Header Ads
Showing 177001 words to 180000 words out of 296907 words

Chapter 60 - A RUBUCE TAKE BOOK COMPLETE DOCUMENT

Ads the beginning of article before Image
Ads at the middle of Article

miki amma uzuri ne ya taso ko?" Kai kawai ta gyada tana maida dubanta ga widad daya hakimce a gaban mota,zuwa yanzun ta zura earpiece a kunnenta ma.

Mintunan agogon wayarta take ta kalla tana lissafa mintunan da sukayi a tsaye shida ita,tanata qoqarin danne abinda yake taso mata harta gaza,ta daga fararen idanunta masu girma,ta sake sauke glass din motar,a shagwabe ta kira sunanshi

"Uncle......don Allah ka taho mu tafi......naaaa gajji"

"Kambu" Wasu tagawayen duka qirjin hafsat yayi,sautin muryar widad din sai ya zame mata kamar saukar ruwan dalma a kunnenta,yayin da ta fusgi hankalin abbas sosai,har dai daya sauke wata qaramar ajiyar zuciya da hafsat din ta jiyota har tsakiyar kanta,wannan ya sabbaba mata maida dubanta kansa cikin sauri ba tare data shirya ba.

Wani irin kallo da ita daya ta sanshi cikin idanunsa ta hanga kwance cikin idanuwan nasa yana yiwa widad din shi,wani malolon abu ya tokareta,dukka juriyar da takeson gwadawa ta gushe

"To uwarmu,saiki saurara mana,ko sallamarma bazamuyi ba?" Ta fada da madaukakin sauti tana duban widad din da wani irin kallo,kallo daya widad din tayi mata ta dage glass din motar,gab da zata kammala rufewar ta daga yatsunta tayi masa sign na i love you,hafsat din bata gane me ake nufi da hakan ba,taga dai ya saki siririn murmushi,sannan ya maida dubansa ga hafsat din da takejin kamar ta taka zuwa gaban motar ta fusgo yarinyar.

Cikin nutsuwa ya miqa mata tattausan hannunsa alamun musabaha,wannan kusan dabi'arsu ce shida widad,sai tabi hannun da kallo

"Amma dai kasan ni ba namiji bace ai" murmushin da bai shirya ba ya qwace masa,ya manta ba widad bace,sai ya matsa gabanta kadan yayi kissing goshinta yaja baya yana mata sallama,yayin da widad daga cikin motar tana hangesu,saita tura baki gaba tana jin haushin abinda yayi mata.

Har abbas din ya shiga motar ya tayar hafsat tana tsaye tana kallonsu,sai da suka fice daga gidan sannan ta koma sassanta da sauri kamar zata tashi sama,yau tabbas dole ta hadu da anty ummee,koda ba anty ummeen ba dole ta nema abokin shawara,tana jin alamu da qamshin lalacewar komai anan kusa idan bata sake daura damara ba,ta gaji da wanna pretending din,gwara ta fito sak a mutum ko zatafi qwatar 'yancinta tare da nunawa yarinyar ita ba kanwar lasa bace,ba kuma sa'ar yinta bace ita.

Juyawa yayi yadan kalleta kadan jin tayi shuru,tunda ya shigo motar batace komai ba,sai yaga titi kawai take kalla,ya motsa kadan ya saka tafin hannunsa cikin nata ya riqe da kyau cikin taushi

"Ba dai shikenan ba,kin hanani zama ko?" Daman jira takeyi,saita turo baki

"Bayan harda kiss dina ka yiwa mummyn mimi" sosai dariya ta kamashi,ya dan daki sitiyarin motar yana dan dubanta

"Wato kiss din ma naki ne.....wai.....yaushe kika koyi qorafi haka ne babyn uncle?" Fuska ta hade bata ce komai ba,ya sake sakin murmushi

"Yaushe kika koyi kishi ne baby?,Ita kiss dinki nayi mata,ke kuma uncle din kika dauke gaba daya,ba shikenan an raba ba?" Murmushi tadan saki ta jijjiga kai

"Good,yanzu bani labari,me dame za'a yimin idan mun koms,kinsan nayi missing dinki.....nayi missing abun nan....." Ya fada ba tare daya qarasa ba,saita juya tana kallonsa,girarsa daya ya dage mata tare da kashe mata ido,abun ya bata kunya sosai,sai ta rufe fuskarta da hannuwanta tana dariya,shima ya tayata dariyar idanunsa na kallon titi.

