Showing 213001 words to 216000 words out of 296907 words
Chapter 72 - A RUBUCE TAKE BOOK COMPLETE DOCUMENT
jiyo su mimi daga falo suna nemanta ta daka musu tsawa ta zaunar dasu waje daya,saida suka fara kukan yunwar da suka farka da ita sannan ta wuto kitchen din daukar musu abinci,sannan harta gama kintsa kitchen din,tana adana kayan cefanen da tun randa suka dawo hafsat din ta karbi girki abbas din yayosu masu yawan gaske,amma haka nan hafsat din ta barsu,komai saidai ta farka ta diba yadda ranta yakeso ta barshi a wajen,hatta da kayan miyansu haka ta wurgasj fridge babu gyara.
Zuciya tazoma hafsat din iya wuya,me yarinyar ke nufi,duk abinda ta fita a girki ta barshi ta sauya masa fasali daga yadda yake wai ita zata karba girki,har tazo fita ta dawo baya a zafafe
"Ke nifa banason iyayin banza da wofi,duk kin kama abubuwa kin sauya musu waje kamar kinfi kowa iyawa?" Tana ware tomatoes din da suka lalace ta daga kai ta dubeta,ido tadan zuba mata ba tare da tace komai ba
"Dake nake magana kika zuban ido,ba zaki zo gidana kice zaki isheni da kinibibi bafa" sai a sannan ta janye idanunta,qasa qasa tace
"Gidanmu dai"
"Qunquni kikemin?,me kika ce?" Ta tambayeta a zafafe
"Gidanmu dai" ta amsa mata kai tsaye tana kallon qwayar idanunta.
Wani abu ne ya saukar mata a kanta mai nauyi,mamaki yayi bala'in cikata,yanzu haka har tana da qwarin gwiwar maida mata magana haka kai tsaye?,lallai tayi sake,tayi kuma barci kwana biyu
"Zaizo me daure miki gindin ya gaya min idan shine ya gaya miki gidan nan kema gidanki ne" sai tayi gaba widad ta rakata da ido tana tabe baki,sai kuma ta gwada yadda tayi maganar sannan ta saki dariya,ita abinda ke bata mamaki,mummy hafsat din babba da ita,amma kullum aikinta tsaiwa taja magana tsakaninta da ita,taja tsaki tana sake tabe baki taci gaba da aikinta.
*H U G U M A*
*Arewabooks:Huguma*
*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
Part 02
Page 07
Wuni hafsat din tayi tana zirga zirga cikin gidan,bata falo bata kitchen,ita kuwa widad hakan bai hanata zagewa ta shiryama uncle abbas dinta abinci lafiyayye ba, hafsat din na zaune daga falo sanda qamshin ya fara mata sallama,ta baza qofofin hancinta, Zuciyarta na gaya mata ko daga babban sashen hajiya na gidan qamshin ke fitowa?,to amma data nutsu da kyau saita gane daga kitchen din gidansu ne,mamaki ya daskarar da ita a wajen,ta gaza daurewa ta nufi kitchen din kamar zata dauko wani abu.
Qamshin da tayi arba dashi yafi na falon,ta gefan ido take kallon yadda yarinyar keta aikin girkinta komai da komai tsaf,kai bakace girki takeyi ba,zarcewa tayi da dauko ruwa zuciyarta na wani irin tsalle daga qirjinta saboda zallar kishi,ta dauka ruwan ta juyo ta fito,saita ajeshi kawai gefanta ranta yana baci.
Tako ina yarinyar ta bata mata tsari,komai na yarinyar canzawa yakeyi ko tace tama canza totally,komai nata a yanzun na cikakkun matan aure ne,yaushe ta iya girki mai bada matsiyacin qamshi haka?,cikin wadanne watannin ne da bata banbancesu ba?.
Tana tsaka da wannan nunqufurcin da tunanin harta gama komai ta kuma fito daga kitchen din zuwa dakinta,a nan yaran suka ganta,suka ruga da saurinsu suka bita dakinta,a sannan bata da kuzarin hanawa,don tayi nisa cikin tunani da lalubowa kanta mafita.
