Showing 216001 words to 219000 words out of 296907 words
Chapter 73 - A RUBUCE TAKE BOOK COMPLETE DOCUMENT
Cikin kwanakin girkin widad din gaba daya hafsat ta tsangwami kanta,ta rasa nutsuwa bare sukuni,bata daki bata falo,komai widad din zata aiwatar idanuwanta suna kai,hakan ko kadan bai damu widad din ba,don zuwa yanzu ta fahimci meye ma'anar kishiya da abinda zamansu yake nufi ita da hafsat din,ko daya idanunta bai sanya widad din ta fasa duk abinda ta saba yi ba,hasalima yi tayi kamar bata gane ba,kamar dai har yau wautar quruciyan ne ke dibanta,abinda ke masifar hargitsa hafsat din,tana ganin kamar abbas din yana biyewa duk abinda takeso ne,yana kuma fifitata a kanta,wannan ya sanya ya ta sake cin alwashin wargatsa komai da lalata duk wani farinciki na widad din kota tsiya kota tsiya tsiya,sam ba zata gajiya ba.
Ta gaza shuru ta gaza haquri da yadda yarinyar ke gudanar da komai kamar wata babbar mace,cikin kwanakin komai na gidan tsaf yake a kammale,bata bari komai ya lalace ko a barshi wasarere,tun daga cikin kitchen zuwa parlor dinsu,duk kuwa da yadda hafsat din keta qoqarin ganin ta watsa komai,widad din taja yaran a jiki,ta koya musu yadda zasu bar waje da kyansa bai lalace ba,ta koya musu koda sweet suka sha inda zasu saka ledan,abun ya yiwa hafsat din ciwo,tayita jaraba tana fadan su yar amma qememe sai suqi,kada ma mimi taji labari,maganar anty widad awajenta kamar fadar Allah,hafsat tayi dukan tayi banbamin ta hanata zuwa duk inda take amma kamar turi,abun ya soma taruwa yana mata yawa,ta rasa inda zata taro,yaran ko abbas din?,dole ta zauna ta fidda kudi sosai ta turawa ummanta,tana hasashen samun mafita.
*******Yammaci ne lis,inda suke zaune cikin falon ita da yaran suna kallo,duk da cewa girkin hafsat dinne,amma ko alamun shirin dora girkin dare batayi ba,hasalima tana daki kwance abinta.
Hakan gaba daya ba damuwar widad bane,don dama da qyar take kaiwa labari da abincin hafsat,wani irin girki mara tsari mara fasali kuma,sam ko a ido bashi da wani qayatarwa bare kakai ga bakinta,Allah ya bata wani irin kurman ciki da har yanxu ya gaza nunawa a jikinta,saidai can cikin jikinta tana jin wasu sauye sauye da ita kanta tasan wani muhimman al'amari ne yake tunkarota,takan zauna tayita lissafin scanning din da dr tayi mata,wai cikinta watanni shida harda kwanaki,ta sha ganin ciki amma itadai ba haka taga ana ciki ba,tasha tsayawa gaban madubi amma bata ganin komai idan ba turoshi gaba tayi sosai ba,duk da yana motsa mata sosai amma yabi jikinta da kyau,ya qarawa breast dinta cika ne sosai,abinda ke matuqar daukar hankalin abbas kenan kamar zai zauce mata.
Waya ce a hannunta tana duba wasu sabbin recipe da Chief deeja Berver ta basu,tana yi tana murmushi,saboda yadda take fahimtar komai kamar a gabanta akeyi,har ya fada hasashen yaddaa gobe zata tashi kan gidan da nau'in kalolin sabbin girke girke.
Taji qarar bude qofad sarai,amma bata ko kalli bakin qofar ba,don tasan wacece,sai taci gaba da duba wayarta kawai ba tare da tako motsa ba.
Idanuwan hafsat din a zube fes akanta,ko wacce rana tana kwana ta tashi da mamakin yadda yarinyar ta gaza tabuwa,duk kuwa da kudin data kashe akanta,sai wata 'yar qaramar nasara data samu,wadda har yau wannan nasarar bata gamsar da ita ba,don bata ga wata alama ta shiga damuwa ko qunci daga wajen yarinyar ba sam,duk kuwa da cewa a yanzun tana iya juya wasu abubuwa na gidan,wanda a kwanaki ko watannin baya bata isa ta juyasu ba.