Ko wanka bata tsaya yi ba,saboda tana ganin kamar zai bata mata lokaci ne kawai,ta canza kaya ta canzawa nawwara pampers,ta kada kan yaran ta zubasu a motarta suka wuce gidansu.

Kallonta kawai mamanta takeyi sanda take gaya mata duk irin abubuwan da suke faruwa

"Amma su uwa sun ha'inceni,keda duk da wadan nan matsalolin cikin gidanki amma kike zaune haka kina amfani da gurguwar shawarar ummee?,don ta kai mata ke lallai ne takai mikin?,bari na kira hajiya shuwa naji wanne malamin zata hadaki dashi" ta cire wayarta dake kusa da ita a chargy ta soma neman number din.

Kamar hafsat tace abarsa,duk ds yadda matsalar take damunta,amma dai sai ta kanne tana sauraren mamar tata sanda suke gaisawa da hajiya shuwa din.

Tana zaune tana sauraren umman nata tana yiwa hajiya shuwa bayani,bayan ta gama suka shiga tattanawa,kusan minti talatin sannan sukayi sallama,ta dubi hafsat

"Baki da wata matsala,itama kanta fadan zaman da kikeyi takeyi,tace yanzu ai ba'a zama,kada kiga wai yarinya qarama,idan batayi ba magabatanta zasuyi mata,bare sadakar yalla?,ai sai addu'a kawai,shu'umai ne" kai ta jinjina tana jin abun yana damunta har cikin zuciyarta

"Yanzu kudi kawai zaki fito dasu,sai mu saka rana mu sameta,tunda baya gari ma komai zaizo da sauqi"

"Kudi kaman nawa?" Ta tambaya tana duban umman nata

"Daga dai dubu dari zuwa sama"

"Za'a kaiwa malamin?" Hafsat ta tambaya tana dan riqe da habarta

"Eh,har miliyoyi ma ai kashewa akeyi,ita ranar biyan buqata rai ai ba'a bakin komai yake ba" janye hannunta tayi tana gyara zamanta,itakam bata jin ko naira dubu goma zata iya fitarwa,kudin da take fadi tashin tarawa rana daya ta wafci wani abun a ciki ta fara kaiwa wani suna raba dai dai,koma ya fita ci

"Shikenan umma,ki bari idan na shirya sai ayi mata magana sai muje" wani kallo uwar ta watsa mata,dama tuni labarin yadda ta baci da son abun duniya yake zuwa mata

"Kudin ne ba zaki iya fitarwa ba kenan?,ko a jikinsa ba zaki tarasu ba hafsatu?,gwara ki zauna da damuwarki kenan?" Kai ta girgiza

"Ni ba haka bane umma,kawai dai matsalar batayi girman da zan kashe wadan nan kudaden ba,mu bari kawai anty ummee din tazo nasan tabbas akwai mafita daga wajenta,basai an kashe komai ba" haushi takaici da baqinciki suka cika umman,saita dauke kanta gefe tana cewa

"To ai shikenan,sai kici gaba da zama har sai sanda matsalar ta girmama ta zama babbar".

***********Tunda suka koma ta tattara ta watsar da batun mommy hafsat din ta shiga sabgoginta,sosai ta maida hankalinta ga karatunta koyon girke girke online da kuma practical classes da akeyi cikin garin kadunan.

Cikin lokaci qalilan ta zama expert,hannunta ya sake fadawa,ta kuma qware da kalolin abinci masu dama.

Zamu iya cewa batason so ba,amma tana jin wani abu mai qarfi akan uncle din nata,wanda inda da cikakken wayo kai tsaye zata fahimci soyayyarsa ce ta fara kafa kanta a zuciyarta,sam bata iya wuni guda cikin nutsuwarta muddin baga ganshi ba,kowanne lokaci burinta shine tayi abinda zaice

"That's my baby.....ma sha Allah baby wannan yayi......baby doll inason abu kaza,babyn uncle wannan yayi dadi ko yayi kyau" wannan ya sanya ta sake zagewa da dukan iyawarta ta haddace abinda tasan yafiso yafi muradi,gefe guda anty deena da anty madeena harda hajja sun zage sosai suna wayar mata da kai dai dai gwargwado.