Sosai yaran suka sake suna wasansu a dakin nata,ta fidda chocolates ta basu ta shiga wanka,ta fito tana baza qamshin shower gel dinta mai taushin qamshi,ta tsaya gaban madubi ta soma gyara kanta.
Tunda wuri yake qoqarin yaga ya kammala duka aikinsa ya dawo gida,duk wani motsi da zaiyi tana maqale cikin ransa,haka yayita kokawa da ayyuka don ya samu dawowa gida da wuri ya kasance da ita,amma hakan bai yiwu ba,sai yamma liqis sannan ya samu ya ture wasu ayyukan ya fito.
Sai daya tsaya ya siya dukka nau'in fruits din da yasan tana so,ha hadama yaran da kayan kwadayi sannan ya dauki hanyar gida,cikin ransa yana jin wani zallar nishadi da farinciki,wata walwala da baisan tushenta ba ita ke wanzuwa saman fuskarsa,lokaci lokaci yakan saki murmushi idan ta fado masa a rai,a haka har ya cimma gida,yadan dannan hon mai gadi ya dage masa qofar.
Sautin hon din motarsa daban yake a kunnuwan widad,ta lumshe ido dai dai sanda ta gama shirya kanta tana duban kanta da kanta cikin madubi
"Ga daddy nan fa ya dawo" tace da yaran tana dan dubansu,wani shauqi da qaguwar riskarsa tana ratsata,sai takejin kamar tayi shekara ne bata rab'i uncle din nata ba
"Yau sai na riga kowa zuwa taro daddy" mimi ta fada tana tattare kayanta,murmushi widad ta saki
"Zamuga waye zai riga wani" sai ta dauki turare ta sake feshe jikinta,sannan ta nufi qofa da sauri tana yiwa mimi gwalo,wannan ya sanyata zubda kayan ta miqe tana qyalqyala dariya
"Allah anty saina rigaki" ganin yarinyar ta biyota sai ta dan saka sassarfa tana mata dariya tayo gaba mimi din ta rufo mata baya.
Dai dai sannan hafsat da taji muryarsa daga waje suna gaisawa da ma'aikatan gidan ta fito falon,daga kujerar dake daura da bakin qofa ta zauna,ta yadda idan ga shigo idanuwanta zasu iya gane mata komai,uwa uba ma tasan babu wanda ya isa ya keta idanunta ya tsallaketa ya isa gareshi,ta baza dukka idanunta tana qarewa gyaran da aka yiwa falon zuciyarta kamar ta fito,lallai ba shakka sai taci uban yarinyar,sai tayi maganin dukka wannan kinibibin nata,taja qwafa tana karkada qafafunta.
Yana doso part din ransa yana sake yin fari,tun bai isa falon ba ya tabbatar ya koma saitinsa yadda yakeso,qamshi mai sanyi ke hudowa ta tsakanin labule da qofar yana fitowa har harabar gidan,ya buda qofar falon a nutse bakinsa dauke da sallama,hafsat din ta miqe tana dan sakin murmushi tare da amsa masa sallamar.
Taku biyu tayi zuwa gaba da niyyar amsar jakar hannunsa muryar widad hade data mimi ta karade falon.
Hankalinsa da nata gaba daya ya koma kansu,sanda suke rige rigen tarbarsa kowa yanason ya fara isa a tsakaninsu.
Sosai ta fusgi hankalinsa ta kuma tafi da dukkan nutsuwarsa,yadda take tahowa da sassarfa yaji ya masa kadan,ya fara takawa shima ha ruskesu,cikin sa'a ta riga mimi isa,ya bude hannunsa ta fada jikinsa tana fadi cikin dariya
"Oyoyo daddyn mimi" sosai yake kallon fuskarta da narkakkun idanunsa dake kanta,yasa hannu ya daga fuskar tata yana murmushi wanda yafi kama da dariyar farinciki
"Kinwa 'yarki wayo ko?"
