Showing 36001 words to 39000 words out of 296907 words
Chapter 13 - A RUBUCE TAKE BOOK COMPLETE DOCUMENT
widad"
"To mu zauna hajiya?" Ta tambayeta cike da quruciya,murmushi hajiyan ta sake,ta waiwaya tana duban hajjaa dai dai sanda ta sallame daga sallar
"nikam da zaku bani widad da nayi murna na kuma gode muku" dariya hajjaa ta saki,ba tare daga fahimci abinda hajiya ke nufi ba,ta zare hijabinta tana cewa
"Widad hajiya?,wannan mara sabo din da rashin sakewa da mutane?,idan muka baki widad ai mun gayyatowa kanmu ummu,takanas zata tahi bauchi ta dauke kayarta,dama 'yar aro ce" kai hajiya ta kada
"Ni ba aro nakeso a bani ita ba,inaso a bani ita na baiwa abbas dina,kinga shikenan ta zama diyata babu zancan aro kuma" a yadda hajiyan tayi maganar yasa hajjaa maido hankalinta jikinta,ta kalli fuskar hajiyan da kyau,sai taga gaskiya baro baro kwance saman fuskarta,kalamanta sunyi kama da kalaman da suke fita daga can qasan zuciya,babu alamun wasa ko kakaci a ciki.
Daurewa hajjaa tayi tayi murmushi,don zancan gaba daya sanyayar mata da jiki yayi,abbas hajiya ke magana,dan gayun matashin nan, mahaukacin damarar nan da kwanan nan aka qara masa rank?,abbas din dake da mata da yara biyu?,,abbas fa
"To ai hajiya idan kinaso sai a bakin ai"
"So kai,saboda inaso dinne ma na sako zancan,amma dai zan sake tuntubarki,ki shaidawa muhsin din"
"To hajiya ba matsala" ta fada tana murmushi,zuciyarta na bata da wasa hajiyan tayi maganar,saita maida dubanta ga widad wadda tuni ta matsa gaba suna magana da nujood,don haka batasan ma wainar da ake toyawa ba.
Sanda suka tashi tafiyar kayan ciye ciye ta hada musu da yawa a leda,hajiyan 'yar gatan tsohuwa ce,babu abinda ta rasa a gidanta,wannan ya sanya babu abinda zakaje baka samu ba a gidan.
*BAYAN SATI DAYA*
Tsaye take hadiyya take cikin kitchen din tana hadawa uncle muhsin abincinsa,gefe daya yaranne gaba daya sun cika mata kunne,hayaniya suketa yi suna tsokanar widad,wadda gaba daya cikin satin ta fara birkice musu,tunda tayi waya da ummun ta gaba daya hankalinta ya karkata zuwa komawa gida
"Ya isa don Allah kuyi mana shuru" waiwaya tayi ga widad
"Zan gayawa uncle dinki kada ki damu,zai kaiki kiga ummun da kansa indai free yake bashi da aiki" kai ta gyada tana danjin relief a ranta,a kwanakin nan ji take kamar tayi tsuntsuwa ta ganta gaban ummun,bata taba zaton akwai abinda zai kawo rabuwarsu haka na tsahon lokaci ba,tama yi qoqari,don ko kwana guda batayi gidan kowa indai ba tare da ita ba,sai gashi yau ta doshi wata kusan guda cur.
Sanda hajjaa ta isa yana amsa waya ne,saita zuba masa komai ta kuma jera a gabansa,tana niyyar tashi don ta koma kitchen din ta sallami yaran yayi mata nuni da hannu kan ta zauna,saita koma ta zauna din,ya kammala wayarsa ya kashe yana dubanta
"Wanne saqo hajiyan abbas ya baki baki gayamin ba?" Cikin mamaki don ita sam ta ajjiye wannan batun tace
"Saqo kuma?,anya kuwa?"
"Gashi yanzun ta kirani tana tambayata,tace idan kin kammala gayamin din zata sake kirana" sai a sannan hankalinta yakai,tadan dafe kanta tana fadin
"Ya salam,wallahi sai da kazo da maganar na tuna" kansa ya girgiza
"Bai kuma.kamata ba,hajiya kamar uwa take a wajenmu gaba daya"
"Ba haka bane abba,zancan ne naji kamar zolaya take yi,hankali na bai kama ba" ta fada tana kada kai
"Wanne irin zance ne haka?" Uncle muhsin da ya fara cin abincinsa ya fada yana kallonta
"Widad takeso a basu ta baiwa abbas aurenta"
*_AREWABOOKS: Huguma_*
*RUMBUN K'AYA*π₯
*DAUDAR GORA*π₯
*IDON NERA*π₯
*A RUBUCE TAKE*π₯
*KI KULANI*π₯
Littafi daya---400
Biyu---600
Uku----800
Hudu-----1k
Biyar din duka----1200
*ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN KI ANTAYA JIRGIN FITON ZAFAFA BIYAR*π₯π₯π₯π₯π₯
0022419171
Maryam sani
Access bank.
Shaidar biya tananππ»
09033181070
*MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN*
09166221261
π³πͺπ³πͺπ³πͺπ³πͺπ³πͺπ³πͺπ³πͺ
*Ina yan uwa 'yan nijer?*
*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*
+227 90 16 59 91
Littafi daya---450CFA
biyu---650CFA
uku----850CFA
hudu----1050 CFA
Biyar----1250CFA
*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*
*SIYAN NA GARI KUMA MAIDA KUDI GIDA!*
*Thanks for choosing us*π₯
*H U G U M A*
*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
*Arewabooks:huguma*
Page 18
Shi kansa zancan yazo masa a bazata,sai ya ajjiye spoon din hannunsa yana duban hajjaa
"Abbas....abbas nawa fa" kai ta gyada
"Eh shi" kamar me jiran hajjaa ta tabbatar masa da batun sai ga kiran hajiya ya sake shigowa wayarsa,ya kalli wayar na wasu sakanni zuciyarsa na gaya masa da gaske hajiyan take,tunda har ta kasa sakat saita samu tabbacin isar saqon kunnensa,ya dauka wayar a nutse ya kara a kunnensa
"Ina fata saqon nawa ya riskeka?" Kai ya gyada kamar tana gabansa
"Eh hajiya,yanzun take isarmin dashi"
"To alhamdulillah" ta fadi tana sauraren ji daga gareshi
"Amma hajiya....wani hanzari ba gudu ba,kina ganin babu matsala daga wajen shi abbas din?" Yayi tambayar saboda sanin halin abokin nasa,sun jima a tare tun zuwanshi bauchi,duk da cewa ya girmewa abbas din,amma suna tare dashi,don itama dama abota ba sai da sa'anka ba,takan iya zuwa ta kowacce fuska,Itama hajiyan kai ta kada kamar yana wajen
"Bani da haufi akan abbas ko kadan,bamu ita din shine mai wuyar" sosai hajiyan ta aza masa nauyin da bazai iya kufcewa ba,tana masa kallon mazaunin uba a wajen widad,tasan kuma ya isa ya zartar da hukunci a kanta shi yasa ta nemeshi kai tsaye,uwa uba kuma abbas din wani irin mutum ne mai kima da daraja a wajensa,yafi kowa sanin irin qaunar da yakema mahaifiyarsa,kamar yadda ta dauki shi shima a mazaunin d'a,bai kyautu ya dubi tsabar qwayar idanunta yace mata bazasu bada auren widad ga abbas din da yana sahun farko farko na wadanda zasu bada shaidar kyawun hali da nagartarsa,bayan gajeran nazarin da bai wuce shurun sauraren hajiyar ba ya amsa mata
"Hajiya ai abbas nawa ne,babu damuwa,an bashi widad,zan kuma sanar da can gida in sha Allah". Irin addu'ar da yaji hajiyan tana kwararo masa sai da abin ya bashi mamaki,wanne irin so take mata haka?,lallai da bai amsa ba Allah ne kadai yasan rashin dadin da zataji,duk da ba zata nuna masa ba.
Wayar ya ajjiye gefe,ya daga kai yana duban hajjaa data tsareshi da idanu,kafin yace komai ta rigashi
"Abbaa,aure fa kake bayarwa,auren widad din da ummu ta baka aronta?,ba tare da sahalewar ummu ko yaaya mahmud ba?" Dan gajeran murmushi ya saki
"Yadda zan bada auren nujood kai tsaye babu haufi haka zan bada na widad,ina da wannan license din"
"Amma kana ganin aurenta da abbas yayi dai dai?" Ta sake tambayarsa cikin jin d'ar d'ar da fargaba
"Yana da wani aibune da musulunci yace idan namiji yana dashi bai cancanci ku bashi auren diyarku ba?" Kai ta girgiza da sauri
"Ko kadan,abbas nagartaccen mutum ne mai kyawawan dabi'u abun kwaikwayo,amma abba kada fa ka manta yana da mata,sannan matarsa din nan ko kwanaki na danji ana kuka da ita,bata da kirki abba,zamansu da widad mai qananun shekaru a mazaunin kishiya zai yiwu?"
"Duka ba wannan bane abun dubawar ba,tunda ba ita zata zauna da ita ba,indai ya cancanta magana ta qare" sai ya dauki spoon dinsa yaci gaba da cin abincinsa,dama tasan haka zaya fada,su maza nasu hangen daban dana mata,gaba daya hanakalin hajjan bai kwanta ba,bawai don abbas bai cancanta bane,aah,tana duba wani abu na dabanne,don haka ta gaza barin maganar
"Gaskiya abba bazan tayaka gayawa ummu wannan maganar ba wallahi,kada ka sani a ciki" dariya yadan saki
"Matsoraciya,yo waye ya sanya dama dake?"
"Amma zataga a gidana aka shirya fa,gashi widad dinma ta matsu tana son zuwa gida,ya za'a yi kenan?"
"Dama ina tunanin next week qarshensa taje taga ummu din,saboda ita kanta ummu kwanan nan maganar na dawo mata da yarinya taketa yi" shuru ya ratsa tsakaninsu,har uncle muhsin din ya fuskanci kamar ta shiga damuwa ne,don haka yayi gyaran murya
"Ni banji komai game da haka ba hadiyya,abbas yana da nagartar da ko nujood yace yana so zan bashi,zai riqe mana widad da amana, sa'annan kuma ina da tabbaci hundred percent karatunta bazai yanke ba,zataci gaba da karatu har zuwa inda takeso,so kinga babu wannan haufin"
"Gaskiya kam" ta amsa masa tana dan jin nutsuwa kadan,to amma batun zama da kishiya tasan ba abu bane mai sauqi,koda ga babbar macace bare yarinya irin widad,GOYON KAKA.
**********
Tunda hajiya ta samu tabbacin samun widad daga wajen uncle muhsin wata nutsuwa da farinciki ta dinga saukar mata,haka kawai ta dinga jin nutsuwa da gamsuwa da al'amarin,ta dinga ji kamar ta daga waya tace yazo tana son ganinsa,to amma tasan zuwa qarshen wata zai zo ganinta,babu buqatar ta daga masa hankali ta sanyashi biyo hanya,sai tayi amfani da wannan damar ta yawaita addu'a kan Allah ya sanya dukkan alkhairinsa akan lamarin,yasa ayi a sa'a,ya kade dukkan fitina.
************
Dukka shirin da yakeyi tana zaune gefan gado tana kallonsa,a yanzun da zai tafi bauchi tana jin inama yace ta shirya ta bishi,zaman garin ya gama kai mata ko ina,daurewa kawai take tana cijewa,ita kam duk inda zama zai kaita indai ba cikin garinta ba bataso.
Bugu da qari taga sabon key din mota garin bincike bincikenta,tana sake dauriya akan dauriya ne cike da fatan wannan motar ta zamana tata ce kamar yadda anty ummee data baiwa labari tayi mata hasashe.
Tsaf ya shirya cikin yadin kufta,wanda yayi matuqar masa kyau,ya fidda kwarjininsa da kuma kyan zubi da Allah ya bashi,saita sake karkata kai tana qare masa kallo,sau tari ita kanta takan gayawa kanta tabbas abbas wani rabo ne nata da Allah ya tsaga mata sai ta sameshi,amma ita kanta idan ta tsaya ta kalli kanta tana gano tarjn banbance banbance tsakaninta dashi,shi yasa take qara matsa qaimi wajen kishinsa,saboda tana tsoro.....tana tsoron kada idanun wata ya fada kansa,ta kuma sani wasu 'yammatan indai suka baza komarsu sai sun samu,bata fiya damuwa dashi ba,tasan sam mata basu a lissafinsa,amma shi din yana cikin lissafin gomayyar mata da suke kwana su kuma tashi da soyayyarsa,koda cikin danginsa kuwa tana da wannan information din akansa.
Hure mata idanu yayi da sassanyar iskar bakinsa,abinda ya sanyata ja da baya da sauri,sai kuma ta saki murmushi
"Har ka bani tsoro" ta fada tana dan harararsa
"Ni kika bawa tsoro,wannan kallon kamar zaki cinyeni?" Murmushi ta saki
"Da da hali cinyekan zanyi,don banason kowacce mace ta kalleka kota rabeka,ni kaina bansan adadin kishinka da nake ba" daga kai yayi ya kalleta daga daura agogon da yakeyi,har launin fuskarta ya sauya,sai ya maida kai yaci gaba da daura agogonsa ba tare da yace da ita komai ba.
Ya rasa wanne irin dan banzan kishi take dashi,wanda kullum baya raguwa saima daduwa da yakeyi,abun takaicin har yau batasan yadda zata tsare masa komai ba,inda yadda take kishinsa haka ta tsaya masa wajen komai da lallai ya gama yin sa'a.
Ganin bai bata amsa ba tasan bazai ce komai ba,don haka ta sauya akalar maganarta
"Nidai da zaka barni Allah wannan watan zan bika,kamar na shekara banje gida ba haka nakeji"
"Sai next month kamar yadda nace" ranta tadan bata kadan,har ya gama shirinsa ya fito bata sake magana ba.
"Rakiyar ta isa daga nan" ya fada yana dakatar da ita daga qofar falon,saboda akwai driver daga waje da zasuyi tafiyar tare,mutum ne shi mai tsananin kishin iyalinsa,yakai bakinsa saman goshinta yayi kissing dinsa yana fadin
"Sai na dawo,ki kula da gida da yaran"
"A dawo lafiya" ta fada a taqaice tana dubansa har ya fice,tana tsaye ta window tana leqensa har motarsu ta fice,taja da baya ta zauna saman kujera tana jan tsaki
"Babu biki ba suna ba barka,an takure a baqon muhalli" ta sake fadi a fili,sai kuma ta miqe ta nufi dakinsa,ta buda ta shiga ta isa inda taga key din motar,ta jawo da zummar sake duba motar wacce ce?.
Wayam taga wajen babu muqullin,ta shiga birkitawa kamar wadda ta bashi ajiya,saidai babu shi ba alamarsa,da alamu ya dauka kenan,to amma me zaiyi dashi?,ta tambayi kanta tana zurfafa tunaninta,to ba tata bace kenan?,amma kuma motar da suka fita cikinta ai tasan motar,ba sabuwa bace,gaba daya sai ranta ya baci,ta jawo waya kamar zata kirashi ta tambayeshi sai wata zuciyar ta hanata,ta shawarceta ta bari ya isa gida tukunna.
*_RUMBUN K'AYA_*
*_IDON NERA_*
*_DAUDAR GORA_*
*_KI KULANI_*
*_A RUBUCE TAKE_*
Littafi daya---400
Biyu---600
Uku----800
Hudu-----1k
Biyar din duka----1200
*ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN KI ANTAYA JIRGIN FITON ZAFAFA BIYAR*π₯π₯π₯π₯π₯
0022419171
Maryam sani
Access bank.
Shaidar biya tananππ»
09033181070
*MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN*
09166221261
π³πͺπ³πͺπ³πͺπ³πͺπ³πͺπ³πͺπ³πͺ
*Ina yan uwa 'yan nijer?*
*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*
+227 90 16 59 91
Littafi daya---450CFA
biyu---650CFA
uku----850CFA
hudu----1050 CFA
Biyar----1250CFA
*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*
*SIYAN NA GARI KUMA MAIDA KUDI GIDA!*
*Thanks for choosing us*π₯
*H U G U M A*
*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
*Arewabooks: Huguma*
Page 19
Kafin ya iso tuni hajiyan ta sanya an tanadar masa abincin da yafiso har kala biyu,irin abincin da tasan zaiyi wuya ya samu a gidansa,duk da qaunar da yake masa,ta kuma hada masa lemo shima kala biyu,zobo da kuma ginger drink da aka dan matsa lemon tsami kadan a ciki qamshinsa ya fito.
Da yake tun karfe tara na safiya ya taso,ana azahar yana shiga layinsu,jakarsa kawai ya bayar aka shiga dasu shi da drivern nashi da yake usulmi ne suka wuce masallaci.
Ana idar da sallah yace masa zai juya ya koma kaduna,yasan akwai aikin da ya baro,saboda haka bai matsashi ba,yadai karba abincin wajen hajiyar ya hadashi dashi,yace yaci a mota,ya kuma fidda kudi masu dan nauyi yayi masa ihsani,wannan yana daya daga cikin abinda yasa abbas din ke samun biyayya da qauna gami da daukaka a wajen aikinsu,duk da biyayya dole ce a tsarin aikunsu,amma suna masa soyayya ne ta har cikin ransu saboda kyawawan dabi'unsa.
Cikin nutsuwa ya shiga gidan nasu,yana jin farincikin ganin hajiyar tasa,jtama tana falo a zaune tana ta dakon shigowarsa,ta amsa sallamarsa ya sanyo kai falon fuskokinsu dukka dauke da murmushi.
Kamar kullum ya duqa a qabanta ya gaidata,ta amsa masa cikin kulawa addu'a gami da tambayar lafiyarsa data iyalinsa,ya tabbatar mata da komai lafiya lau,ya kuma isar mata da saqon gaisuwa daga hafsa din,wanda a zahiri bata samu hakan ba,shi ya qirqira abinsa saboda sama mata soyayya da kuma kare martabarta a idanun mahaifiyarsa.
Da kanta tayi serving nashi,yana cin abincin suna hira,wanda kusan abubuwane da suka dan faffaru da baya nan,ciki harda ciwon da diyar babbar yayarsu tayi
"Zanyi qoqari na shiga in sha Allah"
"Ya kamata,don ka kwana biyu bakaje mata ba,tana ta min qorafi rannan"
"In sha Allah".
Sai da aka kira la'asar sannan ya fita a falon,yace ma hajiyan zaije wajen Suraj,amma bayan magariba zai dawo
"To Allah ya tsare,akwai maganar dama da nakeson nayi dakai"
"To bari na zauna mu gama sai na wuce"
"A'ah,jeka abunka,idan ka dawo mayi maganar,Allah ya tsare".
Tsahon lokaci suka dauka shi da suraj din,saboda kwana biyu basu hadu ba,yanayin ayyuka da canjin muqamai da abbas din ke samu a kufi a kufi,anan suraj din ya samu damar masa qorafin
"Naji mamaki sanda naji ka ajjiye appointment dinka,dama cefa da 'yan sanda da yawa suke jira" kansa ya shafo kadan yana duban suraj din
"Nafi nutsuwa da hakanne suraj"
"To kuma gashi sun biyoka da asp ba"
"Gwara wannan kam,qarin matsayi ne,a tayamu da addu'a Allah ya bamu wuyan dauka da saukewa"
"Ameen ya rahman".
Bayan sun idar da magariba suka sake fita da suraj din a mota ya rakashi wani waje,a hanya ya tsaya qofan wani suya spot yana kashe motar
"Kadan rakani ciki na yima hajiya siyayya mana"
"Ba damuwa muje mana",tare suka jera xuwa cikin,suna tafe suna hira har suka isa,suka wuce kai tsaye inda zasu bada order din abinda sukazo siya din.
Sun samu 'yammata biyu tsaye gaban kantar,wanna yasa abbas din ya bada taqi a tsakaninsu,ya tsaya daga baya baya suna ci gaba da magana da suraj din,irin hirar da ta shafesu.
Tunda suka tsaya din gaba daya hankalinta ya karkata a kansa,ba qaramun daukan hankalinta abbas din yayi ba,shigar qananun kayan dake jikinsa sun taimaka wajen fidda surarshi ta qaqqarfan namiji,har suka gama biyan abinda zasu siya din,saita bude da duba wayarta tadan matsa gefe kadan tana cewa qawarta
"Ina zuwa".
Hankalinsa nakan suraj yana saurarensa yana saka order din abinda yakeso,har yaso yayi mistake ma saida waiter din yayi masa magana,aka hada masa komai ya irga kudin cikin wallet dinsa ya aje musu,saidai garin daukan ledan bai ankara ba ya dauki tata ledar,tana sane ta barshi har sai da isa gaban motarsa sannan yaji ana fadi cikin siririyar muryarta dake nuna zallar yauqi da gwalli
"Hi.....hi,ranka ya dade" cak ya tsaya,don har ya bude murfin motar,ya waiwayo don ganin ko dashi ake.
Da murmushi ta dinga jifansa har ta iso,cikin tausasa muryarta tace
"Yallabai ledata ka dauke" ledar hannun nasa ya daga ya kalla,sai sannan ya lura,ya sauketa gami da miqa mata yana cewa
"Sorry"
"Ba laifi ai,hakan yayimun,kaga ko babu komai leda zata qulla mana zumunci" bai amsa mata ba illa amsar tasa ledar da yayi
"Sunana rafi'ah" tayi saurin fada ganin yana shirin shigewa motarsa
"Good,thank you ko" matsowa ta sakeyi don fa fuskanci rufewa zaiyi
"Ko zan samu digits naka?"
"Am sorry to say no" ya fada yana maida murfin motar a hankali ya rufe,sannan ya tashi motar yayi reverse suka fice daga wajen.
"Har yanxu