawwara,don a nan yau tayi niyyar kwana.
Nawwaran kawai ta dauko,wata zuciyar na cewa ta dauko turare da night gown amma taji ba zata iya ba,ta rufe sassan ta koma nashi. Har sanda ta koma din bai fito ba,sai ta kwantar da yarinyar saman gadon,ta zauna saman sofa bed tana danna wayar ta.
Ringing wayarsa dake saman madubi ta fara,saita miqe da hanzari kai kace ita ake kira,haka dabi'arta take,duk wanda zai kira saita duba waye idan baya kusa da wayar,idan kuwa yana kusa kunnuwanta gaba daya tafiya suke ga wayar,sai ta tantance me yakeyi kafin taci gaba da harkarta,ta nufi wayar tana duba me kiran kamar yadda ta saba,sai taga sunan rose.
*RUMBUN K'AYA*π₯
*DAUDAR GORA*π₯
*IDON NERA*π₯
*A RUBUCE TAKE*π₯
*KI KULANI*π₯
*_uhmmmm_*ππππππππππ
*Nasan zakuce ya da murmushi haka?*
*Wanda bai shigo ba bazai gane ba*
*Sai kin shigo daga ciki zaki gane me nake nufi*βΊοΈβΊοΈ
*KE DAGA JIN SUNAYEN LITATTAFAN MA KADAI KASAN CEWA AKWAI WANI BABBAN ABU MAI MATUQAR JAN HAKALI TATTARE DASU*
*KINA NEMAN INDA ZAKI HUTAR DA KWANYARKI?*
*KI SAMU ZUNZURUTUN NISHADI DA ILIMI?*
Littafi daya---400
Biyu---600
Uku----800
Hudu-----1k
Biyar din duka----1200
*ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN KI ANTAYA JIRGIN FITON ZAFAFA BIYAR*π₯π₯π₯π₯π₯
0022419171
Maryam sani
Access bank.
Shaidar biya tananππ»
09033181070
*MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN*
09166221261
π³πͺπ³πͺπ³πͺπ³πͺπ³πͺπ³πͺπ³πͺ
*Ina yan uwa 'yan nijer?*
*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*
+227 90 16 59 91
Littafi daya---450CFA
biyu---650CFA
uku----850CFA
hudu----1050 CFA
Biyar----1250CFA
*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*
*SIYAN NA GARI KUMA MAIDA KUDI GIDA!*
*Thanks for choosing us*π₯
*H U G U M A*
*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
Page 17
____________________________
*_KAMSHI!_* *_KAMSHI_* *_KAMSHI_*
*TABBAS K'AMSHI RAHAMA NE. INA MASU NEMAN INDA ZASU SAYI TURARUKAN WUTA MASU KAMA GIDAH! DA TURAREN KAYA, TURAREN TSGUNNO, TURAREN WANKA DANA WANKI DA JIKI?*
_KAI BA ANAN KADAI SUKA TSAYA BA. SUNADA TURAREN KHUMRAH KALA KALA DA KULACCAMS NA KECE RAINI._
_AROOS_SCENTS_
_AROOS_SCENTS_
_AROOS_SCENTS_
_KUNJI SUNAN KO? *AROOS_SCENTS*_
_*AROOS SCENTS* SUNA GARIN *KADUNA* SUNA KUMA TURA KAYAN SU A FADIN NAJERIYA DA KETARE_
_LAMBAR WHATSAPP DIN SU :07067786384_
_INSTAGRAM : aroos _scents_
_SCENT HEAVENπSMELL RICH! LEAVE DEM WONDER WHAT YIU USEDβ¦πA SCENT LIKE NO OTHER. SCENT THAT WARDS AWAY SMELLS_
_KYAU! INGANCHI DA KAMSHI MAI SANYAYA ZUCIYA SAI KAYAN TURAREN_ *aroos scents*
____________________________
"Rose?" Ta maimaita sunan da qarfi tana fidda idanu,abu na farko da zuciyarta ta sawwara mata ire iren sunayen soyayya ne da namiji ke sanyawa masoyiyarsa mace,take duk wani jini dake jikinta ya fara tafasa,ta fara fidda huci daga bakinta,mugun kishinta nan ya motsa,ta warfci wayar ta daga ta kara a kunnenta.
Sallamar da akayi da kuma muryar mace ya tunzurata,bata jira komai ba ta fara zunduma mata ashar da zagi
"Shegiya karuwa,riqeshin da kikayi yau duka bai isheki ba,saikin biyoshi da kira yana cikin iyalinsa?,to wallahi billahillazi abbas yafi qarfinki,nawa ne ni kadai,ba wata mace data isa ta rabeshi na bart......."