"Ke mimi..... nawwara,uban me kuke zaune kukeyi a nan?" Ta jefawa yaran tambaya tana zare idanu a kansu,cikin tsoron kada ta hanata zama mimi ke kallonta,yayin da nawwara tayi qirmisisi abinta
"Baba me gadi ne ya kawo kayan abba,yanata buga qofa shine na bude masa"
"Da kika bude masa kuma sai kika samu waje kika zauna?,ina kayan suke?"
"Suna dakin anty widad".
Wani abune yazo ya tsaya mata a rai,ta kalli widad da har yanzu bata kalleta ba koda sau daya,miskilancin yarinyar yana qona mata rai,tanaso tayi mata cin mutunci wasu lokutan,amma bata kulata ma bare ta bata dama
"Ke.....ki tashi ki debo kayan wankin abbansu ki kawomin nan" cak ta tsaya da danna wayar,saita daga kai a hankali karon farko ta kalleta,daga samanta cukurkudadden gashinta data daura dankwalin atamfa,zuwa jikinta dake sanye da rigar atamfar da wuyanta ya yima yawa,ta sauko ga fallen zaninta wani kalar atamfar daban.
Kamar zata fashe da dariya amma kuma bacin ran da take ciki ya zarta tayi dariyar,don cikin kwanakin kawaici kawai takewa hafsat din,ta dauka har yanzu wai widad din dai data sani ce?,cikin kwanakin gaba daya ta fito da wata sabuwar gadara cikin gidan,komai ta taba komai zata gyara ko zatayi amfani dashi sai ta tsoma mata baki,tana tutiyar cewa gidanta ne,yadda takeso haka za'a yi,yadda taga dama haka takeson ta gani.
Koda ranta ya baci bata taba tsaiwa tabi ta kanta ba,abu daya ta lura kamar abbas ya kasa dai daita hakan,abinda ita kuma takejin tazo maqura,ba zata lamunta ba itama.
"Dakina nima akwai wajen ajiya" amsar data bata kenan a taqaice taci gaba da danna wayarta,abinda ya harzuqa hafsat din kenan
"Ba shawara nake baki ba,umarni ne" sake sauke wayar tayi ya dubi idanunta da kyau,ta gaji da rainin hankalinta,kusan fiye da rabin komai da komai na abbas yana dakinta,tunda shine asalin dakinsa,amma ko sau daya bata taba nuna damuwa ko tayi qorafi ba,shine yanzu
"Ajiyar ce akace miki ni ban iya ba?,wai meye damuwarki?,naga dai kayan mijina ne ko?"
"Miji?,ni kike cewa mijinki ne?,turqashi!,wallahi saina nuna miki isata,saina nuna miki ni wacece,kuma wadan nan kayan saikin fiddosu" ta fada tana nunata da yatsa,kamar ma batasan me take ba, saita bawa banza ajiyarta taci gaba da abinda takeyi,ita abinda bata sani ba,tana jin zafinta fiye da yadda ita takejin nata,tana kishin uncle abbas fiye da yadda ita take kishin nasa,saidai ita an gaya mata,matsayinsu daya hasalima gaba take da ita,dole tayi respecting nata,amma ko daya bataga alamun daukar girma a wajenta ba.
Banbami tahau yi tana sauka akan yaran,ta tattarasu ta wuce kitchen dasu,widad ta tabe baki taci gaba da abinda takeyi,saidai can qasan ranta zuciyarta tana mata zugi,ta gaji da rainin hankali irin na hafsat din,ta kuma daina daga mata qafa.
Ko daga kitchen din tana jiyo masifarta da kuma mitarta,ta kasa zaune ta kasa tsaye,daga bisani ta kashe girkin data dora ta dauki yusra suka fito
"Sai maganinki,bazan zauna qaramar yarinya dake kina maidamin magana ba kamar sa'arki" abinda ta fada kenan tana ficewa daga falon.
