Header Ads
Showing 291001 words to 294000 words out of 296907 words

Chapter 98 - A RUBUCE TAKE BOOK COMPLETE DOCUMENT

Ads the beginning of article before Image
Ads at the middle of Article

mata inda zata ba yau ba ita ba kwana lafiya cikin gidan,tana jinta tana cewa

"Ma'a,kazo gata ta dawo.....oho muku,can ta matse muku" sai taja mugun tsaki ta kashe wayar tana mita.

Tunda uwar hafsat ta haifeta bata taba ganin bala'e'iyar mace irin sahura ba,bata gajiya da fada da bala'i,mita kuwa saita kwana tana zarya a tsakar gida tana yinta,dare baya mata kaifi haka rana bata damunta, bala'i idan ta kwan biyu bata yishi ba jinta take kamar mara lafiya,jikin hafsat ya dauki rawa,ta fada dakinta tana laluben kayan da zata sakawa jikinta da suka dan fi wannan kauri,tunda taji tana kiransa a waya lallai yau babu makawa jibga zatasha,babu kuma me qwatarta sai sarki Allaha.

Ai hijabi kawai ta gama sawa taji anyi ball da kwanonta dake falon sannan ya fara magana da qarfi

"Kina ina munafuka,fito nan nace miki" yayi maganar yana nade danqon dake hannunsa,jikinta na mazari ta fito ta qaraso gabansa ta durqusa,baiyi wata wata ba ya fara lafta mata

"Ka tsaya don Allah nayi maka bayani,wallahi ba wani guri naje ba"

"Qarya take munafuka,dama ta saba bin maza,kana fita take sanya qafafunta ta fice,saita dai daici kana dab da dawowa sannan takes shigowa gidan nan" .

Baiko tsaya jin bayanin bakinta ba ya dinga laftarta,garin qoqarin zillewa kudaden da take maqale dasu suka zubo,sahura ta saki salati,ita da mu'awiya duka suka duqa lokaci daya suna qoqarin dauke kudin,sahura da ta fishi son abun duniya ta rigashi dauka,tahau lissafawa.

Dubu tara da dari takwas cif,don tayi kudin mota a ciki

"Ka gani ko,tabbacin bin maza ta koma,kaima Allah ya qara maka,ta yaya zaka dauko matar me kudi kace zaka iya riqeta,aiga irinta nan"

"Miqon kudaden nan" ya fada yana miqawa sahura hannu,wani kallon banza ta jefeshi dashi

"Uban kuturu ma yayi kadan bare na makaho,ka manta kudina daka dinga karba sanda zaka aurota?,ai da haka zan gama fanshe asarata,don ni wallahi mun raba hanya da asara,bana daukarta" daga haka ta soke kudin a brassiere ta fice abinta.

Bulalar yayar cikin baqincikin rashin samun nasarar daukar kudin,ya zauna saman kujera yana huci

"Tashi ki zazzage jikinki ko akwai sauran wasu kudin" haka ta miqe ta zazzage masa kanta,saidai ko sisi bai fado ba,yaja mugun tsaki

"Ki rufewa mutane baki ki daina musu kukan banzan nan"

"Wallahi bana bin maza,Allah maawiya sharri takemin"

"Dalla rufemin baki,bazan taba yarda ni dake ba...."

"Na'am" ya katse maganar yana amsa kiran sahura da taketa qwala masa kan ya fito yaja mata ruwa a rijiya,sai ya fice da sauri kamar wanda zai amsa kiran uwarsa.

A wajen ta zube tana kukan baqinciki,dama haka qazafin zina yake da ciwo ?,haka widad taji lokacin data qulla mata sharri?,sau daya tayi mata ita,amma sai gashi ita kuma Allah ya hadata da kishiyar da kullum ta Allah daga fitowar rana zuwa faduwarta saita jefeta da wannan qazafin,saita rushe da kuka tana tuba zuwa ga Allah,tana tuna irin tashin hankalin data saka widad a ciki,bama ita kadai ba,hatta da abbas din,banda kiyayewar ubangiji da zuwa yanzu yana dauke ciwon zuciya ko kuma mummunan hawan jini,tati amfani da irin son da taga yana mata,ta saka an dasa zargi me qarfi a kanta cikin zuciyarsa,sannan ta jefeta da qazafin,ashe duk jifan da kayi wataran kanka zai dawo,bayan saki data rabauta dashi a wancan karon,yanzun kuma gashi tarihi ya maimaita kansa.

Duk inda takai ga kaidi da jaraba da bin malamai sahura ta dameta ta shanye,a yanzunma ina taga kudin da zatabi malaman?,abinci ma wataran cikin gidan gagararta yakeyi sai tayi biyayya sannan sahuran zata san mata,tunda kusan fiye da rabin qarfin kula da gidan itace.


*H U G U M A*
*Arewabooks:Huguma*

*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
Part 02

Page 45

Sister's duk wacce batayi anfani da sabulun mg's ba ko kit dinsu inamai shaidamuku anbarku acan baya domin duk wnd yajaraba mg's sai sanbarka duk wani Mai tantama Akan kayan gyaranjiki toh tabbas yacire sabulun mg's domin yahadu bakarya zegyarajiki yafidda dattin fata Dama duk wani matsalan fata duk Wanda kefama da matsalan fata walau pimples ko spot, sunburn acne,stretch mark dama dukkan wani prblm yajaraba mg's bi'iznillah komai zaizama labari bayan jikinku yy fresh zaisa jikinku yy smooth yadinga glowing,gawanda basa San anfani da Mai zaku iya using mg's batare da kunbukaci wani Mai b🤗nd wnn new soap din💣ne,😯 bama cika Baki kujaraba kugane ma idanku domin ance gani yakoriji Kuma siyan nagari maida kudi gida
You can check pic👇for the soap reviews🥰
Soap price:4k
maiso yy mgn Whatsapp
08062991549
07046881166
07067210195
Call 08064532391
Instagram:glow_with_mgs
Facebook: mg's skincare

Masu bukatar cream Shima munadashi harda ma complete set nagyaranjiki sannan akwai na amare special Wanda inkinyi using baki Kuma bukatar kiyi Wani gyaranjiki domin keda kanki zaki shaida cewa fatar taki ta wanku tarwai😍08062991549

Munatura Kaya kowani gari dayardar Allah Amma delivery is not free

Be part of the glow team😍karkubari abaku lbr👏
_______________________________


Wanne irin hakki ne haka yake binta?,ta shiga uku,mu'awiya mutumin da yazo mata a matsayin air vice marshall,ashe kurtu ne,kurtun sojoji wanda akewa alfarmar daukarsu a aiki,suke dan aike aike wa manyansu,amma tsabar hakki da kuma ranar girbar abinda aka shuka da take dab da fadawa ta kasa ganewa,tun daga yadda yazo mata,ba wasu cikakkun suturu na alfarma da zasu gaya mata wayeshi,babu wasu securities da akasan dukka masu matsayi irin masa na yawo dasu ko da yaushe ko kuma motoci yaci ta gane amma idonta ya rufe, kwanyarta ta toshe, duka batayi wannan tunanin ba,matsayinsa ke mata kuwwa cikin kunne,ta tuna ranar da ya raina mata hankali yasa ta koma eatery karbar canjinsa,data koma masa da batun sunce ba'a binsu kudi sai yace

"Ayyah,inatason tsaidaki,ai kina shiga ina ganin alert,sunmin transfer yanzu yanzu" da haka ya shashantar da maganar,ashe duka ya shirya aurarta ne ya cinye duk abinda ta tara da abinda ta mallaka,don yanzun haka bata da komai,ko wayar hannu tafi qarfinta,sai azabar da take qunsa daga hannunsa da kuma wajen kishiya.

Watanni shida baya ummarta ta rasu,aka rabon gadon da mahaifinsu ya bari wanda a baya ba'a raba ba saboda ummar ta hana a taba,kowa kuma yana tsoro haka yayi Shuru,nata kason bata sani ba mu'awiya yayi ruwa yayi tsaki ya saida mata,yan uwanta kuma sukace babu ruwansu,sun dauka da hadin bakinta ne,hatta anty ummee yanxu tana gida tana zaman zawarci da nakasar ido daya da mijin ya tsiyayar mata,bayan ya gane dogon lokacin data dauka tana ha'intarsa tare da sanyashi yana cin zarafin uwar gidansa ta hanyar amfani da kissa,ita kanta yanzu ta zama abun tausayi,tayi nadama tayi nadama har babu iyaka,kissa bata amfaneta da komai ba sai dana sani da wahala a rayuwarta,ya karbe dukka yaransa dake wajenta ya danqawa uwar gidansa,ita kuma tana kulawa dasu cikin amana da kulawa
(Babu inda ba na gari,babu kuma side din da babu baragurbi,daga iyayen gidan har amaren,saidai mata muji tsoron Allah,mu yiwa Allah mu yiwa muhammadur rasulillahi S A W mu daina wahalar da junanmu,ke idan zaki shiga gidan me mata kiji tsoron Allah,ki tsarkake niyyarki,ki shiga da niyya me kyau,wallahi wallahi idan kikayi haka bata isa taga bayanki kota tozartaki ko ta samu nasara a kanki ba,indai kinyi da zatin Allah,kiyi haquri da wasu abubuwan ki dauke kai a wasu,amma kada ki yarda da cin xarafi,kema uwargida ki sanyawa zuciyarki haquri,ansani kishi yana da ciwo,amma ki dauka haka taki qaddarar tazo,ki sanya Allah a gabanki,ki toshe kunneki daga 'yan gulma da yan bani na iya masu kawo miki labaran da zasu daga hankalinki,karki yarda ki cutar da ita bayan ta shigo koki qoqarin fiddata daga gidan,kada ki manta ko meye kikayi wallahi ba'a cin bashin Allah,duk wanda yaci sai ya biya ko 'ya'yansa sai sun baya,ko bakya raye kinga kin bar musu musiba,ki kama girmanki karki bada qofar da za'a rainaki,ki yawaita addu'a sai kiga Allah ya kwarjantaki an girmamaki ko ba'a so daga ita har mijin,ki dauki girman da Allah ya baki,Allah ya bamu haquri da juriya gaba daya).

Tana tsaka da wannan tunanin cikin tsananin qunci da tashin hankalin yadda rayuwa ke gare gare da ita aka bankado labulen dakin,ta firgita ta miqe ta zauna suna kallon kallo da sahura

"Badai kin aurar min miji ba?,wallahi babu ke ba sauran zaman lafiya,ki tashi kije ki wanke masa bangon bandaki,yace bai fita ba,bazai dauki wannan qazantar taki ba" daga wannan ta juya ta fita tana karkada mata mazaunai.

Ko second biyar bata qara ba haka ta miqe ta fito tun kafin ya dawo yaci zarafinta,jikinta nata ciwo tako ina saboda dukan da tasha,ta qarewa bandakin kallo,babu qazanta ko dis,kawai tiles din jikin bangonne da bata wanke ba,tunda ta fara zaman aure bata taba yiwa bandaki bautar da takewa bandakin gidan mu'awiya ba,bama bandaki ba,gidan gaba daya,wata muguwar tsafta ce dasu daga shi har sahura,kamar masu aljanun tsafta,sanda tazo da qazantarta taci wahala,kyara tsangwama daga baya harda duka kamar diyarsu,sai ayi shara kusan goma a gidan,bandaki kuwa duk bayan awanni haka zata tashi ta wankeshi tasss,tasha wahala sosai,don bata saba ba,zuwa yanzu kuwa ya zame mata jiki,saidai hausawa sukace ba'a sabo da wahala.

Tana farawa sahura ta dawo bayanta ta tsaya tana mata gyara cikin masifa,daga qarshe ta dauko kofin bandakin ta dinga sheqawa hafsat ruwan tana dirzawa,tana sane da gayya take hakan,don kusan rabin jikin hafsat din sai data jiqa mata shi,bacin rai yazo mata iya wuya,amma bata isa tayi magana ba yanzu suyi kamar zasu cinyeta danya ita dame gidan,yanzun zata hau mata gorin gidanta ne tunda filin da ginin gidan duka ita ta gina,shi kuma zai hau fadin eh dole ta bita,saboda gidanta ne kuma a gidan ta sameta,don mu'awiyan kamar qarqashin umarnin sahura yake rayuwa.

Tunda hafsat ta fita tabar gidan ta barta cikin mutuwar jiki mamaki da kuma juyayi,lallai duniya rawar 'yammata ce,na gaba ya koma baya,muddin bakaji tsoron Allah ba ka shiga uku duniyarka da lahirarka.

Sai zuwa yammaci ta samu ta qwarara jikinta ta shiga kitchen,don bata taba saukewa kanta kula da cikin abbas din duk rintsi indai suna a tare.

Ita da aminatu ne,don haka cikin sauri ta kammala komai,tabar musu gyaran kitchen din ita da mimi dake da himmar aiki,sannan ta dawo parlor din gidan zuwa bedroom ta tabbatar komai yana kan order,ta kuma cikashi da qamshi ta yadda zai dace da yammacin sannan ta wuce bedroom dinta ta fidda kayan jikinta ta fada wanka.

Ta jima a bayi sannan ta fito daure da towel,kome takeyi cikin mutuwar jiki take yinsa,baya ga lamarin hafsat akwai kasala sosai a jikinta,taja kujera ta zauna gaban mirror tana kallon lallausar farar fatarta daketa sheqi.

A nutse aka turo qofar bedroom din,ta cikin mudubi suka hada idanu dashi,kamar an manne idanun nasu guri daya,sai kuma kowa ya janye idonsa daga na dan uwansa yana basarwa.

Saman sofa bed ya zube kayan hannunsa,ta jawo mai ta fara shafawa

"Sannu da zuwa" ta fada ciki ciki ba tare data kalleshi ba.

Dubanta yayi kadan hannuwansa cikin aljihun wandonsa,kamar zai magana sai ya fasa ya amsa mata da yawwa,ya juya kadan ya fara cire kayan jikinshi.

Mamaki ya kamata ganin yadda yau ya yada zango a dakinta,neman rigima ne ko kuwa?,daya gama din yaja towel ya daura saman gajeran wandon jikinsa daya tsaya masa iya cinya.

A bayanta ya tsaya,ya saka hannunsa ta gefen fuskarta ya shafi wuyanta zuwa fuskarta da zummar jin ko da zazzabin a jikinta?

"Alhamdulillah" ya furta qasa qasa harda sakin ajiyar zuciya,sai ya taka ya wuce bandakin,ta bishi da satar kallo,har sai da ya shige sannan ta dauke idanunta,ta saki ajiyar zuciya saita maida man shafawan nata saman madubin kawai ta sanya hannuwanta dukka biyun tayi tagumi.

Komai ya tsaye nata a rai,da alama wannan karon abbas din ya fita fushi,hankalinta sam ba'a kwance yake ba,sai yanzu ta sake ganowa azabtar da miji ko sanyashi cikin baqinciki ko yaushe na iya jefa mace cikin jarrabawa,sai taji qwalla ta cika mata idanu,taji kuma ta damu sosai da fadan nasu,wanda bata taba damuwa kamar yanzu ba,don a baya tana ganin kawai wahala zata sha cikin dake jikinta.

Sanda ya fito a haka ya sameta,sai ya dauke kansa kamar bai gani ba,duk da qasan Zuciyarsa shima cike take da damuwar fadansu,to amma kuma ya koyi darasi daga zamansa da hafsat,ba ko yaushe kake barin mace da zabin kanta ba,hakanan bako yaushe kake barin mace tayi abinda takeso ko kuma abinda yayi mata suger ba.

Yadda ya kauda kai kamar bai kula da taguminta da qwallar dake cikin qwayar idanunta ba sai ya sake sanyaya mata jiki,ta gaza daurewa,sai kawai ta miqe tsaye da sassarfa ta nufeshi,ta fada jikinsa sanda yake ware towel din jikinsa ta ruqunqumeshi.

Cak wutarsa ta dauke,saboda tayi masa ba zata,uwa uba kuma yadda fatarta me santsi da laushi ta manne a jikinsa,sai ya gaza ci gaba da riqon towel din ya sakeshi ya fadi a qasa, yasa hannu ya tarbeta cikin jikinsa da kyau amma kuma cikin dakakkiyar murya da kuma basarwa yace

"Meye hakan?" Muryarsa na danson yin rawa yana qoqarin daidaitata

"Kayi haquri don Allah uncle,wallahi bazan sake ba"

"Laifin me kikayi?,ba haka kikeso ba?,so nake dama na gama shiryawa yanzu ina yin sallar isha'i muje a zubar din,kinga nan da next year na auro wata meson haihuwar harta haifamin babies" ji tayi maganar tasa ta soketa sosai,sai kawai ta kasa riqe kanta ta sakar masa kuka sosai tana kwantar da saman qirjinsa hadi da rungumeshi da kyau cikin jikinta tana cewa

"Na tuba Allah bazan qara ba" sautin muryarta kawai yana sanya masa nutsuwa,wani bangaren kuma yana sakashi yaji ya buqatu da yawa da ita,sai ya dinga lumshe idanunsa yana jin yadda yanayinsa ke canzawa,saboda sautin kukantan sai ya zame masa kamar fami cikin kunnuwansa da kanta dake kwance a allon kafadarsa.

"Ka yafemin don Allah" ta fadi tana qoqarin zamewa ta duqa,yayi hanzarin tattarota zuwa jikinsa,don ko daya bayason ta matsa daga jikin nasa,dumin jikinta ya masifar yiwa jikinsa dadi

"Na yafe miki,na yafe miki har abada,but don Allah.....karki sake zancen zakiyi abortion,kalma ce me muni,don zaman aure mukeyi ba dadiro ba,inason kowanne qwayar halitta data fita daga jikina ta bayar da d'a,ko ana ciki sau goma nine ubansa,kuma inaso" ya fadi yana kallon tsakiyar qwayar idanunta ciken mayen so da qauna.


*H U G U M A*
*Arewabooks:Huguma*

*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
Part 02

Page 46


*_TURK'ASHI!,BABBAN GORO SAI MAGOGIN K'ARFE,KU MARMATSO KUJI,GIDAN KOMAI DA RUWANKA_*

*LIFE STYLE NIGERIA for everything that makes your life style complete*

*GIDAN KOMAI DA KOMAI RUWANKA*

_kama daga kan_


Furnitures
Decoration
Kitchen items &
Boutiques

_our tittle_

Quality is our watch word at lifestyle

shop kano/kaduna

Shop no 58 kabuga housing estate janblo kano on the road in between first gate and second gate near kashe magana suya spot


Instagram@ Lifestyle_Nig
Facebook@ Lifestyleng
Tik tok@ Lifestyle_Nig
Delivery nation wide

_ku tuntubemu ta wannan number_

08036414048

*Muna tura kaya ko ina cikin aminci da yardar Allah*
_______________________________

"Na daina uncle" ta fada tana cusa kanta tsakanin qirjinsa tana shaqo qamshinsa mai kwantar mata da hankali,wani ciki ta samu a wannan karon meson qamshin jikinsa,sai ya saki murmushi yana shafa sumarta

"Nima kiyi haquri,nasan kinyi missing jikina ko?" Ba kunya ta gyada kai tana sake cusa fuskarta cikin gargasar dake qirjinsa,tsigar jikinsa ta dinga zubawa,shima haqurinsa yakai qarshe,dama shima din kawai basarwa yakeyi tsahon lokacin,sai ya zura hannunsa ta baya ya kwance towel din jikinta ya sulale ya fadi qasa ta koma kamar yadda yake,ya maidata jikinsa sosai suka zama abu daya,kowannensu ya dauke numfashi na wucin gadi sannan suka zuqoshi da qyar,cikin rawar jiki ya dauketa cak ya wuce da ita saman tsaftataccen gadonta da baya gajiya da kwanciya a kai.

Ranar dai sai a dakin sukayi sallar isha'i shi da ita,sunyi kewar juna ba kadan ba shi da ita,sun kuma gane yadda suka azabtar da junansu.

Suna gaban madubi yana sharce mata gyara mata gashin kanta kafin ta saka kaya ta kalleshi ta cikin mudubin

"Uncle"

"Babyn uncle" ya amsa mata softly

"Don Allah zaka iya yimin wata alfarma guda daya zuwa biyu?"

"Kinki qarfin komai a wajena" ta dauki hair mist dinta ta miqa masa ya soma fesa mata sanann tace

"Ka yafewa mummyn mimi don Allah,ta roqeni na roqar mata wannan alfarmar"

"Na yafe mata,Allah ya yafemu gaba daya" ya fada kansa tsaye,donshi wani lokacin ma mantawa yakeyi ya taba aurenta,sai idan dalili ya ratso.

"Na fadi ta biyun?"

"Eheen,ina jinki" ya fadi yana buda mata doguwar rigar da zata sanya

"Kasan tsakanin uwa da d'a sai Allah,ta roqeni na gaya maka don Allah ka dinga barinta tana ganin yaran nan....." Kallonta yayi da sauri

Ads At the End of Article
Sidebar Ads

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login
Footer Ads