Ta gefan abbas kuwa abun har baya faduwa,wani irin wawan kamu soyayyar widad tayi masa,ta yadda shi kansa yake mamakin kansa,zuciyarsa ta koma sabuwa,tamkar bai taba qaunar wata halitta ba cikin rayuwarsa,yarinyar ta tafi da dukka zuciyarsa,ta kuma shiga rayuwarsa fiye da kima,har bayason wani abu da zai kawo su nisanci juna,duk da yana fama da shagwabrta sakalci da kuma wauta amma hakan sai ya zame masa kamar wani abun debe kewa,ya kuma zame mata ado,kasancewar bai saba ganin wannan ba.

A koda yaushe hafsatun na masa magana ne a tsaitsaye,tana kuma nuna masa ita din me wayo ce,bata da lokacin shagwaba ko karya murya,kamar yadda take ganin bai kamata ace mutum yana da wani choice a rayuwarsa ba na tsafta abinci turare sutura da sauransu ba,banbancin ra'ayi me girma da kuma tarin yawa ne a tsakaninsu.

Sabanin widad,da komai nata nashi ne,komai zatayi tana duba zai burge uncle?, uncle zaiji dadi?,hatta da shopping tana yinsa ne base on his choice,komai ta dauka saita tambaya cikin shagwabar nan tata

"Uncle yayi?" Wani lokaci yace baiyi ba,wani lokaci kuma ya barta da zabinta,ya zuwa yanzu bayajin akwai wani abu da zai iya shiga tsakaninsa da widad din,ta shiga rayuwarsa fiye da kima,ta samu gurbi a zuciyarsa sama da yadda kowa yake hange.

Tun daga wancan ranar ta rage binsa weeknd bauchi kwata kwata,koda ta bishi ma raba kwanan take tsakanin gidan hajiyan da kuma gidansu,dukkansu shi da hajiyan da suka fuskanci hakan yafi samar mata da nutsuwa sai suka rabu da ita.

Hafsat na gama kwananta baya iya jurewa,haka zai je gidan hajiyan da kansa yayita raragefen daukarta saboda kunyar hajiyan,abinka da uwa,takan bishi da murmushi ne kawai sannan ta sanya widad din shiryawa ta kuma bishi,a yanzun duk duniya tafi kowa samun farincikin canjin da abbas din ya samu,idan ka kalleshi da kyau zaka fahimci hakan,don har wata murjewa yayi,yayi 'yar qiba,ba shakka ko ta iya fannin abinci kawai dole rayuwarsa ta sauya,saboda shi din mutum ne da baya wasa da cikinsa,sai Allah yasa widad din bata da wani fatinciki itin ta ganta cikin kitchen tana sarrafa wani sabon abu da basu saba ci ko basu taba ci ba,koda yaushe hajiyan godewa Allah takeyi da sauyin da abbas din ya samu,nutsuwa sosai tazo masa,duka matsalolin hafsat ma sai suka rahe damunsa,tunda ko ba komai akeai gefen da yake samun nutsuwa gamsuwa da kwanciyar hankali,inda widad din yakeso takai wanda bata qarasa kaiwa ba yanata qoqarin horar da abarsa cikin soyyaya qauna kulawa da kuma nutsuwa.

Gefe daya hafsat din itama bata sake tayar da zancan ba,saboda anty ummee ta kwabeta kan ta barta haka,kada a fahimci takunta,saidai akwai sabbin hanyoyin da zasu sake dubawa.

_wannan kenan_

*Masu karatu muje zuwa,akwai sinqi sinqin CAKWAKIYA a gaba*
*H U G U M A*

*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
*Arewabooks:Huguma*

Page 91

Sassanyan qamshi parlor din yake fitarwa baya ga wani kwantaccen yanayi da duk wanda ya shigo ciki sai ya burgeshi,awa guda kenan da gama dukka aikinta,ta kuma shirya kanta cikin wata gown ta yadin chiffon mai qaramin hannu,plain ne black babu digo ko adon komai a jiki,ta matse gashinta da jiyan abbas ya kaita da yammaci aka gyara mata shi,yana daya daga cikin abinda yakeso,shi yasa shima yake bashi kulawa har fiye da yadda ita ke kula da sumartata,duk sanda take kwance a jikinsa zaka samu hannunsa saman kanta yana yamutsa sumartata mai tsaho da santsi,abinda yake yawan haifar mata da kasala,saita lafe a jikinsa.