Gyara kwanciyarta ma tayi tana maida hankalinta ga kallo,tsahon mintuna kusan goma sha biyar saiga maari matar me gadinsu tayi sallama,widad ta miqe ta zauna cikin fara'a da yake mutuniyarta ce sosai,suka gaisa sannan tace
"Hajiya ce tace ayi kiranki" mamaki sosai ya kama widad din,hajiya kuma?,irin hakan bata taba hadasu ba illa iyaka gaisuwa
"Bari na fito muje tare" ta fada tana miqewa tayi daki,maari tabi bayanta da kallo cikin tausayawa yarinyar,Allah ya hadata da BAK'AR KISHIYA.
Tana sallama ta hangi hafsat daga zaune tana bawa yusra nono,a nutse widad din ta qarasa tana gidata,sama sama ta amsa mata fuska a hade,tun daga nan sai itama widad din ta kama kanta.
"Kinsan alaqata da babanki?" Ta fada kai tsaye,saita dubeta sannan ta girgiza kai,tadai san suna da alaqa amma batasan wacce iri bace,kwanaki da ummu tazo mata suna yawan zama suna hira,hakanan itama tana aiko mata da abinci kullum
"Kamar qanwa nake a wajen babanki,wannan dalilin ya sanya nayi kiranki,mummyn mimi ta kawo qararki,ki shiga taitayinki,banason rashin kunya da diban albarka,kizo ki sameta da mijinta da komai nata amma ki dinga qoqarin nuna kinfi kowa iyawa?,ki dinga yi mata isa da gida?" Wani abu ne ya taso mata,taji sam ba zata iya daukan zancan ba,don haka ta runtse idanu tayi nesa da tunaninta na tsahon wasu mintuna kafin daga bisani ta miqe
"Ai bansan gidanta bane ba,amma yanzu na sani" abinda tace kenan ta soma takawa tana yin gaba,duk sai suka bita da ido,nauyi da kunyar yadda yarinyar tayi yana kama hajiya,yayin da hafsat ranta ya baci,ta kawo qarar wajenta ne saboda taji akwai alaqa a tsakaninsu,amma kuma haqarta bata cimma ruwa ba.
Ranta yanatason ya baci amma tana qoqarin dannewa,tayi nasarar korar wannan,taci gaba da sabgoginta,bata ce ga sanda hafaat ta dawo ba,ta daiji motsinta cikin kitchen da kuma qananun mitocinta qasa qasa.
Kwance tayi a dakinta har aka kira magrib,ta shiga toilet dinta ta sake wanka sannan tayi alwalar sallar magariba,wanna din sunnarta ne,ta riga ta saba koda bata da girki sai tayi wankan nan ta canza kaya,abinda hafsat din tayita son ganin ta hanashi faruwa,a cewarta ba ranar girkinta bane,don me zata dinga fitowa tana mata kwarkwasa da turare da kwalliya,saidai bata samu wannan nasarar ba.
Ana idar da sallah taji alamun shigowar abbas din,duk sanda ya shigo gidan koda motarsa na anesa,ko motar office ce ta ajjiyeshi daga nesa sai taji hakan cikin jikinta,har zuwa sanda ya shigo sassan nasu, tanajin muryar su mimi suna masa oyoyo,taso tashi amma sai taji duka bata da interest akan hakan,kuma ma tasan bazai wuce minti uku bai qaraso dakinta ya dubata ba,don haka taci gaba da zama tana qarasa addu'o'inta da bata rabo dasu.
Tun tana zuba ido harta soma qosawa,shuru bataji sake jin motsinsa ba,ta kalli agogo minti kusan ashirin kenan,tana sauke ido yayi dai dai da tashin muryarsa daga parlor yana kiran sunanta,duk sai taji banbarakwai,abinda bata saba dashi ba,amma kuma yau da gobe sai Allah,sai ta miqe a nutse tana gyara hijabinta sanan ta nufi qofa,gefe daya tana jin yadda cikinta yake qara tauri,wanda ita daya keji da ganin hakan.
*H U G U M A*
*Arewabooks:Huguma*
*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
Part 02
Page 09
Yana zaune saman kujera sanye da uniform din nan nasa dake qara masa kyau da kuma kwarjini,ko boots din qafarsa baikai ga cirewa ba,hafsat na tsaye daga gefansa,hannayenta goye a qirjinta,fushi ne kwance saman fuskarta.