"Dama na gaya mata,sai na rigata" saita jefawa mimi gwalo,yarinyar ta tabe baki kamar zata saki kuka,sai widad din ta miqa mata hannu tana sakin dariya
"Taho.....taho mimin dadd......" Sautin kuka shi ya maida hankalinsu duka ga hafsat,duk sai sukayi sak suna dubanta,har ga Allah abbas din ya manta da wanzuwarta a wajen gaba daya,widad tasan tana gurin amma batajin zata iya fasa abinda ta saba yiwa uncle din nata,uwa uba kuma dazu da taji yana cika baki da tinqaho akan uncle din,abun ya bata haushi amma saita qyale kawai,tana ji a ranta zuwa yanzu ko meye mommy hafsat din tayi mata ta daina qyaleta.
Kuka sosai takeyi,kafin abbas ya samu damar cewa wani abu ta juya da sauri ta nufi dakinta,batason yarinyar taga hawaye har haka a fuskarta saboda gudun raini.
Bayan wucewarta sai suka koma kallon kallon a tsakanin,a nutse ya zare widad daga jikinsa yana cewa
"Ina zuwa" yabi bayan hafsat din,tabe baki widad tayi ta dauki.jakarsa daya aje a wajen suka wuce dakinta ita da mimi,yarinyar nata murnar tare daddy ya tarbesu,saidai sama sama widad din ke amsawa,don dukka hankalinta nakan abbas din.
A nutse ya tura qofar dakin ya shiga,tana daga zaune bakin gadonta tana sharar qwalla,ya taka ya isa gabanta ya tsaya kawai kallonta hannayensa goye a qirjinsa
"Me akayi miki?" Ya jefa mata tambayar data sakata dago kai idanu jiqe da qwalla ta dubeshi,wani baqinciki ya tokare mata wuya,wato baisan me yayi ba?
"Bakasan me kayimin ba abban mimi?,ko yaushe baka da burin da ya wuce ka wulaqantani ka tozartani a gaban yarinyar nan,nice na fara welcoming dinka,amma tana fitowa ka kasa tarata ka koma kanta saboda tsabar cin fuska" iska ya furzar daga bakinsa yana gyara tsaiwarsa
"Yanzu wannan shine abinda yakai ayi masa kuka?" Shuru tayi bata amsa ba tana ci gaba da goge qwalla,baisan yadda takeji ba a yanzun,da bai tsaya kanta yana magana fada fada ba
"Dole sai kinyi haquri kin dauke kai,akwai banbancin shekaru a tsakaninku, infact ma ta riga ta saba ita kadai take rayuwa a gidan nan,wasu abubuwan sai a hankali zata dainasu" saiya fara takawa zai fita a dakin,ta bishi da kallon takaici,bataso ya shigo dakin ya fita haka da sauri,tana so ko yaya ne ta bata masa lokaci yadda zata dasa zargi a zuciyar yarinyar,tunda ta lura zuwa yanzu zaman kishi sosai takeso suyi,ta wuce wancan lokacin da zata dinga juya ta da raina mata wayo yadda taso.
Sunansa ta sake kira,cike da qosawa ya tsaya ya waiwayo,saita taso ta iso gabansa ta fada jikinsa ta fashe da kuka sosai,ba yadda ya iya haka yasa hannu ya tallafeta,rigimar hafsat din tayi yawa,matsaloli kala kala marasa tushe balle makama,qanqanin abu saita hurashi ya zama babba,har yau ta kasa gane girmanta balle ta riqeshi.
"Bansan me yasa kakemin haka ba,bakasan yadda nakeji a zuciyata ba" ta fada cikin kuka,tilas ya bata lokaci yana lallashinta tare da nusashe da ita cikin hikima,saidai abinda bai sani ba,duk abinda yake fada tana bi ta bayan kunnenta ne,burinta kawai ya jima a dakin.
Ta samu yadda takeso kuwa,don ya jima yana jan hankalinta kafin ya baro dakin bayan ya umarceta data sake gyara dakin, saboda tuni ya fara fita daga kamanninsa a kwanki uku kacal,baya jin kuma zai jura,ba kamar bauchi bane,a yanzun bashi da wani dakin daban da zaice zai kebance a cikinsa.