Hankalinta ya dauku ga wayarta sosai,tana karanta wani hausa novel mai suna HANGEN DALA,labarin ya tafi sosai da hankalinta,ya kuma fara ankarar da ita matsayin hafsat a wajenta.

Ya dauki mintuna kusan uku tsaye a bakin qofar yana qare mata kallo ba tare data sani ba,hancinsa kuma yana shaqar daddadar iskar da parlor din yake fitarwa.

Tayi masa wani mugu mugun kyau,cikin kwanakin gaba daya wani kyau take qarawa,ga wani irin fari data sakeyi kamar ka sanya hannu jini ya fito,ta kuma qara qibar data sakata murjewa,alamun hankali da girma sun fara nunawa a jikinta,qibar tayi mata wani irin kyau dake dimauta masa tunani,shi kansa wani lokaci yakan tuhumi kansa

"Abbas anya baka zauce akan yarinyar nan ba?" Bai sani ba ko zaucewar yayi,amma shi kansa yasan yana mata wani irin so da bazai misaltu ba,baya gajiya da kallonta,baya gajiya da ganin shirmenta,baya gajiya da sauraren hirarta,ko ba komai zai samu nishadi irin wanda duk duniya idan ba wajenta ba babu wajen wanda yake samunsa.

Yaga alamun hankalinta yayi nisa sosai,don haka ya sanya qafarsa cikin tattausar muryarsa yayi mata sallama,suna hada ido ta miqe da sauri bayan ta watsar da wayar gefe,ta kuma tako da sassarfa yadda ta saba yi masa ta dane shi,ya sanya dukka hannayensa ya tarbeta,ya kuma dauke abarsa cak ya aza a jikinsa yana aika mata kisses ta ko ina,laushin fatarta da qamshinta kamar zai zautashi.

Kamar ko yaushe ta sunne kanta tana jin kunyarsa,ya saki qawataccen murmushi yana shiga cikin falon sosai da ita hadi da cewa

"Gayamin.....me zanyi na qarasa cire kunyar nan baby......tana qwarata wani lokacin fa" ya fada murya qasa qasa kamar su da wani ne a falon,saita sakar masa murmushi tana shigewa jikinsa.

A hakan yana dauke da ita suka shige bedroom dinsa tana masa sannu da zuwa

"Yau anyi zafi,wanka zan fara yi baby,ba wani abinci yau" dariya ta sakar masa,sannan ta wantsalo daga hannuwansa zuwa qasa,ya tareta da sauri yana cewa

"Yi a hankali,wai bakiga kin fara zama 'yar lukuta ba?,inajin na kusa fara kasa daukarki" baya taja tana bata fuska

"Ka kusa daina daukata kuma uncle?" Ta fadi tana bubbuga qafa a shagwabe,yasan yanzun zai ballowa kansa ruwa,sai yayi saurin yin kwana

"Wasa nake miki fa babyn uncle.....amma fa wait.... seriously kin fara zama 'yar lukuta,ban yarda ba akwai abinda yake faruwa,me kike ci bakya sanmin?" Siririyar dariya ta saki

"Uncle ka fini ci fa,saidai wanda nake ci da daddare kana bacci" kai ya gyada yana dariya

"Harda rabona kike ci ai,kuma ban bayar ba,saina fanshe abuna,zo nan" ya fada yana takawa gabanta idanunsa a narke a kanta,ta saki dariya taa fadawa toilet da gudu.

Tsayawa yayi ya bita da kallo har ta shige,qugunta ya bude sosai,qirjinta ya fara cika irin yadda yakeso,abinda yake sake dimautar dashi a kanta koda yaushe,saidai har yau 'yar shagwabar tasa kukan amarci takeyi bata daina ba,hakan baya damunsa,hakan ma burgeshi yakeyi,ya zauna ya lallashi kayarsa.