Bata qarasa ba taji an warce wayar daga hannunta,tabi inda taji an fusge wayar da kallo bala'i yana cinta,don bata gama fadar tarin tulin qazaman miyagun kalmomin dake bakinta ba,sai taga abbas ne,daure da towel yana duba wanda yayi kiran nasa,tun yana bandaki ya fara juyo sautin muryarta,baisan da waye take wannan hayagagar ba gashi dare ya fara yi,sai daya fito ya fuskanci a waya ne,wayarma kuma tasa.
Already an katse kiran daga can,sai yabi kiran yana sake kara wayar a kunnensa,idanuwansa da suka hautsine saboda baqinciki suna kan fuskar hafsat dake huci,jin alamun yabi kiran sai ta fara matsowa
"Kiranta ma ka sakeyi,kuma a gabana?,wal......" Mugun kallon da ya watsa mata yasa ta danyi laqwas tana dubansa shaidan na sake ingizata.
Murya a sanyaye rose tayi sallama kafin yace komai ta rigashi
"Sorry sir,na kiraka da dare ko?,a baiwa madam haquri"
"No,kada ki damu,wani abunne ya faru?" Cikin gurbatacciyar hausarta ta fara masa bayani
"Eh....dazun da kuna meeting mimi tayi bacci a office ta yar da dan kunnenta ne,dana duba kuma naga kaman gold ne,so don kada ayita nema hankali ya tashi shi yasa nace bari nayi maka magana" ajiyar zuciya ya sauke yana qoqarin cooling temper dinsa
"Is okay,ba damuwa,ki aje wajenki,idan na shigo gobe zan karba,idan ban shigo ba zansa ko samuel ki bawa sai ya kawo"
"Okay sir"
"Sorry rose,am sorry"
"No sir,babu komai fa,nasan bata ganeni bane"
"Good night" ya fada yana datse wayar,ya cillata saman gadonsa,sannan ya waiwayo gareta.
Bacin ran data gani cikin idanunsa ya sake sanya jikinta yin laushi,bayan ta gane wace rose din
"Indai rashin hankali da rashin nutsuwa zaki saka a gaban hankalinki zakita aikata abinda zai kaiki ga nadama mara amfani,tsabar banzan kishinki yasa idanunki sun rufe ki kasa gane wace tayi kiran,rose dince baki sani ba?,kiyi a hankali dani ki fita idanuna hafsat,idan kika kaini bango zan baki mamaki wallahi" can qasan ranta taja tsaki,ya jima yana fadin zai bata mamaki,wanne mamaki kenan,amma a saman fuskarta saita yamutsa fuska tana nuna rashin jin dadi
"Ai kasan bansan ita bace,inda na sani ai bazanyi mata haka ba,kuma itama ta yaya zata kira.mutum da aurensa a irin wannan lokaci?"
"Bakiji dalilin da yasa ta kira bane?" Ya fada a tsawace ransa na sake baci,har abada kenan ita ba zata gane tayi laifi ba saita kawo nata uzurin?
"Ina jaddada miki ki shiga hankalinki,bani da lokacin kule kulen mata,amma idan naso ke baki isa ki hanani ko ki tsaidani ba" ya fada yana nunata da yatsa.
Maganar ta doketa itama,to me yake nufi?,taso hasala amma sai ta bagarar,tasan ya fada ne kawai don ya tunzurata ya bata haushi itama,tafi kowa sanin waye abbas din,bata da wannan damuwar don ya fada.
Yadda ya banzatar da ita yana shiryawa taji duk ta takura,saita taka a hankali ta isa inda yake tsaye,ta rungume faffadan bayansa da yake shirin lullubewa da riga
"Kayi haquri don Allah,kuma na shirya zan bika kadunan" maganar tata tazo masa a bazata,wannan yayi nasarar saukar da fushinsa cikin qasa da second biyar,ya ajjiye rigar hannun nasa,ya waiwayo ya kama hannyenta ya zaunar da ita gefan gadon sannan shima ya zauna.
Cikin qwayar idanunta ya sanya nashi sannan ya fara mata magana a tausashe
"Bansan me yasa kika kasa fahimatata ba har yanzu,tsahon shekara biyar cikin ta shida,bani da burin da ya wuce naga gidana da iyalina cikin walwala fahimta da kuma qaunar juna,wannan rayuwar ba itace mafarkina ba a rayuwar aure na,inason gidana ya zama very romantic place,matata ta zama tafi kowacce mace iya soyayya tsafta tattali da iya kula dani,wannan shine nawa qarfin gwiwar da zai bani damar tafi da ayyukana yadda ya dace,ya kuma qara kusancinmu,ban takuraki zuwa kaduna saboda radin kaina ba,nayi hakanne saboda na jawo kusanci a tsakaninmu,kusancin da zai sake haifar da sabuwar soyayya da shaquwa tsakanina dake,ni abbas babu wata mace a gaba a yanzu,duk sanda kuma kikaga wata mace ta shiga rayuwata ba shakka gazawarki ne,daga gareki ne,na baki wannan satar amsar,ruwanki ki tare ko ina kiyi gadin qofar,ruwanki ki bada dama a shiga,amma kiyi qoqari mu zauna lafiya" a daren dai anyi abun arziqi,duk da daurewa kawai takeyi,abubuwa biyu ne sukayi mata tsaye a rai,maganarsa ta qarshe da kuma taraddadin barin bauchi ta koma rayuwar kaduna.