Idanunshi a kanta,wani abu daya kasa tantance meye yana tsinkulin zuciyarsa,mabanbantan abubuwa guda biyu daketa faman gogayya da juna,har ta iso ta zauna gefan kujerar dake daura dashi tana masa sannu da zuwa.
"Me ya hadaki da hafsat.....har kikayi mata rashin kunya?" Maganar tazo mata a bazata,mamaki ya kamata,ta dubi hafsat din suka hada ido,sai hafsat din ta aike mata da saqon harara,ta daure ta shanye sanann tace
"Ni bansan yaushe nayi mata rashin kunya ba"
"Kina nufin bakisan maganar kayan da kika kwashe ba?" Ta tambayeta kamar wata diyar cikinta,sai abbas din ya daga mata hannu
"Ya isa.....me yasa kika kwashe kaya da aka dawo dasu daga laundry?" Cak ta tsaya ta zuba masa idanu,mamaki yana kasheta,duk yadda taso hana taruwar qwalla a idanunta amma ta gaza,saita gyada kai tana hadiye wani abu mai tauri daya tsaya mata,cikin rawar murya ta fara masa bayani
"Baba mai gadi ne ya kawo su,tana.bacci yace a kwashe maka kada yara su tattaka,don ma debe shine nayi laifi?,ina cewa kusan kaso uku cikin hudu na kayanka suna dakinta a wajenta,na taba magana?" Sosai ta taba zuciyarsa yadda hawaye ke sauka saman fuskarta,tana kuma maganar muryarta tana rawa cikin sautin kuka,yanason yace ta tashi taje,tayi dai dai amma kuma kamar ana ingiza zuciyarsa,kamar kuma ana hura masa bacin rai haka yakeji.
"Tashi kije ki debosu!" Yadan fada a kausashe,idanunta ta sanya cikin nasa mamaki yana sake daskarar da ita,totally uncle abbas din canzawa yakeyi cikin kwanakin,ba yau ya fara ba amma na yau yafi qona mata rai da tsaya mata a rai,ba yau ya fara ba,cikin kwanakin ko meye hafsat din tayi gaskiya yake bata,yana kuma qoqarin goyuwa da bayanta,sai ta miqe tsam cikin matsanancin bacin rai,ta dauke idanunta daga kansa ta maida ga hafsat,sai taga tuni yanayin fuskarta ya sauya zuwa madaukakin farinciki.
Janye idanunta tayi daga kan fuskokinsu gaba daya,ta kuma juya da sauri ta nufi dakinta, abbas ya rakata da idanu yana jin kamar ya bita amma kuma wata zuciyar na gaya masa yayi dai dai,sai yaci gaba da kallon qofar da kuma tsammanin fitowarta.
Cikin bacin rai ta fara tattara dukka wani abu da tasan nashi ne cikin daki,bata bar komai ba koda kuwa agogo ne,tana hade kayan hawaye na fita a idanunta,ta tsani rashin gaskiya,ta tsani a bata rashin gaskiya a rayuwar ta,ta tsani batayi abu ba ace tayi,tana jin kamar ta mutu idan akayi mata haka.
Debo kayan ta fara yi hannu bibbiyu,ba ruwa ta da wadanda suke zubewa ta riqosu zuwa falon,tana zuwa batayi wata wata ba ta watsar dasu a wajen ta juya da sauri taci gaba da debo sauran tana zubarwa a wajen,ran hafsat ya sosu sosai,wanne irin raini ne wannan?,ta tsammaci zaice wani abu,sai taga bai ko motsa ba yana kallonta ne kawai,yana karantar zallar fushin dake fuskarta,wanda bai taba ganin irinsa ba a tattare da ita ba
"Wai baka ganin abinda yarinyar nan takeyi?,kaga fa yadda take watso mana kaya?" Maganartata yayi da gama kwaso kayan,ta juya abinta da nufin komawa dakinta
"Widad" ya kirata a tausashe,bata ko waiwayo ba bare ta saurareshi,don kuka takeyi sosai ta wuce daki abinta.