Bacci ya dauke mimi sai widad dake zaune gefan gadon,ta cika tayi fam,bata taba jin bacin rai irin wannan ba,shi yasa sam ko ganin mummy hafsat din batasonyi,tana jin wani zafi a zuciyarta duk sanda ta fahimci ko taga sun kebe,koda yayi sallama saita zumbura baki ta miqe ta nufi toilet kawai tana amsa masa ba tare daya tsaya a nan ba,qaramin murmushi ya saki bayan ya kalli agogo,sai a sannan ya fuskanci laifinsa,ya qarasa bakin gadon ya duqa ya dauki mimi ya maidata wajen hafsat sannan ya dawo dakin,ya jingina da mirror yana jiran fitowarta.
Kamar bata ganshi ba sanda ta fito daga bandakin,ya bita da kallo yana sake tantance kyan da tayi,wani abu na motsa masa a ransa game da ita,a strong desire,idanunsa na zagawa bisa jikinta,bomshort din jikinta yayi masifar fidda shape na qugunta,kaman ana fusgarsa haka yaji,ya isa gareta cikin sassarfa ya jawota jikinsa.
Abun yazo mata a bazata,wanann ya haifar da motsi a cikinta,abinda yayi matuqar firgitata tunda bata bata taba ji ba,a zabure ta saki ihu da ya sanya abbas riqeta da kyau yana lalubar abinda ya faru,hafsat kuma dake maqale a bakin qofa tana jiran jin taqaddamar da zata faru a tsakaninsu sanadin dadewarsa a dakinta ta sake gyara tsaiwarta da kyau,dadi yana cikata da jin ihun widad din,may be ta masa wani rashin kunyar ne yaji bazai iya jurewa 'yar cikinsa tayi masa haka ba ya kaiwa bakinta bugu.
"calm down.....menene?" Kasa amsa masa tayi sai hawaye da ya fara bin idanunta,ta kama hannunsa ta dora saman cikinta,dai dai sanda motsin ya ratsa tafin hannunsa ya aika saqo kwanyarsa,sai kuma ya tsaya cak.
Sosai ya shiga mamaki da tunani,ya dubeta cikin mamaki
"Yaushe ya fara irin wannan motsin?"
"Bai taba yi ba sai yau" ta fada tana sharbe hawaye,qaramin murmushi ya saki,saita saki baki tana kallonsa
"Karki damu,zan kira dr yanzu nayi mata bayani,zauna a nan ki nutsu,don't bother".
A nutse ya zaunar da ita sannan ya lalubi wayarsa ya fara neman number din dr maryam,daya daga cikin personal doctor dinsa.
*H U G U M A*
*Arewabooks:Huguma*
*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
Part 02
Page 08
Bai jima yana kira ba aka daga,suka gaisa cikin yanayi na sanin juna,sannan yayi mata bayanin dalilin kiran nata idanunsa akan widad da dukka ta sauya lokaci daya tayi wani laushi,idanunta cike da tsoro.
"Indai cikin yakai watannin da zaiyi motsi ai zaiyi dama,hakan kuma alamu ne na cikin lafiyayye ne,watansa nawa?" Kai ya girgiza
"Bansan watanninsa ba"
Dan murmushi ta saka mai sauti
"An gaisheku gaskiya,ina ganin gobe ka kawota asibitin sai ayi mata scanning da komai da komai,har EDD dinta sai mu gani,amma kace mata kada ta damu,babynta ya fara rayuwa sosai cikin qoshin lafiya ne" godiya yayi mata ya ajjiye wayar,ya saka hannayensa a aljihun uniform dinsa daya kasa cirewa tun shigowarsa gidan, idanunsa a kanta yana sakar masa murmushi,duk da cikin tsoro take amma hakan bai hanata basar dashi ba,zata miqe ya kamo hannunta da sauri ya sakata cikin jikinsa yana sansanarta kamar wata 'yar mage,yunqurin tureshi takeyi amma yaqi bata dama
"Ka koma wajen hafsa kawai" ido ya fidda yana dariya
"Yau kuma?,hafsa zalla?"
"Eh sunanta ne ai" ta fada tana dan murguda bakinta,har qasan zuciyarta tana jin kishi yana tsunkulinta,juyo da ita yayi suna fuskantar juna
"Yanzu dai na gane,kishi ne kikeyi,to ayimin afuwa" kafada ta maqale
"Ni ban haqura ba,saidai idan zaka kaini na siyo ice cream" kai ya girgiza bayan ya fidda ido
"So kike ki debarwa babyna sanyi?,bayan dr tace da alama lafiyayye ne?" Fuska ta kwabe ta langabar da wuya,yadda tayin tilas tasa yace
"Shikenan ki shirya,amma yau kawai" cikin farinciki ta amsa masa,tuni har ta manta komai ta fara shiryawa,shi kuma ya fara rage kayan jikinsa don ya shiga ya watsa ruwa,wanda already ta hada masa,yana shiryawa shima yana tsokanarta akan cikin,ita kuwa kunya takeji,saida tayi masa kamar zatayi kuka sannan ya qyaleta.
Sai da qafafunta suka gaji da tsaiwa bata sake jin komai ba,uwa uba da taga lokaci yana matsowa na fitarsa zuwa masallaci,dole taja jikinta tabar gurin tsakanin kokwanto da rashin tabbas na samuwar matsala a tsakaninsu,saita koma dakinta tabar dan space tana leqensa,har ya fito daga dakin tsaf dashi ya wuce masallaci yana baza qamshi,saita koma bakin gadon ta zube tana riqe da kanta,idan akwai abinda ta tsana a duniya shine taga walwala da zaman lafiya na gudana a tsakaninsu,dole ta sake kashewa tsinanniyar yarinyar kudi,dole ta sake aiki a kanta.
Sai da yasa yara suka kirata sau uku akan ta fito suci abincin dare sannan ta fito,dai dai lokacin da widad ta fito daga kitchen dauke da babban try data zuba.
Kofta(ire iren abincinsu ne na 'yan yemen da ake sarrafashi da nama).
Hafsat din na shirin zama sai taji qafafuwanta zuwa bayanta ya sage,da qyar ta danni zuciyarta ta zauna zuciyarta na wani irin tuquqi da suya,wannan zallar cin fuska ne kawai abbas din yaso yi mata,banda haka ta yaya zai kirata cin abinci jikin yarinyar da wadan nan kayan?,duk kuwa da cewa ta dora wata 'yar kyakkyawar farar riga mai budadden gaba,amma hakan baikai ga boye dukkanin adonta ba.
Da ido kawai take bin abincin,sunata walwalarsu tsakaninsu,abbas din yana tsokanar mimi widad na tare mata,ta gama serving kowa suka fara ci a nutse.
Har qasan zuciyarsa yakejin nutsuwa tana saukar masa,ba shakka lafiyayyen abinci mai daddadan dandano ma rahama ne a rayuwa,bashi ba,hatta mimi ta soma santin abincin,abun ya taru.ya yiwa.hafsat yawa,duk yadda qamshin abincin ya karade falon yake tsinkar da yawu amma sai taji ya fice mata aka,ta ture plate din ba tare da tace komai ba ta saba yusra a kafadarta,tana gyara zaninta daya tattare.
Sai da yakai lomar kufta din bakinsa sannan ya daga kai a nutse ya dubeta
"Ya haka?,ina zuwa?"
"Bazan zauna a nan ba tarbiyyar yara na ta lalace ba,don ba wajen zama bane,ta saka wasu kaya fingil fingil yarana suna zaune suna kallonta?,ke nawwara......mimi ku tashi muje" ta fada a tsawace,haushin yadda yaran ke wasoson abincin yana sake qureta
Bata fuska dukkaninsu sukayi,saboda sudai suna jin dadin abincin sosai
"Mommy ki zauna kici,da dadi wallahi" mimi ta fada fuska a narke,abunda ya sake hasala hafsat din ta kwaza mata tsawa,sai abbas din ya daga mata hannu
"Kinga ya isa,jeki abinki ke daya" yadda yayi maganar tayi mugun baqanta mata,nan da nan hawaye suka cika mata idanu,sai ta girgixa kai kawai tayi gaba da sauri hawayen nason subuce mata.
Ko tunata babu wanda ya sakeyi,abunda yayi masifar baqanta mata rai kenan,don tayi tsammanin zai biyo bayanta kamar dazun,saidai a maimakon haka ma sai tashin motarsa da taji,koda ta fito Parlor din wayam babu kowa,saita zauna anan hawaye na qwace mata,ya wankin hula yake shirin kaita dare?,saita miqe zumbur ta koma dakinta tana lalubar wayarta.