A dukka hasashenta bata ga wata qofa da ta baiwa wata mace ta shiga rayuwarsa ba,tana kishinsa irin kishin dake matsewa kowacce mace qofar shiga rayuwar mijin wata,tana kaffa kaffa da shigarsa da fitarsa,a gida gwagwadon abinda zata iya tana masa,saidai shi da baya gani ma,amma tana takura a abubuwa da yawa duk don sabodashi,batasan kuma me ya rage ba,me yakeso kuma?.
_wannan kenan_
Kwanaki biyu suka qara suka gama shirinsu,har zuwa lokacin yana mamakin abinda ya sauya mata ra'ayin binsa kadunan,saidai bai matsa da sai ya sani ba,tunda zurfafa binciken a wadansu lokuttan ba alkhairi yake haifarwa ba.
Ana gobe zasu tafi ya sanyata ta shirya don suje su yiwa hajiya sallama,daga nan kuma ya sauketa a gidansu,tana ta qoqarin danne zuciyarta ne,da kuma bin dukka abinda yakeso,saboda bataso ta bata hanyar data fara sharewa kanta,don antyn ummee tana ta jan kunnenta kan sai tayi juriya,kuma saita kula,don haka ta shirya ta bishi.
Hannu bibbiyu hajiyan ta karbeta kamar yadda ta saba,cikin kirki da karamcin nan nata,ba laifi hafsat din kadaran kadaham itama,har suka gama gaisawar suka taba hira sama sama,saita miqe tana duba agogo gami da kallonsa
"Inaga ya kamata ka saukeni a gidan,lokacin yana tafiya" kansa ya dauke daga kan jaridar da yake dubawa ya kalleta,har ya buda baki zaiyi magana hajiyan ta rigashi
"Gaskiya kam,kuma sallama zakuyi ya kamata ace kinje da wuri don ki samu isashen lokaci,tashi ka sauketa abbas" baice uffan ba,saboda maganar hajiya gaba take da maganar kowa a fadin duniya,banda haka xamanta a gidan yayi kadan sosai,duka duka ko awa guda bata rufa ba,sai ya ajjiye jaridar ya miqe yana daukan key din motar sa ya fice,ta yiwa hajiya sallama,ita kuma tasa muneera ta bita da kayan amfanin kitchen data tanadar musu,kamar su kuka kubewa daddawa kanwa da yaji da sauransu,saboda tasan abbas din ma'abocin son tuwo ne,a halayya kuma irin ta hafsat din babu lallai ta tsaya tunanin tanadarsu,ta bisu da addu'a suka lafiya,qwaqwalwarta fal mamakin yadda hafsat din ta sauya ra'ayi,duk da bata tsaya tambayar abbas din ba.
***********
Gab da sallar magariba hajjaa ta iso gidan hajiyan,cike da gajiya da kuma farincikin gama cooking classe din da sukayi na kwanaki biyar,wanda dai dai yake da na kwanaki sittin a wata makarantar,ita kanta tasan ta qaru over da abubuwa masu yawa.
Tana shiga ta miqawa nujood jakarta ta daura alwala kawai sannan ta shige falon hajiyan,ta zauna suka gaisa hajiyan tayi mata sannu,sannan ta kira muneera kan ta zubo abincin dare suci kafin su wuce
"Hajiya da kin barsu,yauma kafin na fito sai da nayi girki"
"Me yasa kike nuna wa gidan nan kamar ba gidanku bane hadiyya?,kinga muneera zubo,idan ba zata ci ba yaran zasu ci,xakuci ai ko widad?" Tayi tambayar tana kallon widad,wadda keta faman hada kayansu a jaka tana kammalewa.
Murmushi ta saki tana sadda kanta qasa,ba tare data amsawa hajiyan ba
"Au,babarki zaki goyawa baya kenan,sai faman hada kaya kike,kamar dama kin gaji da zuwa gidanmu " wannan karon har sai da haqoranta suka fito tana dariya cike da kunya
"Ba haka bane hajiya,muna ta saki aiki fa kwama biyar din nan,kema zaki huta" maganar yarinyar saita burgeta,ta kuma sake saka mata qaunarta a zuciyarta,haka kawai cikin kwanakin taji yarinyar ta kwanta mata,tana kuma burgeta,saboda taga bambancin dabi'a tsakaninta da sauran yara,sau tari takan zauna nan kusa da hajiyan suyita hira abinsu,widad din najin hajiya kamar ummunta,idan tana tare da ita sai taji kamar ummu,tana debe mata kewarta sosai.
"Ni ai ban gaji da ganinku ba