Cikin qarfin ikon Allah ya miqe da wani irin zafin nama,zuciyarsa yaji kamar zata fashe da kukan da widad din keyi,ya tuna meye a jikinta,ta yaya zai barta tana irin wannan kukan?,sai ya nufi dakin da wani irin sauri wanda yasa hafsat ta zaci zuwa zaiyi yayi maganinta,ya dauki mataki akan abinda tayin yanzu,don haka ta saki wata qaramar dariya cikin nishadi da jin dadi,ta tako cikin rashin damuwa ta fara tsince kayan tana dibansu zuwa dakinta,sai a sanann ta lura da mimi dake sharar qwalla
"Ubanki kike a wajen?,wato an saka uwarki kuka shine kikazo kika rabe a nan kina naki kukan,zaki tashi ki wuce ciki ko sai nayi ball dake?" Ba shiri yarinyar ta zame ta wuce daki tana tura baki gaba hadi da ci gaba da goge qwalla.
Rub da ciki takeso tayi kukanta yadda takeso ko zata rage zugi da radadin da zuciyarta ke mata,amma tudun da takeji a cikinta ya hana,dole sai saman pillow ta dora fuskarta tana sakin kuka sosai.
Jiki a matuqar sanyaye ya qarasa shigowa dakin,sai ya kasa qarasowa ya tsaya daga bakin qofa yana kallonta,shi kansa baisan me yake damunsa ba,baisan me yasa yake wasu abubuwan ba,duk da abinda yakeyi din bata taba nuna damuwarta ba,koda ta nuna mintuna kadan take sakin fuskarta kamar ba'a yi ba,sai ayau data nuna fushinta har haka.
A nutse ya qaraso ya zauna gefanta,tunda ya buda mata qofar daki tana jinsa amma bata nuna tasan da shigowarsa bama,hannu yasa a tausashe ya zare pillow din ya maye gurbinsa da tattausan tafin hannunsa,sai tayi saurin kawar da fuskarta daga wajen kamar ya dora mata wuta,yasan halin kayarsa,ta iya rigima a duk sanda taso ko aka tabota,don haka yayi amfani da dukka qarfinsa ya azata saman jikinsa.
Dukka qarfinta ta sanya ta zame a jikinsa,bai gaji ba ya sake maidota yana kiran sunanta tare da qoqarin son su hada idanu amma taqi bashi wannan damar.
Kin zama tayi bare ta saurareshi ba,haka ya gaji da son yin magana da ita ya haqura ya fice yana sauke ajiyar zuciya,ransa gaba daya a jagule babu dadi.
Da kanta ta lallashi kanta,saidai a ranar ta yiwa kanta hukunci qauracewa abbas din da dukka abinda ya shafi hafsat dama cikin gidan,ba zata iya gani ba bazata iya jura ba,duk jarumtar ta abun ya taba ranta,tana iya bakin qoqarin bashi farinciki da son ganin walwala da nutsuwarsa.....gefe guda yana bawa hafsat go ahead tayi duk abinda yake shine dai dai,yana kuma mara mata baya,ta yaya ita tata zuciyar zata samu nutsuwar bashi nutsuwa?.
Washegari ranar girkinta ne,tun safe tana kwance a dakinta wanda tun dare ta saka muqulli ta rufe abinta,tana da abubuwan ciye ciye da yawa a dakinta da bata rabo dasu,don a lokacin abbas da ya shafe babin fita da iyalinsa zuwa wasu guraren shaqatawa a baya,a yanzu widad din ta dawo masa da wannan dabi'a tasa,ko rana daya hafsat din bata taba yunqurin binsu ba,sai mugun haushi da takaicin da take fama dashi,har zuwa sanda zasu dawo cikin gidan,takan ce ita tafi qarfin zuwa nan wajen.
Zamu iya cewa borin kunya ne takeyi,don tun sand yake marmarin kaita take watsa masa qasa a ido,take nuna tafi qaunar ya bata abinda za'a kashe a wajen ta adana,har abun ya fita a kansa,ko ssnda ta haifi su mimi yana son kaisu amma bai samu wannan qwarin gwiwa daga wajenta ba,don haka sai a jima bai fita da yaran ba sai sanda ya samu hutu mai tsaho,gaba daya ita din opposition na rayuwarsa ne totally,bata kuma taba sawa a ranta ta sauya wani tsari yanayi hali ko dabi'a tata saboda shi ba,saboda a samu dai daito da zama me dorewa.