Gaban mudubi ya taka ya zuge jakar daya shigo da ita yana duba takaddun daya shigo dasu,ya sake sakin murmushi yana tunanin irin yadda zataji idan ya gaya mata komai na tafiyar ta saudiyya ya kammala,yana tsaka da dubawar kuwa ta fito tana goge ruwan hannunta da qaramin towel

"Uncle ka shiga na hada" ajjiye su yayi,ya matsa zuwa gabanta,a tausashe ya kamo qugunta ya hade da nashi yana duban qwayar idanunta,itama shi take kallo,tana samun kanta cikin wani irin yanayi a duk sanda irin hakan zata faru,tana ji da ganin wani abu na musamamn cikin idanuwansa

"Amma dai na gaya miki,indai kina yin wankanki bakya jirana,zaki dinga wanka biyu ko?" Fuska ta narke masa sannan ta turo masa dan qaramin bakinta

"Uncle saina zauna ka dawo kaga qazantata?" Bin siraram lips dinta daketa qyallin lip gloss yayi da kallo tsigar jikinsa na zubawa,sannan ya dauke ya maidasu cikin manya kuma fararen idanuwanta,har cikin zuciya da ruhinsa yana yaba mata,yadda bata qaunar ya ganta ba wanka,naturally haka take,sometimes kafin ya dawo daga salla tayi wankanta

"Okay,tunda haka ne zaki biya ladan qin jin maganar uncle" bai barta ta samu damar cewa komai ba ya hade bakinsu waje daya ya shiga aika mata da wani zazzafan kiss da ya sanya taji kwanyarta tana yamutsawa,cikin lokaci kadan ya sauke mata wani saqo mai nauyi daya sanya jikinta saki gaba daya,yayin da ilahirin nashi jikin ya dauki rawa gaba daya,kusan ta saba da wannan yanayin nasa,tun tana tsoro harta saba gani,ta saba ganin wannan romance din mai zafi daga wajensa,fice mata a hayyacinsa yakeyi cikin lokaci qalilan,wannan yake rudata itakuma tayita masa kula,kukan da baya samun damar lallashinta sai bayan komai.ya kammala.

Yau dinma daga bata ladar rashin jin magana ya zarme,shi kamsa baisan me yakeyi ba,illa dai zuciyarsa da qwaqwalwarsa yaji sun kasa jurewa,bai kuma barta ba sai daya isa ga muradinsa duniyarsa qarshen farincikinsa.

Tana a jikinsa tana masa 'yan koke koken data saba,hannunsa cikin sumarta yana yamutsata,idanunsa a rufe,lips dinsa kawai ke motsawa suna fidda sautin wasu kalmomi masu zaqi da kwantar da rai,yayin da zuciyarsa tayi nisa wajen son gano iya matakin matsayin da widad ta tsaya a ransa,ko yaushe yana jin kamar a ranar ya fara saninta,tana da wata irin baiwa da bai taba tsammanin za'a sameta jikin kowacce diya mace ba,a duk sanda ya kasance da ita burinsa na sake kasancewa da ita baya raguwa saidai ya qara hauhawa

"Uncle wayo" ta fada a shagwabe da siririyar muryarta, murmushi ya kubce masa,hakan take yawan gaya masa duk sanda irin hakan ta faru

"Kiyi haquri dani babyn uncle,na jarabtu dake har bansan iyaka ba,am sorry....but I have something special for you,muje muyi wanka ki gani".

Tare sukayi wankan duk da tana dan zuzzulle masa,suka shirya ta gabatar masa da abinci yaci cikin nutsuwa da kwanciyar rai,best taste for ever a wajensa.

Bayan ya kammala ya jingina bayansa da kujera qafafunsa a miqe harde wajen guda,yatsun hannunsa ma a hade yana dubanta,kamar cin abincinta yadan ragu,tun ranar nan ya gani,amma kuma bai sakashi damuwa sosai ba,ganin bata canza ba,saima murjewa da jikinta yakeyi,hannu ya miqa mata alamun ta taho,saita maqale kafada

"Uncle wayo" ta fada tana dariya,bai shirya ba dole shima dariya ta kubce masa,a baya yakan jima baiyi dariya irin haka ba,amma a yanzu.widad ta maidata abu mai sauqi a wajensa idan yana tare da ita,dukka tsare gida shan kunun nan da kamewa sun koma office da sauran guraren aiki

"Kizl ki karba albishir din naki,ba wayo bane yanzu" matsawa jikin nasa tayi,ya kuwa riqeta gam yana fidda takaddun ya fara mata

Ads At the End of Article
Sidebar Ads

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads